Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 6
abbana, still fuskarta dauke da murmushi tace tace dan Allah kayimani arziki. kadubi girman maraicina. daya yana zasushiga kabama *JAWAD AUREN FAREEDA* a duk ranar danacika ukku da komawa agun mahaliccina, tuni abba jikinsa yafara rawa damshi baicika yin karfin halin nanba irin na maza, yanada saurin karaya, "uncle justice" zufa duk takaryo masa ne yayi saurin taronta, yace ai ciwo bamutuwa bane zeeta kidainayin ire iren wadannan maganar, takoma kai hannun ta tana shafa fuskarsa, tace kayi hakuri jawad nayi imanin bazakuyi maraiciba fareeda rainonace tuntana yar kankanuwarta nakejinta araina, lumfashi tadan sauke sannan ahankali tajiyo inda nake dan naisa da gadon dama nitun sanda tafara Magana bazance namasan kallar tunanin da nakeba, amma nasan hankalina ne yatafi na wuchin gadi. *⚖️UNCLE JUSTICE⚖️* *STORY WRITINNG BY UMMU SHAREEF* *DEDICATED TO UMMU SAYYID* *WANAN LITTAFIN NAKUDINE* *KIBIYA HAJIYA KIKARANTAZAKIKARU DA ABUBUWA DA DAMA WAN NAN LABARIN* *LABARIN KAGAGGENE BA AYISHI AKAN WANI WATA KO WASUBA* *IDAN KINSIYA KINKARATA KIKABAMA KAWARKI YAR UWARKI, KO KIKA TURA A GROUP HAJIYA NAYAFEMIKI* *IDAN KINA DA HALI DAN ALLAH KIBIYANI TYPING AKKWAI WAHALA* *KIBIYA 300 TA WANNAN ACCOUNT NUMBER 3195366407 HAFSAT ABUBAKAR SADEEQ FIRST BANK* *KO KITURO KATIN WAYA NA 200 TA WANNAN LAYIN 08036833612.* *TAREDA TURO SHAIDAR BIYAN KO DATA TA 300 ZUWA GA WANNAN LAYIN 0803683312* *DUKKANMU MASU LAIFINE ALLAH YA YAFEMANA* *FREE PAGE* *xvii* Ummu salma ce tariko hannuna, takawo har gaban gadon tadora saman na Aunty Raheema, data miko mun natan inna daurawa kuwa tariko na "uncle justice" tadaura saman nawaa tahadesu guri daya, tajinke su tace Allah narokeke alokacin dankee gargara kayddada da wannan auren da alheri. Shakuwace ta sarketa tafara shakuwa ba kwakkwautawa, wani abu kamar alam yafara kara likitochine suka shigo suka bukaci kowa yafita. amma abunka ga manya sungane komai mai martaba ne yace ah ah kar kowa yafita sai baba mairoce kawai akace tafita dasu little da daddy, wanda kuka suke kamar kamar me, marafa yabada umurnin wata nurse takawomusu towel da ruwa maisanyi. A yayinda abbansu samie tuni yadauki kalmatush shahada. K'owa kuwa yadauki kaalmatush shahadar, bandani da ahakikanin gaskiya tsaye kawai nake bansan menakeyiba kuma ban ma san me ake cikiba, ankawo towel din daruwa masu sanyi acikin roba abba marafa yamika ma "uncle justice" yace yarika bi duk yanashfa mata ajikinta! Ba musu kuwa yafara tsawon misali mintuna ukku shakuwar ta tsaya saidai takurama "uncle justice" ido bata ko kiftawa ayayinda shikuma yaketa aikin goge mata jikinta. Zuwachan cikin dan daga murya kamar wadda take kokayi da abu mai nauyi itama ta mashi kalimatush shahadar tanayi ajere har saida tazo tabakwai sai shakuwa kut saitayi ajiyar zuciya sai kuma rai yayi halinsa! Allahu akbar maso rai wawa bawanda yayi hayaniyar kuka "uncle justice" ne dai magajin gari yayi saurin jayeshi domin kamota yayi ya kankame ta, amma abun mamaki sai yace