Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

damu zan sanar miki, amma ba yanzuba.
To shikenan asmy tafad'a, tacigaba da lallashin yasmeen, yasmeen ta ce, "Asmy kiyi hak'uri zan tafi gida, dan kaina yana mini ciwo.
Asmy ta ce, "babu damuwa dear kije gobe ma had'u, ngd da k'ok'arinki.
Yasmeen ta mik'e tana neman Ameena, bayan ta ganta suka fice, duk abinda take Nawaff yana kallonta, suna fita yarufa musu baya, shima mas'ud binsu yayi.
Yasmeen tana k'ok'arin neman balarabe saitaji an fisgota ta baya, tajuyo da sauri, gabanta yafad'i rass dan ganin NAWAFF,
Ya had'e fuska kamar bashiba, yasmeen ta ce, "lfy konaci bashinkane??.
Nawaff ya damk'i gashin yasmeen data d'aure abaya, ya murd'e da karfi, tako kwalla k'ara, saidai babu maijinta saboda hayaniyar wajen tayi yawa, gakuma kid'a yana tashi, gashi a tsakankanin motoci suke.
Cikin sark'ewar murya ya ce, "nikika mara ko??, to wlhy ki rubuta ki ajiye, wannan marin saiya zama FANSAR BUDURCINKI, NA MELODY , saikinyi dana sanin aikata hakan agareni, ya hankad'ata tadaki motar bayanta.
mas'ud dake bayansu yabi NAWAFF da kallon mamaki, shin miyake nufi da marin datayi masa saiya zama FANSAR BUDURCINTA!!!!????.
Da sauri yarufa masa baya, yayinda ameena ta k'araso takama yasmeen dake kwasar kuka, hannunta kawai taja batareda tace mata komaiba, mota suka shiga bala yajasu suka tafi.
Ahanyama yasmeen sai kuka take, dan furicin NAWAFF yayi matuk'ar gigitata,
ya dawomata da tunanin rayuwarta ta baya, lallai itakam tana cikin tarkunan maza azzalumai, shiyyasa takema maza KALLON KITSE na @UT@R H@JIYA@",, shin wai ita haka rayuwarta zata k'are, kowane NAMIJI burinsa yarabata da Abu mafi muhimmanci ARAYUWAR ta, miyasa haka???, mina musu???, miyasa suke son su rabani da mutuncina???, ta fad'a tana wani irin kuka mai ban tausayi,, Ameena da balarabe duk tausayin yasmeen ya cika musu zuciya, dan afili take maganar batareda ta saniba.
Ameena ta rungumeta tana lallashi, dahaka suka k'arasa gida..........................✍🏻





© 2016


💞Bilyn Abdul💞
💞Mrs Abdus'salam💞
💞LUV U OLL😘😘💞
[1/12, 8:54 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾NAWAFF🎾
☆☆☆☆☆☆☆





NA BILKISA IBRAHIM💞




Page👉🏻6

........Nawaff kuwa tafiyarsa yayi yabar mas'ud, mas'ud bai damuba dan dama batare suka zoba, komawa yayi wajen taron dan baikama ta ace suduka sun tafi ba.

NAWAFF kwance afalonsa dayaji kayan more rayuwa iri2 yana kwance saman doguwar kujera idanunsa lumshe, tamkar maiyin barci, amma idanunsa biyu, yana cikin tsananin b'acin raine kawai, tunani yake mizaima yarinyar nan ya huce haushinsa, dan ya tsaneta, hangota kawai yake lokacin data maresa, yakai hannu yashafa fuskarsa.
Yay kwafa, wlhy sai yarinyarnan ta raina kanta inhar yana numfashi.
Kofa aka kwankwasa, ya ce, "kowaye ya shigo.
Wata 'yar aikin gidansu ce, d'auke da tiren kayan marmari, ta d'ora asaman tebirin dake tsakiyar falon, tad'an jawo tebir d'in gaban kujerar da Nawaff yake kwance.
Watama tashigo da kuloli, ta d'ora inda 'yar uwarta ta d'ora, sannan suka duk'a suna kai gaisuwa wajen oga Nawaff!!.
Hannu kawai ya d'aga musu sannan yay musu nuni dasu tafi.
Da sauri suka wuce dan sunsan halinsa baya son wargi.

