Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 9
ajiyar xuciya maiƙarfi,yanajin yadda xuciyarsa ke axalxalarsalda soyayyar samha, tsorone yakamashi dayatina cewa ita baisaniba koyayimata .lallai akwai masala matukar banyimataba,dik dana hango alamun nasara da karɓuwa acikin kwaran idaniyanta,lallai xanyi nasara, Taɗan jima da dawo hannunn duk biyu tasa taɗauko kujerun roban tana waresu ta ajemasa ɗaya tasa ɗaya wakanta Kazauna inatasallama bakajiba. Yaysaurin ke idonsa akanta yana murmushi tare da jan kujeran yaxauna. Amm banjikiba yi haƙuri Bakomai Tace tana sauke kanta ƙasa, tanawasa da wayarta Am bakice komaiba akan maganandanayi ɗaxu samha. Ahankali tafara motsa baki. Amm naji amma inabuƙatar loƙaci gaskiya domin nai tunani Yaxaro ido kamar maishirin kuka Tunani kuma samha please karkimin haka,wlhnariga danagama faɗawa tarkon ƙaunarki banadawata mafita datafuce nasameki,xurfin cikinayi amma batunyanxu nake sonki ba, Tabuɗe baki xatai magana yadakatar da ita Dan allah karkice wani ya rigani domin abbanmu yasanarmun abn aurenki,, Taidariya har haƙoranta masu ƙyau da haske suka bayyana, Ba haka xanceba ai Yasaki ajiyar xuciya Takara kallonsa lallai taga tsagwaron son dayakemata acikin idaninsa tabbas ba ƙarya yake mataba, Sunana al ameen, anma anfikirana agida ameen,nasan xaki tuhumeni akan hakan sbd na fara neman aurenki bataredana xo nasaurari ra ayin xuciyarkiba akan, hakan nake baki haƙuri hujjata ta aikata hakan itace inatsoro naxo neman soyayyarki,narasa kice anrigani komai xai iyafaruwa dani samha shiyasa nayanke shawarar aikata hakan, kigafarceni. Tasauke idanunta akan kyaƙƙyawar fƴuskarsa dake ɗaukeda murmushi yabirgeta sosai gayen yashiga ranta itama Nikuma rayyanatu anma kamar yadda kasani samha ake kiranadashi,. Gaskiya ne amma baka ƙyautava dakafara neman soyayyata afarko, xaifi tamiƙe tana haɗe rai Donhaka ni baxan soyayya dakaiba ameen Aidasauri yatari gabanta yana tsuma Karkimin haka,in kika gujeni ayanxu amatsayin ramuwa,kincutardani amatsayina na masoyi agareki. Takaudakai. Yakuma gewayawa inda tajuyar dafuskar ƴanahaɗa hannayensa dukka biyan kamar meneman gafara Tafashe da dariya tana riƙe bakinta "Yayƙyau kacinye Yaxaro ido Me nacinye, Tanutsu sosai tamkar ba ita ke dariya yanxuba Jarabawata tafarko mana saura biyu agaba kajirasu akodaƴaushe xasu iya xuwa gareka Yalumshe ido ƴanakomawa yaxauna Allahamdulillah,lallai tunda nacinƴe tafarko ina maitabbatar miki nagabanma nine mainasara.insha allah Humm tace tana murxa 'yan yatsunta nahannu Takallesa kunakama da maryam sosai, tawani ɓarin hartafika ƙƴau Yaɗanɓata fuska Waɗin ni hmm tab aimaryam mummunace ki kalleni kice muna kama Tai dariya shima yayi. Tohh kuwa tafikama ƙyau Yaharareta Kincimun fuskadayawa ammaxanrama,abindayasa baxanramaba yanxu,sbd karnaje ko wannanma nacikin sauran jarabawan, Ta ƙyalƙyale da dariya tana cewa Aa bawannanaciki allah Haka sukaɗantaɓa hiransu amatsaƴinsu na sababbin masoya xuwa mangaruba yayimata sallama yatafi,xuciyar cike da kewarta, Jikin umma tafaɗa tana dariya Shafa kanta tayi tana cewa Naga alama afuskarki samha allah yasatunanina yaxama gaskiya Taɗago tana damƙe hannun umma Umma hakane tunaninki wlh al ameen yayimin sosai ɗangayu ne umma gashi daƙyau kamar abba usman nakaduna, Dariya umma tayi Hh kai samha amma gaskiya al ameen yayi sa ah,inbanda abinki ai duk ɗayane shida abban naki usman tunda ƙanin alhajine, samha ta jijjiga kai Hakane umma toh ameen yafimaa abba fa Hhh umma ta ƙyaƙyace da dariya ke ba saikisa cikina ciwo kinga tashi kijeki cire kayannan kisa wasu kixo