Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fata dijangala ta auri Nawaf kodansu 'kara hutawa.
Nawaf ya kalli yasmeen data cika tayi fam kamar zata fashe saboda kishi, shi dariyama ta bashi, amma saiya gimtse ya ce, " 'yammata tashi muje munada sauran gurin zuwa.
Yasmeen tami'ke tana zuzzun6ura baki, sukayi musu sallama suka fito, bayan Nawaf ya ajiye musu kuďi da tsaraba.
Amma ko godiya basu yimasaba, shima bai damuba, dan hakan yafi sau'ki, inashi ina wannan kucakar yarinyar mai kamada 'yar bori.
Koda suka fito yasmeen sai wani shan 'kamshi takeyi, Nawaf ya ce, "yammata tunkan nayi auren har kin fara nuna kishi??.
Yasmeen ta murguďa baki😏tana harararsa🙄ta ce, "ALLAH ya kiyaye, miye abin kishi awurinka, ai abinda kakeso kakeyima kishi.
Dariya Nawaf yayi yana faďin aii kuma kin makaro yarinya, fuskarki ta nuna sirrin zuciyarki, dan haka babu abinda zaki faďa na yarda.
Tsaki yasmeen tayi tana faďin matsalarkace dai.
Yahau mashin ďin yana faďin kokuma takiba, kina ba'kinciki nasamu amarya, aiko saidai ki fashe nanda wata shekarar za'a sha biki.
Banza tayi masa ta haye mashinďin tana hawaye.
Yanajin shashshekar kukanta, yayi murmushi kawai, azuciyarsa ya ce, "yarinya ta kamu.
Haka sukaita zagaya dangi har yamma, sanan suka koma gida, aďakain hajiya iya suka yada zango, ta ce, "sannunku, kishiya kinsha yawo ko?, yasmeen tayi dariya tana faďin ai daďi, naga gari.
Hajiya iya ta ce, "yayi 'kyau.
Bayan magriba ta tafi 6angaren su kuluwa matar basiru, dayake duk sa annintane, saidai kowaccensu tanada yara uku zuwa huďu, idan ka gansu saika ďauka sun haifeta, yasmeen ta ce, "azuciyarta dayanzu nima haka nakoma a kwangwalan, kai ALLAH na gode maka.
Hira tazauna sunayi, suna labarin bikinta da 'kauyancin dasukayi awajen anata tuntsura dariya, firera matar salmanu ta ce, "aini da akaje wajen dakuka saka waďan nan rigunan kamar aljanu, da hasken wajen ya haskani saina ruďe nashiga ďimuwa, saida basira ta taimaka mini.
Gaba ďaya suka kwashe da riya, hira sukeyi sosai har wajen 'karfe tara, mazajensu suka fara shigowa gida, yasmeen tami'ke tana faďin bari naje na kwanta nima, wlhy duk nagaji.
Tana tashi ta kwalla 'kara, ta zube awajen, cikin tashin hankali suka shiga tambayarta lafiya??.
Ta ce, "wani abu ya cijeni a'kafa, wayyo ALLAHna, da sauri sha'aibu mijin barira ya haska, zuwa sanan Nawaf ya 'karaso waje danjin 'karar yasmeen.
'Katuwar kunama suka gani ba'ki'k'kirin, ta tada bindi sama🦂, sha'aibu ya ďauketa da hannunsa, ya kashe, Nawaf ya'karaso wajen yasmeen daketa zabga zufa.
Ya ďagota zuwa jikinsa, ta ce, "modebbo ka taimakeni tafiya takemin, sai asanan kuluwa tai saurin cire ďankwalinta ta ďaura mata a'kafar.
Nawaf ya rungumota zuwa jikinsa yana share mata zufar, yana faďin sannu kinji yi ha'kuri, salmanu yazo yasaka mata magani, sai sannu suke mata, aka zuba wani aruwa aka bata tasha, dandanan zufar ta 'karu, salmanu ya ce, "yaya ka ďauketa kujecan zata faďi insha ALLAHUi.
Nawaf ya ce, "to, cak ya ďauki yasmeen zuwa 6angarensu, suka rakasu da ALLAH ya kiyaye gaba.
Saman katifa ya direta tanata zufa, ya ce, "sannu".
Ta kaďa kai tana hawaye.