D'aya acikinsu ta ce, "wlhy talatu yaya Nawaff yana burgeni, dama zaice yana sona!,
Talatu ta rik'e baki, lallai ladidi yau na tabbatar bakida hankali, garama tu wuri ki fidda wannan tunanin a ranki, tun kafin wanima agidannan yajiki, in banda wuce gona da iri, yazaki had'a kanki da wannan had'ad'd'en mutumin, mai ilimi da kud'i, ga k'yau, wanda duniya tasan da zamansa.
Ladidi tayi dariya kujimin wannan talatun, to kika San abinda ALLAH zaiyi ne??.
Talatu ta ce, "A'a.

Tunda suka fita baiko motsaba bare yaga abinda suka kawo masa, wayarsa tashiga k'ara cikin sauti mai dad'i, idonsa arufe ya mik'a hannu ya d'auka, ahankali ya bud'e idanu dan ganin wake kiransa, momcy yaga ansaka.
Wayar ta k'atse aka sake kira.
Cikin ladabi ya ce, "momcy barka da dare.
Daga can ta ce, "barka dai, wai lfy banga kashigoba?, kuma ance mini kadawo.
Wlhy babu komai momcy ina d'akine, nagajine shiyyasa kika ga ban shigoba, inaso nayi barcine da wuri, dan gobe d'aurin auren SAFWAN, banaso nak'i zuwa gashi kuma na safene.
Okey to shikenan, dama nazata ko bakada lfy ne??.
A'a lfyta k'alau momcy na!!.
To shikenan saida safe.
ALLAH yakaimu my sweet mom!!!!.
Saida takashe sannan ya kashe.
Number mas'ud yakira, batareda yayi sallamaba ya ce, "waikai malam kana inane??.
Gani nanma shigowa gidan mas'ud yafad'a.
Kashe wayar yayi batareda ya ce, "komaiba.

Mas'ud yaturo k'ofan yashigo da sallama, bai saurari amsaba, dan yasan bazai samuba, saboda mutumin yau cikin fushi yake.
Kujera yanema ya zauna, tareda fad'in gani neman mi kake mini??.
Nawaff yatashi zaune, yad'an tsurama mas'ud idanu, bayan kamar minti d'aya ya ce, "bro's plz inaso ka taimaka mini??.
Mas'ud ya ce, "to wane irin taimako kenan??.
NAWAFF yad'an cije leb'ensa na kasa, ya ce, "na nemo yarinyar nan, inaso nasan ita wacece?, 'yar kuma wacece?.
Dan wlhy idan banyimata rashin mutunciba zuciyata zata iya fashewa, ALLAH na tsaneta, kuma saina koya mata hankali, daga kaina bazata sake rashin kunyaba, ko kuskurwn marin wani.
Mas'ud yay masa kallon tsaf dan ganin yanda yafita hayyacinsa yau d'aya.
Yaja numfashi, Nawaff! Yakamata kadawo hayyacinka, karka manta kaifa kafara tsokanar yarinyarnan, kamareta, kayimata dariya.
To dankuma yau tarama saikaji haushi, yakamata ku tsaida fad'annan haka tunda kowa yayima kowa, sannan ka janye k'udirinka na d'azu, dakace marin data yimaka shine zai zama fansar budurcinta, Nawaff bansanka da irin wannan halinba, kar ka aikata abinda zaizo ya dami kowa, wannan ba hanyar bullewa bace, kai dama soyayya kuka koma dan wlhy kun dace da juna sosai.
Harara Nawaff ya watsama mas'ud, wadda dama tun d'azu ita yake masa bai ganiba.
Ya ce, "ALLAH kuwa mas'ud yau dawanine yafad'a mini maganar nan wlhy dasai na bubbugeshi, amma............. yay kwafa kaiwai batareda ya karasaba.
Mas'ud yay murmushi ya ce, "amma mi....?, ka karasa fad'a mana, to konima zaka bibbigeni ne?, ka huce haushinka!!,.
Tsaki NAWAFF yayi yatashi zaibar falon, mas'ud ya tuntsure da dariya, tareda fad'in sakai a wahala kenan,, duk wanda dai yaga wannan fad'an naku yasan na masoyane😜.
Har Nawaff yakai k'ofa yadawo ya ce, "kai dallah malam sauraramin!, mixanso a jikin wannan faratun yarinyar mai kama da aljana, kai dana so wannan yarinyar gara naso 'yar k'auye wlhy.
Dariya mas'ud yake tuntsurawa harda hawaye, cikin dariya ya ce, "aii kaima faratunne Nawaff, koka manta?, amma mudai 'yan kallone mijin faratu, mas'ud yafad'a cikin tsokana😜.
NAWAFF ya kula mas'ud yana neman maidashi wani sakaraine, dan haka yashige bedroom yay kwanciyarsa.
Dak'yar mas'ud ya lallab'ashi yafito sukaci abinci.


