Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wa nayi na kalle shi ba tare da na amsa ba.

Ci gaba yayi da cewa "nasan kina jin haushin abin da na miki ran da muka fita ko? kina d’auka na a mara adalci wanda yake k’ok’arin matsa miki, a guri na ba haka na d’auka ba, du kina miki haka ne ke da Anisa dan ganin yadda yanzu rayuwa ta koma, nasan nan gaba za ku gane hakan, za kuma kisan dalilin da yasa nake miki haka, anyway ga wata sabuwar waya na kawo miki, ina fatan za ki min uzuri akan wayar ki da na fasa".

Mik’o min wayar yayi na k’i amsa saboda yadda zuciya ta ke tuno min san da ya fasa min d’ayar wayar inda a gani na ko zai yi amfani da wannan damar ne ya samu hanyar k’ara cusguna min.

Wata zuciyar kuwa ingiza ni take yi akan in amsa tun da shi ya fasa min wayar.

"Fatima, ba ki da wani za’bi da yafi ki amshi wayar nan, dan ba zan koma da ita ba" abin da yaya Faruk yace kenan.

Ba ni da za’bi da ya wuce in amshi wayar dan nasan kafiyar shi.

"Na gode" na furta mai a gajarce.

"No need to thank me Teemah, komai zan iya miki ke da Anisa saboda ku k’anne na ne".

"kamar gaske" abin da nace a raina kenan.

Jin kiran sallar magrib yasa yaya Faruk ya mik’e da niyyar tafiya masallaci, ni kuma na koma cikin gida.

Ko da na shiga d’aki, kwalin wayar na bud’e naga model d’in wayar Tecno K7, ko ba a fad’a min ba nasan babbar tawa ce saboda ni a da ina rik’e Tecno W4 ne.

Dad’ i ne ya kama ni, ganin na samu promotion.

Bayan sallar magrib ne na ji shigowar yaya Faruk da yaya Aminu, da alama had’uwa suka yi gurin shigowa.

Zama na nayi a d’aki yayin da na jona sabuwar waya ta a charge.

Ban fito ba sai da nayi sallar isha’i dan nasa yanzu Abbu zai fara tambaya ta.

Zama nayi akan kujera ina jiran fitowar su, shigowar yaya Aminu da yaya Faruk ne ya katse min shirun da nayi.

Guri su ka nema suka zauna yayin da yaya Aminu ya kalle ni.

Da sauri nace "sannun ku da hutawa, ina wuni yaya Aminu" saboda nasan yanzu sai ya fara min fad’a dan shi ma kamar yaya Faruk yake, sai dai shi ya fi shi hak’uri.

"wai dama kina cikin gidan nan tun d’azun amma ban ji motsin ki ba" yaya Aminu ya tambaye ni.

"ina ciki, ina yin wani abu ne a ciki" na ba shi amsa.

"yayi kyau"abin da yace kenan, ya juya ga yaya Faruk suka ci gaba da hira.

Shi kuwa yaya Faruk tun san da yaya Aminu ya fara min Magana naga ya maida hankalin shi kaina, ko me yake so ya gano? Oho mishi.

Ummu ce da Abbu suka zauna aka ci gaba da hirar dasu, duk hirar da suke yi sauraren su nake yi kamar ba na gurin ganin yaya Khalil ba ya nan, sai naji hirar ta ginshe ni.

Ummu ce ta umarce ni da in d’akko food flask akan dinning a ci abincin a falo ba sai an koma kan dinning ba.

Serving d’in kowa nayi na nemi guri na zauna nima na fara cin abincin.

Muna cikin cin abincin ne yaya Kalil ya shigo parlour d’in yayi sallama.

Amsa masa muka yi kana yazo kusa dani ya zauna.

sannu da gida yayi wa Abbu da Ummu, ya gaisa da su yaya Aminu.

Spoon d’in shi yasa a cikin abincin na muna ci muna hira k’asa k’asa.

Bayan Abbu ya gama cin abincin ne ya kalli yaya Faruk ya kira sunan sa

"Faruk".

Tattaro hankalin shi yayi ya mik’a shi ga Abbu dan jin mai zai ce mai.

Abbu ne yaci gaba da cewa "Lokaci yayi da ya kamata ace ka ajiye abokiyar zama, rayuwa ba za ta tafi ba sai da abokiyar zama, ya kamata ka bincika ka samo matar, kai kan ka za ka fi jin dad’in aikin ka da mu’amalar ka da mutane".

