Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

saina nemi me gidan nan wanda ya baku haya ya koreku ya tasheku da gidan nan,mu Malam Salisu dake kasanku mutumin kirki ne.Amana ce ta janye Alim,haka tsoho ya gama surutunsa ya tafi.

Kitchen Amana ta shiga Alim ya bita ciki suka fara girki tare,Alim Bai iya komai na girki ba kawai batawa yakeyi,
Garin yanka Alaiyafu ya yanke a yatsansa sai jini shar....Amana kamar itace ta yanke kwace wukar tayi ta kama yatsan toilet ta kaishi ta wanke masa hannun ta sa masa hydrogen ta manne masa da plaster,
Kallonta kawai yakeyi ji yakeyi kamar ya hadiyeta ya huta yanda take matukar Kula dashi.lips ta cuno masa shi kuwa ya miko nasa ya manta kiss,murmushi sukayi taci gaba da aiki a kitchen yana zaune a gefe yana kallon ta idan ta juyo suka hada Ido sai ta cunno masa lips ta turoshi sosai shi ma ya miko nasa sai muahhhhhh..... zuba masa kunun Aya tayi da ta hada yana tasha tana aikinta
Waist dinta ya rungumo ta baya da hanu daya daya hannun kuma yana Shan kunun ayarsa,
A hankali yake magana ayi sauri a gama girkin nan,mene kake sauri yunwa?hmm kema fa kin sani tun kafin ki bar lagos rabona dake nazo nan kina period da kyar nake manage,kin gama kin hana min abina har kinyi kusan 4 days da gamawa ya karasa kamar zaiyi kuka.duk sai taji tausayinsa domin iyakacinsu romancing yana so haka zai hakura saboda tace tana Jin zafi kuma karyar Amanace kawai wai itama dan aji ta ja masa amma ko ita watarana tana so musamman Idan ta kalli kyakyawar surar Alim dinta me tsananin kyau da haduwa.

Bayan ta gama girki abinci suka ci tayi gyare gyarenta,fitowa tayi ta shiga bedroom dinsu Alim ta gani ya fito a wanka yana shafa Mai ba komai a jikinsa,
Amana dai wani yarrrrr yarrrrr take ji a jininta ,nan take taji tana matukar bukatarsa,sha'awarsa taji wacce bata taba jiba a rayuwarta, tsayawa tayi tana ta kallonsa kamar mayya,tongue dinta ta zaro ta lashi lips dinta sai lumshe Ido takeyi tana ta kallonsa,sai ta fara sosa wuya idan ya juya har dogon wuya takeyi wajen leko kirjinsa etc
Yana kallonta ta mirror amma bai Kula ta ba domin ta dan bashi haushi dazu a kitchen yace yana bukatarta ta shareshi ko kulashi ba tayi ba,
Rigar wankansa ya mayar harda kara daureta ya rufe jikinsa kirjinsa kadai ya bayya,Matsowa tayi tana soshe soshe Him.... uhmmmmm...uhm kallonta yayi tare da lullube jikinsa da towel yace lfy?
Uhmmmmm ba komai,dayan Bed room din ta wuce tayi wanka tare da sako wasu shegun kayan bacci masu Jan hankali tasha kyau tana bulbula kamshi,
Saman bed ta hango shi shima cikin shirin baccinsa ya mike kafafu sai danne danne yakeyi a system,
Jiki a mace tana karairaya hadi da lumshe Ido tana fari,Alim ya kalleta sama da kasa sai da ya girgiza ta gama tafiya da imaninsa,
Sha'awarta ta dawo masa sabuwa fil amma ya daure ya shareta,gyaran murya tayi hade da Zama kusa dashi tana ta binsa da kallo tana ina ina tace um.um..ta sosa kanta taci gaba baza...baza...kayi bacci yanzu ba?
Alim ya kalli yanda take kallonsa idanunta sun canja tsab ya ganota yasan me take so amma ba tare da ya kalleta ba yace kwana zanyi ina aiki yau,

