Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ni na dauke masa yarinya ne amma me dan na aika masa da abin alkairi zaice sai nazo yaganni Sani yace "haba yallabai taya zai gane bayan bawan da yasan wanan sirrin sai ni sai ku kawai alheri ne yaga yayi yawa kafasa masa gida za amasa ginen zamani ka dauki nauyin matar sa za amata aikin ido a kasan waje kaga ai dole yanemi waye ya masa wanan abin alkairin ai Nabil yace" to yanzu wannan har yakai yace muhadu agaban sarki SHEHU nema nafa yayi afada ina tsoron ace yasani fa kasan Malaman nan fa anya ba istahara yayi yagani ina tare da yarsa ba shikan isan da yatuno da haka sai gaban sa yayi wani irin faduwa har sai da yaji hanjjin cikin sa ya muda..... *Muje zuwa* *Me zannah zai* *cewa Nabil* *Nabil zai samu* *daman lalabawa yaje Landon kamar yanda yatsara* *B JATTKO* [12/15, 8 PM] ‪+234 902 426 6343‬: *DAMA TA* *NA* *BATUL ADAM JATTKO* *Mmn Waleeda* *Ina miki fatan* *alkairi da fara wanan kaya taccen* *novels naki* *YAROMA NAMIJINE* *ALLAH yasa agama cekin sa a* _Godiya nake_ _Marya_ _Ummiee_ _H Bilkisu dan mlm_ _Amal biebie_ 🤝❤ 🌈Kainuwa writers Asso🤝 *25* Sani mai da hankalin sa yayi kan titin yana cewa "insha Allah ma yallabai ba hakan bane ma haka suka karasa cikin sheuri daga shi sai sani amma da motocin security dinsa suke binsa abaya dan idan zaije irin wanan wajen da security din sa yake fita suna kara sawa fada dogarai da mutane cikin fada harma da yan sarautan ma kowa iban gaisuwa yake a wajen *Shidmas* Dogare sai washe baki suke dan wanan ganin suke cewa farin gani dan ganin Nabil fari ganine cikin kasaitar sada iya rike girma yafito yana daga musu hannun biyu biyu sai kirari dogarai suke masa yaro da kudi abokin manya mekyu d kyun hali makiyan fadawan ka aljanin kudin dan Habubakar jikan DAMASAK har suka shiga ciki direct cikin fadan suka Nufa sai da suka kai inda yaka mata su tsaya suka ja burki security din har zasu bishi ya daga musu hannun cak suka tsaya daga shi sai sani suka shiga wanda yafara cingaro da shisai da gaban shi yayi mugun faduwa wato Malam Zannah Modu sai yau yagan shi ido da ido dan dama wani lokaci yana ganin sa a TV suna mugun kama da Fandau Zubewa yayi agaban su yana kwasan gaisuwa dan da hakimai da sauran yan kusa da fada suna nan lawuwan girgiri ne yafara magana yace a a manyan gyaran wasa Muhammad Nabil hasken Barnawu SHEHU murmushi yayi yace dana yaushe kazo garinne sai jiya Malam yake cewa wai wani ya tura turawa gidan sa sunyi aune aune sannan yaturo wani har sun fara gini anfasalta tsarin part na mata acikin gidan inda ake karatu dare wai matan sa ake ginawa idan aka gama sai sukoma ciki da kuma wasu manyan kudi shine yake sanar dani da ga gomnati ne ko meye muka binci ka ba daga gomnati bane Shine ya da katar da aikin dan Malam yace bayaso sai yasan wannda yayi masa tukun shine da wannan yaron naka yaje duba ma aikata nace akawo min shi yana zuwa naga yaron kane dan nagane shi nace yace maka kazo kugana da Malam din mana shima kansa Malam kaine baka sani ba kodan bakayi rayuwan nanba ai mutumin baban kane sosai Gashinan matsa kusa dashi kugai sa Nabil tashi yayi cikin baduwar gaba ya karasa inda Zannah yake ya zube guiwowun sa yace Baba barka da warhaka Dafa kansa Zannah yayi yace "modu kaine haka kai kazama haka Nabil ya daga kai ya kalle Malam ya