Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 7
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels *πŸ’”πŸ’”IN SO CUTANE πŸ’”πŸ’”* Copied by serdiq☠(YNG-talent)07033438934 *Fasaha Online Writers.* *By Anty Rukie (Mmn Abduljalal.)* 1. πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’” *Godiya ga Allahu (S.W.T) mai kowa mai komai da ya bani ikon fara wnn novel cikin koshin lafiya.* *Alhamdulillah Hamdan katheeran d'ayyiban mubarakan fiih.* *Fatan alkhairi gareku masoya aduk inda kuke ,ku ke bani kwarin gwiwa ako wani lokaci nagode kwarai da gaske Allah ya bar k'auna.* ****** ***** ***** Da d'add'aya suke fitowa, dan zuwa ganin Wannan mai sa'a da ya sace zuciyar yayarsu har ta fita ta saurareshi. Ba ma fitar ne yafi basu mamaki ba, sai jimawar da tayi wajen zance daga cewa bari Inga waye ne in dawo. Kanwarta mai bi mata Nusaiba,wacce kusan kansu d'aya ita ta fara zuwa ta gaisheshi, sai Fati, itama taje da sunan taje gaisheshi, daga nan sai kannenta maza Nafi 'u da Hamza . D'an autansu khalil ne kawai baije ba .dan shi d'an ba ruwana ne. Gulma ajali. Hhhh gulma harda maza. Abinne kam da mamaki dan ko Mamansu da suke kira da Ummi ma cikin mamaki take fitar 'yar tata da rashin Dawowarta da wuri. Ummussalma kenan 'ya ga Mal. Abdullahi. Mahaifin Ummussalma Babban malami ne wanda yake karantar da manyan mutane da matasa. Har islamiyya na musamman ya bud'e kusa da gidanshi dan koyar da yaranshi da na makwabta. Cikin ikon Allah islamiyyar ta hab'aka har daga wasu anguwanni zuwa karatu akeyi . Ummussalma wacce aka fi kira da Salma, kunnenta kuma suke ce mata Aunty Salma, itace 'ya ta uku a wajen iyayenta amma itace mace babba a gidan. Yayyunta biyu maza ne Allah yayi wa d'ayan rasuwa Saura d'aya wadda suke kira da Ya Al-amin. Wani lokaci su ce mishi yayanmu. Tun tasowar ta tashi da burin ta zamo likita, ita kuwa a rayuwarta babu abinda yake burgeta irin taga nurses sanye da fararen kayannan Suna bawa mara lafiya taimako. Sosae take son karatu dan ita a rayuwarta babu abinda ya fiye mata karatunta muhimmanci. Tun gamawanta secondary school mahaifinta yaso ya aurar da ita amma ganin yadda ta nace kan karatu kuma bata da wani tsayayye dan ita Sam bata sauraron samari dan a ganinta b'ata lokaci ne, kuma hakan zai iya hanata karatunta yadda takeso. Babban abinda take gudu shine, kada babanta yasan tana da wani yace zai mata aure. Shi yasa Shima babannata ya hakura da batun aurar da ita kuma ya nema mata karatu a school of nursing. Karatu take ba wasa dan samin cikar burin ta, kuma cikin ikon Allah tana samun nasara dan tunda ta fara bata tab'a samun matsala da karatun ba. Duk yadda wasu suke nuna mata Suna son ta, wasu ta hanyar kannenta suke bi,wasu kuma ta wajen yayanta wasu kam direct wajen Mal. Suke zuwa da bukatarsu ta aurenta, saidai yace musu sameta Su daidaita kansu dan shikam alk'awari ya daukarwa kanshi bazaiyiwa 'yarshi auren dole ba, ko wacce zai bata dama ta zab'i wanda takeso, nashi dai yayi bincike ne idan an dace da nagari Falillahil hamdu. Idan kuma akasin haka ne sai ya bata shawarar