Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sarki Amana ana nan ana Jin dadi ta sanadinta ita kuma tana can ma ba ita ke Jin dadin ba haka ikon Allah yake.
Saura kwana biyu a fara biki misalin karfe biyar Amana da Umma suka kwado Sallama cikin gidan Baba Sulemanu,
Kaf gidan suna nan ana ta shirye shirye,nan kowa ya tashi da ihu ana rige rigen rungume Amana,Mazan kuma suka tafa tas tas da Amana suna ta kashewa ana dariya,da karfi Amana tace surprise no going back sai ihu yeeeeeee,Amana ta rike kugu tare da juyawa ta furta look at me ? Ya kuka ce heeeeeee wlh a basu wuta,Amana tace ai da girma ya fadi gwara na kwana da yunwa,nan suka hargitse da murna yara da manya Amana ta dawo gaba daya,kowa sai cewa yake I missed u Sis,yaran gida suka hada baki we missed u Anty Amana,murmushi Amana tayi tana daukansu daya bayan daya tana ajiyewa,

Nan fa aka fara labarin bayan rabuwa daga nan suka bawa Amana labarin komai na yadda suka shirya biki,suka bata labarin yadda Angwaye da iyayensu suka taimakesu sosai da kawo agaji,a karshe suka fara bata labarin kaf alkhairan da Alim ke musu,suna fada mata Amana kuma bata San sanda Ruwan Hawaye ke bulbula a idonta ba,
Yana yin wannan taimakon a danginta amma Bai taba tambayarta ba lallai badan ita yakeyi ba don taimakon Allah yakeyi,ba komai hakan ma an gode masa cewar Amana.
Lallashinta akayi sosai harda su Gwaggo,Umma kuwa tuni ta sa kayanta a dakinta ta yi sallah ta huta ta fito wajen kishiyoyinta sukayi hira sannan ta basu hakurin abinda tayi,sannan tayi musu godiyar Kula da yaranta da sukayi,
Gwaggo tace ba komai ai daki har yau nakine tunda yakice ta siya,mukan munji dadinmu arziki sai bunkasa yakeyi ta hanyar mijin Amana nan suka bawa Umma ma labarin,umman Amana ta saki baki tare da cewa ohhh....rashin rabo ya sa na tabi ina ta Shan wahala,iyyyeeeee kuce sai cin jar miya da zaki,Inna tace ah mu sai Sam barka Allah ya kai gaban Annabi,wannan yaro Allah masa Albarka,Hajiyayye kuwa daya matar ta shanye hannu tare da bugar cinya tace ai dadi ya barki baki ga yanda muka canja ba harda dunkuna naki yana wajena kala Uku Alim Bai manta dake ba harda ke,
Umma ta rike haba tace oh kinjiiii na gudu na bar ladana,to ai ta faru ta kare yanzu mun dawo kenan,gwaggo tace af wa yagaya miki barni gabas take gane min hanya yar uwa cewar Hajiyayye.

Amana kuwa Badriyya ta jawo akwati guda na kayan Alim da ya dinkawa Amana,Badriyya kuma ta cika alkawari tace Huzaifa ne yayi mata Amana tayi mamaki tayi godiya sosai.
Tace dan Allah ki fada masa idan kunyi waya to kawai Badriyya tace,

Badriyya a cikin wayoyinta biyu ta bawa Amana daya tasa sim dinta da memory wayace me kyau,sosai yanzu gidan Sulemanu suka kara nutsuwa suke zumunci,suka samu zaman lafiya ba a ware kowa.
Dama sai ba wani wasu zasu gyaru,ranar da wani ke kukan babu wani shi kuma ranar yake samun nasa kudin.
Sai yaba kyan da Amana tayi akeyi,kowa kallonta yakeyi har yan uwanta mamaki sukeyi,Amana ta kara gogewa ta Zama mace sosai,
Wannan bacin ran da ta shiga yasa ta Zama miskila,bata magana irin da,ba fada ba masifa,amma duk da haka me Hali baya fasawa watarana sai an dan gwadashi,

Alim kam rashin Amana da halin da yake ciki yasa ya tashi daga miskili, shuru shuru, mararar magana, ya dawo kasurgumin masifaffe number daya,abu kadan zaka masa ya zage yaci mutuncinta,ko maganar arzikice sai ta koma fada a wajensa,kullum cikin hade rai da bakin ciki yake,
Ko Aabid yanzu tsoronsa yakeyi da yayi abu zai ci Ubansa,Duk yan gidansu basa ma ganin fara'arsa,bare Mum da yake gani ita ce ta jawo komai.
Mum kuwa bata zo Kano biki ba sabo da bata son dangin miji,tace ranar yini zata zo a flight ta koma da yamma.