sake sunkuyar wa Zannah cigaba da cewa ni ban sankai ne meyin wanan a bubuwan ba duk sunbi suncan zamin sunan ka wani shidmdas wanan sunan kawain nake ji ana cewa me kyauta to dana jin ace dan kwallone ban damu na bin cika nasan waye ba ana fadan alkai randa kakeyi abin da yafi burgeni shine daukan dauyin yan shijira da kuma bada tallafi magani ga mata masu ciki da kananan yara da ka dauki nauyin bazan manta ba lokacin da aka fara daukan ka kwallo saida na kira Habubakar nace bakyu wasan kwallo ya hana dansa amma da yake anan abin cinka yake dana kuma na al umman da ka dauki nauyi kaga bai hanaka ba yanzu nima nabin cika naji boll ba haramun bane inde zaka tsare mutumci adi ni Alhamdulilah naji ance kana da kishin addinin ka Kuma nima na sheda Allah yamaka Albarka duk wajen suka amsa Ameen Ameen Ameen Nabil sake dunkufar da kansa yayi Azuciyar sa yana cewa _Da gasan mena maka da bakamin wannan sa albarkan ba_ Bayan anga ma wasu tattaunawan Malam yace" kiramin Habubakar din Nabil ya dauko wayan sa yakira abban sa yame kawa Malam abba yace "Nabil fasa tafiyan yau din kayine Zannah yayi murmushi yace "wannan baban Nabil ne abba ko daga Baccci aka tashe shi zaigane muryan malamin sa kuma uban gidan sa zannah modu Kamar yana gaban sa sai na yadan rissina yace"gafanta ina wuni ya fama da jama a Malam yace "Alhamdulilah yau gani ga dana ko jika zancene kuma me sunana Cikin zunudi da murna abba yace duka duka zaka kirashin gafarta dan yaji dadin kiran Nabil da yayi da me sunan sa dan Nabil tabbas me sunan zannah ne Zannah yayi murmushi yace"idan ka samu lokaci kazo inada magana da kai Abba yace malam daga yanzu zuwa lokacin da kake son gani na duk lokacin kane yanzu kake son kaganni Malam yace "Eh to kazo yanzun Nabil _azuciyar sa yace meyake faruwa yau dan ma abba yasan mutu minnan haka anya ban shiga ukku ba_ Malam yaka shi wayan yame kawa Nabil Malam ya juya yana kallon SHEHU yace to *alguro* nizan wuce gida da dan nawa zan tafi dan zamu hadu da Habubakar a can malam yata shi SHEHU ma mekewa yayi shida sauran hakimai da sauran su dan girmama Zannah modu dan yana da girma sosai awajen ko wada yake cikin meduguri Ai Nabil kasa tashi yayi dan shi har yanzi bai yarda Malam bai san komai ba da idan baya sani ba na meye zaice wani sai yaje gidan sa kuma ma yakira abban sa Zannah ne yaka ma hannun sa yace "taso ko ka tsaki jikin ka zaka yi mamaki idan kasan nidin waye a wajen ka yaro ai Nabil jiyayi ya koma yazauna jabar atake wani irin gumi yafara sassafo masa zannah yasa ke sa hannun ya da gosa yace muje shiko Sani dan karewa yayi awajen aiko suna fita Sani yayi hanyansa ya lalaba yafice zannah yana rike da hannun Nabil din harsu ka karasa inda moton zannah yake driving sa ya bude musu suka shiga dogarai da sauran mutane sai cije hannun suke dan sunyi mugun sa raida abin da Nabil zai basu har suka fice basu dina hangen moton ba ga ba daman tambaya ko yimasa kirrari ga SHEHU nan ko idan SHEHU yana waje ba ayiwa kowa kirari SHEHU yarako Malam ne Nabil tsumu yayi a moton zannah kaman anka kamo barawo _Koda yake nide a gani na kamun barawon yaka mata a masa ranan da a sirin ya saya tonu_ Har suka karasa kofan gidan zannah zannah ne yafara fitowa Nabil yana ciki driving yazo yabude masa amma yakasa fitowa Malam ya leka yace "fito mana modu Nabil yace "ina