Had’a ido muka yi a lokacin da Abbu yake mai magana, ganin kallon da yake min ne yasa na kau da fuska ta.

Cikin ladabi yace "insha Allahu Abbu na kusa fito da matar da zan aura, akwai abin da ya tsayar dani ne shi yasa, amma a taya mu da addu’a".

"Ana nan ana muku Faruk, Allah ya za’ba muku na gari da kai da ‘yan uwan ka". Abbu yace dashi.

Yaya Faruk ne ya amsa "Amin Abbu" .

Nan ita ma Ummu tayi ta mishi nasiha akan ya kamata ya fito da matar aure..

A raina kuwa cewa nayi "mutum ya girma amma yak’i yin aure ko mai yake jira? Gwara ma Allah yayi ya kawo mishi matar yayi auren ko ma samu sauk’i".

Ummu ce da Abbu suka mik’e suka mana sallama, suka nufi side d’in su.

Yaya Khalil ma sallama ya mana ya tafi d’akin shi saboda yace min yau bacci yake ji da wuri.
Ya rage daga ni sai su yaya Aminu muka rage a falon.

[4/6, 22:04] Mrs Mansoor: *MAKAUNIYAR SOYAYYA*💝💖💞


🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀


*STORY & WRITTEN*


*BY*


*MARYAM AHMAD PAKI*





*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*🤝🏽




*Wannan shafin naki ne*

*Nasiba Isma'il Uba* (marubuciyar Sanadin Aboki)💞

*My friend ina miki fatan alkhairi*





*MUNA TARE*❤

*'yan Mufy & Maryam A Paki fans*

*Maman Walida*

*Auta mama*(Aisha)

*Tawerh*

*Hajara Tijjani*

*Ramlerh*

*Hauwa Hussaini*

*Queen Aysha*

*Maymoonah*

*Fadeelah*

*Barrister Teemah*

*Har kullum ina tare daku ‘yan group d’ina da kuma son da kuke ma wannan novel d’in*.

*Ba abin da zance daku sai godiya*

*Sauran da baku ji sunan ku ba za mu had’u a next page*.


*Tawerh ina miki fatan sauk'i, Allah ya baki lfy yasa kaffara ne*




*Question of the Day*

K’ofofin aljanna guda nawa ne? Lissafo sunayen su.




35&36


Maida hankali na nayi gaban allon Tv ina kallon tauraren d’an adam a tashar MBC Bollywood, jefi-jefi nake jin hirar tasu.

Yaya Aminu ne naji yana cewa yaya Faruk "kai ma Soja ya kamata ace ka fito da matar aure, tun da iyayen mu sun nuna suna son kayi aure, in kuma baka fi son azumi in yazo a fara kad’a maka ganga ba"

Murmushi kawai yayi kana yace "very soon insha Allahu zan gabatar da wanda nake so, kafin in koma aiki zan zo in same ka akwai maganar da nake so muyi" cewar yaya Faruk.

"Ok sai kazo" ya bashi amsa.

Yaya Aminu ya mik’e cikin wasa ya kalli yaya Faruk yana cewa "ni zan gudu, nasan madam nacan na jira na, kai ko k’arfe nawa zaka kai a waje ba matsala, ba mai tambayar ka".

Shima mik’ewa yayi yace "nima tafiya zan yi".
Sallama suka min suka tafi.

Kasancewar yanzu ba ma zuwa ko ina tun da muka zana SSCE exam d’in mu, Abbu ne yasa yaya Khalil ya siyo mana form ni da Anisa a Al-Mannar Academy na shiga Mutawassid tun da mun yi saukar Al-qur’ani.

Bayan mun cike form ne muka fara zuwa makarantar.
Daddy form d’in computer training yasa yaya Faruk ya amso mana a Bintalya computer institute.

Sai ya zamana yanzu ba mu da wani time, da mun dawo daga computer training, ba jimawa zamu tafi islamiyya, ba mu zamu dawo ba sai yamma.

Yanzu tsakani na da yaya Faruk ba wani takurawa, ni gani nake yi neman shiri yake yi dani saboda yadda yake d’an ja na da wasa da kuma hira.

Duk wannan abubuwan da yake yi ba wai na sake dashi bane saboda sanin hali.

Yau ranar ta kasance ranar lahadi, yaya Faruk ne cikin shirin shi ya fito ya shiga side d’in Momi, bayan sun gaisa ne yake ce mata zai lek’a gidan yaya Aminu ne, fatan a dawo lafiya ta mai da sak’on gaisuwar ta ga Anty Jiddah da Humaira da Nabil.