Ana gobe Amare zasu dawo Kano a fara biki angwaye tuni ma sun fara zuwa domin wasu duk daga kasar waje suka sauka,sai na wasu state duk sunzo,Alim yana cikinsu sun cika a Palo yana kwance a 3seater baya magana duk hirar da sukeyi,bacci kuwa ya daukeshi Bai Dade da bacci ba ya fara mafarkin Amana,Yana ta dariya a mafarki yana washsh....Amana zaki kasheni,sai yayi dariya yace my wife I love u,do u know what? Can yayi shuru sai sukaji yace I missed u,
Mika ya karayi ya ci gaba da mafarkinsa yana ta furta I love u.......I missed u......sai hawaye zirrrr zirrrr ta idonsa suna ta gangarowa yana I missed u kuka na kara yawa,sai yi yake ta yi,yayan Huzaifa Ahmad ne ya danawa Alim duka tashi banza na mamajo,zumbur Alim ya tashi yana taba fuska alamar Bai San ma yayi mafarkin ba,sai da ya nutsu ya tuno mafarkin Amana ya kara yi dama kullum aikinsa kenan,da masifa yace mene haka zaka tashe ni,Ahmad yace to dan iska kaje can wajen Amana ka sauke gajiyarka da kwadayinka zaka zo nan kana mana kukan banza da wofi,mayen mata kawai manniru,kwana dayan ma baza ka hakura ba,me yasa Baka taho da ita ba kasan Baka iya Zama saida ita,Alim ya cika tam amma ganin mutane sai ya share zance sai tsaki da yaja kawai yana turo bakin shagwaba kamar mace,Ahmad yace Allah....sannu Ayu....mu zaka kawowa iskancin shagwabarka nan to bada mu ba kaje can gaban Amanan ka mata, Huzaifa yace pls Babban yaya a kyaleshi haka.

Gobe dai za a fara party daya dan haka Amare da kawaye yan makaranta hadaddu Sabo da Badriyya duk kawayenta yan cikin birni ne bata kula na kauye,Sakina kuwa nata duk yan makarantar boarding schl dinsu ne,sai da suka zabo gogaggun yan wanka da masu kyau hadaddu su suka gayyata dinner saboda kar a lalata musu party,tuni Ishaq ya turo abokansa aka ebi Amare da kawayensu da wasu manyan ma da zasu dinna,Hamza ma yana da Mota yanzu zai tafi da kb,Isa da Haladu, Alim ne yace dole sai sunje dinner har dinkin dinner ya musu.

To fa Badriyya da kawayenta da sauran yan Uwa yan mata suna cikin kano gidan su ango Huzaifa,suna part dinsu maman Su Huzaifa rakanas ta dauko musu me lalle da kwalliya,dama Amare sun kashewa jikinsu kudi sunyi gyara sosai,Amana ta rasa me zata siyawa Amare gudun mawa kawai ta je gidan Me gari aka bata Saniyarta ta gado ta sa aka girba saniya da wuka,aka gyarata ta karbi motar Hamza aka zuba nama a buhun huna,ta figi motar Hamza sai cikin birnin kano,wani waje da akeyin kwangilar hada take away takai tace ayi dambun nama lafiyye a zuba a abin take away unique color na alfarma,
Zoben Gold na Alim da ya taba bata ta cire ta ba dashi jingina hhhh jinginar zobe huuu Amana aka bata kudin da niyar idan ta samu kudi zata basu su bata zobenta zoben Alim ne baza ta iya siyarwa ba,baza ta iya rabuwa dashi ba,haka ta karbe kudi ta biya masu dambun nama,computer Laptop dinta ta Nemo ta siyar da ita nan ta kara figar kyakyawar motar Hamza ta tafi Saloon da lalle cikin city,
Sai dare aka gama mata,a daren sabo da rashin tsoron Amana ta koma garinsu Wudil,
Amana fa ta fara daukan haske shining kawai takeyi,ga lalle ga gashi yasha gyara,washe gari Badriyya sai waya take radowa Amana tayi sauri tazo a fara kwalliya da ita,Amana kuwa kwalliya ta cancada kai kace yaune party, Hamzane yace kiyi amfani da matata Amana kije da ita kawai ni zamu yi Amfani da ta friend dina tafi tawa girma sosai kinga muna da yawa kuma zan kai su little Zaliha ma.
Tnx Bro cewar Amana.