tsoron nafito ne saboda yanzu mutane idan sunga ni zasu cika gidan baza su bari muyi abinda yakawo nin ba Malam ya huya yabawa driving umarnin abude get dan a shiga da Nabil ciki ai hakan akayi bangaren Malam sukayi shikam ba ataba shiba dan ginin zamani ne ba abin da babu dan governor ne da kan sa yasa aka rushi aka masa gini part din sa shikaru 2 da suka wuce malam yazauna a kasa akan wani kaya taccen Capet dinsa da Nabil har yanzu bai saki hannun nasa ba Suna zama ABBA yana shigowa abba zubewa yayi yana kwasan gaisuwa cikin girmamawa Malam yake amsawa cike da fara a irin nasa Malam yayi gyaran murya yace abin mamaki kazo kasame nida Me sunana ko abba ya gyada kai to yanzu na dawowa da shi yakoma me sunana kamar yanda yake da Habubakar kaya femin magan ganun da nayi akan ka mesunana a yanzu nabin cika na kuma gane ball sana ane ide zaka kare addini ka ayanzu nake son ka gayan wa Nabil waye ni da dangan takarmu. abba sai da yabari Malam ya gama maganan sa, Shima cikin adabi ya fara magana yace "haba Malam yaza kace min na yafiya maka bayan nine me lefin da shekara da shekaru kunya ya hana ni neman yafiya kabari bana ni nane ma kai din tam kar ubane awajena dan ni uban ma ban shaku dashi kamar kai ba ni zanne mi yafiyar rashin min umarnin ka danayi na bijirewa umarnin ka abba yakalli Nabil da sai faman zare ido yake yace "Nabil wanan shine malamina awajen sa nayi duk maratu na shine yane mamin auren fari da nabiyu kuma shine me sunana ka amma tunka na dan shikara 4 yace na basa kai za afara koya maka karatun allo to ni kuma ganin kaine Babba na kwallafa rai azakayi bokon ban bashi ba saima na dena kawo ka dan hutun da nake dan kawo ka dan yadena min zancen aiko yadena din yaga bana son zancen sai yabari, Karin riki cewan abin de lokacin da yaji kana ball ne yakirani yace na hana ka nace masa to amma ban hana ba kwatsam yaji zancen andau keka an kaika England makarantan koyan ball Aranan naga bacin ran malam dan kasan yanda Malamai suke kyaman ball aranan yace idan nasa ke dan ganta ka da sunan sa bai yafe min ba kuma kar na nuna maka hanyan gidan sa, Kai kadai ne baka san Malam ba amma su kamal yan gidan nanne sosai haka su ummin ka Kaima rashin zamane dana san koda baka zodin kamar yanda Malam ya hana nasan zaka san dangan ta garmu amma ina maka murnan sa santawa da me sunanan dan kasamu jagora mana garci idan ka sabawa umarnin sa bazan yafe maka ba dan nima shiya zaman ubana Ya huya ya kalle Malam yace "Malam kayi hakurin na rasa wani dalilin ne yasa na kasa bin umarnin ka akan hana Nabil ball Murmushi Malam yayi yana dafa kan Nabil da yara sa duniyan da yake ma Malam yace "dalilin da rabon Albarka acikin sana ar mana gashi yadauki daushin al umma da dama dana hana ai hakan bata faruba Allah yakara daukaka Muhammad Nabil ABBA yace Ameen _Nabil yayi shiru azuciyar sa yana cewa da kasan mena maka da baka zauna zaman samin albarka ba_ Daganan suka shiga fira da Abba shide Nabil yana zaune ne kawai abba yace "bari nashiga mugai sa da su Bagaji Malam anan yake gayawa Abba abinda Nabil yayi na gyaran gidan da kuma sawa dayayi za akai Aisa wato maman Fandau India dan amata aikin ido Abba rungume Nabil yayi yana masa godiya dan atunanin Nabil danshi yayiwa mal wanan abin Shikon Nabil dadi yaji dan bai taba gani farin cikin awajen Abba haka ba dan yayi