WAYE NAWAFF SA'EED MODEEBBO???????, kubiyoni danjin wannan amsar😜.





©2016


💞Bilyn Abdul💞
💞Mrs Abdus'salam💞
💞LUV U OLL😘😘💞
[1/12, 8:54 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆☆
🎾 NAWAFF 🎾
☆☆☆☆☆☆☆☆





NA BILKISA IBRAHIM💞





Page👉🏻7

......WAYE NAWAFF SA'EED MODEEBBO???.
ALHAJI sa'eed umar modeebbo shine mahaifinsa, babban alak'aline mai gsky da rik'on amana, bashida tsoro Ko kad'an, yakan yanke maka hukunci dai2 da abinda ka aikata, duk kud'inka ko mulkinka bazaisa ka kub'uta ahannunsa ba, sai dai gskyr ka ta kub"utar dakai.
Kaifi d'ayane shi, idan ya ce, e, "baya cewa A'a.
Alhaji sa'eed bafulatanine irin na daji, dan k'yak'yk'yawane abin so dagani, d'an asalin garin safana ne dake k'aramar hukumar caranchi, safanar ma acikin wani k'yauye suke cikin rugar jauro, amma yanzu yana zaune a kano.
Matarsa d'aya hajiya ummul'khairi, balarabiya ce cikakkiya, k'yak'yk'yawar mace, mai hak'uri da ilimin addini, ga son mutane.
A Egypt ya aurota lokacin yana d'alibin ilimi a jami'ar AL'AZHAR, soyayya sukayi har ALLAH ya mallaka masa ita amatsayin mata.
Momcy Nawaff tafara haifa daga shi ta dad'e bata sakeba, sai bayan shekara bakwai ta haifi Abdallah, sai auta Anwar,
Nawaff k'yak'yawane fari amma ba tas ba, ya biyo momcy sosai, dan shikad'aine yake tsananin kama da ita, kana ganinsa kasan itace ta haifesa, sai dai ita tafishi fari.
Momcy tanada hak'uri batada hayaniya ko kad'an, amma Nawaff yanada zafi, indai wajen haline papa yabiyo Alhaji sa'eed kenan, Nawaff baya son raini ga son girman tsiya da miskilanci, gakuma ilimi, dan yanada sani wajen addini sosai, shima yanada son mutane.
Nawaff yana son k'annensa sosai, duk abinda sukeso yana musu, shiyyasa suma suke sonsa da girmamasa.
Nawaff tun yana primary yakeson kwallo har yashiga secondary, lokancin dayake a secondary sukanje gasar kwallo zuwa wasu makarantun, cikin ikon ALLAH sai sun ciyo kuma Nawaff ne mai zira musu kwallon.
Bayan ya kammala secondary saboda k'aunarsa da kwallo papa, wato mahaifinsa ya nemi shawarar momcy domin kai Nawaff wata makaranta da ake kira School Academic domin k'ara samun ilimi a fannin kwallon k'afa.
Fatan alkairi momcy tayi masa tareda addu'ar samun nasara arayuwa.
Babu dad'ewa aka kaisa wannan makaranta ta (School Academic dake jihar kwara) iyaye da 'yan uwa suka bishi da addu'ar samun nasara, aiko ansami nasarar, dan addu'ar iyaye babbar katanga ce.
In tak'aicemuku dai, Nawaff bai rufa shekara biyu ba yasamu nasarar shiga jerin wad'anda (NAJERIA's Foodboll Asocion NFF) suka gayyata zuwa abuja dan yin screening nazuwa kwallon kasa da kasa, na 'yan kasa da shekara 17, (under 17 play engle of Najeria ).
Awannan screening ansha gwagwar maya, har ALLAH yabawa Nawaff nasarar fitowa d'aya daga cikin wad'anda aka zab'a, harda muk'amin capten na k'ungiyar kwallon kafar Najeria wato ta (under 17).
Shigarsa (under 17) ta bashi damar wawuro nasarori da dama, dan sun ciyo kofin duniya na wannan lokaci, yasamu damar zurama Najeriya kwallo 9, wannan yasa yazama (here Gold scores )na wannan gasa, har aka bashi k'yautar, ( Golden but)
wannan nasace tajawo hankalin manyan club club na duniya kansa.
Samun wannan nasara yasaka family nasa cikin farinciki, yayinda shugaban k'asa na wannan lokacin ya shirya musu liyafar cin abinci tareda shi, da k'yautittikan ban girma.
Bayan dawowarsa daga kwallon k'asa da k'asa wani (club na F,C 20)dake k'asar HOLLAND yasami damar d'aukarsa.
ya rattab'a hannu✍🏻 da k'ungiyar na tsawon shekara 5, shigarsa wannan club ya k'ara fito da kwazonsa, yasamu nasarrar buga musu kwallaye masu yawan gsk.
Awannan lokacin duniyar masana kwallon k'afa suka saka idanu k'ur akan Nawaff, manyan club club suka fara jawarcinsa.
Daga k'arshe wani club mai fad'a aji yasamu nasarar sayen NAWAFF.
To ayanzu haka dai girma da cigaba yazo masa, yasamu nasarar tsintar kansa a cikin club d'in (Barcelona F,C )dake k'asar Spain, wannanne ya tabbatar dashi zama babban d'an kwallon k"afa, wanda duniya tasani take kuma alfahari dashi, musamman ma k'asarsa NAJERIA.
yanzu haka yazo hutun k'arshen shekarane da sukan samu, kwanansa d'aya dazuwa suka had'u da Yasmeen, har ya takaleta.
Wannan shine tarihin NAWAFF SA'EED MODEEBBO atak'aice....................✍🏻