da zai amfaneta sai kuma ya bisu da addu'a. Samun ta a daidaitan shine matsalar dan ko kad'an bata bada fiskar da za'a kawo mata irin wnn maganar ta soyayya. Ko yaya mutum yaso tunkarar ta sai abin ya gagara dan Allah ya bata baiwar k'warjini, ga uwa uba d'aure fiska da takeyi idan ta fita waje, ko da mutum yayi dauriya da k'arfin halin yi mata magana ma daga kallon da Zata maka zaka San babu nasara ,gata kullum cikin zumbuleliyar hijabi ,zaiyi wuya Kaga dariyarta shi yasa Yawancin mutane suke ganin zata yi wayar shaani. itakam haka yafi mata Dan babu wanda zai kawo mata cikas a Karatunta. Kannenta ,Nusaiba da Fatima duk suna da masu zuwa wajensu, fatimar nema Salma take hanata fita a cewarta idan auren takeso ma ta bari sai ta K'are secondary school. Itama Nusaiba dan ta K'are ne. Wani lokaci haushi suke bata idan taji Suna maganar soyayya, ko kuma idan aka ce wani yazo wajensu taga suna rawan Kai. Yawancin mutane Suna gani girman kai ke damunta ko kuma dan taga tana da kyau yasa takeyin hakan wasu kuma cewa suke mai kud'i take son ta aura. Saidai abin mamakin masu kud'in ma ba sauraransu takeyi ba. Abinda basu sani bama shine ita Sam a tsarinta bata son auren mai kud'i dan gani take auren mai kud'i sawa Kai damuwa ne. Na farko gani take kamar baza ta samu attention d'inshi yadda ya kamata ba. Ta iya yiyuwa ta zamo kamar abokiyar gabar danginshi dan zasu sa mata ido sosae ganin d'an uwansu na da kud'i. Gani take shi dinma zai ga kamar dan kudinshi takesonshi ba dan Allah ba. Shi yasa take da burin idan Zata yi aure ta auri talaka d'an uwanta mai rufin asiri wanda kuma zai barta tayi aikin asibiti su zauna lafiya su rufawa juna asiri. *Mmn Abdul and Noorain.* [10/17, 2:32 PM] MMN ABDULJLL: *πŸ’”πŸ’”IN SO CUTANEπŸ’”πŸ’”* *Fasaha Online Writers.* *By Anty Rukie.(Mmn Abduljalal.)* 2. πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’” *Wannan shafi nakine Ummu D'alhat Allah ya ja kwana ya albarkaci zuri'arki baki d'aya.* ****** ******** **** Yanzu Saura shekara guda ta gama karatunta. Kwatsam sai Allah ya had'a ta da wanda ya shiga zuciyarta lokaci guda ba tare da ta shiryawa hakan ba. *Love at first sight.* Wajen bikin kawarta suka had'u dashi,wajen dinner bikin, Allah yayi zasu had'u dan ita ba mai zuwa ire iren guraren bane. Kallo farko suka yiwa juna saida zuciyarsu ta amsa lokaci guda, tun da take a rayuwarta bata tab'a jin abinda taji game da shi, bata tab'a ganin mutumin da ya burgeta lokaci guda kamar shi ba. AHMAD kenan, yaro d'an kwalisa. Maraya ne mahaifinshi duka biyu sun rasu a gidan yayanshi babba yake da zama. D'an kasuwa ne , ya fara saida 'yan kunne daga kad'an kad'an Allah yasawa abin albarka har ya bud'e babban shago a kasuwar jalingo. A hankali yanzu har Allah ya albarkaci sana'ar shaguna uku yake dasu. Asalinsu yan Gassol local govt ne, Rasuwan iyayenshi yasashi Dawowa jalingo da zama gun d'an uwanshi. Iya secondary school ya tsaya a matakin karatu, dan gidansu basu bawa karatu muhimmanci ba Sam, sun karkata ga noma, da sana'a. Idan ka ganshi Sam baza Kayi tsammanin baiyi zurfi