yabarshi yanayimata addu'a ne anshirya komai akawuce masauki. Da Asuba bayan salla aka kai Aunty Raheema ma kwanchinta Allah yasa muyi kyakkyawan karshe, sai kuma alokacin karfin halin uncle juatice yasamu rauni domin sharaf yafadi, a makabarta, aka daukeshi zuwa Asibiti wuni guda anayimashi karin ruwa, Yau kwana ukku da rasuwar Aunty raheema, Zuwa lokacin uncle justice duk yarame yazube bahawaye sam a taredashi koma yanayin kukan to watakila sai da dare idon ido ya dauke, saidai adam apple dinshi dazakaga kowane lokaci yana sama, yana kasa, a nanriyard aka rufe Aunty raheemar ba awani wahalar maidata gida ba, tunda ko inna musulmi yake rahamar ubangiji kawai yake nai ma YA ALLAH kasa mucika dakyau da imani kasa mutuwa hutuce ga dukkan musulmi baakidaya, bazan iya tsaya fadin takamai men halinda kowa yashigaba saidai tawakkali irin na mumuni, na kwarai kawai zance. Abbana kuma yakira Daddy Alh sameer mijin Ammi yafadimasa abun dake faruwa yakuma bukaci idan dahali zuwa ranar ukku da rasuwar zaiso ace yana nan yasamu addu'ar Bai musa masaba ya shida masa ai baya U.K suna Turkey Inda yaraka khaleepha end of the year vocation da aketurasu different countrys daga shcool saboda haka insha Allahu suna hanya. Haka kuma bayan gabatar da adduar ukku a harami atake anan magajin gari yafitar da kudi riyal dubu goma yamikama abba amatsayin kudin sadaki fareeda, a yayinda abba kuma yayi umurni da abama abban su samie, sai kuma Abban su samie shima yafitar da riyal dubu goman yamikama Ubangari a matsayin sadakin khairat! ya karba tunda Abban su samie shiyazama waliyina , ayayinda mai martaba ya zama waliyin khairat domin ubangari shiyamikama kudin. Bayan sallar azahar anan cikin haramin aka nadamun igiya ukku ta auren "uncle jawad" ni fareeda abunfa tamkar acikin shirin wasan kwaikwayo a yayinda akakuma daura auren Al'Amin khalipha da khairat akayi addu,a akashafa, Haba ai da gudu khaleepha yaje yadurkusa agaban Abbana muryarshi har sassarkew take yace Abba you give my dream! She is my day dream and my night mere! She is my world Abba kuma my choice, ganin tamkar sakin layin zaiyi yawa yasa waziri yazo yadauke shi, shima Daddy ganin irin farin cikin da dansa yakeciki yasa, yakama hannun daddy sukayi musabuha, Dukkan mu matan muma muna daga gefe, kuma muna kallon duk abunda kefaruwa. Duk dayake da akwai wasu daga cikin larabawa na nan kasar saudiya da na wata kasarma akaraba dabino nakwali kowa yasan yama auren albarka, tareda fatar alheri tareda addu,ar Allah yabada zuria tagari. Sauran kadan na kurma ihu ummu salma dama ankare take dani tayi saurin rufemun baki, tareda gargadi na gaske da ido, sabon kukan ne yakubbuce mani dadan sauti nace aunty raheema ke kintafi taki tayi kyua kuma burin ki yacika amma ni kindoramun abunda bazan iya ba!. Daganan inna hango uncle justice shima kukan yakeyi sai yau naga kukanshi khsanma kowa saiyau yaga zubar hawayenshin hadda shesheka ba wanda yayi yunkurin hanashi, acewarsu gwanda yayin. mai martabane ya taramu duka gabadaya yace to Alhadulillah! Muncika