Kafin ya isa gidan sai da ya tsaya a wani super market, ya tsaya yayi wa su Humaira da Nabil shopping.

Da isar shi gidan ya same su a falo da yaran suna kallo, su Humaira kuwa sai murna suke yi da ganin yaya Faruk saboda yadda yake kawo musu kayan zak’i da kayan wasa.

Hannu ya mik’a wa yaya Aminu suka yi musabaha kana ya samu guri a d’aya daga cikin kujerun dake kewaye da falon ya zauna.

Anty Jiddah ce ta gaishe shi tana tsokanar shi tana cewa "su Anisa ba su baka sak’o na ba?

Ta’be baki yayi yace "wane irin sak’o ne".

Dariya tayi ta d’aura da cewa "ce musu nayi su ce maka ka bani za’bi in za’bar maka mata tun da kai naga har yau ka k’i fito da wacce ta yi maka".

Murmushi yayi yace

"Madam kenan, ke kin san class d’ina yafi a ce za aza’bar min mata saboda ba ki ga yadda ‘yan mata ke so na ba a Kaduna da Abuja, infact nan ba dad’e wa ma zaki ga wacce nake so".

"haka muke so Soja, gwara kayi zuciya kayi auren ko ka huta da gori" Anty Jiddah ta fad’a da alamar wasa.

Yaya Aminu kuwa bai ce komai ba in banda dariya da yayi.

Kayan motsa baki taje ta kawo mai ta ajiya ta nufi d’aki ta barsu dan su zanta.

Nabil ne yaje kusa da yaya Faruk ya manne a jikin shi ya fara Maganar shi ta ‘yan koyo yace

"Uncle Soja ina bindigar da kace ja ka ciyo min".

Kunnen shi ya kama yace "sorry Nabil na manta ne amma in zan k’ara zuwa zan siyo maka".

Tsalle Nabil ya fara yi yana cewa "yeh Uncle soja jai ciyo min bindiga".

Humaira sai faman zun’bura baki take yi ganin ance za a siyo wa Nabil bindiga amma ita ba a ce za a siyo mata ‘yar baby ba (toys)"

"zo nan Humaira" yaya Faruk ya kira ta cikin lallashi.

"Me ya faru ne baby naga kina so kiyi kuka".

Cikin shagwa’ba tace "ba kai bane kace zaka siyo wa Nabil bindiga, ni kuma ba kace zaka siyo min ‘yar baby ba (toys)".

Dariya suka yi shi da yaya Aminu kana yace "ke ma zan siyo miki, an shi wannan ki kai ma Momi ta raba muku"

Cikin murna ta amsa tana cewa

"Uncle soja mun gode" ta tafi d’akin Anty jiddah da gudu.

ganin haka ne yasa Nabil shima ya bi ta da gudu.

5 alive na kwali da Anty Jiddah ta kawo mai ya d’auka ya tsiyaya a glass cup ya sha, ya juya kallon shi zuwa gurin yaya Aminu yace "Aminu shawara nazo nema a gurin ka game da yarinyar da nake so".

Yaya Aminu ya yalwata murmushin shi yace "Masha Allah ina jin ka, kace mun kusa yin suruka".

Sai da ya numfasa kana yaci gaba da cewa "Aminu ba kowace yarinya bace na dad’e da fad’a wa tarkon son ta illah Fatima, bazan iya fad’a maka adadin son da nake mata ba, sai dai kawai in ce maka, I really love her".

Da mamaki yaya Aminu yace "wace Fatiman kake nufi?

Gajeren tsaki yayi kana yace "Akwai wata Fatima ce da ta wuce k’anwar ka".

Dariya Aminu ya fara yi yana kallon yaya Faruk wanda ya tamke fuska ganin dariyar da Aminu yake mai.

Wani dogon tsaki ya k’ara ja wanda yafi na farko yace "wai Aminu miye abin dariya, daga na fad’a maka sirrin zuciya ta, ka tasa ni sai dariya kake min kamar kaga wani mahaukaci".

Tsayar da dariyar yayi yana cewa

"Sorry Bregadier, my inlaw, abin ne da ban dariya da mamaki wai kai kake son Fatima, gashi kana da son girma, baka son raini, ita kuma Fatima ga rawar kai, amma soyayyar nan za ta ba da ma’ana, naji dad’i da Sister ta samu gwarzon namiji kamar ka, congrat".

"Kai matsala na da kai Aminu, kana mai da zance mai mahimmanci wasa, nazo dan ka bani shawarar amma kana d’aukar zancen as a joke".