abin alkairi Nabil yayi mamakin girman gidan dan part 4 aka fitan na mata wana buyu suna kallon juna buyu ma haka tsarin ginin da girman kowane ban gare ya burgeshi dan turawane suka fasalta bangaren matan sa nada yananan ko taba wajen ba ayin ba Nabil sai mamakin girman gidan yake dama acikin garin ana samun irin wanan girman gidan har suka karasa ban garen matan wanda suke cikin ginin ajere reras kamar islamiya dakunan 4 da duguwar baranda kowa yana saf gan gaban sa su bagaji da bafanta suna ganin abba suka fara washe baki dan sunsan yau zasu sha raban naira Duk a tsakar gidan suka gaisa da sauran matan mama ce kawai basu gani suna ta tambaya sa ya Hajja bintu da Hajja Hajara yace lfy Bafalta ce tace Alhajji kowannan shine mesunan Malam yace "shine aiko sai sabon gaisuwa yaran da sauran mutanen gidan wanda suke daki m a sai suka fito dan kallon Nabil Abba bai ga mama ba ya tambaya sukace tana daki kai tsaye Abba yatufi dakin dan yana ji da Aisa duk da sai da yayi aure mada dadewa aka auro ta Tana zaune kamar kullum ita daya dan Bagana da take e be mata kewa anyi auren ta wata daya da yawuce da shateema tana jin sallaman sa ta juyo kamar me gani tana murmushi tace a a Alh Habubakar ne yau agidan namu yace nime harda megidan ki Nabil Mama ta meka hannun tana laluman ida suke tana cewa megida matso nagan ka rabuna da kai tun ina daukan ka akan cinyana daya ke lokacin da ake kawo Nabil mama amarya ce tana da son yara dan ta dade bata samu haifuwa ba idan aka kawo Nabil jitake kamar kar azo daukan sa ita ta matsawa Malam ma akan yace sai anbashi Nabil din Abba yace "jeka wajen ta wannan mamar kace ita take renon ka kana yaro ba irin ta adin da baka mata ba Cikin sanyin jikin Nabil ya karasa inda mama take ya durkusa ta kamo hannun tana cewa Nabil sarkin kirini ina ball tana maganan tana laluman kansa tana shafa Nabil mgn ma gagaran sa yayin sai bin matar yake da ido yanzu Wannan ita na cuta ita na daukewa y'a anya Allah zai ya femin mutanen da suka soni tun ina yaron na cuta ya daga ya sake kallon ta cikin tusayin parlour taba kujeru sai leda amma kakal ashare ba kace na makawuwa ba dan yanzu shateema yana kula da ita sosai shiya tsiye ledan ma ya shin fida mata Nabil dakyar ya iya bude bakin yace "Eh nine mama nadawo gareki kuma zan cigama da zumuci insha Allah amma kiyin hakuri bazan samu daman rakaki India ba ina da wani uzuri mai karfi gobe zanyin tafiya ku kuma jibe ne tafiyan ku amma idan nasa mu yanda nake so zan taddaku acan naga yanayin Anan mama tasan Nabil ne yadauki nauyin a fita da ita Mama tafara kuka tace nagode nagode nagode bana shikarana 13 da dena ganin amma yanzu antabbatar min idan akamin wanan aikin san samu lfy Nabil bai san sanda ya fada jikin matar ba yana bata hakuri tadena kukan ba wani irin tautsayin tada kaunar ta yake ji yana ratsashi Har suka fito mama tanayi wa Nabil fatan alkairi Abba ne yace re kudi yabayar araba dan Nabil bakudi ajikin sa yana mota A motan abba suka tafi abba yana sake gaya masa yanda zannah yake awajen _Nabil Azuciyar sa yace dame yahana ka gaya min sai da me afkuwa ta afku_ Afili yace "ai abba da kagaya min koda ba zanje ba akalla nasan da shi ai Driving din ABBA ya sauke gida sannan ya kawo Nabil gidan sa Hadim ce zaune cikin kanen ta dana Nabil sai lisafin shidi manda zasuyi asuna suke suna