kikulamin da miƴarcan. Allahamdulilahi tunda dai yamiki, Tamiƙe tana ficewa. Ummu tunda al ameen yadawo yasata agaba yaketa bata labarin samha har maryam tashigo itama taxauna sailabari yake basu sukuwa mexasuyi inba dariyaba, umar ne yashigo tareda alhaji ɗan axeemi suna magana, Jikin ummu al ameen yabari yanatshi yarungumi alhji yashafa bayansa suna gaisawa yasakeshi yamiƙawa umar hannu sannan duk suka xauna anaɗan hira sama sama kafin alhaji yatashi yahaura sama, ummu tabisa, umar yayi musu sallama yatafi gidansa.al ameen yadubi marƴam cike da son amayar da maganar dake ƙunshe acikinsa Amma gaskiya ƙawarki nada kirki. Ya ya ameen ainasan samha sosai wlh ka aureta kasamu mace tagari Yayi murmushi, insha allahu ke su daddy fa harsun tambayomin kuma abby ya amince yaban samha abindayarage mufahimchi juna,mutaimaka muku kusha biki, Tai kwashe da dariya Lallaima yaya watakam ma muxaku taimaƙawa,hamm kutaimakawa kanku dai kaida ita. Ya harareta Ehmana ke da ummyna ai ina luradaku harso kuke kuji biki ko suna jikinku yahau ɓari da maxari,ƙafa na ƙaiƙayi anajiran ƙiras afice ana iyayi, Tashagwaɓe fuska tana hara rarsa Gaskiya kachimana mutumci yah amin, muɗinne haka xanfaɗama samha abindakike mana nida ummyna, Yaxaro ido Tace Donkuwa wlh ummyna mutuniyartace tanaƴinta sosai Yariƙe hannun marƴam Wayyo kiyi haƙuri karki rusamin xuciya Yaymaganar yanadafe ƙirjinsa, Tai fashe da dariƴa tana cewa Amma yaya gaskiya ka kamu dayawafa Yamurgina kai tareda miƙewa yanufi ƙofa Ke in anamaganar kamuwa kamuwaɗayama wlh har bansan yadda xanbuɗi ido inga rayuwar dababu samha acikinta naxaunaba, nima xantafi irin tata rayuwan ne mukasance wuriɗaya sabd itace farincikina, Yafice yana daddana waya tare da duban numbarta wacce ya amsa daƴaje itama ƴasamata tashi, 💛💛💕💞💛SAIKA AURI ƘAWATA💛💛💕💛(DAFIN SO NE) 👉 MATAR YAYA ce KADUNA Ummyna! Momy aysha ke kiranta tana ƙara gyara xama mayafin dake jikinta.tasha ƙwalliya cikin jar shadda maiɗaukar ido anmata aiki baki ga sarka tafkekiya awuyanta da awarwaro na gold daxobina,saiɗaukar ido suke,tamkar wata matar kwamishina,ko chiaman, Mommy momy har kinfito? Nafito xantafi in daddƴnki yafito yasaukeki amakarantar nikinga sauri nake Ummyna ta langwaɓar dakai toh momy ai inagama baxanje ba yau gaskiya Kallonta momy aysha tayi tana san gano wani abu gameda 'yartata Banason wasa fa ummyna kimaida hankali kingafa makarantar nan daƙaruwa sosai duba dayadda kika fara iyagirki yanxu da kalolin kayan fulawa, Tohm shikenan momy xanje saikin dawo Taimata sallama tafice Ummyna takoma ɗaki tana tunanin abindaya tsayamata arai tundataganshi take jin wani abu yatsayamata aƙasan ranta yaƙi tafiya,gatunaninsa da take duk inda tai fuskarsa take kallo ko rufe idanunta tayi shitake gani,har xuwa yanxu datagama yardarma kanta sonshi ne yakamata kuma batada wata dabara domin kullun ƙara axaƙxalarta soyayyarsa take idonta yarufe ba abindatake inba tunaninshiba, hartayanke shawarar faɗawa maryam koxata faɗamasa,amma itakam baxata iya furtamasa soyayƴartaba dakanta ba Donhaka takira maryam suna ta hira har maryam tace Nikam kinga banfaɗamiki ba ko kinsani ne ummyna tace Aa wlh bansan komaiba faɗamun Maryam tace Yaya ameen baifadamiki ba, Eh ummyna tace dasauri jin ance amin baifaɗamata duk saitunaninta yatafi akan shima sontayake.baifaɗamataba, dandanan farinciki ƴarufeta har murmushi yafara bayyana afuskarta, Maryam me yaya amin ɗin xaifaɗamin? Maryam tasheƙe da dariya Aa waƙa avakin mai ita aitafi dadi.amma nai mamaki da har ita rabin rannaki bata sanar dakeba Ummyna tai dariya, Kai wlh maryam