Magana tayi tace to..to..to naga Alama tana ta zaune taki kwanciya sai satar kallonsa takeyi,
Kashe computer yayi Amana na ganin haka tayi Hamdala a ranta,bai kwanta ba sai ya zauna cure a bed din,Hannunta ta mika a hankali ta kama wasa da kafarsa,
Dauriya kawai yakeyi,gajiya Amana tayi matsa jikinsa cikin sigar shagwaba tace am in...in....the...mood kaji kayi wani abu sweet mana,ta kare zancen tana shafa hannunsa,matsawa yayi gefe yace dazu da nace I need u me kika ce min?sai yanzu zaki neman da yake bukatarkice I hope zan iya miki yanzu amma na gaji kin makara
Jiki a sanyaye ta Mike zata bar dakin tare da cewa ahhhh.....ok.....never mind ta fara tafiya ya fisgota ta fado kansa flat ya mata ya fara kissing dinta dama Amana jiran kadan takeyi ba bata lokaci suka gigita Kansu kamar mayunwata,Sosai Amana ke enjoying din abinda Alim ke mata ta bada hadin kai ta dage tayi iya yinta,ta gama baje basirarta a kan Alim,ta mishi abubuwa masu rikita hankali wanda ya Sha mamakinta yanda ta tafiyar dashi,gata gwarzuwa ce akwai juriya da jajircewa na ganin ta bawa Alim abinda yake so ,shima hakan take
Yau su Alim harda kwallar dadi da farin ciki,bai taba Jin makamancinsa ba,Amanansa ta dabance sai da yayi round 3 ya kyaleta hakanma kawai kyaleta yayi dan kar ya shiga hakkinta Bai sani ba domin Amana Idan zaiyi sau 100 baza ta nuna masa alamar ta gaji ba sai ta daure,duk da cewa itama tana da karfin sha'awa kuma uwa uba tana Jin dadin harkar kasancewar mijinta ya hadu ta ko ina,style iri iri sunyi shi,tasha sambatu wajen Alim itama haka,saida suka nutsu ya shiga sa mata jerin Albarka,wanka sukayi tare da tsarkake jikinsu sai nafeela da sukayi da adduoi suka fada Bed hade da manne juna sai bacci.

Sulemanu Harka jiki yaki dadi duk yanda za ayi anyi masa ana ta kashe kudi amma kafunsa sunki doruwa,sai ma kara lalacewa sukayi yanzu kullum sai an fitar dashi an Shanyashi a rana a kofar gidansa,
Yauma yana kwance a tsakar gida sai numfarfashi yakeyi ya tambayi Badriyya ke ina Amana ta ke zaune a garin nan?Badriyya tace Baba nima ban sani ba tana dai zuwa dubaka kuma ta ebi kayan sawa ta tafi,duk kusan ta kwashe kayanta na sawa,
Baba yaga bashi da kudi kudinsa ya kare gashi ba fita yake ba ba lfy,ga ba Amana ba mijinta babu me bashi domin ko sanda Amana na lagos har kudi take tura masa.
Baba ya kwalla kara yace Wannan kwai gantalalliyar yarinya akan wannan shegen yaron ta bar gidana saboda nace baza ta koma ba,
Indai Namiji ne gata gashi na yafe mata taje tabi mijinta akan haka harda barin gidana,to ni dai na yafe mata ta koma dakinta yarinyar kirki ta gari bani da kamarta ga biyayya tafi kowa Jin tausayi na da bin umarnina,matansa da yaransa ya Tara ya fada musu dalilin barin gidansa da Amana tayi,babu wanda ya kulashi sai Umman Amana tace Baka kyauta ba kayi butulci,nan dukka gidan Akayi caaaaa akan Baba,yace to kuzo Ku dakeni Ku huta

Isa yace Baba matar da kake zargi itace Umman Alim wlh ba ita bace Baka ganeta ba,ni naga matar ganin idona,Babar Alim fara ce waccen kuma Baka ce,
Ka bari ayi bincike tukun amma mijin Amana mutumin kirki kalli yanda ya mai damu mutane,

Nan Sulemanu Harka yace to latso min waya ka kira min Amanata,Hamza ya fara kira amma bata shiga har Number Alim duk basa shiga,

Da dare Alim Zaune a saman kujera Amana na kasa magana ya mata honey yau mu dan fita mu zaga gari mana,
To bari mu shirya ko,wanka sukayi fes dasu suka hade cikin shiga me matukar kyau sannan suka kulle wajensu suka fito,da yake akwai wuta ko Ina da haske ba laifi,
Sunzo tsakar gida su shiga Wajen Sa'adatu suka gaisa sai ga Yarta budurwa Iklima ta fito sai kallon Alim takeyi taga baiwar cikar zati

Mum gaba daya ta rasa sukuni sabo da rashin Alim,gashi Abba yaki saurarar zancenta yace karyane dansa yana nan lafiya,
Su Nura ma shareta sukayi kowa ya kama harkar gabansa,matar Nura shanawa sukeyi da mijinta saboda Mum tana cikin damuwa bata kulasu,Matar Nura ke Kula da Aabid sosai.Mum kuwa kullum kuka takeyi harda Jin haushin Abbansu Alim shi ya cuceta ya tura mata da yaro aiki wani state.