"Ok sorry, joke aside, yanzu fad’a min shawarar da kake so in ba ka" yaya Aminu ya fad’a.

"Kaga dai Fatima ba ta dad’e da kammala Secondary School ba, nan ba da jima wa ba admission zai fito su fara d’auka lectures, yanzu abin da yake damuna shine har yau ita Fatima ba ta san ina son ta ba, tsoron da nake ji shine kar in bari ta fara high institution ta had’u da wani su fara soyayya alhalin ni ina nan ina jiran ta, kar kuma in fad’a mata yanzu in katse mata karatu tasa soyayya a gaban ta? kai menene shawarar ka".

Yaya Aminu in ban da bin shi da kallo ba abin da yake yi.

mamaki yake yi wai Faruk ne ya zauna yana expressing d’in feeling d’in da yake ma Fatima, "lallai ya yarda Love is everything, you don’t have any choice to control yourself when you fall in love, ya kuma yarda da son da Faruk yake ma Fatima".

"A shawara ta Faruk, ina ganin ka fad’a mata yanzu saboda tasan kana son ta da wuri, kaga ko nan gaba tasan da kai, ba za ta bari ta sa soyayyar wani a ranka ba, kasan A bari ya wuce shi ke kawo raban wani".

Yaya Aminu ci gaba yayi da cewa 'yanzu kayi amfani da DAMAR KA ka k’ara jan ta a jikin ka na yadda SHAK’UWA CE za ta k’ullu a tsakanin ku, kaga daga nan sai ka nuna mata ZAZZAFAR K’AUNAR da kake mata, I know, she will not reject you, because you are one out of thousand".

Wani murmushin dad’i yaya Faruk yayi saboda yadda yaji yaya Aminu ya bashi shawara da kuma yadda yake fasa mishi kai, hakan yasa ya k’ara samun k’arfin gwiwar tunkarar ta.

Shawarwari yaya Aminu ya dinga ba wa yaya Faruk akan yadda zai shawo kan Fatima ba tare da wata matsala ba.

Canza akalar hirar suka yi kana yaya Faruk yace ya kira mishi Anty Jiddah ya mata sallama ya tafi.

Tun daga wannan time d’in ya zamana yaya Faruk na zuwa gidan mu yana ja na da hira, ga siyayya da yake min akai – akai, yanzu har dama ya bamu wai mu dinga yin chating, ga kira na da yake yi akai-akai.

Ni ko mamakin mai ya canza yaya Faruk a lokaci d’aya nake yi, yadda ya dawo so cool da friendly damu.


Yau da daddare ina zauna a d’aki ina buga game a waya ta, naji alamar shigowar war calling a waya ta.

Sunan yaya Faruk na gani a jikin screen d’in yana yawo, d’auka nayi na amsa mishi sallamar da ya min.

'ki same ni a falo akwai maganar da za muyi" abin da yace min kenan ya katse wayar.

Tunani na fara yi wace Magana ce zamuyi dashi da ba zai bari gobe ba sai da daddaren nan.

Hijab kawai na d’aura akan night gown d’ina da zani akai na nufi falo.
Samun shi nayi a falo shi da yaya Khalil suna hira.

Guri na samu na zauna na gaishe shi.

Ganin bai ce min komai ba yasa nace

"gani yaya Faruk"

Yaya Khalil ne ya mik’e yayi wa yaya Faruk sallama ya tafi side d’in shi.

Shiru falon ya d’auka na d’an mintina kamar ba kowa a ciki.

"TEEMAHHHH"

Saurin d’ago kaina nayi saboda yadda naji yaya Faruk ya kira suna na wanda ya banbanta da sauran lokutan da yake kiran suna na.

D’aga kai nayi na kalle shi ba tare da na amsa ba.

Shiru yayi kamar mai tunanin abin da zai ce yake yi.

"Fatima! ina so ki bani aron time d’in ki saboda maganar da nake so muyi a yanzu is ver important".

Wannan wace Magana ce kuwa da yaya Faruk yake son fad’a min mai mahimmanci haka? nasan wannan tambayar ba ni da amsar ta sai dai in jira ya fad’a min ba.

"Teemah, duk maganar da zan fad’a miki ki d’auke ta da mahimmancin saboda har cikin zuciya ta haka take, kar ki zata ko da wata manufa zan fad’a miki sai dan in fallasa abin da ya dad’e a cikin zuciya ta yana damu na".