a karatu ba dan kud'i da wayewa Sun sashi ya goge. Kyakkyawan saurayin dogo fari, mai d'an fad'i. Yana da bille a fiskarshi na gado, duk yaran gidansu Suna da irin wnn billen, sosae bille ya masa kyau kamar dama dashi aka halicce shi. Tun daga lokacin da suka had'u yake zuciyarshi na harbawa, so yake ya mata magana amma kwarjininta ya hana shi har aka gama biki aka watse. Lokacin da zasu watse yabi bayanta dan ya samu magana da ita unfortunately sai ya ganta tare da wani Sun kama hanyar tafiya. Hankalinshi ba k'aramin tashi yayi dan duk a zatonshi saurayinta, sai bayan ta tafi yake tambaya aka ce mishi yayanta ne, tare suka zo, da ya Al -amin da yake ba jimawa sosae za'a yi ba ya jirata suka koma tare . Bai bar wajenba sai da ya samu cikakken adress d'inta da sunanta, har da fatan Allah ya bada saa ango ya mishi dan yasan halinta Sarai ba lallai bane ya samu karb'uwa. Suka k'ara da ce mishi sai fa yayi da gaske dan bata sauraron kowa idan yayi hakuri da halin wulakancinta watakil yayi nasara. Cikin d'oki yake cewa in Allah ya yarda ma zaiyi nasara, dan yana gani itace first and last love d'inshi. Har cewa yayi bari yabi bayansu yanzu yaga gidansu. Cikin dariya angon yace, "Me ma sunanka? " Kamar jira yake yace ,"Salman. " Dariya aka ta mishi a wajen wato har ya tashi daga Ahmad ya koma SALMAN. "To Salman, abi a hankali kada zarbabin yayi yawa kaje kuma ka rasa abunda zaka ce mata. " Cewar wani daga cikin abokansu. Dariya sukayi dukansu cikin sauri ya juya yana cewa "Allah ya bada zaman lafiya ango nima na tafi neman aure. A hankali yake binsu da mota har kofar gidansu, sai da yaga Shigansu snn ya koma. Koda ya komama babu abinda yake gani sai fiskarta duk da baiga fara'a ba kokadan a tare da ita amma shi dai ta mishi a hakan. A b'angarenta kuma tunda suka bar wajen tunanin wnn saurayin da taji an kira shi da Ahmad yake manne cikin zuciyarta, duk wani motsi nata fiskarshi take gani, tad'inma da sukeyi da yayanta yawanci shi yakeyi dan hankalinta na kan AHMAD. Bai kawo komai ba yayi tunanin gajiyar biki ne ya maida ita shiru shiru. A wajen bacci ta dad'e tana tunanin shi da duk wani action d'inshi da yayi a gun haka yake mata yawo a ido kamar film take Kallo. Kwana tayi tana mafarkinshi kamar yadda Shima hakan ta kasance gareshi. Hakan yasa Washegari da sassafe ya je kofar gidansu yayi parking a d'an nesa da gidan kad'an yana kallon k'ofar kamar yana jiran fitowarta. Ya dad'e a zaune a gun yana tunanin ya aika a kira mishi itane ko ya bari sai zuwa anjima. Fitowa tayi sanye da uniform d'inta na school of nursing farare tass wando da riga, sai babban hijabin da ta d'aura kan uniform d'in, kafarta sanye da bak'in takalmi sau ciki. Binta yayi da Kallo ,duk da ba kwalliya a fiskarta ta mishi kyau dan kyawunta naturally ne. Chocolate colour ce, ba za'a sata sahun farare tass ba bata kuma cikin bakake, ba za'a sata a sahun farko na kyawawa ba amma Sassanyar kyau gareta. Baza a iya gane dirin da Allah ya mata ba dan kullum cikin lullub'e jikinta takeyi da hijabi. Nitsuwarta yake k'ara fizgar hankalin duk wani