wasiyar marigayiyah, ya mayarda dubanssa zuwa bangaren "uncle justice" tukunnah yajuyo bangarena nima yace to yanxu aikine yarage akanku. jawad daku yi kokari kuci kama mariganyiya burinta. jawad, Uncle yace na am mai martaba yace mike tsaye, inna fareeda nima nace na,am yace na mike tsayen yaje da kansa yarikohan nun "auncle justice" sukazo har inda nake yakamo hannunah, yahada dana" uncle justice"akaro nabiyu hannunmu ya koma haduwa, wanchen karon munacikin tashin hankali amma yanxu sauran kadan nazube jikina yafara karma, sauran kadan nayanke nafadi yanda naji zuciyata tatsinke, jini na sosai yatsinke yana gudana, Yace aurenku yadauru, yace yanxu kuje kuyi dawafi na nasamun ingattattaciyar rayuwa. anan gaba da zuria,a dayyiba. Kaima Al'Amin kaje kayi karokarmuku rayuwa mai inganchi anan gaba muma zamutayaku da addu, a Haba wani irin shaking hannuna yakeyi wanda shima kanshi "uncle juatice" jikin nasa rawa yakeyi dukkanmu munshiga tsananin rudani fulani bababba ce tabiyo baya dukkanmu, kawunan mu akasa maimartaba ya umurchi kowa dasu tashi su tafi. muna nan tsaye harsuka bacema ganinmu. tukunna cikin sanyin jiki "uncle justice" yazare hannunsa daga nawa yajuya batareda yacemun komaiba araina nace mai yake shirinyine, badai shiyana nufin ya yadda da aurenba. ai wannan auren tamkar wasan yara haka nake ganinsa. suma su mai martaba sunyi hakan ne saboda yanxu mutuwar tana da zafi, ne bayan ankwana biu zasu gane illar abunda sukayi. Jiki bakwari nabi bayansa mungabatar da daawafin dan naisa da juna dukkanmu abunda akace muyi bashi mukayinba, dukkan rokonmu yatafine ga naima ma Aunty Raheema mungama bamu damu da yunwar cikin muba muka kama hanyar jidda! inda zamu hadu dasu mutashi zuwa gida gobe. Yau wata ukku cif, da rasuwar Aunty Raheema kuma kamar kowane mumuni dayayi imani da Allah yasan kuma da akwai mutuwa da karan kwana, to dele zai maida lamuransa ga Allah akowaane lokachi to dahakan idan tsanani yazomasaa sai yayi hakuri! Ya kuma yakoma ga Allah to kusan hakance takasnce damu kodayake tunda da muka dawo daga saudiya, nakoma gidanmu da zama tareda su little ayayinda baba mairo takoma gidan mai martaba, kuma kowa natsananin tausayama "Uncle justice" wallahi nama kasa zuwa gidan ko kayana dake gidan na dauko, baba mairo kuwa duk bayan kwan biyar ko sati taknazo ganinmu saboda sabo wataranma har takan kwana a inda gefe daya kuma muma munyi nisa da karatunmu kullum a school khoolsum tana kokarin debemun kewa, da nusar dani. hakan kuma yataimaka sosai wurin cigaban karatuna karatunmu yayi nisa sosai yanxu har anfara turamu asibitochi babbar asibiti aka turamu nida khoolsum, federal medical centre ita asibiti wurine da duk wani mai imani idan yana mu amala acikinta zaikara jin tsoron Allah! da tsananin tausayin al ummah asibiti kusan ince wata makarantace da wanda kusan kullum da yanayin darussan da bawa yake kara fahimta abubuwan tausayi kala kala dalilin kenan danakoma wata shiru shiru banida dawani aiki sai yin abunda yakawoni, sai kuma nakan taimaki al ummata