Ya ce, "haryanzu tana miki yawon??, tace ba sosaiba amma.
insha ALLAHU zata daina gaba ďaya, bari acire miki waďanan kayan kinga kinata zufa, batareda yajira amsartaba, yakama zip ďin ya sauke zuwa 'kasa, yasmeen ta rintse ido tana huci, yakama bra ďinta xai cire, da sauri tajuyo tana kallonsa, shima kallonta yakeyi, amma yaďan ďaure fuske, ya ce, "kafiya??".
Cikin rawar murya ta ce, "plz kabarsa kawai, ya ta6e baki yana faďin keni bana son iyayi, bakida lafiyarma saikin jawo munyi, ko ba'kya ganin zufar dakikeyine??,.
Ta ce, "to kafita zan cire da kaina nidai.
Tsaki yayi saidai idan bazaki cireba kuwa, dan wlhy babu inda zanje.
Ta ce, "to maidamini zip ďin rigata, tunda ni yaronkine ba, yafaďa yana kwanciya.
Hijjabi ta jawo tasaka, sanan ta cire rigar, taja zaninta zuwa sama, yana kallonta tana ta zufa, ya ta6e baki, daga nan ya ďauki wayarsa yana danne2nsa, sai wajen karfe goma kunamar ta faďi, yasmeen ta mi'ke waizata tayi wanka.
Nawaf yashiga tuntsura mata dariyar mugunta, cikin jin haushi ta ce, "malam lafiyarka kuwa??, Nawaf yacigaba da dariyarsa batareda ya kulataba, harta kai 'kofa zata fita, ya ce, "wlhy kije kiji'ka tadawo sabuwa, kezakai sha wahalarki ke kaďai, danni ficewata zanyi nabar miki ďakin wlhy.
Ita sai yanzuma tatuna idan kunama ta harbeka ba'a saka ruwa, tadawo bakin katifar ta zauna ta rabga tagumi.
Nawaf yacigaba da dariyarsa ta rainin hankali, itadai banza taimasa ta'ki kulasa.
Yafara faďin modebbo ka taimakeni tafiya takemin.
Tagane kwaykwayon muryarta yakeyi, dan haka ta harareshi tana murguďa baki, ya ce, "yarinya ashe zaki sake shan wata wahalar wlhy.
Ta ce, "wlhy saidai musha, dan ba 'kyaleka zanyiba, yatashi daga kwanciyar dayayi, ya ce, "sake murguďa wannan bakin maikama da na tsintsaye kigani.
Saida tazamo daga katifar sanan ta murguďa😏.
Tami'ke da sauri, zata gudu, taku ďaya yayi ya dam'kota, yamaidata saman katifar, saman cikinta yahaye, yakama fuskarta da hannu biyu, ya haďe bakinsa da nata yashiga kissing ďinta.
Itako sai mutsu2 take nason ta kwace amma takasa, gashi ya danne mata ciki, saida yayi mai isarsa sanan yasaketa yana maida numfashi, tabirkice zuwa rubda ciki tana kuka, tana tofar da yawu, 'kazami kawai, zakawani ta bani yawunka inasha, sai ALLAH yasaka mini wlhy.
Kusada ita yakwanta, yadafa bayanta, 'yammata gobema ki 'kara yimini murguďa baki ki gani, saina miki abinda yafi haka, ya 'kare maganar yana dukan bayanta.
Ta mirgina 'kasa tana cigaba da goge baki da hijjab, Nawaf kuma yana mata sassanyar dariya, yajuya ya kwanta yana murmushi wanda shi kansa baisan na miyeba, a hankali yafurta 'yar rigima.
Saida taga yayi barci sanan tadawo saman katifar, takwanta agefe nesa dashi kamar yanda tayi jiya.
Washe gari tunda safe saddiqu ya wankema Nawaf motarsa, zuwa 'karfe goma suka baro 'kauyen cike da kewar muta nan garin, masu kirki da karrama ba'ko, yasmeen harda hawaye.
Suma 'kyauyen sun tafi sun barsu da kewarsu.
A safana suka yada zango, gidan wani abokin papa, nanma sun zaga dangi, ananma yasmeen taga 'yammatan dasukaje bikinta dayawa, sunyi farincikin ganinta itama haka.
Anan batare suka kwana da Nawaf ba, aďakin matar abokin papa ta kwana, shikuma ďakin ba'ki.