©2016


💞Bilyn Abdul💞
💞Mrs Abdus'salam💞
💞LUV U OLL MY FAN's💞
[1/12, 8:54 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾 NAWAFF 🎾
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM💞




Page👉🏻8 & 9

.....Mas'ud d'an abokin papa ne Alhaji khasim, tare sukayi karatu da papa a Egypt shima masanine ab'angaren ilimin addini danshi har isalamiyya gareshi.
NAWAFF da MAS'UD tare suka tashi tun suna k'anana, bayan sun gama secondary ne kowa yakama inda yafi wayau, Nawaff yatafi makarsantar koyon kwallo, Mas'ud yatafi kasar INDIA domin k'aro ilimi a fannin Likitanci.
Yanzu haka shi cikakken Likitane, a babban asibitin Aminu kano, Nawaff bashida wani aboki wanda ya wuce mas'ud, haka shima Mas'ud.
Sun shak'u da juna matuk"a suna kuma k'aunar juna, saidai halinsu ya babbanta, domin mas'ud mutumne mai sanyi da hak'uri, amma Nawaff yanada fad'a, kuma baya son hayaniya.
Basa shaye2 bare neman mata, hasalima shi Nawaff baya dariya gaban mata, dan ya ce, "yawan yima mace dariya yakan sa ta rainaka.
Hummm kunji son girma, naga yannda za'ayi yayi aure tunda baya son mata su rainashi😏.


A'ban garen yasmeen kuwa tunda suka shiga gida take kuka, umma bata tanbayeta abinda yafaruba, saidai tanata lallashinta, yaseer yashigo hannunsa rik'e da leda, yazauna kusada umma yana turo baki.
Umma ta ce, "kaikuma lafiya??, ya nuna mata yasmeen data d'ora kanta saman cinyar umma, waishi adole kishi, ya ce, "ALLAH umma wanima saiya d'auka itace auta!.
Umma tayi masa da'kuwa tana fad'in kaci gidanku bakaga halin datake ciki bane.
Yaseer yad'an le'ka fuskar yasmeen saiyaga hawaye, yad'an zaro😳idanu yana fad'i sister miya faru dake??, tad'ago tana kallonsa saikuma ta fashe da kuka, da sauri yadawo kusada ita yana share mata hawaye, ya ce, "haba auntyna yakamata ki daina saka damuwa azuciyarki haka nan, ki manta da komai na rayuwa, idan kuma wannan d'an iskanne yake saka ki kuka kiyi ha'kuri ALLAH zai mana maganinsa, kuma insha ALLAHU abinda yake burin bazai ta'ba kasan cewaba, kullum muna miki addu'oin samun nasara a rayuwa, yafad'a shima yana hawaye.
Da sauri yasmeen tatashi ta rungimeshi suka cigaba da kuka, sun bama umma tausayi, dan haka itama ta share nata hawayen, saida sukayi kuka mai isarsu, daga baya sukayi shiru.