marrasa lafiya da iya kwarewata ko aljuhina kokuma nayimusu Magana maidadi nakanyi iya kokarina wurin danne bachin raina. agurin duk wani majinyaci, dayabatamu rai tunda a kulluma iyaye suna gayamana ita jinya ko aikin jinya namai hakurine shifa majinyachi wani lokacin kome zakayimasa bakayimasa dai dai, sabodaa halin dayake cki saikayi hakuri gefe daya kuma ga wannan igiyar auren "uncle justice" datake kaina kamar wasa wallahi abun nakegani tamkar ashirin firm. Shiru tunda muka dawo bawanda ya komayimun maganar kusan shima din uncle justice din tundamuka sauka a jirgi rabona dashi kenan, tunda koyazo nan gidan wurinsu little danaji muryarshi nake tashi nashige dakina narufe, kofa ba irin yanda su daddy basucemun wai in daina guduwa idan abbansu yazo narika zuwa muna gaisawa, nikuma sai naimusu wayau nace musu idan naganshi yana tunamun ne da rasuwar aunty raheema ne sainayi kuka kuma kunsan mallam yasha fadimana cewar baa son yima mamachi kuka duk suka kada kansu a lamun gamsuwa, kuma tun alokacin basukoma yimun maganarba sam. *⚖️UNCLE JUSTICE⚖️* *STORY WRITTING BY UMMU SHAREEF* *DICATED UMMU SAYID* *A FIRST TIME WRITER* *WANAN LITTAFIN NAKUDINE* *KIBIYA HAJIYA KIKARANTA ZAKIKARU DA ABUBUWA DA DAMA WAN NAN LABARIN* *LABARIN KAGAGGENE BA AYISHI AKAN WANI WATA KO WASUBA* *IDAN KINSIYA KINKARATA KIKABAMA KAWARKI YAR UWARKI, KO KIKA TURA A GROUP HAJIYA NAYAFEMIKI* *IDAN KINA DA HALI DAN ALLAH KIBIYANI TYPING AKKWAI WAHALA* *KIBIYA 300 TA WANNAN ACCOUNT NUMBER 3195366407 HAFSAT ABUBAKAR SADEEQ FIRST BANK* *KO KITURO KATIN WAYA NA 200 TA WANNAN LAYIN 08036833612.* *TAREDA TURO SHAIDAR BIYAN KO DATA TA 300 ZUWA GA WANNAN LAYIN 0803683312* *DUKKANMU MASU LAIFINE ALLAH YA YAFEMANA* *FREE PAGE* *xviii* k'amar yau bayan mungama sallar magariba, inna zaune inna raira karatun Qurani cikin natsuwa. bayan nagama karantarda su daddy nasu, kafin malam yazo kasancewar sosai hankalina yatafi ga karatun sam banmaji shigowarsa ba. Kasancewar karatun nima kaina yanamun dadi barinma dayake nashigo cikin suratul yaseen ne, zuciyar al qurani kuma nima bana gajiya da karantata saboda haka sam banmaji shigowarsa ba. har sungaisa da maman fareeda, duk banjiba har saida ummu salma tashigo tareda su daddy, kafin sannan na ankaro. W'ayyo tamkar nakurma ihu naji. saboda bahalin nagudu ayanda nalurama ummu salma sai hararata take yi, tuni nataso daga inda nake na matso nadurkusa har kasa muryata tayi sanyi sosai kamar banice yanxu nabade gida da karatun alqurani ba, inna wuni ya gida ya aiki. nafadi duk ajere bai amsaba saida maman fareeda tace wai bakajine anna gaidaka kafin sannan a gajerce ya amamun da lafiya kalau, kawai kafin sannan ummu salma takwadamun kira naje nasameta a k'itchen, shigata kenan ta balbaleni da maseefa, waike nalura rayuwarki sam bakida lissafi, inna lura dake ko ganin jawad bakisonyi! To tunwuri kishiga karatun tanatsu, aure dai anriga da andaurashi, saboda haka yakamata kinutsu kisan mekikeyi, domin badai gudu kuma ba jada baya, kuma kina dadai ilmi kinsan girma da darajar miji