ta iface ifacen yasmin tace nin anty cikin ma yaki fitowa mugan shin dan na fison naga yafito yayi tibibi dariya suna dukan susa ce Eh wlh zainab kusan dama ace me zuguda ba agane cikin ta dawuri yakura tace " kuma ma ance cikin fari baya fitowa dawurin jidda tace mude katon da muke so Ko sallama bai yiba yawuce su suna cewa yashid sannu da zuwa bai ko kalli idan suke ba yawuce part din su Hadim ta tashi tabisa zaune ta samesa kan kujera yazuba uban ta gumi dafashi tayi ta zauna kusa da shin tasa hannun ta cire masa ta gumin amma ta ga bai dago kai ba dago kansa tayin taci karo da idon sa daya kada yayi jajir wanda ita de zata iya ratsewa bata taba ganin sacikin wanan hali ba Cikin firgice tace Subahanallashi my star meyake faruwa wllh kasa min faduwan gaba mahassa dako ture hannun ta yayin cikin bacin rai yafara magana dagaskiyan da suke cewa kwakwalwar macce karami ne ban taba gaskan tawa ba basai yau na biye wa karamin tunani irin na macce na janyowa kaina abin kunya da k'askan ci da tozar ce a idon Duniya nayi zalinci naci amanan wanda bai kamata naci musu amana ba nayi karya nayi yaudara awajen wanan yarinyar data yar da ni nayi lefin da nasan abba bazai yafenin ba asanadin macce nayi abin da ko a tatsuniya ban taba jin irin saba......... Hadim daka tar shi tayi ka bar jan zancen kagayamin abin yake faruwa bani da hakurin saura ron kaga min abin da yake faruwa kawai Yace"ai Fada mikin yazama dole dan ke direction tun a farkon aikin Daganan ya she komai ya gaya mata Itama Hadim gaba tane yafadin amma dayake idon ta arufe yake da kudirin ta. Sai cewa tayi to yanzu yaka kewa son muyi meye mafita ga cikin mu ajikin ta cikin. tsawan da Hadim bata taba jin yana yiba yace kekan wuwuyace ina mikin naganan yarinyar tamkar kanwata take gareni ina magana cikin ki yanzu bana bukatan naji shawaran kin dan nacire ki cikin masu lissafi nawa za abin kuma yaza ma dole cikin buyun kizabi daya Tace "fadi najin Nabil yace "na farkon mu dauko yarinyar nan tunka fin abuyayin nisa muje gaban Mahaifinta nagaya masa gaskiya na ne mi yafiyar sa sai naro keshi yabari murenin cikin mu ko........ Ai kafin ya karasa Hadim tace Nabil kanka daya kuwa kasan mekace mudauko ta muce me Mununawa Duniya muce kayin tarai ya dawata kuma cikin da nake tutiya dashi ba nawa bane ni nato zarta a idon Duniya yin hakan zai ba damar mayar da ita matar permanent dan nasan baban ta kai din zai lanja nawa yin hakan yana nuna kenan kishiyar da nake gudu nayiwa kaina da hannuna kanan kawaye na da sauran mutane surai nani kamata da kishiya cikin da nake fariya yaza ma banawa ba Lalle idan hakan yafaru nagama tozar ta tozarcin da zai za memin gwara mutuwan daya daga cikin mu Wllh wllh Nabil dahakan tafar.... Shima kaseta yayin cikin huci da bacin rai Yace "to sai ki tsaya kijin dayan idan kuma bawanda yamikin ni nazabin wanda yamin a ciki Na biyu za muje na musa azubar da cikin sai na kawota wajen iyayenta nace tsintar ta nayin a wani garin nasam........ What Hadim tace da karfin tare da cikumo wuyan Nabin ihun da tayin da karatun data fara shi yajan yon hankalin su jindda da gudu suka iyo wajen..... *Sorry masoyan* *DAMA TA* *Zakijin shirun har zuwan Monday dan muna da bikin* B JATTKO [2/7, 8:33 PM] ‪+234 905 844 3838‬: *DAMA TA* *NA* *BATUL ADAM JATTKO* Mufeeda Hafbee Munan tare🤝 🌈Kainuwa writers Asso🤝 *26* *GiDAN ZANNAH* Bayan sun fito daga tara sun da Mlm yayi na gaya musu yayiwa Fandau aure ne da bako sun tafi matan gidan guna guni suka fara har ayi aure afita da yarinya muna gidan bamu sani ba bagaji tace "yo ai gwara da akayi hakan idan ance auren za ayi me uwar ta ta ajiye a wannan zamanin da kayan turaren tuta kawai ya isa uwa tanadi. Bagana ta kama hannun mama suka shige cikin kuryar dakin su Suna shiga Bagana ta fada jikin mama cikin kuka sosai ta fara mgn tace "mama yanzu kin yarda Baba baya son mu ko ai dama Ya Fandau kullum tana gaya miki kina kin yar da gashi Ya Fandau ta gudu dalilin zaman kunci irin na gidan nan na shiga ukku ne Bagana wazai mayemin ke yayata bani da kamar ki meyasa kika mana haka kin tafi kinbar ne cikin yan uba masu nuna yan ubanci kuka take sosai Mama ta shafa fuskan ta tace"karna kara jin kince baban ku baya sonku... Bagana katse ta tayin tace "da yana son mu me yasa bai yi yunkuri ne man taba tunda bashida ni yar ne man ta tunda gashi nan ya rufe bakin mutane dace wa ya mata aure daker mama ta lallamin bagana Auren su Bagana ya gabato mama kullum cikin tunanin Fandau da kuma abin da zata hadawa Bagana take kishiyoyen ta kullum suna cikin siyayya na nasu yaran da za ahada da Bagana Akwai ranan da duk tawakali irin na mama sai da kishiyoyi suka sata kuka Irin kwalaben bama nan da robobi na chug gum fararen nan suka tar kato mata sukace gashi idan kika samu ikon siyan turaren wuta kya zuba a cikin tunda yanzu duk karyan yakoma kan jeren turare wuta mukam mun kokar ta mun siyawa namu yaran kwalabe na yayi da kayan kitchen dan , mun san mlm shine kawai baya siya ke kuma gashi dan ginkin sun sallama ki balle kisa ran zasu sayawa yarki tukunya ke kuma baki ajiye ba baki bawa wani ajiya ba Kirike wannan kafin musa mu mu kokar ta musa yaran mu su tsaya mata tukunya dan baza mu bari ayiwa Bagana aure ba tukunya ba tunda tana mana biyyya amma da wancan fisararriyar ce yaran mu ko cokali ba zasu siya ba. Suka fita Bagana da ta ke kwaleman daki ko ajikin ta sai da taga mama tafara kuka tazo ta rungume ta tace mama karki damu ALLAH yaga maraicin mu tunda ya hadani da Shateema wanda ya san komai namu yace ma badan abubuwan sun masa yawa ba da duk abin da uwa takeyin zai min kuma yanzu ma yace yayi bakin kokarin sa zai kawo mana mufitar ki rabu dasu duk bakin cikine na yaran su basu samu kaman shateema ba yanzu damu wata ta inda zan samu Ya Fandau kawai Mama dan ALLAH nasan kina mata addua amma kikara dan ALLAH Mama tace "naji je kiyi aikin ki Bagana tana cikin aiki taci karo da jakan kayan Fandau tace Allah sarki Ya fandau tabude ta fara zazzago da kayan wasu leda ta ga sun zubo guda 2 dauka tayi tana bude wa na farkon ta koma baya cikin tsoro amma ta sake bude dayan shima kudinne amma wannan din da letter aciki hannun ta yana rawa ta bude taci karo da tubutun Fandau gaban tana faduwa ta fara karan tawa _Yagana wanan kudin nakune keda mama kar kuyi zargin na sameshi ta hanyan haram a a bani shi akayi kyuta dan nasan inda zanje za samu finwanan nabar muku ne bani da buka tan sa_ Kuka ta kara fashewa dashi ta jeta nunawa mama Mama tayi shiru tana dafa kudin Ta sauke Ajiyan zuciya tace " "Ni kam bana so bazan iya amfani da kudin da bansan tawane hanya aka same shiba Amma ke nasan kina da

Chapter 14 of 39