kinfiye jan magana kinga bari nakira samha itaxanji abakinta komenene yakefaruwa Toh yawwa yafima kigaimin da momy da dady, Takashe wayar tana lalubo numbar samha takira amwa wayar akashe haka tahaƙura dk dataso ace taji komenene yanxu domin tagama yadda akan al ameen ke sonta ƴakasa faɗamatane, game xoma takama takeyi zuciƴarta cike ɗa tunani, Samha bayantadawo daga makaranta tasa almajirin gidansu ya amso matachajin wayar datakai kafin tatafi islamiyya, Tanakunnawa kuwa kiran ummyna nafaɗowa tai murmushi game da ɗagawa Angaida ummyna Ummyna tai dariya Nima nagaisheki wai inakika shiga kwana biyu samhat? Wlh ina nan karatune yaɓoyeni amma inata xuci xuci inkiraki ƴamomy da daddyna? Ummyna ta amsa Suna lfy ƙalau aiɗaxu nakira umma mungaisa dana kira wayarki naji akashe Ok wlh tana ɗanshamin chaji wayarnan kwana biyu xanba abby yasakemin Ummyna tai murmushi Kai samha yanxu ke avvy xaki takurawa yasayamiki waya ina saurayinki? Ko har yanxu kina nan da hanlinki Tai dariya ah haba ni na isa ai yanxu nasamu wanda nikeso Ummyna tace Kai masha allah naji daɗi sosai samhat allah yabarku tare Samhat tace Hanmn ke aibaki saniba yayan maryam ne nibansan indama yaganniba amma saikinga yadda yake bala in sona,like dai yadda nakeso wanda xan aura yakasance Suka tintsire da dariya ummyna gabanta yafaɗi bayansun nutsu Samhat yaya umar ko yaya al ameen. Al ameen ɗin Aitini ummyna tatafi hutun rabin loƙaci tamakar wacce tasuma haka takoma wayarma sai samhat ce tagaji dacewa hello hello taƙashe Kukatake sosai tamkar ba gobe sbd ƙuncin dayaxo ƴarufemata xuciya dandanan damuwa taxama abokiyar ummyna sbd ta tabbata baxatasamu ameen ba tunda yace ga wacce ƴake so kuma taƴi al ƙawarin cire soyayayyarsa aranta sbd baxata taɓa bari tarayu da soyayyar saurayin samhat ba sbd taɗauki samhat tamkar 'ƴar uwarta tajini batajin akwai wani abudaxai iya rabasu da ita, domhaka tundaga loƙacin tafara cire ameen aranta duk da abin yagagara saima ƙarajinsa take axuciyarta,bata da aiki sai addu ah da kuka tana neman taimakon allah akan yayayemata wannan bala in soyayyar datake tafama dashi kuma ta tabbata shi baisan tanaiba.momy aysha da daddy ƙwarai sunkula da ramar da 'yartasu daƴa tilo tayi harkayanta naƙoƙarin yimata ƴawa,amma koda suka tsareta da tambaya saitace vavu komai har daddy yagaji yaƙyaleta momy kuwa tana tambayarta saita fashe da kuka tanacewa ita ba komai, Yaukam ta tashi dason ganin al ameen a idanunta gashi kuma bagarinsu ɗayaba,falo tafito jikinta asanyaye take tafiya daddy yakalleta Ummy na kiwa allah kifaɗamana abindaƴake damunki,kinga kuwa yadda kika koma kwanakin nan Daddy yay maganar yana kamo hannunta kanta aƙasa tace Daddy karkudamu dan allah xanfaɗamuku amma bayanxuba kaji ɗaddy Yace shikenan amma kisaki jikinki daranki kidaina damuwa kidawo walwala kamar dah kinji kuma idan nadawo xami wata maganadake, Tariƙe hannunsa dake cikin nashi daddyna inaxaka dasassafennan Kano xani Tai tsalle axuciyarta tace Gadama tasamu xanje naga yah amin koxanji sassauchi acikin xuciyata Afili kuma ta langwaɓe kai tana cewa Daddy xani nima pls Aa vasaikin kukaba ummƴna shirƴa muje Tasaki murmushi tana shigewa ɗakinta taciko akoti dakaya tafito cikin doguwar riga daƙaramin hijjavi iya ƙirji dama tayiwankanta kenan tafito, Momy da daddy suka bitada kallo ganin kaya niƙi niƙi Aa ummyna dik wannan kayanfa ko ba biyoni xaki gobe mudawoba, Aa daddƴ ni xanɗan juma gaskiya. Momy taimusu adawo lfƴ suka fice sai kano, 💛💕💞💛SAIKA AURI ƘAWATA💛💛💕💛 (DAFIN SO NE) MATAR YAYA ❤️ Loƙaci xuwa loƙaci Awwab abbansa nakawosa gidan kahkanninsa