a rayuwa. nayishiru inna saurarenta batareda nacemata komai ba. Araina dai nace umma wannan auren ai sunansa marigayi, domin nifa banga tayanda za,ace in iyya zaman rayuwar aure da mijin auntie raheema ba, matar da nadauka tamkar ya yata uwa daya uba daya, baccin hakama "uncle justice" ne fa haba inna! jindai umma salma nata fadanta abinchi tashiga hadamsa tuwon danyar shinkafa da miyar danyar gyada, sai lemun jinger da fura kayan cikin basket bata kalleniba tace dauki kikaimasa abinci. Nadawo nasameshi inda nabarshi, koda bankallesaba sosai amma alamu sun nuna duk yarame, yaran duk sun kewayeshi nalura cewar har wani extra ordinary close mark yakebama yaran, tun bayan rasuwar mamansu sannin cewar baya chin abinchi har sai anzuba mashi anhada mashi komai yasa dana kawo banban dagaba harsaida nahada masa din kamar yanda nasan yake bukata komai kuma saida nazubamashi inna zubawar hanunnah nakakkarwa, alokacin nekuma naji yanayin firar dasukeyi da maman fareeda, wai mai martaba yana bukatarsu za,ayi meeting ranar jummua idan ansauko daga masallaci. Budar bakinta sai tace ai yakira abban su fareeda sunyi Magana daman maganar tarewarkuce gaskiya yakamata kam yanxufa wata ukku cikin na hudu kuke, yakamata kam autan Fulani kutare haka nan. muna muku fatar alheri habawa aikuwa tuni jikina yafara rawa, gabana yatsinke yafadi inna kokarin bude ruwa ai tuni gorar ta sulbe ga hannuna tafadi. Allah yaso basaman abincin tafadaba sai dai tafada asaman baban dan yatsan kafar "uncle justice" dagashi din har maman fareeda nisukabi da kallo, duk nawani tsure ga tsoronshi dayakamani. Nace dan Allah kayi hakuri nacemasa batareda nadago nakalle saba "as usual" daii yace mani "is ok! kawai banko tsaya zubamashi fruit dinba namike natafiyata daki nafada asaman godona afili nace ni fareeda wai me yakeshirin faruwa da nine ta yayama zan iya rayuwar aure da "uncke justice" ni na uyya yinta nadaukama anbar wannan maganar tun tuni tunda dai ainagadai ancikama auntie raheemar burin natan, yanxukuma ia sai adubi yiyuwar abun araba auren kawai. Haka dai nayi ta saka da warwarewa nasan dai suma kansu abun yanazuwa musune badaidaiba inna fatar tunaninsu yadawo dai dai nan da zuwa jumu'ar, amma saukinama wata zuciyar nacemun ai dole mai martaba zaisaka akirani yatambayeni ra ayina nikuma ba kunya zance mishi ban aminceba, kuwa tuni kuwa zaisa a warwareshi, idanma auren zumunci idanma aurenzumunci yakeso shi "uncle j" din tobaga ya yan dangin mai martaba nanba sai yazaba acikinsu, tunda aurenshi da aunty raheema daga dangin fulani babbane yanxu sai yayi nadangin mai martaban da wannan tunanin nasamu zuciyata tayisanyi kuma talafa daga fargabar danashiga naci gaba da hidimata bandai san tafiyar "uncle justice" ba su little dai sunkawomun tsarabar da yayimusu kaida komai zaisiyo hudu ne little da daddy da Aslam da khairat. kasncewar lecture daya kegareni ranar jummu a kuma lecture dayace 8-10 ga malamin baya kara ko digo kuma da yashigo zai rufe kofa shiyasama bantsaya jiran su abba ba, kasancewar shike sauke