Akwatinta guda tasa a bayan Mota,t a cokala takalmi me shegen tsini cikin kayan da akace na Huzaifa ne a cikinsu tasa wata arniyar atamfa baka da green,dinkin riga da skert yayi mugun da Meta fam,da kyar take mitsi a ciki,ga takalmi da gyale siriri na daukan magana malam,ta sha kyau kamar a sace ta kamar wata yar shugaban kasa,
Dama ga tafiyar Amana tun asalin ta takama da gadara ce,

Sai zuba kamshi takeyi gashin ta glass a fuskarta brown yayi mugun mata kyau gashi sake a gadon baya.
Wajen masu take away ta nufa tuni an gama mata komai nata na take away yayi kyau shi kanshi plastic da marfinsa da aka zuba dambun naman a ciki abin kallo ne,Bare ledar da aka sa plastic din a ciki wai wai,buhunan take away ta zuba a Mota,sannan ta sa kati a wayarta,sai canjin kudi sababbi dal dal yan dari dari da ta canja rapa biyu,ta zuba a pose din dake hannunta
Direct gidan su Huzaifa ta nufa da motarta,

Yan mata da samari sai sintiri sukeyi a gidan,wasu tsakanin mata da mazan ma har sun saba da juna sai shagali akeyi tare,musamman aka dauki dj aka sa a tsakar gida zai dinga kida kwana da yini har a gama biki,Alim duk wacce ta shige sai ya kalleta ko Amana ce ,amma Amana shuru,ko yaushe yana tsakar gida ko zai ga tazo amma shuru,Shine ya kutsa wajen Badriyya wai lallai sai ta kira Amana tayi sauri tazo ayi mata kwalliya,Badriyya shine fa take ta faman kiran Amana,
A waya.

Dama in baku manta ba Amana tasan gidan su Huzaifa,Alim yana zaune a farar kujera a tsakar gida gindin bishiya ga dj na tashi wasu na rawa wasu na hira,wasu matam gulmar Alim sukeyi ga wani me kyau ga haduwa kamar bature,wasu suce dan india ne,musamman kawayen su Asiya da kannen su Huzaifa yan iyayin tsiya yan kwalliya da daukan wanka,har fada sukeyi wai ina marar mutunci matar yaya Alim ne,gwarzuwa me tuko Mota from lagos to kano,sun ga Alim ba fara"a yanzu shi yasa basa tambayarsa Amana,wasu yan matan kuwa cewa suke mutum baya kula kowa sai ya dinga fitowa yana wayon kallon yan mata,
Wasu sukace munafukin banza ba fara'a baya kallon ko wacce da mutunci kamar yaga kashi to uban waye ya sa ya fito waje.

Amana ce ta danna uban Horn a kofar gidan,me gadi ya wangale kofa,ta shararo motar cikin gidan da Alim tayi tozali.


Sorry masu karatu bakuwa nayi yau shi yasa ban gama typing da wuri ba,n asan kun jirani,gashi ku karba na wullo muku.........



AsmaBaffa
✳CIRANIN AMANA✳


165-170




Official



By
AsmaBaffa






INA GAISHE KU MAKARANTA CIRANIN AMANA.





Da Alim tayi tozali ya harde a kujera ya tsirawa gate ido,tuni gaban Amana yayi mummunan faduwa,da kyar ta iya parking din motar sannan tasa hannu a saitin kirjinta ta dafe tana maida numfashi ga mugun sabon Son Alim da ya taso mata,tunani ta shiga na abinda ya faru a baya, Hawaye ke neman kwace mata a hankali ta maida kukanta tare da furta ah...Oh God ....bazanyi kuka ba...karki yi kuka Amana ke me dauriyace,amma duk da haka saida hawaye kadan ya fito tasa yatsa tare da dauke hawayen,sai da ta daidaita kanta sannan ta bude kofa tare da zuro kafarta daya waje,bata ma son ta kalli bangaren da Alim yake bare ya mata wani wulakancin tunda yace duk hanyar da zata hadasu kar ta sake ta bi ta wajen,sannan yace mata ya tsaneta,amma kuma dole sai ta wuce ta gaban su Alim sannan ta shiga cikin gidan part din Amare,
Alim kuwa kalle kalle yakeyi yanda Amana zata bullo bai kawo itace a Mota ba domin bata da Mota amma sai kallon motar yakeyi yana tuna inda ya san motar,

Alim a ransa yace wannan kamar motar Hamza,gashi wata kyakyawar kafar mace ya hango kamar ta yar India,takalmin kawai ya gani ya gane takalmin da yasiyo ne a London ya kaiwa Badriyya ta bawa Amana,wannan kenan Amana ce tazo da motar Hamza tunda dama yasan Amana ta iya driving,yes itace Alhmdllh cewar Alim.