yakwana yanaxuwa gidansu samha yayini suna hirada ita sbd shaƙuwan dasukayi.yaɗauketa tamkar yayarsa itama taɗaukesa tamkar ƙaninta, kuma yayi murna harda tsalle jin al ameen ne xai auri samha. Samhat nason Awwab,har addu ah take Allah yabata ɗa maiƙƴan Awwab,,haka ummah ma nason yaron,haka xataɗaukesa takaisa gidan xoo sudawo bayan tayo masa siyesiyen kayan xaƙi da besct . Haka xaikwana biyu inxaitafi har kuka suke tana jin badaɗi sosai inxaikoma gida. Maryam da ummu nakitchen suna aikin girkin dare saijin sallamar ummyna sukayi maryam takwaso dagudu tana rumgume ummyna saimurna kuma daddy yafice falon yabarsu anan sai murna suke ummu databiyo bayansa da roban ruwa da cup Sannunku daxuwa ya hanya ummmu tafaɗa tana maitsiyayamasa ruwan tamiƙa masa Allahamdulillahi hanya ƙalau munsameku lfy Lafiya ƙalau ai alhajinma yanxu yadawo yake faɗamun baku ƙarasoba nace eh Umhum aimuntsaya gidan bahbahne kuma taxaunar damu bari nashiga wurin nasa Alhj. Ɗan aximine yake saukowa fuskarsa ɗauke da murmushi Aa usman kunƙaraso kenan Daddy yafaɗaɗa murmushinsa tareda tarar ɗan uwansa Yaya allah yanufa Toh allahamdulillahi yayikyau tashi muje kaiwanka akawo ma abinchi Tashi ƴayi suna jerawa sunatafe suna hiransu na xuminchi. Maryam kwa kaitsaye ɗakinta taxarce da ummyna, tashiga tawanka takawo mata abinchi sukaci sannan suka fito falo kallo loƙacin mangaruba ake kira daddy da abba sukayi alwala sukatafi masjid sukuma umnyna da maryanm ɗaki sukatafi sallah. Bayansunƴi sallah sukama ummu sallama xasu gidan su samha, Taimusu adawo lfy suka fice Ehu samha tayi tana rumgumar ummyna "wayyo kece haka umnƴna yaushe kikaxo dan allah? Tasaki dariyan yaƙe domin bahar xuciƴarta bane Ɗaxu danko sallah anan mukayi, nifada daddyne Kai gaskiya najidaɗin ganinki amma kuma banji daɗin ganin wani sauyinba ummyna Murmushi suduka suka iita da maryam banda samhat dataimaganar kamar xataikuka Kushigo ciki natsayar daku acikin gida. Ɗakin umma suƙa shiga tana cikin bedroom Samhat takirawota Saiyau taga ummynan da samha kebata lbrin yadda iyayenta sika kulada ita. Suka gaishe da umma tasamusu albarka sannan tafice bed rom tabarsu suyi hiransu na ƙawaye Ummyna takallesu Nifa bantaɓa xuwa kano ba sai wannan karon Kai dan allah fa Samha tafaɗa Allah kuma inaso naxagaya sosai naga yadsa kanon take naji har wani take akemata (kano tadabotinbin giwa kodamai kaxo anfika) Maryam ta tari numfashinta Ƙwarai kuwa wannan haka yake Kinga maryam xamu nunamata gari watsƙila takasa komawa kauyensu Ta harari samha Maryam nadariya Tab allah yaƙyauta aini bamai rabani da kaduna, kuma ke kanki kinsan garinmu ba ƙyauyebane Hhh suka fashe da dariya Sannan samha ta kama hannun ummyna tana ƙara nutsuwa kafintaimagana Ummyna menene yasameki kikarame haka?ko kinyi rashin lafiyane bamusaniba, Hankalin ummyna yatashi dajin wannan maganar take kuma ciwon dake cin xuciyarta yafamu.lallai batada wata mafuta datawuce tace rashin lfy tayi Nima kuma inaso intambayeta kikarigani Ɗaya hannun nata taɗora akan na samha Hakane nayi rashin lfy kuma najuma akwance kawai banfaɗamukuba sbd kar hankalinku yatashi, Kai baki ƙyautaba allah yabaki lfƴ sistana Samhatace tana duban wayarta dake haske kira yashigo amma ameeting wayartake Murmushi tasaki tana sawa akunneta Bansan meyafaɗamataba tamiƙe tana murmushi, Ummyna ga al ameen can aƙofar gidanmu yace muje kinzo baigankiba har kunfito Dariya sukayi tareda miƙewa atare Ummyna tajidaɗin yadda ƴanuna kulawarsa akanta Haka sina fita yasauke idonsa akan tauraruwasa yana kashemata ido ta kaudakai tana yarfa hannu dayake su ummyna