Washe gari suka haďa inasu2 suka garzayo kano, cikeda uwar tsaraba, yasmeen takali Nawaf daketa wani ďaure fuska, ta ta6e baki tana faďin mutum tamkar mai aljanu, yanzu zaka gansa yana dariya, yanzu zai ďaure fuska kamar rundunar sojoji, har suka iso kano basa wata hirar arzi'ki, saidai ita dake tambayarsa sunayen garin dasuke wucewa, ada'kile yake bata amasa, itama daga baya saita kulle bakinta gam.
Dahaka suka iso kano, cikin farinciki su momcy suka taresu, momcy ta ce, "ďiyata kinyi ba'ki wlhy, yasmeen tai murmushi tana sissine kai, hajja ta ce, "Nakuwa haďa muku abinci mai daďi na tarba, dan haka saiku shirya ci.
Nawaf ya ce, "kai hajja da kanki, amma kinyi 'kokari.
Ta ce, "nayi kewarkune shiyyasa.
Nawaf ya ce, "to mungode miki hajjarmu abin alfaharinmu.
Yasmeen ta ce, "momy wai ina su Anwar???, suna islamiyya fateema, amma nasan suna hanyar dawowa, dan tun safe ake shirye2 dawowarku.
Yasmeen tayi murmushi tana faďin ALLAH yadawo dasu lafiya...................✍🏻



Assalamu alaikum
Nagode da sakwanin gaisuwarku gareni, harma waďanda basu sami damaba,,,,, happy juma'at khareeeeem! !!!
Luv u oll😘😘😘😘❤❤



©2016



💞bilyn Abdul💞
💞Mrs Abdus'salam💞
💞luv u oll my fan's😘💞
[1/12, 8:59 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾 NAWAFF 🎾
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM💞



Page👉🏻35 & 36

......Tunda suka dawo basa shiga harkar juna, sun koma zaman doya da manja, gaisuwa ce kawai ke shiga tsakaninsu, saikuwa girki da yasmeen zatayi, yazo shikuma babu kunya yaci.
Abin yana bama yasmeen mamaki, idan ta tuna abinda Nawaf yarin'ka yimata a safana, takai dubanta ga 'katon hoton Nawaf dake falon, yana sanye cikin jan jc yayi 'kyau sosai, afili ta ce, "mutun 'kya'ky'kyawa a waje, amma azuciyarsa yafi maciji mugunta, ta gallama hoton harara.
Nikam danake gefe na tuntsure da dariya, dan tabani dariye, kome hoto yay mata??.
☆ ☆ ☆ ☆
Ayaune kuma hajja zata lula saudia, fuskar kowa ka kalla a gidan babu walwala, amma babu yanda zasuyi, haka sukai gayya suka rakata airport Anwar sai kuka yake wai saiya bita, papa ya ce, "yabari ayi hutu saiya tafi, hakadai suka dawo gida kowa yana zum6ura baki.
Yasmeen ma dabata daďe da sanintaba saida taji babu daďi, dan hajja tsohuwace mai shiga rai, ga kirki da son mutane, lallai anan momcy ta kwaso 'kyawawan halaye, to saimuce hajja ALLAH ya kiyaye hanya.
Tunda suka dawo daga 'kauye yasmeen batada cikakkiyar lafiya tana 6oyewane kawai, amma yau dole ta kwanta, shi oga Nawaf ma bai saniba, dan yanata hidimar komawarsa Spain.
Saida momcy taga har la'asar yasmeen bata shigo wajensu ba sannan, tafara tunanin ko lafiya, ta mi'ke ta nufi 6angarensu, babu kowa a falon saidai an gyarashi tsaf yanata 'kamshi, kai tsaye bedroom tawuce, da sauri ta 'karasa bakin gadon domin ganin yasmeen a 'kudundune cikin bargo.
Momcy ta zauna agefen gadon taďan ďaga bargon tana faďin ďiyata kina lafiya kuwa?....ta 'karashe maganar a ahankali, danjin zafin zazza6i a jikin yasmeen.
Dan danan momcy ta ruďe tashiga tambayar yasmeen tun yaushene batada lafiya?, yasmeen ta buďe ido da 'kyar, ta ce, "momy tunda daddarene.
Cikin damuwa momy ta ce, "amma shine baki faďaba?, ina modebbo??.