kowa a school dinsu kafin shikuma yawuce aiki da wuri nafita nasamu abun hawa mungama lecture kenan fitowata daga school sai ga kiran abbana, bayan sallama har saida nadan rusuna nagayar dashi tamkar yana gabana. tukunna nace jayi hakuri abba bantsaya jirankuba banasone namakara yace hakkan ai yanada kau yar gidan Asiya, yace kunfito daga daukar karatun nace eh! yanzunan fitowarmu abba yace sai tanawa kuma nace ai mungama yau kuma sai Monday, Abba nace kowani abun kakeso nakoma gida nayimaka, Abba kokuma zakayi bakine yace ah ah bakodaya inna son dai yanxu kihau abun hawa yakawoki gidan mai martaba. domin da akwai wata muhimmiyar Magana da za,a tattatuna. A'take naji dadi araina, nace toh abba yanxu kuwa arina nace yau za,arabani da kadaddararen aurenka. "uncle justice" cikin saukri mukayi ban kwana da ummu khoolsum, har take tambayata wai baxan tsaya muje capteria ba nace mata ah ah suje kawai abba kejirana bazanso nabata mashi lokaciba. F'adar maimartaba tashika makil kuma duk wani wanda keda wata alaka daga dangin mahaifina dana mai martaba martaba sun duk sun hallara. k'asancewr ummu salma ba yarnan bace bakowa nata a wurin amma itama tana wurin tareda maman fareeda, sai itama Fulani babba banata dangin a wurin kenan dagani din har "uncle justice" kowa ba daga bangaren mahaifiya saidai itama tana wurin. Baban limamin dake bayarda sallah anan cikin fada shine bude taron da addu,a sai addu,a da aka gabatar musamman saboda aunty raheema. aka shafa mai martaba ne yafara bayanin makasudin taruwar mu anan saboda wata alaka ta auratayya da aka kulla watanni kusan hudu da aka daura tsakanin jawad da freeda to dayake abun yaratsa da alhinin rashi da mukayi yasa mukayanke shawarar mudan badalokaci har natsuwa tazoman kuma Alhamdulillah mun dan samu natsuwar. FAREEDA! maimartaba yakira sunana tuni gabana yayiwwani irin faduwa tun baicedani komaiba naji fitsari uacikamun mara da hawaye sunfara gudana afuskata na,am rankadade taso nan yanunamun saman wani capet dake da laushin gaske dake tsakiyar falon, tuni natshi jikina sai bari yake naje inda yanunamun nazauna. JAWAD! maimartaba yakirashi shima ya amsa shima yayimasa umurni dayazo saman capet din inda nake yazauna to jama,a wasunku sunanan sunga zahiri wasunku kuma basu nan sundaiji labaria daura auen jawad da fareeda aranar takwaas gawatan mayu shera ta alif dubu biyu da gomsha bakwai a babban birnin kasar saudiya, kuma adakin Allah!🕋 akokarinmu nacika wasiyar da matar shi jawad tabari a inda tayi duba da wadda tadace data damkama ragamar kulamata da zurarta da kuma maigidanta, taroki alfarmar hakane gaban mu kuma alhamdulillha kuma Allah cikin ikosa yabamu ikon cikamata bukatunta na wasiyar data bari, na wannan buri munafatar ubangiji Allah yayimata rahama! yakarbi bakuntar ta Amin! kowayace saidai wani hanzariba guduba wanda shine dabamu tsaya mukaji tabakin ma auratanba. Da amincewar su ko kuwa mai martaba yamaido da kallonsa zuwa ga "uncle justice" banajin ta jawad domin shi babbane shi yamallaki hankalinsa kuma yasani