WAI WACECE YASMEEN????.
FATIMA shine cikakken sunanata, malam Yakubu shine mahaifinta, su 'yan asalin kasar Nijar ne, awani gari kwangwalan, kwangwalan yana nan kusada jihar katsina, dan za'a iya cewa a boda suke.
Kharima itace mahaifiyarsu wato umma, malam yakubu makiyayi ne a garin kwangwalan mutumne mai tsananin hak'uri, 'yan uwansa basa sonsa, kasancewarsu 'yan ubane, shi kad'ai mahaifiyarsa ta hafa a gidansu.
Yaransa biyu Fatima sunan mamansa aka saka mata, shiyyasa suke kiranta da yasmeen, saikuma ABUBAKAR shima dai sunan baban umma ne, shiyyasa suke kiransa da yaseer.
Yasmeen da yaseer k'yawawane, dan sunada kala irinta asalin buzaye.
Yasmeen tun tana yarinya takeda farin jini, kowa sonta yake, dan haka dangin babanta suka tsaneta laifin babanta ya shafeta.
Lokacin da yasmeen takai shekara 12 sai dangi suka matsa akan ayi mata aure, zuwa sannan yasmeen tanada wanda takeso wani sule, tana sonsa sosai shima haka, dan haka lokacin da'akace za'ayimata aure saitayi murna.
Amma saidai kash, dangin mahaifinta sunce sun za'ba mata miji, d'an wan babanta wato Tanimu, yasmeen sam bata son Tanimu dan d'an iskane kowa yasani kuma, amma babu yanda zatayi.
Aka saka biki wata hud'u, amma amarya bata so, dahaka biki yarage saura sati d'aya.
Ana saura kwana hud'u d'aurin aure Tanimu yazo gun yasmeen, abin yabata mamaki dan bai ta'ba zuwa wajentaba tunda aka saka musu rana.
Da'kyar umma ta lalla'bata ta fita, ko sallama bata yimasaba bare gaisuwa, yasaki baki yana zuba mata surutan banza, wai idan sunyi aure randa aka kaita zaiyi kaza zaiyi kaza.
Yasmeen taji yana d'akko mata zancen daya fi karfin tunaninta, dan haka takama hanyar gida zata tafi, da sauri Tanimu ya dam'ko yasmeen, ya matse abango.
Yasmeen tafara ihu dan ganin abubuwan daya ke mata, kafin mutane su kawo mata d'auki ya turmushe ta ak'asa, lokacin da mutane suka zo yana saman yasmeen amma baiyi mata komai ba, sai rigarta daya yaga, nanfa mutane suka shiga jibgarsa dan dama haushinsa akeji.
Kafin safiya labari ya baje garin kwangwalan wai Tanimu yayima yasmeen fad'e a daren jiya.
Duk gari ya d'auka cewa an lalata yasmeen, dan hakama fita ta gagareta, dan babu wanda zai yarda da ba haka bane, aranar kuma dangin mahaifinta sukace sun warware maganar auren, wai yasmeen 'yar iskace tana neman maza.
Abu kullum k'ara gaba yake, harta kai umma da baba basuda ikon fita sai ayita zind'ensu, harda yaseer dabai san komai ba, idan yafita sai ayita tsan gwamarsa, itako yasmeen ma aibatada ikon fita ko k'ofar gida.
Ahaka aka kulla wata 7 amma komai bai canja ba, kuma babu mai zuwa wajen yasmeen, sule ma iyayensa sun hanashi.
Bak'in ciki da damuwa suka ishi baba, dama akwai wani Alhaji dayake zuwa sayen dabbobi a wajensa, shi d'an Najeria ne a jihar kano.
Baba baiyi k'asa aguywa ba wajan sanarma Alhaji halin dasuke ciki,, Alhaji buba ya tausaya musu sosai, dan haka ya ce, "su baba su shirya yatafi dasu Najeria.