sunɗanriga fitowa amma duk da haka ummyna takula da abindaya faru amma taifuska tana ƙaƙalo murmushi sbd takori xuciyar dake ƙoƙarin tonamata sirrin dake ajiye aranta wanda har abada tai alƙawrin ɓoyeshi bamaisani koda kuwa soyayyar ameen xata xama ajalinta baxata rusa farincikin samhat ba sbd tafuskanchi yadda samhat itama take bala in son ameenɗin, Wasu hawaye masu ɗumi ke ƙoƙarin fitowa daga idonta dasauri taiƙasa dakanta tana ɗora ahannunta afuskar Wayyo idona wani abu yafaɗamun maryam Dasauri sukayi kanta su biyun maryam da samhat Tagoge hawayen afakaice tanacewa Ohhh kamar yaji wlh kunga nagoge ma Sannu dakinkawo nahuremiki Samht tace maryam tace sannu Aa aiyadaina kaɗanne xafinma yakemun yanxun Ameen dake tamurmushi yana tsokanar ummyna ta kallesa xuciyarta take kaƙarayin rauni amma saita ƙaryan dakai tana cewa Hakama xakace yah ameen Yasaki murmushi Ehmana inba rakiba daga ɗan abun yafaɗamiki ido, Sukayi dariya samhat tace Komai ƙanƙantarsa dai ailafiya yataɓa kaga kuwa bamaganar ragwanta Yace Ai dik ɗaya kuke dole kitaremata Sukai dariya Dik loƙaci xuwa loƙaci ummyna nafakar idaninsu tatsirawa ameen ido daya yi kamar xaijuyo saita ɗauke idanunta,sinyi hira sosai kafin suƴima samhat sallama sukatafi,sikabarta itada al amin sunata shan soyayyarsu, Saida suka kwanta maryam kefaɗama umnyna saranar yah amin da samhat gobe.ummyna saiyanxu tagane dalilin xuwan daddynta kenan, allahsarki batasan sanda hawaye ƴafara xubowa daga iɗanuntava,datasan hakane dabataxoba domin tasan dole saitakwanta tunda xuciyarta takasa haƙura taciresa acikinta lallaitasan tana tareda wahala, Maryam tini tai bacci amma ummyna tashi tayi tashige bathrm taci gabada kukanta daga ƙarshe alwala raɗauro tafito taxo tafara sallar nafila tana miƙawa allah buƙatunta, allah yaciremata soyayyar amin domin baxata iya auren saurayin samhatba sbd akwai amana atsakaninsu, Kamar yadda suka shirye ƙarfe goma daddy da alhj.ishu da manyan abokan daddy guda biyu suka tafi gidan malm sulaiman shima daga ɓangarensa yatara 'yan uwa anxo anyi abindatarasu kuma akatsaidaaure wata uku,. Akayi addu ah sannan kowa yakama gabansa.ranar al ameen kamar anmasa ƙyautar aljannah yadda yake ta ma su maryam ƙyauta harda ummu ,sukuma sai tsokanarsa suke ummyna sai fara ah take tana tilastawa kanta dariya da nuna farinciki, har tana yiwa al amin taya murna ita ƙyautar ƙuɗi yayimata yariƙe hannunta ƴana jinjina murnarsa Sololo takoma tanabinsa da idanu bakiɗaya yana kama hannunta dk wani abi yatsargomata tindaga ƙafa harkanta, kallonsa kawai take ba wanda yakula afalon da yake 'yan uwane akataru ba laifi anataya ummu murna, Umar ne yashigo ɗauke da ɗansa akafaɗa matarsa hadixa nabiyedashi abaya kallon ummyna yayi da al amin dake riƙe da hannunta hankalinsa kuma nakan tsohowa da mama bara sai hira suke shiyamantama da ummƴna daya janƴo Umar dakishi yakamashi yaja tsaki umar dama son ummyna yake tunda sukaje kaduna taron family yaganta yakamu da soyayyarta amma sbd jinkai yakasa ko nunamata alama balle ƴafurtamata.saiyanxu daya al amin riƙe da hannunta yaji kishi yakamasa da haushin al amin. Donhaka yanahaɗa ido da ita ummƴnan yaƙwalamata harara dasauri takwace hannunta daga ameen tana ficewa ɗakin maryam dasauri.tajin wani tsoro na umar sbd masifarsa,tunsuna yara insukaje daxaran sunlaifi xai xaxxanesu,gashi baida fara ah yayta tamke fuska, Yinin ranan gidan ummu 'yan uwa akaitaxuwa taya murna sai dare kowa yakama gabansa, loƙacin daddƴ yake shirin tafiya gobe dasafe dama tun agida ummyna taxo dakaya dayawa xatajuma Dagari yawaye ƙarfe takwas daddy