cewar gatace ita marigayiyar tayi masa, sai dai bansaniba koyanada wani ra,ayi akan haka, sai kuma ita yarinyar bazamu tauyemata hakkiba duk zamuji ra,ayinsu kome kenan sai anaimi maslaha. Ko jawad kanada wata Magana da kecikin ranka dangane da wannan auren! uncle yayi dan jim aransa yanacewa a gaskiya bayajin zai iya rayuwar aure da wannan yar kankanuwar yarinyar dayake tunanin yabata akalla shekara shabakwai zuwa ishirin, da haihuwa bakamar raheemaba da duka shekara hudune tsakanin su, shi a raayinsa yafison mace mai shekaru dayawa, bayarinya ba to amma kuma bayajin zai iya rabuwa da ita saboda yaranshi.kar maraicin yayimusu yawa, dama sun saba da ita kuma zuwa yanxu baisan wadda zai kawoba, maraicin yayimusu yawa yanajin koda zaiyi wani yunkurin aure yanxu to sai nan gaba zuwa lokacin yakara natsuwa sosai. Gyaran murya mai martaba yayi wanda hakan tasa uncle yamagantu yace Allah yataimakeka ni nakarbi auren da kyakyawar niya ni agurina hakan da kukayi yayi dai dai saboda. *⚖️UNCLE JUSTICE⚖️* *STORY WRITTING BY UMMU SHAREEF* *DICATED UMMU SAYYID* *A FIRST TIME WRITER* *WANAN LITTAFIN NAKUDINE* *KIBIYA HAJIYA KIKARANTA ZAKIKARU DA ABUBUWA DA DAMA WAN NAN LABARIN* *LABARIN KAGAGGENE BA AYISHI AKAN WANI WATA KO WASUBA* *IDAN KINSIYA KINKARATA KIKABAMA KAWARKI YAR UWARKI, KO KIKA TURA A GROUP HAJIYA NAYAFEMIKI* *IDAN KINA DA HALI DAN ALLAH KIBIYANI TYPING AKKWAI WAHALA* *KIBIYA 300 TA WANNAN ACCOUNT NUMBER 3195366407 HAFSAT ABUBAKAR SADEEQ FIRST BANK* *KO KITURO KATIN WAYA NA 200 TA WANNAN LAYIN 08036833612.* *TAREDA TURO SHAIDAR BIYAN KO DATA TA 300 ZUWA GA WANNAN LAYIN 0803683312* *DUKKANMU MASU LAIFINE ALLAH YA YAFEMANA* *FREE PAGE* *xvix* Haba aibansan sanda nasaki baki kunai hanchi da ido ba inna kallonsa, da mamaki. Ayayinda shikumma ya sadda kansa kasa ni innaga ma tunda nake arayuwata bantaba yimasa irin wannan kwatankwachin kallon kurillar ba.nan take fadawa suka dauka sannu dan Albarka kayi biyayyah Allah ya inganta rayuwa, sunatayimasa kirari har saida sarki yayi gyaran murya, fada takoma daukar natsuwa, tsit kowa yayi shiru. tuni mai martaba yamaido da hankalinsa aguna. To masha Allahu fareeda munji daga wurin jawad saura ke! munason muji naki ra,ayin insha ALLAHU bazamu tauyeki ba, nagayara zama kenan nabude baki zankoro bayani, sai kawai naji Abban su samie daga bayan mu, wato waliyin aurena kuma madaurin auren na kuma yaya agurin Abbanmu ai ranka ya dade ubane akabama ikon zabama yarsa budurwa miji aure na farko! kuma nida yan uwana kaf da iyayen yarinyar munyarda da zabin da Allah yayi mata, kuma zabinmu saboda haka muna rokon Allah yasanya ma auren albarka, ya ba su zuria tagari! Jinayi cikina ya murde ya juye gefe daya tuni jiri yakamani gashi dai inna son inbude baki nayi Magana, amma inna hakorana da lebunana sai kakkarwa sukeyi, tuni fadawa suka dauki sowa. maimartaba godiya yake da wannana karramawa, da kukayi msa masha Allahu! da ahalin kirki mutanen mutumci irin albarka, mai martaba ya'yi gyaran murya, aka natsu yace yana godiya da wannan kyautar