Amana na kallon yanda Iklima yar Sa'adatu take kallonsa ta faki idon kowa ta dallawa Iklima harara,radawa Alim tayi tashi mu tafi tare da tamke fuska wai haushi,a hankali yace mu dan zauna ayi hira ko ma Saba dasu,Amana tace pls kaga ni Bana son wani sabo,mu kadai zamu dinga rayuwarmu.
Me za
Muyi a wajensu dama mutuncin makwaftaka yasa muka shiga,
Sa'adatu ce ta fito dauke da lemo da ruwa amma Amana tace sun koshi tafiya zasuyi,Sa'adatu tace da kun zauna munsha hira?Amana tace zamu dawo watarana ai,Alim yace to Mene mu zauna mana Amana cikin Jin haushinsa tace ko second Biyar bazan kara ba tashi mu tafi kawai ai yawo zamuje.muje to ya Mike sukawa matar sallama Amana tasa Alim a gaba kamar danta,suna fita Iklima tace Mama wlh wannan matar tasa masifaffiyace kuma kamar itace mijin yanda take abu ta gama mallake bawan Allah, wa ya sani ko asiri ta masa da ganin Alama,Sa'adatu cikin fada tace ina ruwanki dasu ki iya bakinki,Iklima tace ai naga ta gama mallakeshi wlh har ya bani tausayi.

Alim suna fita Amana tace Allah ya taimaki yarinya watarana ta gwada min hauka kamar yau ta gane shayi ruwane da kanta kamar kwallon kwakwa,Alim yayi murmushi ke ki kwantar da hankalin ki ke kadai ce ba Kari don ta kalleni sai me ni kinga na kalleta ne?to me yasa zaka ce mu zauna?nufina mu dinga zumunci,to bazamuyi dasu ba karma ka jawo na koresu daga gidan nan.
Sorry sarkin zuciya ni dai ki huce kar mu koma gidan ki hanani Harka,da wasa Amana ta dalla masa harara sunan Babane fa Harka,sorry na manta I swear
Dariya Amana tayi tare da rungumeshi tsam haba dai ai kome zaka min bazan hanaka komai ba,ba wannan shirmen ai sai kace yarinya marar tunani,idan ana Jan fada haka ai aure baya lasting duk fadan da zakuyi da mutum matukar baza Ku raba makwanci ba to dole a shirya da wuri bare har ya kai ga saki,kiss ya manna mata tare da shafa wuyanta a rungume da juna suke
Suna tsaye sai ga Baba tsoho yana takawa da kyar ya dawo daga masallaci ya kara biyowa ta wannan lungun me duhu,wannan karan tsohon masifa yakeyi a hanya sosai,Alim yace laaa ga tsohon nan na ranar nan mun ga ta kanmu