Yasmeen ta ce, "yafita tunda safe.
A'a, baisan bakida lafiyaba ne??, yasmeen ta daga kai alamar eh.
Waya momcy ta ďauka takira Nawaf, modebbo kana inane??, Nawaf ya ce, "ganinan zuwa gida ma.
To saika iso momcy tafaďa.
Abinci mai sau'ki momcy tasaka su talatu su dafoma yasmeen, ta taimaka mata tayi brosh da wanka dantaji daďin jikinta, tana fitowa Nawaf yana shigowa, tayi tsaye kamar gunki shima tsayen yake yana 'kare mata kallo, dan sukaďaine a ďakin, momcy tana falo.
Da sauri yasmeen taja hijjabin sallarta ta kudundune aciki, baki Nawaf ya ta6e yana wani yatsine fuska.
Itakuma tawuce ta zauna bakin gado, momcy tashigo da sallam tareda talatu.
Sai asannan Nawaf yazauna akan kujera, momcy ma ta zauna talatu kuma ta ajiye abinda takawo ta fice, momcy ta ce, "ďiyata saboda mi baki gayama mijinki bakida lafiyaba?, dan ya ce, "mini shima bai saniba.
Saida yasmeen ta kalli Nawaf sannan ta ce, "banaso hankalinsa ya tashine.
A'a wanan ba hujja bace, yaza ayi ki zauna da ciwo saboda kar hankalin mijinki yatashi, daga yau karki sake kinji ko?, yasmeen ta ce, "to momy insha ALLAHU baza'a sakeba.
Nawaf ya ce, "momcy bari na kira mas'ud yadubata, dan naga bai fitaba.
To, yakamata kuwa.
Momcy dakanta ta bata abincin taci, sai yatsine fuska takeyi, ahaka su Nawaf suka shigo suka isketa, mas'ud yay mata sannu, tana gama cin abinci ta tashi da gudu ta nufi bayi, amai ta ringa zazzagawa kamar hanjin cikinta zasu fita, momcy tabiyo bayanta dasauri, ta taimaka mata hartagama tagyaramata jikinta, sanan suka dawo ďaki.
Su Nawaf suka shiga yimata sannu, ahankali take amsawa, tahau gadon ta kwanta, momcy ta ce, "mas'ud ai inagama wanan ciwon na yasmeen baya bu'katar gwaji.
Mas'ud ya ce, "momcy saboda mi??, momcy tayi murmushi tana shafa kan yasmeen ahankali, ta ce, "mas'ud inaga lokaci yayi dazamuga yara suna tsalle2 agidan nan.
Nawaf da mas'ud suka kalli juna cikin zaro idanu.
Mas'ud yadaure ya ce, "dukda haka dai momcy barina dubata, saimuga maganin daya dace abata.
Momcy ta ce, "to zoka dubata, ta tashi takoma kusada Nawaf daya shiga cikin waswasi da faďuwar gaba, momcy tadafa shi ya ďago da sauri yana kallonta, saikuma yamaida da kai 'kasa da sauri, momcy tayi dariya tana faďin modebbo yaukuma kunyata akeji??, ai wanan abin farincikine.
Nawaf ya daure ya ce, "momcy bafa ciki garetaba, ciwone kaiwai nake gani.
Mas'ud ya katse musu hanzari da faďin bari naje nayi text daga nan asamo mata maganin daya dace.
Nawaf ya mi'ke yana faďin muje tare, momcy tabisu da kallo tana murmushi.
Suna fita mas'ud ya tuntsure da dariyar mugunta, Nawaf yabishi da kallon mamaki, kai wai lafiya?, ko ciwon haukane yasameka yanzunnan?.
Cikin dariya mas'ud ya ce, "mutumina aikaine lamarin naka yay kama da abin dariya, wai yaushe akaje wajenne??, har saka mako yafito?.
Nawaf ya yatsine fuska yana faďin ban ganeba?.
Mas'ud ya haďiye dariyarsa, ya dafa kafaďar Nawaf yana faďin abinda nake nufi ai afili yake malam.
Nawaf ya ta6e baki, kai nifa abinda kuke zargi daga kai har mom ba haka bane, babu wani ciki da yarinyarnan take dashi.
Mas'ud ya ce, "ban ganeba kai kana nufin yasmeen batada ciki, harara Nawaf ya sakarma mas'ud, to ana shan cikin aruwane dazakace wani baka ganeba, kainifa wlhy babu abinda yashiga tsakanina da yarinyarnan.