Amana kuwa kasa fitowa tayi saboda da gudun kar tayi kuka,amma haka tayi shahada ta fito gaba daya da kyar saboda yanda dinkin ya tamke mata ko ina cip cip,tuwon mazaunan nan gasu sunyi dam sosai,
Ko mayafi bata yafa ba yana hannunta saboda taga cikin gidane kuma tayi ne Sabo da Alim yaga fa ba ta tashi takeyi ba wai irin ta manta dashi ma wanka take dauka shiga takeyi yanda taga dama,bayan kwalliyar duk dan shi akayi,shi kuwa Alim yaga duk kayan da ya siya matane a matsayin na Huzaifa,sai farin ciki ya lullubeshi,ga wani kyau na ban mamaki da Amana ta karo,da gogewa tare da zama hamshakiyar wata yar budurwa,
Ka rantse bata taba aure ba,

Nan take kishi ya tasowa Alim za a kalli Amana ga maza,to wai ma ina cikin dake jikinta tambayar Alim,ko ta zubar dashi lallai ma yarinyar nan zanyi maganinta,
Yana ta magana a zuci ji yake kamar yaje da gudu ya rungumeta,yama rasa inda zaisa kansa,Amana kuwa juyawa tayi tana fito da buhun hunan take away,da akwatinta,mayafinta na rike a hannunta tana ta tunanin Alim,ji take kamar taje itama ta rungumeshi yanda taga ya kara kyau da haduwa yar ramace kadan jikinsa ita ma sai kayi masa farin sani za kace ya dan ragu kadan,Amana a ranta tace uhmm dan gayu wannan uban daukan wanka da yayi haka kamar zaije dinner,
Ya wani zo ya zauna cikin mata sai kallonsa akeyi,awai dan a kalleshi an fada masa kowa ce zata soshi dan yana da kudi da kyau ya wani zo sai tallar kansa yakeyi,salon wai ace ana sonsa tsaki taja a hankali,kaji fa Amana to ina ruwanki.

Buhu buyu ta dauka tana tafiya das das kowa mata da Maza sai kallonta akeyi,Alim kuwa dafe kai yayi yana hadiyar yawu,yace lallai yarinyarnan kalli yanda take wani bawa mutane show kalli Maza sai kallonta akeyi lallai zan gyara mata zama wannan ai tangal tangal ne da aure kaji Alim to ina ruwanka da ita kaida ka tsaneta,

Garemu matan Aure,zawarawa,yan mata,karki bari mijin ki ya dinga dawowa yana ganinki bakya daukan wanka kamar zaki party,bazawara da budurwa ko kun rabu da mijinki ko saurayi ki sani bafa mantawa yayi dake ba ko ya daina sonki yana nan yana sa miki ido yana bibiyar halin da kike ciki,kinci gaba ne ko kin lalace,namiji yana bakin ciki yaga sun rabu da mace taci gaba,tafi da haduwa kyau da komai da komai,yafi so yaji ance ai naga wance rannan baka ganta ba ta lalace ta rame ta fige,duk kwalliyar wance tab ai kasa ganeta nayi a hanya,ta dawo abar tausayi,ko kuma shi wanda kuka rabu ya ganki da kansa,kin lalace murna zaiyi ba zai damu ba,cewa zaiyi ma wa ya gaya mata,da tana jin dadi a gidana tayi min kaza na kori shegiya gwara haka gashi ai yanzu ta dawo abar tausayi,ai Baza ta samu kamata ba,tayiwa kanta,yanzu ni aka bani wannan me zanyi da ita,ai gidansu wuya suke sha etc.idan kuwa ya ganki kinci gaba,idan yana sonki sai yayi dana sani tayu ma ya dawo yayi ta naci ki koma,ya rude a kanki zaman da kukayi tare ya dawo masa,ko labari yaji saiya nemi ya ganki face to face ya ganewa idonsa,idan budurwace sai yaji takaici ko bai aure ki ba,idan matar aure ce zai kara dinga kaunarki,dan karamin neman aure sai kiji ya fasa,ko ya auro ma yasan kin fita,kowa yana son gyara,tsafta,kwalliya etc duk da cewa suma mazan suna da matsala,amma mata shine ur eye woooo a kara dagewa a daure a cire kyuya da son jiki kiyi iya yinki,

