Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 11
yace " ku ajjeni a waje zafi nakeji "dan har lokacin gumi yake,sannan a lokaci guda jikinsa na karkarwa. "Hashimu" ya fada a lokacin da wani farin abu kamar kumfa ya fito daga bakinshi,sai yasa hannunshi ya goge "ka kiramin inna"ya fada hawaye na zuba daga idanunsa.wanda koshi bazai ce yasan da zuwan hawayen ba,kawai yaji suna bin kumatunsa.amma ba tasu yake ba,innarsa yakeso ya gani "a bari sai da safe yanzu darene kar a tada mata hankali" hashimu ya fada shima yana hawayen,wanda tunda ya fara daga kofar gida har yanzu be tsaya ba "ita kadai gareni sai sadiya,ka kirawota ita nakeson gani " ya fada yana mai riko hannun hashimu "ka kirawo masa ita tunda yanason ganinta"mai machine din ya fada. "Toh"ya fada kamar bayason zuwa ?dan har baiso a fadi silar abin saboda yasan dole sunansa zai fito.wato ace "fada ake da hashimu shine ya shigar masa" dan kowa yasan tasi,u mutum ne marar hayaniya bashi da abokin fada. "Lpy"sukaji muryar matar hashimun tana tambaya dan bacci take, takejin magana sama sama, shine ta fito aikwa tayi tozali da tasi,u kwance cikin wannan halin."ni ne sila"hashimu ya fada ai nan take sadiya ta tsaya da kukan da take dan tunaninta hashimun ne ya masa raunin kan nasa, dan taga kan da me ma machine dn nan ya haska.sai kawai ya juya domin fita daga gidan,zuwa kirawo inna sarai.". Allah kara afuwa "mai machine din nan ya fada yana bin bayan hashimu, " amin nagode" tasi,u ya fada har lokacin wannan farar kumfar tana fitowa daga bakinsa. "Na wuce Allah kara afuwa"ya Veda hashimu lokacin da suka fito kofar gida yana kokarin hawa machine din, "malam ga Wannan mun gode sosai da taimako"hashimu ya fada yana mika masa dari biyu "wlh ka barshi Allah bashi lpy,kuma Allah ya saka masa" "mun gode" hashimu ya fada yana tafiya dan zuwa gidan inna. shi kuma mai machine ya kama hanyar rugarsu,yana jimamin abinda ya faru.a bangare guda kuma yana ganin sai kwana ne zai tashi marar lapiyar.domin kuwa akwai wani kawunsu da irin haka ta sameshi,amma shi dutsine aka kwala masa kafin ace sun nemi machina sun tafi baban asibiti a wani gari,har ya fara fidda kumfar nan daga baki.suna zuwa likitan yace ai kwalkwalwarsa ce aka daka dan Wannan kumfar daga kwalkwalwar kanshi yake fitowa,kafin azo ga bashi taimakon gaggawa rai yayi halinsa. ya dade tsaye a kofar gidan yana tunanin shiga,kafin daga bisani yayi shahada ya shiga.kafin yakai ga yin sallama sai ganin inna yayi gabansa,tana kuka ta nufoshi tana tambayarsa me ya sameshi,domin nafarki tayi yana cikin wani mayuwacin hali.Shine fa ta kasa komawa bacci take kuka tana additional,,a Allah yasa ba wani abinne ya sameshi ba." Bashi lpy ne, shine yace in kiraki "ai kafin me wannan inna ta ware dankwalin kanta irin na tsofaffi ta yafa sun fito suna sauri. Lokacin da suka isa gidan har tasi,u ya fara fita hayyacinsa "wayyo babangida me ya sameka"ta fada tana kara karfin kukanta dan ganin halin da yake ciki, "innaa" ya fada kamar an fisgo maganar daga bakinshi "gani babangida ko baka ganina"ta mika hannu ta kamo nasa hannun." Inna ga ...sadi..ya nan nasan ...zaki ku...la da ita da abin....da za...ta haifa"ya fada yana mai ciccira kalmomin domin tari daya sarkeshi da kuma kumfarnan data yawaita fitowa sosai,danma sadiya tana goge masa da dankwali."duk da na...san ke...ma baki....da mataimaki....sai tarin ya kuma sarkeshi kumfa mai yawa ta ambulo,sai yaci gaba,sai Allah" inna ga abin...da sa...di...ya za...ta..hai...fa sai idon ya kafe lunfashin ya fara jayuwa da kyar,cikin yana sama yana kasa har rai yayi halinsa.... Allah sarki rai bakon dny=?-? Allah jikan mahaifanmu Amin. ؚ?B ?p?>?p?