yaɗau hanyar kaduna, Gidan abby kuwa nan watace sabuwa domin ummei sam batasan ɗa al amin ɗangidan ɗan aximi xa ahaɗa auren samhat ba saijiƴa da akasarana,takeji, sannan ƙuma babbar damuwarta da abby yace yabawa haulat sati biyu tafito damiji yahaɗusu da samhat ko shi yaxaɓamata amasu xuwa neman aurenta,domin anaxuwa wurin abby neman auren haulat.take ƙin aminxewa sabd xigar ummei namaiƙuɗi xatabawa 'yarta, Yanxu kuwa yabuɗemusu wuta akan inbata ƙawo wanda takesoba tohkuwa xaixaɓa mata dakanshi. Ummuce xaune afalo ummyna da maryam namatsa mata ƙafafunta, Al ameen yashigo kamar kodayaushe fuskarsa ɗauke da murmushi cikin shadda ruwan xima maihaske dahula ruwan xima dajakarsa taoffice, Ummu hartafara gyangyaɗi jinmaganarsa yasa tabuɗe idanunta akan ɗannata Au al ameen dama baka fitava Yayi murmushi Banfitaba ummu bayan mungama breakfst nashiga ɗaki sainakwanta naƙarayin bacci saiyanxu nafarka naga har rana yafito. Kai aikaine akwai wasa al amin toh aisaikai sauri katafi kagama kayi lt. Yayimata sallama tafice su maryam naɗagamasa hannu, Ummƴna takalli maryam bar xanje ɗaki nadawo Kafin maryam tace toh ummyna tahaye sama dasauri. Jikin windon dake fuskantar farfaajiyar gidan taƙasara dasauri tana sauke idanunta akan abindatasaba tsayawa kallo kullum safe da loƙacin dawowarsa Cikin tafuyarsa taƙasaita da isa yake takawa,fuskarnan asake gawani kyau dayake dashi gwanin birgewa dogone maiɗan faɗinƙirji dai daishi, fuskarsa gewaye rake da ƙasinba,baƙa ƙirin harɗaukan ido take haka suman kansa yakwanta lub lub hartaƙasan hulansa yafito yakwanta Ummyna tashagala dakallon al amin tareda lissafa yadda yahaɗa duk wani abu da takeso mijin aurenta ƴa mallaka, Har yashige mota yayimata key yafice batasaniba saiganin get man taiyana maida get yanaxugewa,tai dariya,dan itakanta yanxu dariya take bakanta domin tasan zuciyarta yaudararta take akan al amin donbaxata taɓa aurenshiba mutiƙar samhat takasance matarsa,daliline kawai itama tarasa naƙincire wannan soyayyar tasa datake tadakonta aƙirjinta, Takoma gefen gado tanaxaunawa tare da tallafe fuskarta da dukkan hanayenta tafara faɗawa tunanin sarauta dake sonta sadeeq yake nick name nashine sarauta,mafita kawai xata amince sadeeq yaturo iyayensa ta aureshi inbahakaba soƴayyar amin xata hallakata. 💛💞💛💛SAIKA AURI ƘAWATA💕💛💛💕💞(DAFIN SO NE) MATAR YAYA ❤️ Ummie kinsan halin avvy wlh xai iyaxaɓamin dikk wanda yagadama kuma badamuwarsa bane danyahaɗani da talakan talak muyabari aruwa Haulat taimaganar tana sharar kwallah Knga nifa banason sakarchi menene kuma nakukantoh ehye kekina ganin daraina ina numfashi adoranƙasa xaki wahalane wlh vaxaiyuwuba ainii tinranan dayayimun maganar adaren banbacci ba saidana yanke shawarar abindayakamata muyi kuma shine kaɗaimafita. Haulat takalli ummie tana share ƙwallah Yawwa ummeina yanxin nafarajin sanyi domin nasan shawarrki mafitace kaitsaye,agaremu Ummie tai dariya Kinsan abindanayanke shawara akai? Haulat tace aaa saikin faɗa ummie Yawwa abindaxa ai yanxu ina alhji ghali wani saurayinki dayake ɗaukarki kunafita naji kwankin baya kina faɗamun ƴace xai aureki inkin amince Hault tace Eh hakane ummie amma ni gaskiya baxan aureshiba Ummie taxaro ido Lallai ke shashashace haula tavbas naga bakyaƙaunar farincikina kumadama masu iyamagana sunafaɗi 'ya macce taƙi gidan daɗi.toh kwa nagani agabana,wlh tallahi infaɗamiki inkinki wanann alhajin tohkwa kinxo ubanki yaxaɓamiki wandaxakuxo kuna ƙaƙanakayi donkinsan baƙaunarki yakeba balle yaxaɓamiki nakirki irin na 'yar uwarki, nikuwa kinsan bana xama inda ba arxiki wlh sakinki xan