Amarya Sakina ce ta fito ita da ango Ishaq wai yazo kawo mata abinci ta kasa cin abinci shine yazo da take away sai da ya tabbatar taci ta koshi ta rakoshi zai tafi kafin zuwa after magrib dinner party,
Da Amana suka ci karo,dariya Sakina tayi oyoyo Anty muna ta jiranki ba dadi ba kya nan,to banza take away na tsaya daukowa laaaaa hado mana kikayi? Yeah cewar Amana,Nan Sakina ta dinga godiya Suka gaisa da Ango shima harda godiya,
Sakina ce tayi magana to ki mayar cikin motar kinga ko an kai ciki sai an kara fitowa fa dasu dole ga mutane,Amana tace af hakanefa na manta kinsan ni ba kawaye ne mata dani ba,sannan bikina ban samu gatan haka ba ban san ya abin yake ba,bari na maida,ango dai tuni ya hau mota ya tafi,Sakina ta dauka bari na tayaki...Amana tace commot abeg Amaryace ke ba aiki ai,matsa ko na makeki,Sakina ce ta radawa Amana ga mijinki can kamar zai cinyeki da kallo,kinga kalli yadda yake ta muzurai,kamar kishi yakeyi fa,Amana tace zan mareki Sakina ban son shirme na fasa kaiwa motar ebi ki kai ki zuba,

Kai Amana saurin zuciya da fushi yana nan dai,kyaleta Amana tayi ta koma ta kai kayan cikin Mota da kanta ta dauko trolley dinta ta juyo kenan taga Alim a bayan yana huci kamar zai daketa har ta tsorata sai ta tsinci muryarsa yace gyara parking din motarki zan fita da tawa,Amana itama a fusace tace duk filin nan bai Isa ka dauki Mota ba sai na gyara parking?Alhmdllh Alim ya furta a ransa saboda dadi hade da sanyi da yaji a ransa Amana tayi magana yaji muryarta,

Cike da masifa ya kara cewa ko bazaki janye bane?Amana shuru tayi don taga kamar zai daketa yanzu kuma bata fada,kawai sai ta shiga motar ta janye ta can lungu ta fito a fusace fuuuuuuu ta ja akwati ta wuceshi.

Badriyya sai murna takeyi Amana tazo Sakina har ta fesa mata Labarin Alim da take away na Amana da ta musu,
Bayan Amana ta huta saiga Asiya kanwar Alim tazo tana cewa Badriyya wai ina matar Ya Alim ne?
Da sauri Badriyya ta nuna Amana dake kwance saman gado tana faman tunanin Alim,
Anty Amana ina yini cewar Asiya Amana ta amsa cikin fara'a da sakin fuska,Asiya suna kama da Alim sai take ganinta kamar Alim,kallon Asiya takeyi tana ta murmushi tana jin sanyi a ranta,sai suka fara hira, har muryar Asiya kamar ta Alim,Amana sai hira take kakalowa,Asiya tace muje wajen su Abban Huzaifa da Mama ku gaisa da sauran dangi,Amana ba musu ta yafa mayafinta tare da kara gyarawa suka wuce,da dan Auta Kanin su Alim suka ci karo Asiya tace Bro kaga matarfa ya Alim na san baka santa ba lokacin kana schl,Amana a ranta tace wannan yama fi kama da Alim dina,gaisawa sukayi sosai yana ta tsokanar Amana ashe matas ce ma,gaskiya na iya zaben me kyau,suna tsaye saiga Nura ma Babban yayansu shida matarsa da yarsa sun dawo daga shopoing,Asiya tayi sauri ta nuna musu Amana suka gaisa harda hira sosai da sosai saboda Nura akwai nutsuwa, Amana a ranta ta ce lallai ai wannan Nuran ma sunfi kama sak da Alim. matarsa ma sai jan Amana take da barkwanci,tambaya Amana tayi wai ina dana ne Aabid?