Babu musu suka yarda, batareda kowa yasaniba suka baro kwangwalan, koda Alhaji buba yakawo su gidansa sai hajiya jummai ta nuna musu tsangwama, ta ce, "saidai baba yarink'a musu gadi dama mai gadinsu yagudu saboda wahala.
Baba bai musaba yakar'bi tayinta, baba yana gadi umma tana taya hajiyar wasu 'yan ayyukan gida.
Alhaji buba yanada wani yaro mara jin magana, sunansa Fasal, shikad'ai ya haifa dan haka ake nuna masa gata na tsiya, tunda faisal ya 'kayalla idanu yaga Yasmeen ya kafa mata k'ahon zuk'a.
Yasmeen bata manta da abinda yafaruba a garinsu dan haka take baya2 da faisal, duk abinda yake faruwa hajiya jummai tana kula, tasan kuma halin d'anta yanzu saiya 'bata yarinyar mutane, dan haka ta tsawatar masa.
Alhaji buba yasaka su yasmeen makaranta , ahankali k'yawun yasmeen yafara fitowa, zawa sannan faisal yakai 'kololuwar sha'awar yasmeen, awata ranar lahadine, yad'auki hanyar cimma burinsa, yasaka yasmeen ta gyara masa d'aki, daga haka ya rutseta a d'aki, ihu takwala wanda yasa hajiya jummai isowa da gudu d'akin faisal, saita tarar yana shirin aikata ta'asa, ta daka masa tsawa sanna ta 'ban'bare yasmeen dak'yar.
Babu wani mataki da 'aka d'auka, dan ko fad'a basuyima faisal ba, dan haka hankalin umma da baba yatashi, suka fara tsanar zaman gidan, dan indai aka cigaba da tafiya haka wataran faisal saiya lalata musu yarinya.
Da alhaji buba yaga hankalinsu yatashi saiya ce, "yana nemawa faisal auren yasmeen idan yadawo daga karatu america za'ayi biki, inko har basu aminceba to zasu barmasa gida, indan suka amince to zai siya musu gidan dazasu zauna ya nemawa baba aikinyi yabar gadi, zaikuma d'auki nauyin karatun yasmeen da faisal harzuwa inda suke buk'ata.
Da farko basu aminceba dan sunsan faisal bashida tarbiya, amma dasukaga babu sarki sai ALLAH saisuka amince.
Aka saka rana da komai, faisal yatafi america karo karatu, badan yasoba, dan yaso saiya mallaki yasmeen kafin yatafi, bawani so yake mataba sha'awarta kawai yakeyi, daya sami biyan buk'ata zai watsar da banxa😔.
Bayan komai ya kankama alhaji buba yacika al'kawarin duk daya d'auka yasiyama baba gida madaidaici, yakuma d'auki nauyin karatun su yasmeen, yanzu haka yasmeen tana karatu a (FCE KANO ) yaseer yana shekararsa ta k'arshe a secondary, idan yasmeen zata makaranta ko anguwa kaita akeyi, dan an d'akko mata direba na musamman wato balarabe, duk motar dayaso yake d'aukowa a gidan su faisal yakai yasmeen makaran ta daduk inda take buk'ata.
Sutura kuwa mai tsadar gsk su alhaji suke sayama yasmeen, haka kayan kwalliya, hajiya jummai tana k'ok'ari wajen sayama yasmeen, waya mai tsada yasmeen take ri'kewa, wata sa'in agidan take weekend, sunayin waya da faisal, saidai hirar tasa duk takan kasance batsa, abun yana damun yasmeen amma babu yanda zatayi.
Yanzu haka saura wata 5 faisal ya kammala karatunsa, yana dawowa kuma za'asha biki, saidai yasmeen da iyayenta duk basa son wannan aure, kullum addu'arsu ALLAH yakawo sanadin da auren zai rushe, wannan shine tarihin yasmeen....................✍🏻