Taf ďijan inji mata, mas'ud yafaďa, to malam momcyfa jika suke so, dan nakula tana cikin farin ciki, amma gsky wannan ba dabara bace, idan kai zaka iya jurewa ai ita kana shiga ha'k'kinta ko??.
Tsaki Nawaf yayi, yana faďin matsalarta ce, nibabu wani ha'k'kinta dake kaina malam kaji.
Dariya mas'ud yayi, humm Nawaf kenan, akwai lokacin dazai zo, kazo neman shawarar hakan agurina, kuma wlhy tanada ha'k'ki a wajenka, kaima kasani sairai, saidai katake sanin,.
Hhhhhh ashe shekarun dayawa kuwa, Nawaf yafaďa.
Dahakadai suka 'karasa asibitin, bayan sunyi duk abinda yadace suka dawo gida da magunguna, amma dai text yanuna ba ciki bane.
Koda suka gayama momcy saitace, babu komai shima cikin yana zuwa insha ALLAHU.
tunda yasmeen tasha magani take barci, bata farkaba sai cikin dare, tajuya taga Nawaf agefenta kwance yana kwasar barci, ta lumshe ido ahankali ta sake buďewa, sakkowa tayi tashiga bayi tayi wanka dan jikinta duk ciwo yakeyi.
Jin motsin ruwa yasa Nawaf farkawa shima, ya laluba gefensa saiyaji babu yasmeen yatashi yanufi bathroom ďin, ahankali ya tura 'kofar saiyaji ta a buďe, yako tura kai cikin bayin batareda neman iziniba.
Dasauri yasmeen tajuyo danjin motsi, ta kwalla 'kara dan ganin Nawaf tsaye yana kallonta, ta rarumi tawul ta 'kudundune jikinta.
Da sauri Nawaf ya'karaso gabanta yana faďin "k dallah karki taramin mutane.
Da'karfi ta ce, "to kafita mana, miye haka zaka wani shigo mini ina wanka.
Tsaki Nawaf yayi ya ce, "ubammi zan kalla ajikinki, aikin banza kawai, yafaďa yana ficewa.
Yasmeen tazauna jagwaf tana maida numfashi da'kyar, ta runtse idanu gam tana hawaye.
A6angaren Nawaf madai hakan take, jagwaf yafaďa saman gadon yana fitar da huci mai zafin gaske.
Yasmeen tadaďe bata fitoba, saida ta daidaici Nawaf yayi barci sannan tafito, ta saka riga mai ďan kauri ta kwanta saman kujera.
Nawaf yana kallonta, yaja Numfashi ahankali, gsky shikam yana bu'katar matarsa, amma yarasa hanyar dazaibi yacika burinsa, dawanan tunanin barci yakwasheshi ___________________________________ haka rayuwa taci gaba da gudu da sauri, Nawaf yanata shirin komawa Spain.
Yauma yana wajen papa suna tattaunawa, papa ya ce, "yanzu idan katafi sai yaushe??.
Nawaf yay 'kasa da kai yana faďin papa da'an gama kakar wasanni insha ALLAHU zamuzo hutu.
To shikenan, ammafa idan kadawo da matarka zaka koma, dan bai daceba ace kana can matarka tana nanba, tunda kana daďewa baka 'kasar.
Kan Nawaf a'kasa ya ce, "to shikenan papa, ALLAH yakaimu lokacin.
Papa ya ce, "amin.
Daganan Momcy tashigo itama suka cigaba da tattaunawa, sun daďe suna hira saida papa ya ce, "yatashi yaje wajen matarsa, Nawaf yami'ke badan yasoba yatafi.
A falo ya isketa tana waya da umma tana hawaye, ya zauna kujerar dake kallonta jiki a sanyaye, itako bama tasan ya shigoba, tacigaba da wayarta, umma wlhy iya gsky ta nake gaya miki, nikam nagaji wlhy.
Tai shiru zuwa wani lokaci, tasaka hannu tana share hawaye, ta ce, "to shikenan umma nagode sosai, to ALLAH yakaimu.
Sai asanan takula da Nawaf, ta kauda kai daga kallonsa.
Nawaf ya ce, "k dawa kikeyin waya?, kuma wayace ki ďaukarmin wayata kiyi kira?.