alheri. Kuma shi amatsayinsa na uban yarinya yayimata kyautar mota benz, da saitin gado na japan ga amarya a yayinda yayima ango kyautar gidansa da ke GRA a isa kaita road, bankaiga da wowa cikin natsuwataba naji kawai jekadiya tazo tsakiyar kaina tarangada wata uwar guda, asaman kaina shiyayi dalilin dawowata firgigit a haiyachina. jinake fitsari kamar zai zubomun, daganan inda nake zaune yau nashiga ukku kallon kowa nake kamar sun samu tabin hankali idan bahakaba nita inna mazan fara rayuwar aure da uncle justice Abban goruba yakuwa san meyakeyi, bamazata sabuba sarkine yayi gyaranmurya fada tayi shiru maman fareeda tamike tayima mai martaba godiya kyautar dayabani.sai "uncle justice" daga nan zaune shima yayi tashi godiyar, ayayinda nikuma sai kukanake kamar zanshide ganin nake kowama awurin tunaninsu yagurba taccene amma tayaya suke tunanin nafara rayuwar zaman aure da "uncle justice" haba haka akarufe taron da addu a muka dunguma zuwa gida. Da zumar cewar idan su Abba dayan uwansa suka yanke lokacin tarewar, to zasu sanarma dasu mai martaba. Tun dawowar mu nashige dakina nakulle bana bukatar kowa awannan lokacin, duk nattara tunanina nayanda zansamu mafitar afasa wannan auren nayi amma nakasa samun takammamen idea, daya dazatabani mafita, innayin sallar isah I nakwanta duk da dai cewar gobe assabar banida zuwa aji amma muna da kai ziyara dazamuyi zuwa asibitin babbar ruga, akwai wasu aikin da lecture dinmuzai nunaman. idanuna har sunkumbura saboda kukan danasha kuma da nayi tunanin kona fadima khairat abunda akeciki zanchen aurenta da khaleepha saboda dama tun a sudiyar ance kar afadimata, kuma kiri da muzu nashige daki bansake futowaba, sam banbari kowa yaganiba nadaiji sanda maman fareeda tadawo bayan magariba. tana tam bayata umma salma, tace mata inna daki tunda ita dazu dazamu dawo bada ita muka xoba, munbarta chan wai sunason sufara shirye shiryen tarewa, inna shirin kwanciyane naji anturo kofar anshigo ummina sannu da zuwa, ashe kindawo sam banji shigowarkiba jinayi kawaai ankama hannuna inna jiyowa naga ummu salma ce, madadin maman fareeda da natsamata, shiiiii 🤫 da hannu tanunamun nayi shiru taja hannunah har zuwa sashenta, tasakani dakinta tarufe kofa! Fareeda takirani atake gabana yayi wata irin tsinkewa yafadi!. da wahala takira sunanan kai tsaye, saidai takirani da yar gidan Aseeya! aikuwa da jinhaka nasan tabbas babu wasa acikin maganarta, kuwa na'am na amsa mata tarda kallon fuskarta, tuni ni na sadda tawa fuskar kasa, ganin yanayin fuskarta din in a serious manner Nakuwa san magana ce maimuhim manchi zangaya maki fareeda! barokonki zanyiba fareeda umurni zan baki, domin nalura tamkar kinason kinunama duniya cewar ke butuluce, cikin dan sauri dakuma razana nadago inna dubanta, yoh a irin halin dakikeso kinuna sam bakiyi na'am da auren nanba naga alama inna hankalinki yake, domin fareeda nikawai haihuwarki nayi amma amma kashinki fitsarinki amanki duk kwacha kiyarrki ajikin maman fareeda kika yishi, ai nadauka irin kaunar dake tsakaninki

Chapter 5 of 6