Tsoho Ashe yaji me Alim yace yace bakuga ta kanku ba sai Allah ya damkeku da kansa,
Yau ba ta Ku nakeyi ba domin kun Zama Bala'i sai sadaka,
Amana tace Malam me aka maka yau kake fada?yace kedai bari karuwai wlh wasu yarane suka bata min tsoho ya fara basu Labari wai wasu Samari ne a masallaci kullum sai sun dagashi bayan an idar da sallah saboda bashi da karfi da kyar yake tashi ma,
Kawai sai rannan matarsa ta haihu gobe suna shine ya bada Sanarwa a masallaci gobe za a rada suna matarsa ta haihu samarin nan suna jin haka suka saki dariya tare da cewa ah....tsoho Ashe kana da karfi yanzu har matarka ta samu ciki ta haihu ta wlh baza su kara dagashi ba sai dai idan ya kasa tashi ya kwana cikin masallaci tunda har yasan zai iya wata ciki,ai kuwa su Alim suka dinga dariya,Amana tace Baba dai dai sukayi wlh gwara haka,
Tsoho yace ai gwarani ba dan iska bane irinku,karuwai shedanu,Amana tace wlh Tsoho muna da aurenmu fa,yace ban yarda ba ko sama da kasa zata hade bazan yarda ba kuna da auren zaku dinga bin lungun masu shegen duhu ba kunya ba komai,
Da Allah kar Ku kara min takaici wai yanzu ace yaronka Bai jawo ma magana ba wasu a titi na kwararo su dinga sawa zuciyarka na tafasa.
Dariya suka karayi tsoho yace kwayi da wani marasa mutunci.
Alim ne ya zaro kudi masu yawa ya mikawa tsohon Baba ga wannan ka siyi rago ko
tsoho yace wuuu...rufani ka sayani dannan niiiiii na karba kudinku na haramci inma cin hanci ka bani wato dan na dinga rufa muku asiri kuna shekewa to ni Bana karbar cin hanci,bazan rufa muku asiri ba,zan karba na gode kuma amma kar kusa rai zaku zauna lafiya a unguwar nan sai na sa me gidan ya koreku,tsoho ya karbe kudinsa yana godiya,wata mata tazo wucewa Ashe tasan Amana nan suka gaisa sosai,tsohon nan har ya fara tafiya ya dawo yace Delu wato ke kike daure musu gindi ko har gaisawa kukeyi?Delu tace kaji tsoho da sa Ido to har duwaiwai na hada na daure musu karewarta,tsoho yace Bana ja'in ja da matar wani yayi tafiyarsa yana masifa wlh sai ya tonawa su Amana Asirinsu.

Delu tace tsohon nan sai hakuri ta wuce,su Alim suka tafi yawonsu sosai suke Jin dadin yanayin.

Saude ce zaune a wani rubabben dakinta dake kauyensu tana waya tana faman sheka dariya,ba a Jin me suke fada sai dariya r Saude kawai kake ji.
Alim da Amana sun Dade suna zaga garin har 10 na dare sannan suka dawo gida hannunsu rike da ledar da suka siyo gashashiyar kaza da yogourt.
Suna shiga cikin gidan Amana tace ayi rige rigen zuwa Palo,ai kuwa Alim yace 1,2,3 go suka zura da gudu Amma Alim ya Dade da shiga Palo sannan Amana ta karaso ciki tana nishi tare da kukan shagwaba ni... ban yarda ba Allah,dariya sukayi gaba daya suna ta faman haki,ta fara masa rigimar sai ya goyata,haka ya goyata har saida ta fara bacci a bayansa sannan ya samu lfy,
Dole ya tasheta suka ci namansu da wanka sai bacci,
2:30 Alim ya farka da rigima ya fara tashin Amanarsa Babyna Baby,cike da maganar bacci tace naam mene?cikin kulawa tayi magana tana mayen bacci ruwa zaka Sha?yace ae Mikewa tayi zaune zata bar kan bed ta kawo masa ruwa,cike da sha'awa yace honey naki nakeso fa,dukan wasa ta kai masa sukayi murmushi nan suka karashe Daren suna ta faman raya
sunna.




AsmaBaffa


Ina godiya masu sharhi kune nawa.

✳CIRANIN AMANA✳



150-155



Official




By
AsmaBaffa





ZAUREN QUEEN MERMU DA TASKAR FIDDAUSI SODANGI WANNAN PAGE NAKUNE. TNX ALL.





Bayan 3months Mum Alim ta shiga damuwa,zuciyarta dankare da bakin ciki,haka Sulemanu Harka komai sai dai ayi masa baya iya komai ya rame yayi baki ya tashi daga aiki,gashi Bai yiwa yaransa abinda ya kamata ace iyaye sunwa yayansu ba,bai sauke hakkinsu ba,ya gama zubar da mutuncinsa duk da cewar suna masa komai da ya dace amma basu damu dashi ba ko ya mutu ko yayi rai harkokinsu sukeyi domin mazan ma sun koma state din da suke business wasu kuma sun dawo Kano da kasuwanci duk cikin tallafin Alim gashi Hamza Babban yaya da kb sun samo matan aure a city har an musu engage,
Badriya ma maganarta da Huzaifa tana tabbata sai karfi takeyi,