©2016

💞Bilyn Abdul💞
💞Mrs Abdus'salam💞
💞LUV U OLL MY FAN's💞

[1/12, 8:53 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾 NAWAFF🎾
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM💞




Page👉🏻10

......Yau takama d'aurin aure amma yasmeen batada niyyar zuwa, umma tayi mata maga ta ce, "bazata jeba sai anjima.
Shima dai Nawaff ya halarci taron d'aurin auren daganan yakama gabansa, dan shi mutumne dabaya son yawan hayaniya, gashi da mutane sun ganshi bazasu bari ya huta ba.

3:30pm
Yasmeen kwance a falo tana kallon film, umma tafito daga d'akin abba, ta zauna kusada yasmeen.
Yasmeen ta d'ago tana kallonta, umma ta ce, "mamana yau bazaki wajen bikin asma'u d'in ba??, yasmeen ta ce, "gsky umma bazan jeba bana jin dad'i, amma idan naga zuwa anjima naji sauk'i sai naje.
To shikenan ALLAH ya sauwak'e.
Amin yasmeen tafad'a tana kallon tv, lfyr yasmeen k'alau, batason zuwa wajenne su had'u da Nawaff, tana tsoron karya aikata mugun nufinsa akanta, jadabaya ga rago 🐏kuwa aiba tsoron fad'a bane, inji masu iya magana.

Badan ALLAH Nawaff yay shirin zuwa wajen walimar ba, yajene kawai domin yasmeen, amma saidai kash ita batajeba, tunda yaje yake baza idanu, amma komai kama da ita bai ganiba.
Duk abinda yake mus'ad yana kallonsa, dukda yasan Nawaff bazai aikata abinda yafad'a akan yasmeen ba, amma yayi matuk'ar farin ciki da bata zo wajenba.
Bayan antashi daga walimar su Nawaff sukai saurin guduwa, saboda mutane, amota mas'ud ya ce, "bro's waimi kake nema d'azu kaketa lek'e2.
Nawaff yad'an ja hancinsa tareda kwantawa sosai ajikin kujera yana kallon titi, daga bisani yadawo da kallonsa wajen mas'ud dake tuk'i, ya ce, mara kunyar yarinyar nan nake nema, amma ban gantaba, inaga tsoro yahanata zuwa.
Mas'ud yay murmushi, hankalinsa na bisa titi, ya ce, "aii masu iya magana suna cewa hanyar lafiya abita da shekara, nikaina naji dad'i dabata zoba.
Nawaff ya harari mas'ud, kai malam mikake nufine?? wai ko dai son k'abar nan kakeyi??.
Mas'ud yay dariya yana fad'in A'a alhaji maida wuk'ar niba sonta nakeyiba, kada kishi yasa ka b'arar dani.
Banza Nawaff yay masa, dan yasan halin Mas'ud sarai yanzu saiyayita jan wannan maganar har momcy taji.
Dahaka suka k'arasa gida, kai tsaye b'an garen momcy suka nufa, afalo suka iskesu itada papa da Abdallah.
Nawaff yazauna kusada k'afar papa yana kwasar gaisuwa, shima mas'ud ya gaisheshi, suka gaida momcy, Abdallah ya gaishesu.
Papa ya ce, " 'yan samari daga ina haka??.
Nawaff yad'an sosa sumarsa ya ce, "papa daga wajen bikin Safwan muke.
Papa ya ce, "masha ALLAH, ALLAH yasanya alkairi, kuma aii yakamata kufito da matan auren ko??, da sauri Nawaff yad'ago yana fad'in papa aurefa kace??.
Papa ya ce, "o, ashe kajini modeebbo!!.
Nawaff ya ce, "papa 27year's fa.
Momcy ta ce, "toshi wannan dakukaje bikin ba abokinku bane, amma gashi yayi, kudai nakula daga kai har Mas'ud bakwa sonyin aure, ko sokuke saikun tsufa??.
Barsu ummul'khairi, aimun yanke magana da Alhaji, nanda k'arshen shekara idan har basu kawo matan aureba, tomu zamu nema musu.
Nawaff ya ce, "papa saikace mata.
Papa yakama kunnensa, yana fad'in toku zauna kukagani, sadaka zamu badaku.
Abdallah ya tunysure da dariya.
Nawaff ya harareshi yana mazurai, kai wa kakema dariya??, mas'ud

Please Login or Register in order to submit comment