Banza tayi masa kamar batajiba, tamaida kanta tsakanin cinyoyinta tana kuka, haushi ya tokare ma'koshin Nawaf, jiyake kamar ya doketa agurin, dan bayason kuka musamman kukan mace, yami'ke cikin haushin rashin amsa masa maganarsa datayi, kujerar datake zaune yadawo, yasa hannu yaďago fuskarta.
"K!!! Wai wane irin iskancine zaki zauna kinama mutane kuka, kamar wadda akaima wani abu, kuma kinaji ina tambayarki amma kikayimini banza.
Cikin rawar murya ta ce, "tomi kakeso nace maka?, aidai kasan babu wanda zankira a wayarka sai 'yan gidanmu ko, kuma aiga wayarnan kaďauka kakira number dana kira saikaji waye??.
Kuma wayarka dake faďin wayace na ďauka, kai wayace ka fasa mini tawa wayar??.
Nawaf ya zazzaro idanu yana faďin "k!! Wlhy ki kiyayeni, kar 'kuruciyar ki tajaki ki ďakko mini zancen wani 'kato anan, dan wlhy zan iya zaneki!!!.
Yasmeen ta tsorata da Nawaf sosai, amma bataso ta nuna masa tana jin tsoronsa, dan zai samu lagontane.
Itama ta zazzaro nata idanun, ta ce, "aikai kajika, sai ba'kin kishin tsiya, wlhy kayi wasa sai zuciyarka ta tarwatse abanza, nikam an cuceni wlhy da aka haďani aure da kai, shiyyasa bazan ta6a sonkaba kuwa har.........
Kafin ta rufe baki ya matse bakinta da 'karfi, yasa ďayan hannunsa ya matse gashinta, ya ce, "k!! karki ďauka kishi nake akanki, karki ďauka nima zan soki, dana soki gara naso dijangala, domin koba komai 'yar uwatace, inada waďanda suka fiki komai dayawa yarinya, ki kalli ummu habiba, yarinya 'kya'ky'yawa jinin larabawa, mai ilimin addini dana boko, akwai irinsu dayawa dasukeson na kasance mijinsu, tundaga turawa har ba'ka'ken fata, dan haka ki daina ďaukar kanki "k wata tsiyace awajena.
Ya fisga gashin sanan ya hankaďata ta bigi kujera, yabuga yatsun hannunsa biyu yana faďin "k ba komai bace, face 'yar aiki, mai jiran tsammani, ki ďauka darajar iyayenace tasa nake zaune dake, kuma ina ganin mutuncin iyayenki, domin muta nen kirkine, amma daba hakaba hummmmm ya 'karashe zancen acikinsa.
Yasaki bakinta yashige bedroom, sai asannan tasamu damar yin kuka, takoyi kuka mai isarta harta koma bani tausayi.
Ranar afalo ta kwana,.
Washegari Nawaf tunda yafita daga gidan bai dawoba sai dare.
Afalo ya isketa zaune ko kallo bai ishetaba shima ďin haka, yay wucewarsa bedroom.
Tsaki yasmeen taja tana faďin mugu kawai mai ba'kin hali, koda yashiga ďakin kayansa yashiga haďawa dan gobe zai ďage zuwa Spain, amma bai sanarma yasmeen ba.
Yagama haďa komai sannan ya kwanta yana tunanin yanda zaiyi da yasmeen dan shidai bazai sanar mata zai tafi gobe ba, kuma bayaso papa ko momcy suji cewar bai sanar mataba.
Yajawo ledar daya shigo da ita, yaciro wata haďaďďiyar waya akwali, yabuďeta ya'kare mata kallo, sannan ya ďakko biro da takarda yafara rubutu📝yagama ya ninke yasaka acikin wayar ya ajiye yay kwanciyarsa.
Saikuma wata dabara ta faďo masa, yaďauki waya yana surutu kamar yanayi dawanine, harfalo yafito yana faďin karka damu insha ALLAH gobe zan iso Spain, zan biyo jirgin 'karfe bakwai nasafe da ixinin ALLAH.
okey babu damuwa nagode zataji saina iso.
Yasmeen tanajinsa, sai abin yabata mamaki, wai kana tareda mijinka amma yagagara sanar dakai zai tafi, wanan wace irin rayuwace, wasu hawaye suka wanke mata fuska, shikuwa tuni yakoma bedroom abinsa.