>?p? "To da ke tunaninki wacece MARYAMU" inna sarai ta fada tana kallonta da kuma son ta gano manufarta. " wai kina nufin Wannan yarinyar ce MARYAMUN da kika ce zamuyi maganarta, dama MARYAMU aka sakawa yar sadiya,ni wlh na dauka wata MARYAMU babbace zamuyi wata magana,dan na daukama ko kuli kulina zata sara" lantana ta fada cikinta mamaki daya baibaye mata zuciya. "Kuli kuli kuma lantana?" Inji inna sarai "eh mana"lantana ta fada. "Kuma a rasa wanda zai kawo miki abokin cinikin kuli kuli sai ni"inna sarai ta fada tana nuna kanta da yatsa. "Yo idan Allah yasoka da ciniki duk inda yake ai sai yazo gareka"cewar lantana cikin fada fada dan yanzu ta gama gane inna sarai magana tazo mata da ita akan talle (marainiya) wato MARYAMU. "Yanzu dai inajinki da wacce kika zo"lantana ta fada tare da mikewa domin sauke dambun data dora ya nuna."to ai sai kin dawo kin zauna zamuyi maganar kokwa" inna sarai ta ce yayinda da take ta jijjiga MARYAMU dake kuka,dan kukan na taba zuciyar inna sarai saboda tasan koshine batayi da madarar data bata ba,shisa take faman kuka."zaki iya maganarki ni dambun nan ma zan karkasa,dan yunwa nake ji kamar me.cewar lantana tana jera Kwanikan da zata kasa dambu. "Lantana dago ki kalleni dan Allah" Inna sarai ta fada lokacin da hawayen halin da suka samu kansu ita da marainiyar Allah(MARYAMU) yake ita rashin danta tasi,u ne ya sanyata a halin da take ciki,da yana raye tabbas bamai wulakanta ta=?-? haka kamar yadda mutanen rugarsu suke mata da kuma lantana dan sunga bata da kowa=?F? @&? Ita kuma MARYAMU rashin iyaye,musamman mahaifiyarta sadiya,da sadiya tana raye lallai ba mai neman nonon lantana, bare aje ga bata na akuya." Ya ilahi" me ya kawo kuka kuma kamar gidan mutuwa inna"lantana ta fada baki cike da dambun data afa a baki wai nan tabin manda akayi=?? shine aka cika hannu akaci "haba lantana sai yaushe ne zaki tausayawa yarinyar nan ki karbeta,ni wlh ko da bazaki iya shayar da ita ba zuwa a yayeta ba,to dan Allah ko wata takwas ne ki barta tayi,nasan zuwa Wannan lokacin tana cin abinci,tana shan koko.kuma nasan zuwa lokacin na samu yadda zany,wlh ko rugar tamu sai in bari saboda RAYUWAR MARYAMU". "Sannan na samu inda zan koma,na samu tsayayyar sana,a wacce zan iya siya mata koda madarar bature ta gwangwani ba ta akuya ba,wacce ko roka nayi ba,a bani ke koda siya zanyi wlh bame saidamina dan yau ma koko na karawa ruwa na bata " ta fada tana share hawayenta da gefen gyalenta. Wanda zuwa lokacin jikin lantana ya danyi sanyi,amma ba sosai ba dan ba alamar saduda a tare da ita."nifa inna duk abin nan da kike ba,aje ga haka ba,meye kuka"lantana ta dawo kusan inna Sarai dauke da dan chaina, wanda ta zuba mata danbu a ciki."abin yama wuce haka lantana ya kikeso inyi da yarinyar nan idan tana kuka rasa me zan mata nake ko cikin dare haka zatayi ta kuka kuma wlh ba komai ke damunta ba sai yunwa sai dai nima intayin kuka=?-?. "Da ace bana shayarwa zan dauketa in shayar da ita,amma nima goyo nake to ya kikeso inyi da nawa dan" cewar lantana" ni wlh bawai sai kin bata nonanki ba,tunda kina ganin bazaki iya shayar dasu su biyu ba,to ita kike na akuya tunda kuna da kiwo gasu nan,amma ni acan bana samu wlh lantana" inna sarai ta fada "Bazaki fahimta ba nifa bazan karbeta ba na gaya miki tun ran sadakar ukun mutuwar sadiya,bayan nan ma zuwanki nawa gidan nan wai akan me zakina zuwa har gidana jina daga mun hankali,duk akan jaririya bandama gudun wahala da kikeyi mezai sanya kike neman kai da jikar da ita tilo kike da ita" "Mubar maganar nan,kuma har duniya ta nade bazan kara kawo MARYAMU wurinki da sunan ki shayar da iyaba,nima ina zuwa ne dan nasan bata da uwar data fiki,daman tunda mahaifinki ya tsawatar miki akan ki karbeta kika ki kuma yace bashi bake,amma hakan besa kin karbeta ba ai banga wanda zaisa ki karbeta ba tunda ke baki da imani" "Anki a karbetan ni naga mata da karfin hali wlh, kamar ni na kashe mata uwar zaki damu da sai na bata no no" Bata bukata ki rike kayanki,abu guda na sani shine da ace kece kika mutu kika bar jaririya wlh nasan sadiya sai ta shayar da abinda kika bari koda kuwa goyon tagwaye take,kuma sai ta nunawa yaron so da kulawa fiye da wanda zata nunawa yayanta"inna sarai ta fada tana goya MARYAMU dan tayi barci saboda kukan da tayi. "Wannan kuma fadarki ce" lantana ta fada tana daukan danta dake kuka,wanda ta kwantar a kasa kan dangoyo . "Zo yaka,yo kake kuka ga gyatumarka a kusa kai ba maraya ba"ta fada da gayya dan ta konawa inna sarai rai."gashi innar rugar marayo ki bata" yahuza ne yake mikawa inna sarai madara a cikin wani koko,yayin da sarai ranta yakai kololuwar tashi ta sunkuya daukan ledar kayan MARYAMU. COMMENTS DINKU SHINE KWARIN GWIWAR YAWAN TYPING NA

Chapter 2 of 11