mutumin kirki zuwa gareta. Ji yake kamar ya fito ya mata magana amma kwarjininta ya hana shi. A nitse take tafiya har sai da yaga ta d'an yi nisa snn Shima ya tada motarshi ya bita a hankali. Har ya isa kusa da ita da zummar yi mata magana amma ganin yanayin fiskarta ya dakatar dashi. A daidaita ta tara ta shiga snn ta sanar da shi inda zataje. Har suka isa bai daina binsu ba. Tana fitowa tasa hannunta cikin hand bag d'inta Zata biya kud'i, sai ganin mutum tayi..... *Mmn Abdul and Noorain .* [17/12 06:24] Hajara: *πŸ’”πŸ’”IN SO CUTANEπŸ’”πŸ’”* *Fasaha Online Writers.* *By Anty Rukie.(Mmn Abduljalal.)* 2. πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’” *Wannan shafi nakine Ummu D'alhat Allah ya ja kwana ya albarkaci zuri'arki baki d'aya.* ****** ******** **** Yanzu Saura shekara guda ta gama karatunta. Kwatsam sai Allah ya had'a ta da wanda ya shiga zuciyarta lokaci guda ba tare da ta shiryawa hakan ba. *Love at first sight.* Wajen bikin kawarta suka had'u dashi,wajen dinner bikin, Allah yayi zasu had'u dan ita ba mai zuwa ire iren guraren bane. Kallo farko suka yiwa juna saida zuciyarsu ta amsa lokaci guda, tun da take a rayuwarta bata tab'a jin abinda taji game da shi, bata tab'a ganin mutumin da ya burgeta lokaci guda kamar shi ba. AHMAD kenan, yaro d'an kwalisa. Maraya ne mahaifinshi duka biyu sun rasu a gidan yayanshi babba yake da zama. D'an kasuwa ne , ya fara saida 'yan kunne daga kad'an kad'an Allah yasawa abin albarka har ya bud'e babban shago a kasuwar jalingo. A hankali yanzu har Allah ya albarkaci sana'ar shaguna uku yake dasu. Asalinsu yan Gassol local govt ne, Rasuwan iyayenshi yasashi Dawowa jalingo da zama gun d'an uwanshi. Iya secondary school ya tsaya a matakin karatu, dan gidansu basu bawa karatu muhimmanci ba Sam, sun karkata ga noma, da sana'a. Idan ka ganshi Sam baza Kayi tsammanin baiyi zurfi a karatu ba dan kud'i da wayewa Sun sashi ya goge. Kyakkyawan saurayin dogo fari, mai d'an fad'i. Yana da bille a fiskarshi na gado, duk yaran gidansu Suna da irin wnn billen, sosae bille ya masa kyau kamar dama dashi aka halicce shi. Tun daga lokacin da suka had'u yake zuciyarshi na harbawa, so yake ya mata magana amma kwarjininta ya hana shi har aka gama biki aka watse. Lokacin da zasu watse yabi bayanta dan ya samu magana da ita unfortunately sai ya ganta tare da wani Sun kama hanyar tafiya. Hankalinshi ba k'aramin tashi yayi dan duk a zatonshi saurayinta, sai bayan ta tafi yake tambaya aka ce mishi yayanta ne, tare suka zo, da ya Al -amin da yake ba jimawa sosae za'a yi ba ya jirata suka koma tare . Bai bar wajenba sai da ya samu cikakken adress d'inta da sunanta, har da fatan Allah ya bada saa ango ya mishi dan yasan halinta Sarai ba lallai bane ya samu karb'uwa. Suka k'ara da ce mishi sai fa yayi da gaske dan bata sauraron kowa idan yayi hakuri da halin wulakancinta watakil yayi nasara. Cikin d'oki yake cewa in Allah ya yarda ma zaiyi nasara, dan yana gani itace first and last love d'inshi. Har cewa yayi bari yabi bayansu yanzu yaga gidansu. Cikin dariya angon yace, "Me ma