Haka takwana rabi barci rabi tunani, aiko dasafe ta makara, sanda ta tashi 7:30am tadiro dasauri daga kujera tanufi bedroom wayam tagani Nawaf yatafi, hawaye suka shiga yimata ambaliya a fuska, jiki asanyaye tayi alwala tayi sallar asubahi.
Tana zaune saman sallaya momcy tashigo, yasmeen taďago da sauri tazata Nawaf ne saitaga momcy, batasan sanda sabon kuka yazo mataba.
Momcy tazauna ta rungumota zuwa jikinta tana lallashi, yihakuri barkuka, shiyyasa mijinki ya ce, "kar'a tadaki daga barci, dan tunjiya kike kuka, to kiyi ha'kuri aiba daďewa zaiyiba zai dawo, kuma idan yadawo tare zaku koma kinji.
Azuciyar yasmeen ta ce, "wato 'karyar daya shirya muku kenan?, ba komai zanyi maganin shi dakaina agidannan, komai yanada lokaci, nasan nima nawa lokacin yana zuwa.
Nan momcy tayita lallashinta, daga 'karshe ta ce, "idan kinajin tsoro kishirya kayanki, ki koma ďakina, idan yadawo saiki komi nan kinji, idan kuma ba'kyajin tsoro tokiyi zamanki anan ďin.
Da sauri yasmeen ta ce, "momy zanbiki can.
Toshikenan tashi ki shirya kayanki kinji, bari na turo miki Anwar yatayaki ďauka, ta ce, "to.
Ta shirya duk kayan dazata iya bu'kata, sai asanan taga ledar daya ajiye, yarubuta nakine idan kina bu'kata.
Kai kawai ta girgiza taďauki ledar tasaka cikin kayanta, Anwar da Abdallah sukazo suka tayata ďaukar kayan, suka kashe duk wani kayan wuta na wajen, suka rurrufe ko ina.
Tundaga ranar takoma ďakin momcy da zama, tanajin daďin zaman, saidai tunani Nawaf da kewarsa duk sun addabeta, har takanyi mamakin kanta, yanda tadamu da mutumin dabai damu da itaba, wanda bazaman lafiya sukeyiba sanda yana nan, taja 'karamin tsakai tareda gyara kwanciyarta, 'kilama shi yamanta dawata halitta yasmeen.
Tasan Nawaf bazai ta6a sontaba sai wani abu ga ALLAH, wanan kuma ikonsane, yakan aikata duk yanda ya so, alokacin daya so.
________《》__________
To shimadai Nawaf hakan take agareshi, tunda yasauka 'kasar Spain bashida wani sukuni, tunanin yasmeen duk yacika masa zuciya da ruhi, bashida aiki sai tunaninta, yakanyi dariya idan yatuna wani faďan nasu, yayi waya da kowa nagidan amma banda ita, yatambayi Anwar ya ce, "baiga ta haďa wayar daya saya mataba.
Yana matu'kar bu'katar yin magana da'ita amma yarasa hanyar dazaibi.
Ya lumshe manyan idanunsa masu haske, ya maida kansa jikin luntsume miyar kujerar dake falonsa yakwantar, tabbas yasan yafaďa tarkon son yarinyarnan, kuma yalura ita bata 'kaunarsa, haushinsama takeji, saboda har yanzu soyayyar tsohon mijinta tana tareda ita.
Ya'karashe maganar kamar xaiyi kuka, yashiga girgiza kai yana faďin A'a FATEEMA ZARAH karkimin haka, nine kawai yadace ki so, domin dani kika dace, jiki yana rawa yaďauki ďaya daga cikin wayoyinsa yashiga kiran Anwar, harta tsinke ba'a ďaukaba, yatuna yanzu yana islamiyya wajen karatun dare.
Yamaida akalar kiran zuwa Abdallah shikuma tashi akashe, yayi tsaki, saikuma yakira momcy, bugu ďaya biyu ta ďauka, bayan sun gaisa yatambayi lafiyar kowa.
Ta amsa dakowa yana nan lafiya, ya ce, "masha ALLAHU haka akeso, yanaso ya ce, "tabama yaameen amma yanajin kunya, dan haka sukayi shiru suduka, momcy takatse

Please Login or Register in order to submit comment