inbartakanki nakama sana o ina, Haulat tariƙe hannun ummie tanamagana Ummie ba akan komine banason na auri alhaji ghli ba sbd matarsa 'yar masiface shikansa bata barsaba balletana ni daba kowaba, kuma yaransu biyar dashi amma batadaina axabtar dashiba da masifa,ba Ke da allah can gafara kanwaccan shashshae dakika kwatantan halinta xakibi kiwani ruɗu yoo duk masifarta takaini ne 'yarjakar uba kinga share wannan gidahumar haulatuna domin tacancanci acireta alayinta mata wlh tinda tarasa hikimar lallashin miji saidai tacikashi da masifa kullum toh wlh asarar riyace,kuma yaxama dole mudage muxage dantse muƙwace mijin taje can taci masifar, Haula tai dariya tana daɗa samun ƙwarin gwiwa daga mahaufiyarta nan suka cigabada tattauna har suka tsaida magana akan xa aje gun malm na tudu kafun aiwa alhji magana yafito donkarma yakawo wani rainin wayo. Xaune suke kan kujerun roba aƙofar gidan su samha kanakallon masoyan kasan sunason juna daga yanayin yadda suke tafi da firan nasu dayadda fuskokinsu suke cike da farinciki maiwuyar musaltuwa. Yakafe ta da idanunsa yana murmushi Ameeen Takira sunansa tareda jan sunan Aiharcikin ransa yaji wannan kiran rikitattun idanunsa yawatsa mata yanasauke kƴakkyawar ajiyar xuciya cike dakulawa yafaramata magana Kamar kinfi kowa iyafadar sunana tawan,wlh daxaran kinkiraa sunana sai inji harcikin raina sunana yafi daɗi abakinki kinfi sauran mutane iyafurta sunana kinabawa kowanne harafi haƙƙinsa, tattausar murƴarki maidaɗi harbanaso tayanke faɗar sunana Tai murmushi Duk wani salo naxuga ka iyashi wlh wai niɗince duk haka Yaharareta Badan amarya bata laifiba dakinyi yanxu, Tace Karka adana laifina kafaɗamin koxangyara Bafaxaki laifiba,agurina,karki manta ke amaryace amaryanma kuma ta al amin ɗan aximi, damma kinaso kisawa ango raxani ne Taxaro ido Wayyo ka ajekomai kafuskanchi amaryarka amin Yakalleta saikuma taji kunya Dama dam dam tahau inna ina Kinsan menene komai nafaɗa akanki gaskiyane samhat sainaga kamar bakiyarda dayabon nawa ba alhalin ninakeda alhakin yabonki najinjina miki daxaran kinyi....... Yatsaya cak ganin yadda take kallonsa kamar maishirin kuka Menene xaki kuka samhat? Taiƙasa dakanta Abindakake faɗa ne .... Yajinjinakai cikin lallashi Toh yihaƙuri nayi shuru dabakina Taɗago kai takallesa saitaga yasa hannu abaki tamkar anɗagawa yaro kara ance yariƙe bakinsa Yakashe mata ido Taimurmushi Ameen ba bana yadda dayabonka gareni bane,aa inaganin kamar bankaiba s.... Yadakatar da ita aa kinkai harkinfi yadda nake faɗamiki wlh dakinsa yadda kike dabaki furtakomaiba,sbd acikinmata samun irinki yanabala in,wahala.samhat kina da ɓoyayyen ƙyau maijanhankali, daxaran mutum yanutsu yagane wacece ke,toh koda kuskure baxaiso rabuwa dakeba,dohaka nibaxan dakataba wajen ƙara faɗamiki ba.sannan ki adanamin kanki.keɗin amanace wakanki nabaki. Bakiɗaya jikinta yamutu yayi sanyi tarasa yadda xatayi tanaɗaga kai tahango mas'ud daf dasu atsaye yaƙuramata ido ransa aɓace tamkar wani yaki, jikintane ƴashigarawa acan ƙasan ranta tafurta Yaushe yadawo Dasauri tafice ta nufi gida duk yadda al amin yadikkan kiranta batadawova. Tsayawa tai cak data shiga suron gidan sakamakon cinkaron datayi da ummyna jingine da bangon soron giɗan tanakwasar kuka kamar an aikomata da ga kaduna momy aysha tarasu,dasauri samhat tarumgumeta xuciyarta cikeda mamakin meyakawo ummyna soron gidansu, tafara lallashinta Lfy ? Ummyna lfyarki kuma? Menene yasameki dan allah ? Ummyna wacce fargabada tsoro yadirarmata axuciya tashiga ruɗani da tsaka maiwuya gaxafin abindake damunta najin irin masayar ƙalaman da