sunanka? " Kamar jira yake yace ,"Salman. " Dariya aka ta mishi a wajen wato har ya tashi daga Ahmad ya koma SALMAN. "To Salman, abi a hankali kada zarbabin yayi yawa kaje kuma ka rasa abunda zaka ce mata. " Cewar wani daga cikin abokansu. Dariya sukayi dukansu cikin sauri ya juya yana cewa "Allah ya bada zaman lafiya ango nima na tafi neman aure. A hankali yake binsu da mota har kofar gidansu, sai da yaga Shigansu snn ya koma. Koda ya komama babu abinda yake gani sai fiskarta duk da baiga fara'a ba kokadan a tare da ita amma shi dai ta mishi a hakan. A b'angarenta kuma tunda suka bar wajen tunanin wnn saurayin da taji an kira shi da Ahmad yake manne cikin zuciyarta, duk wani motsi nata fiskarshi take gani, tad'inma da sukeyi da yayanta yawanci shi yakeyi dan hankalinta na kan AHMAD. Bai kawo komai ba yayi tunanin gajiyar biki ne ya maida ita shiru shiru. A wajen bacci ta dad'e tana tunanin shi da duk wani action d'inshi da yayi a gun haka yake mata yawo a ido kamar film take Kallo. Kwana tayi tana mafarkinshi kamar yadda Shima hakan ta kasance gareshi. Hakan yasa Washegari da sassafe ya je kofar gidansu yayi parking a d'an nesa da gidan kad'an yana kallon k'ofar kamar yana jiran fitowarta. Ya dad'e a zaune a gun yana tunanin ya aika a kira mishi itane ko ya bari sai zuwa anjima. Fitowa tayi sanye da uniform d'inta na school of nursing farare tass wando da riga, sai babban hijabin da ta d'aura kan uniform d'in, kafarta sanye da bak'in takalmi sau ciki. Binta yayi da Kallo ,duk da ba kwalliya a fiskarta ta mishi kyau dan kyawunta naturally ne. Chocolate colour ce, ba za'a sata sahun farare tass ba bata kuma cikin bakake, ba za'a sata a sahun farko na kyawawa ba amma Sassanyar kyau gareta. Baza a iya gane dirin da Allah ya mata ba dan kullum cikin lullub'e jikinta takeyi da hijabi. Nitsuwarta yake k'ara fizgar hankalin duk wani mutumin kirki zuwa gareta. Ji yake kamar ya fito ya mata magana amma kwarjininta ya hana shi. A nitse take tafiya har sai da yaga ta d'an yi nisa snn Shima ya tada motarshi ya bita a hankali. Har ya isa kusa da ita da zummar yi mata magana amma ganin yanayin fiskarta ya dakatar dashi. A daidaita ta tara ta shiga snn ta sanar da shi inda zataje. Har suka isa bai daina binsu ba. Tana fitowa tasa hannunta cikin hand bag d'inta Zata biya kud'i, sai ganin mutum tayi..... *Mmn Abdul and Noorain .* [17/12 06:24] Hajara: *πŸ’”πŸ’”IN SO CUTANEπŸ’”πŸ’”* *Fasaha Online Writers.* *F.O.W.* *By Anty Rukie (Mmn Abduljalal.)* 3. πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’” *Kun jini kwana biyu shiru ,wayar ce ta d'an samu matsala t goge min duk typing da nayi ,so bear with pls my lovely fans.