Alim ne yayi shiri da safe da wuri yace zaije banki ya curo musu kudi,cikin shadda dakakkiya yake dinkin fited yasha kyau har bakin titi Amana ta rakashi ya shiga taxi drop ya wuce
Ta dawo ta gama komai na gidan tana Jin zazzabi kadan kadan har ta kwanta tana tunanin rayuwarsu ita da mijinta,
Gaba daya jinta take bata da lafiya kawai hijab dinta tasa ta tafi hospital sabi da ta tsorata this mnth bata ga period ba,kuma Alim yace mata indai unguwa ta kama da lalura to ko baya nan taje kawai ya yarje mata,
Karamin asibiti taje a cikin garin saboda yana da girma garin nasu,ana aunata ciki ya bayyana a jikinta wata daya,magungunan da aka rubu ta mata ta siya ta wuce da result a hannunta tana ta murna,ta matsu Alim ya dawo ta bashi labari,
Kasa hakura tayi tun a hanya ta danna masa kira a waya cike da nishadi shauki na kwasarta tace my Man yaushe zaka dawo? Alim yace nan da 3-4hrs na biya ta wani waje,
Amana ta saki murmushi tare da furta Allah dawo min da kai lfy,murmushi Alim yayi cike da zallar
Kauna ta gaske sannan a hankali yace Ameen sai na zo me zan kawo miki?anything kawai cewar gogar,sallama sukayi ta koma gida tare da bajewa a 3seater.
Alim Bai dawo ba sai 9pm ya kwankwasawa yayi tare da murda handle,Amana ta fito daga kitchen tasha kyau da sauri ya jawota jikinsa yayi hugging dinta yana murmushi sannan ya mika mata ledar hannunsa,

Wani dan kyakyawan saurayine ya fito fit daga bed room din su Amana yana sweetheart kin barni ina t faman jiranki kiyi sauri muyi abinda za muyi kafin dare yayi nisa ina da aikin yi ....kamar gaske saurayin nan ya tsaya cak yana hangame baki yace dama cutata kikeyi kin San kina da aure kika ce nazo,
Da gudu saurayin nan ya nufo Amana tare da kwasheta da wawan mari yace kin cuceni Allah ya isa ban yafe ba nayi tarayya da matar aure.
Ya bude kofa ya fice fit,Yana barin gidan wata dalleliyar mota ta tsaya gabansa ya shige suka bar garin gaba daya.
Alim kamar gunki haka ya tsaya yayi poster sai hawaye da suke ta bulbula kamar famfo daga idonsa,Amana kuwa da ledar da Alim ya mika mata da result na ciki na hospital ta saki a kasa,
Kafin kace me ta sume sharab a wajen,
Alim kuwa innalillahi kawai yake maimaitawa sannan ya shige bedroom ya tattara nasa ya nasa kaf,ya fito ganin Amana har yau a sume sharab a kasa kallo daya ya mata ya tsugunna tare da daukan result din hospital dinta ya duba hawayensa ne suka karu kamar ba Namiji ba ya zauna ya dinga rusa kuka,
Yana why....why.....na bar yan uwana da iyayena duk sabo dake,Mum dina ban San wannan Hali suke ba,sai yanzu Alim ya gane kuskuren biyewa shawarar Amana da yayi sabo da so ya rufe masa Ido,Mum dinsa tana can cikin bakin cikin rashinsa har cuta tayi sabo da son da take masa,ta dauki cikinsa,ta raineshi amma yanzu ya gujeta duk da Mum Nada babban laifi amma uwa uwa ce baza ka biyasu abunda suka maka ba,sune sular zuwanka duniya Harka hadu da wata,
Amma yayi fushi da Mum dinsa ya barta saboda matarsa kuma yasan dole tana cikin wani hali tunda duk tafi kaunar Alim cikin yaranta,
Kuka sosai Alim yakeyi,ashe Amana dai Amanarsa take ci,yana ta shirme akanta yana biye mata,bai taba zatan zata aaikata haka ba,tunani yayi sosai da karfi ya furta no.no...nooooo...baza tayi haka ba,
Amma Sam zuciyarsa ta hanashi tunani bare wani bincike,ji yayi ya tsani Amana gaba daya baya kaunar ya bude Ido ya ganta,sambatu yakeyi sosai idonsa jajir jijiyoyinsa sun tashi rada rada ji yake kamar ya kashe Amana ya huta,
Ya yarda a gaban ko waye zai iya zubar da mutuncinsa kan Amana domin ya faranta mata,
A titi,a lungu,a kwararo,a bainar jama'a duk saboda yayi proving dinta yanda yake sonta,dan yasa taji duk duniya ba kamarta tafi kowa sa'ar miji,har ana ce masa kwarto sabo da ita,
Abinda watsatsun yan mata keyi a boye a titi yayiwa Amana shi tana matarsa amma duk wannan Bai hanata neman maza ba,
Ashe makaryaciyace,ta yaudareshi,mikewa yayi da niyar tafiya