al amin da samhat kewa junamasu nuna tsantsar soyayya, dakulawa.gakuma yadda samht tasameta talaɓemusu.batada amsa ko mafita shikenan asirin xuciyarta xaitono.shikenan xumincinsu da samht xaixama sheƙaƙƙe, Maganar samha rakuma dawo daita daga tunanin data tafi taƙara fashewa dakuka Samhat tace Mushiga ciki Ta tirje tana girgixa kanta tareda yarfa hannun nantake shawara tafaɗo mata domin farko ɗaxu data shigo gurin ummataje xasugaisa tasameta batada lfy xaxxaɓi maixafi yarufeta ranskwance sairawar sanyi take,saitamata sallama tafito ganin avvy yashigaɗakin. 'yar uwa ummah Ummah Take samha tajahannunta suka ruga cikin gida ɗakin umma samha tafaɗa ummyna namara matabaya Kamaryadda ummyna tabarta haka take yanxuma daƙyarma take iyabuɗe idanunta, Wani kuka samht tasaki tana rumguma ummah dika jikinta tana kuka saiyanxu tagane dalilin kukan ummyna allah sarki ashe haka tadamu da uwata lallai ummyna 'yar uwace tagari. Kuka suke tare saiga abby yaturo ƙofan yashigo tareda dr, daƙyar abby yasamu suka tashi domin adubata, Gameda al amin kuwa ganin taƙi ko juyowa yasa yaƙaɗa kaiyahau mashin ɗinsa yafice aɗari.sambai kulada mas ud ba dake tsaye ba sbd yadda kansa yaɗau ruɗu Mas ud kuwa wasu siraran hawayene suka sauko akan kumatunsa nabaƙincikin yadda yanaji yanagani xairasa farincikinsa, wacce tintana yarinya yaɗauki soyayyar duniya yaɗoramata Inna dake ƙoƙarin naɗe sallaƴan dataisallar isha i taxauna tai laximi tashafa fatiha kenan yashigo awani rikice idanunsa jajir alamun yacikuka harya gode allah mas ud baxakaji maganataba kenan, nafaɗa maka kadaina xuwa kanatsayawa aƙofar gidansu balle harkagawani abindaxai dameka,tunda kadage kai baxakacireta aranka ba, toh haryaushene xakaɗauki shawarata akan karavu da yarinyarnan donme xaka sawa rayuwarka takunkumi kana takura kanka,akan abindayayimaka nisa,karkamanta saura wata biyu bikin yarinyarnan, dan allah karufamin asiri karka kashe kanka da damuwa mas ud. Takama hannunsa jikinta yaxuve yana kuka sosai kamar ƙaramin yaro Shikenan inna,amma nayi babban rashi.baniɗa tamkar samhat,sbd nariga danasata araina,inna bansan ta indaxanfara ciretaba Kayi haƙuri shine kaɗai mafita mubamu da ƙuɗi kaga kuma maiƙuɗi akabamawa.saimu miƙa lamarinmu ga allah shine kaɗai xaimana kamar ƴadda yay musu Yalafe jikin ina ƴanacigaba da shrar ƙwallah. Likita nagama duba ummah yaba abby ktin abubuwandaxa asyo magungunane ciki harda ruwa abvy yaje yahaɗo likita yaɗaura mata ruwan sannanyay musu sallama yatafi Ummynada sammhat sukagyara ɗakin tsab Harsaida ruwan da akasama umma yakare tatashi sikataimakamata tawanke jikinta ,ummyna datakanta taɗauko abinchi tanaba ummah abaki samht nagiogemata baki hartaɗanci balaifi ta ɓaɓɓalo magungunan daxa abata tasamata abaki da kofin ruwa tasha sannan tagogemata bakin samhat nagefe tanakallonta sai farinciki takeji tanaƙarajin ƙaunar unmyna harcikin ranta tana fatan allah yakawo loƙacin daxatamata itama watabajinta Ummyna tariƙe hannun umma Umma bari natafi saida safe allah yabaki fy Umma tashafa kanta Nagode ummyna allah yayimuku albarka Tamiƙe tana miƙawa samhat hannu Kamawa tayi tana miƙewa Muje narakaki Harkusa da gidan kaɗan yarage taƙarasa da ita saikuma tatsaya Nagode sosai dayadda kike nunaƙaunarki da kulawarƙi akn mahaifiyarmu ummyna allah yabar xuminchi Ummyna tamurmushi amin bakomai samhat mahaifiyarki ai mahaifiyatace.karkiji komai iyaƙoƙarina xanyi danganin xumincinmu bairusheba. Samhat tai dariya Nima naimiki alƙawarin hakan ba abindaxaitaɓa xumincinmu. Sannan sukai sallama tana tsaye sotake tagashigar ummyna

Chapter 4 of 9