* *** *** *** Ganin mutum tayi yana mikawa mai napep kud'i ,ga kamshin turarensa da ya bud'ad'e wajen. Yana kokarin bashi canji ya mishi alama da hanu ya barshi ya tafi . Hanun ta fara bi da kallo a hankali har ta sauke idanunta kan kyakkyawar fiskarsa. Rass taji kirjinta ya amsa. Shine. To me ya kawo shi nan ? Kallonshi ta tsaya yi ,sanya yake da shadda dark brown colour , d'inkin half jamfa ,kalar kayan ya dad'a haska fatarshi. Hannayenshi duka biyu ya zura cikin aljihu yana kallon wani wajen . A hankali ta juya ta kama tafiya tana jin wani irin yanayi a tattare da ita. Ajiyar zuciya ya sauke snn ya bita da kallo, a ranshi cewa yake ashe da gaske suke cewa saiya yi da gaske zai iya yi mata magana, dole ma ya cire fargabar da yake ji ya mata magana. Binta yai a baya har ta shiga cikin makarantar. Yana kallonta ta zare babban hijabin da ke jikinta, 'ya karamar farar hijabi ta bayyana ,tsawonta iya kirji. Wani irin takaici yaji ya rufe shi. Yanzu a haka zata tsaga cikin mutanen ajinsu ta shiga. Yanzu haka kullum take yi ,kuma tayi yawo cikin makarantar kowa yana gane masa ita. Take yaji wata matsananciyar kishinta lullub'eshi. Tsaki yaja lokacin da yaga ta shige cikin class. A bayyane yace "Meye amfanin irin haka." Ya kuma jan 'yar guntuwar tsaki. Ya jima tsaye gun yana ta sak'a da warwara daga k'arshe dai ya bar gurin ya tafi sabgoginshi. Haka ta wuni da tunaninshi da mamakin abinda ya yi d'azu. Duk abinda takeyi yana manne cikin zuciyarta ,hotonshi ke mata yawo cikin idon zuci. *** *** *** Napep ne ya sauketa kusa da masallacin kofar gidansu. Hanyarta ta shiga gida jikinta ya bata ana kallonta ,hakan ya sa ta d'an dubi gefenta. Karap suka had'a ido a tare kuma suka kawar da kansu. "Inna lillahi "tace tana dafe kirjinta dake bugawa da sauri. Sauri ta kara ta shige cikin gida tana maida numfashi. Mutuminnan fa yana so ya mata illa. Dan baisan yadda takeji idan ta ganshi bane da ko da wasa bazai rika zuwa kusa da inda take ba. Bata ankara ba taji an amshe jakar hanunta ,dubawan da zatayi taga Nusaiba ce tsaye a gabanta tana kallonta tamkar maison jin wani abu daga gareta. D'aure fiska tayi snn tace "Ya dai." "Ke zanma wnn tambayar aunty Salma, kin shigo kamar an jefo ki ,snn kuma kika tsaya kika kurawa waje d'aya ido, me ya faru." Nuna kanta tayi da yatsarta "Ni d'in?" "Muje ki huta da alama gajiya tayi miki yawa likita." Nusaiba tace ba tare da ta amsa mata waccar tambayar ba. Tare suka shiga d'akin ta tub'e uniform ta shiga wanka amma zuciyarta fal tunani. Bayan fitowarta Faty ta shigo mata da abincinta na rana ,duk da yamma tayi amma ta saba takan d'an tab'a kafin taci na dare. Amma yau ko sha'awar cin abincin batayi. Tsura mata ido Nusaiba tayi can tace "Aunty meke damunki sam ban gane miki ba." Basar da tambayar tayi tace "Ina Ummi Faty." "Tana d'akinta "tace gami da ficewa dan itakam ba mai yawar magana bace Nusaiba ce mai surutu ,ga san jin kwakwaf. Ganin da tayi baza ta samu bayanin da takeso gun auntynta ba yasa "Allah ya baki hakuri ." Ta tashi ta fita itama. Binta Salma tayi da kallo snn ta d'an murmusa ,a hankali ta ce,"Kusasu." Jingina tayi da jikin gado taci gaba da tunaninta. *** *** *** Tsaye yake yana mamakin kanshi da kanshi. Wannan wace irin yarinyace haka? Kwarjininta yayi yawa. Shawara ya rikayi da zuciyarshi. Shin ya aika ta fito ne ,ko ya hakura sai gobe. Dafe kanshi yayi yana magana shi kad'ai. "kada kuma na aika ta fito na gagara yi mata magana. Gaskiya da naji kunya yarinya karama." Shi kad'ai ya kuma cewa kanshi "Ka tabbata zata fito d'inne tukuna." Murmushi yayi ya kuma cewa tunda na ganki ma yayi ba sai na aika ba. Shiga motarshi yaja ya tafi zuciyarshi fal tunanin yadda zai b'ullowa al'amarin. *Mmn Abdul &Noorain.