Amana ta ja dogon numfashi ta farfado,zumbur ta Mike tare da rike rigarsa tana kuka wiwi kamar ranta zai fita,da kyar tace pls....ka...sau...rareni...dan Allah wallahii ban sanshi ba,kayi tunani da bincike sharri aka mana kasan muna da makiya,hannu biyu Alim yasa yaci kwalar Amana tare da girgizata da karfi ya makata jikin bango ya shaketa sosai tana ta kakari,... sannan yace ohhh makiya ko......da karfi yace makiya Mum ce makiya ko?Amana ta kasa magana sai hawaye nan Alim ya jefar ta kasa ta zube rigip,juyawa yayi tare da cewa kar ki sake ki nemeni,kar naga kafarki a gidanmu bana son ganinki na tsaneki,
Inda kika San zamu hadu kar kibi ta layin coz idan na ganki cikin karaji ya karasa I will kill u.
Result din ciki kuma ki haihu ayi DNA test idan har nawa ne zan karba.ya bude kofa baram ya kara makota ya bar gidan,
Direct airport Alim ya wuce ya bi flight sai Lagos inda akafi wayo.

Amana kuka takeyi tana salati sallah tayi tayi addua sosai hawaye kuwa yaki tsayawa a idon Amana,bata San wannan tsinanne ne ya hada mata wannan sharri ba.
Tattara nata ya nata tayi itama cikin dare tana zabga kuka ta bar gidan ko su Sa'adatu bata yiwa sallama ba,tana fita ta fara tafiya a kasa wani Almajirin kusa da gidansu ya biyota yana dan Allah Anty ki bani sadaka dare yayi banci komai ba,wani takaici ne ya kara kama Amana ta kara harzuka ta hayayyakowa Almajiri da masifa cikin kuka kai dalla karka dameni ka kyaleni naji da matsalata,da wannan matsalar dana shiga gwara na kwana 3 banci komai ba,dallah matsa ta furta tare da tallafewa Almajiri keyarsa ta jefa masa Dari Biyar,
Tana yin gaba ta hadu da karamar kanwarsu Zaliha ta siyo sugar a kanti na gobe da safe,Zaliha tace Amana kece da dare yau me ya sameki Baba yana ta nemanki har ya rasu ma naga su ya Haladu suna ta kuka da Umma,ai Amana kafa tasa tayi short da Zaliha,
Ta kara gaba,Zaliha ta gama kukanta ta bi bayan Amana suka shiga gida,tun daga tsakar gida taji kukan su Haladu da gudu ta fada dakin Baba,Baba ne a kwance yana ta suma yana farfadowa ya suma yafi sau saba'in gashi yace Baza a kaishi asibiti ba,an tafi dashi yace duk wanda ya kaishi asibiti Bai yafe masa ba,haka aka dawo dashi,
Amana kan Baba tayi tana kuka ta cakumeshi tana Baba dan Allah karka tafi ka barmu muna sonka Baba,
Farfadowa Baba yayi tare da damke hannun Amana ya fara magana da kyar Amana...ta....da yan uwanki Ku yafe min ban muku tarbiyar kirki ba na sabawa Allah da yawa kin min Wa'azi naki ji ga yanda duniya tayi min juyin wainar Asabe,ki rokar min matana iyayenku su yafe min,gwaggo uwar gidan Baba tana sheka kuka tace mun yafe maka Allah Baka lfy,

Sauran matan ma suka ce sun yafe suma ya yafe musu domin irin zagin da tsinewa Sulemanu mijinsu da suka dingayi kullum a maimakon suyi masa addua,
Tari Baba yayi yace Amanata ki koma dakin mijinki na yafe miki ki yafe min kin Sha wahalar rayuwa na turaki Cirani saboda kina min Wa'azi kaico na,
Badriyya tace Baba mun yafe maka dan Allah kar tafi ka barmu muna sonka,muma munyi maka laifi sosai bamuyi ma biyayya ba,Sakina cikin kuka tace Baba wa zaimin kayan daki idan ka tafi wayyo gashi na samu miji gatana ya kare bango ya

Please Login or Register in order to submit comment