Nura yace yana wajen Maman Huzaifa yana ta bacci,ok kawai Amana tace taja Asiya suka wuce cikin part din su Huzaifa,Da sallama suka shiga palo da Alim suka fara hada ido yana saman kujera yana cin snacks da Icecream a gefe,
Huzaifa Ango yana gefensa,mama tana zaune tana jira lallenta ya bushe,ga sauran yan Uwa mata nan gaba daya cike dam a palon amma Alim yana ciki yana cin abu sunki tashi,,tsugunawa Amana tayi har kasa ta gaishe dasu kaf cikin mutunci,Mama da fara'a ta tarbeta tana yata sai yau kika zo muna ta jiranki,dariya Amana tayi,Alim a ransa yace wayyo ta kasheni da murmushinta,
Tambaya Amana tayi ina Abba da yar tsohuwa kaka kenan idan masu karatu baku manta ba,Tace tsohuwa tana daki da bakin ta har danki Aabid yana wajenta,Abba kuma yana sama ke Asiya rakata ta gaida kowa,

Sun mike sunje ko ina sun gaisa da kowa cikin mutunci sun dan dade suna hira da kaka tsohuwa Aabid bacci yakeyi,kowa na dangi sai da aka nuna masa Amana suka gaisa

Fitowa sukayi amma still Alim yana palon kusa da Mama,Huzaifa kuwa ya koma jikinta ya nanike ya kwanta a cinyarta,kowa ya shigo sai anyi dariya Ango kamar Amarya me jimamin rabuwa da gida,
Mamace ta kalli Amana dake shirin fita tace zo yata,dawowa Amana tayi tare da tsugunawa har kasa,duk wanda yasan Amana a da sai yayi mamakin canjawar halinta yanzu har Alim,Mama tace zaki dawo dakina da kwana ne? Da sauri Amana tace a a zan zauna wajen frnds,Haushi Alim yaji a ransa yace da kin dawo nan ai nafi ganinki,Huzaifa yace Anty tafi son cikin yan mata,hararar wasa Amana ta cilla masa,
Yana dariya yace to mene na harara,kowa yayi mamaki ana cewa matar Alim ce amma anga basuyi magana da juna ba sai kallo da yake binta dashi kamar maye yana shan Icecream,
Mama ta fuskanci kamar da matsala tsakaninsu Amma sai kowa ya share tunda ba wanda yasan komai akai,Mama tace to ga dakin mijinki ko can zaki zauna dan iyayi dakinsa shikadai ne ko angon ma su biyu ne amman wannan marar kunyar Mama taja kunnen Alim tace dakinsa daban kullum yana cikinmu,yaki bari mu sake,dariya akayi banda Alim da Amana, Umma duk bata sani ba Alim ne ya tura Asiya ta kawo Amana su gaisa da danginsa shi yasa ya dawo palon ya zauna Sabo da ya kara ganinta,

Mama tace zauna yata,Amana kallon dakin tayi kaf ba space kujera 2seater ce kawai ta rage me dama dama,itama Alim ne a kai ya wani kwanta,Mama tace zauna kusa da wannan kwadayayyen Alim kenan,Amana bata son tayi musu,gashi bata so a gane halin da suke ciki da Alim tunda shima ya boye,Mama tace gyara musu su zauna mana, Asiyace taje ta fara Zama sannan ta jawo Amana ta fada kujera suka sa Alim a tsakiyarsu,
Tofa an Dade ba a hadu ba.

Jikinsu ne ya gogi juna,wani uban shock ne da faduwar gaba ya shigi masoyan biyu,
Haushi Alim yaji kar ma tace ya damu da ita,itama Amana haka,Alim ya matso jikin Amana ya bangajeta da kafada tayi gefen kujera haushi taji a ranta tace dan yana Jin haushi na sai ya bangajeni,gyara Zama tayi,ya kara bangajeta,Amana a ranta tace kai Kai kai da Zafi fa Bai isa ba saina Rama wlh ina ruwana dashi,Amana ta matso itama sosai ta bangazo Alim Bai zata ba ai kuwa ya rikita jikin Asiya,
Asiya tana kallonsu tayi murmushi,Alim a ransa yace halinta Ashe yana nan,nan ya samu ya kara turota tare da kara hade rai,Amana ta kyaleshi ganin mutane kara bangazota yayi,Ai kuwa ta samu ta sa hannunta iya karfinta ta turashi jikin Asiya tana nishi da cijewa,kuma sunyi mukus suna ta faman ture turen juna,haka suka dingayi sai kallonsu yan biki keyi suna dariya,mitsini Alim ya kwanyawa Amana a cinya da sauri ta sosa waje tasa kafa ta take masa kafa tare da murzawa,Alim yaji Zafi amma ya cije, hannu yasa ya yakusheta a wuya har wajen yayi danja

Please Login or Register in order to submit comment