* [17/12 06:24] Hajara: *πŸ’”πŸ’”IN SO CUTANEπŸ’”πŸ’”* *Fasaha Online Writers.* *F.O.W.* *By Anty Rukie (Mmn Abduljalal.)* 4. πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’” Halima Auwal .(Mmn Aysha) Maryam A.I Gital. Teemerlurv. Khairat Up . Mamyn Najma. Fashuna. Hawwer (Autar Fasaha.) Aysha Ali Garkuwa. Raheenat. Aisha s.Bayero (Kalar Gayu.) Rahmat Nalele (Samareen Bana) Xaynab πŸ’€(Rouky Pinky.) Ummin Weedyan . Dss. *Fasaha grp nvl members muna alfahari daku ,Allah ya kara baseera fasaha da zakin hanu.* **** **** **** Har Ummi ta shigo d'akin ita a tunaninta ko Salma bata jin dad'ine dan tasan ko yaya in ta dawo sai ta nemeta sun gaisa. Amma yau shiru. "Ummulu yau kuma lafiya kika zauna cikin d'aki shiru." Kakaro murmushi tayi snn tace "Lafiya lau Ummi sannu da gida." "Yauwa sannu ,amma me ya ajiyeki cikin d'aki kikayi shiru haka." Ta tambaya tana naxarin 'yar tata. "Ba komai Ummi yau munyi wani practical ne mai wahala, na gaji da yawa ne." Hhhhhh Practical indeed Aunty Salma." "Sannu ,Allah ya albarkaci karatun ,yasa ya amfani al'umma." "Amin Ummina ." Tace tana murmishi dan sosae take jin dad'in addu'ar da Umminta ke mata ko wace rana. Kiran sallar Magrib da taji anayi ne ya tayar da ita daga inda take zaune. Abincin daren ma dan kada Ummi tayi tunanin wani abu yasa ta daurewa taci. Ga kuma 'yar sa ido Nusaiba. Haka yau ma ta kwana mafarkinshi . Har mamakin kanta take ji ,wai ita ce ta fad'a ,ta tsunduma cikin kogin son wani wanda bai furta mata kalmar so ba. Dauriya kawai takeyi kada a fahimci halin da take ciki har ta shirya ta fita dan tafiya makaranta. Ko da ta fita sai da ta tsaya ta tsurawa inda ta ganshi jiya ido kamar an ce mata zai b'ullo ta ganshi. Abinda bata sani ba shine yana daga nesa yana kare mata kallo. Ganin tsayuwar bazata k'areta da komai ba yasa ta kama hanyar tafiya inda zata samu abin hawa. Kokari takeyi ta yakice damuwar da ta take ciki. Shi yasa da ta dawo daga makaranta bata yadda ta zauna ita d'aya ba gudun kar tunani ya addabe ta. Sa hanu tayi aka karasa aiki da ita kamar yadda ta sabayi kullum. Washegari ma haka da ta fita take ta tsammanin ko zata ganshi amma shiru ,kwana biyu kenan take ta zuba ido bashi ba labarinshi. Hakan yasa ta dage lallai sai ta yakiceshi daga zuciyarta,dan wasa wasa tunaninshi yana so ya zame mata matsala. Kamar yadda ta saba yauma haka ta sauka dadai masallacin kofar gidansu . Kallon inda ya zame mata kamar jaraba tayi dan duk lokacin data fita sai ta kalli wnn wajen . Abin mamaki shi ta gani jingine da jikin motarshi ya zuba mata idanu. Sanye yake cikin shigar yadi mai laushi ,milk colour ,d'inkin tazarce ,kanshi ba hula sai kwantacciyar bakar sumar shi irin ta asalin fulani,wanda ya dad'a k'awata mishi fiskarshi. Wannan karo murmushi mai narkar da zuciya da gabb'an jiki ya sakar

Chapter 1 of 7