Duk da ban san wace Magana ba ce, sai naji gaba nay a fad’i duba da yadda yake amfani da cool sound wajen maganar.

"Teemah! ba kowace Magana bace da ta wuce in ce miki INA SON KI FATIMAH, I know I am in love with you because my reality is finally better than my dreams".

Gaba na ne ya fad’i na yadda maganar tazo min a bazata da firgita da nayi a lokaci guda wanda hakan ya kasa ‘boyuwa a fuska ta.

"mai yaya Faruk yake nufi da wannan kalamen nashi, ko in ce tatsuniyar da za ayi ta a lokacin a gama, an ya yaya Faruk yana cikin hankalin shi da zai tunkare ni da wannan tsadaddiyar kalma mai wuyar furta wa? ya ma san wacce yake fad’a ma wannan kalmar" na tambayi kaina.

Kamar ya san tambayar da nake yi wa kaina yace

"Teemah, kar ki yi mamaki ko shakkar maganar da na fad’a miki, kar kuma ki d’auka da wani nufi a raina yasa na fad’a miki haka illah ina fallasa miki abin da ya dad’e a raina, duk wasu abubuwa da kika ga ina miki wanda kike d’auka a matsayin takurawa, ina miki shine dan ina kishin ki da kuma son da nake miki".

Ci gaba yayi da cewa "Teemah! True love doesn’t have a happy ending because true love doesn’t have an end. My love 4 u has no end, farin ciki na shine samun Ki, there is only one happiness in this life, to love and be loved".

Ni dai rasa a wani hali nake ciki, rasa wani hukunci zan yanke ma wannan maganar mai kama da labari shuni ya yi, na yadda namiji bai da kunya, tun da har yaya bai jin kunyar fad’a min abin dake ranshi ba, ya kuma manta abin da yamin a baya, duk ma ba wannan ba, zuciya ta ce tak’i marhabin da sak’on da yaya Faruk yazo mata dashi.

Jin bance mai komai ba yasa yace

"Fatima zan baki time kije ki yi tunani kafin in koma aiki saboda hutuna ya kusa k’are wa, dafatan zaki yi ma Magana ta duban basira".

Ya mik’e yana duba wrist watch d’in shi yace "Gud night Teemah, na barki lafiya".

Bai jira jin abin da zance ba ya tafi.
[4/10, 20:51] Mrs Mansoor: *MAKAUNIYAR SOYAYYA*💝💖💞

🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀


*STORY & WRITTEN*


*BY*


*MARYAM AHMAD PAKI*




*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*🤝🏽



*Wannan shafin naku ne*

*Hussaina Ahmad da duk wanda ke group d’in Ni da yaya Farooq*

*Ina muku fatan alkhairi*



*Sak’on gaisuwa ta gare ku*

*Sakina ilyas*

*Sarah*

*Umin kareemah*

*Lubiee*

*Fauxiya Masha Allah*

*Doctor Maryash*

*Ash, beely*

*Aysha a*

*Aeeshart*

*Maman nabeel*

*Hafsat m Goni*

*Da duk wanda ke cikin group d’in Mufy & Maryam A Paki fans*.

*Sauran wanda ba su ji sunan su ba, mu had’u a next page*.



Wannan karan ba samu wanda ya kawo complete answer na question of the day, sai dai akwai wanda suka yi matuk’ar k’ok’ari irin su

Meeynah

Auta mama (Aisha)

Xarah auwal

Sulaiman Abdullahi (facebook)

Amsar question of the day shine k’ofofin aljanna guda takwas ne (8)
1. Jannatul Firdausi
2. Jannatul Na’im
3. Jannatul Aliya
4. Jannatul Adnin
5. Jannatul Ma’awa
6. Jannatul Darul kuldi
7. Jannatul Ar-rayyan
8. Jannatul Darul salam
Allah ka sa da mu daga cikin wannan k’ofofin.



*Tunatarwa*

Kar ka/ki bari fushi ya dinga ziyartar zuciyar ka/ki, saboda duk lokacin dab ka/ki yi fushi, shaid’an ne a cikin jinin jikin ka/ki da ruhin ka/ki.
Wannan nasiha ce.

Idan mutum yayi maka/ki abu mara kyau, ka/ki tuna da mai kyau da yayi maka/ki, saboda ko wane mutum yana da hali maii kyau, yans da mummuna.
Wannan nasiha ce.




37&38

Tun da yaya Faruk ya tafi na ji ban da wani sukuni, jiki na a sanyaye na mik’e na nufi d’aki na.
Akan gado na zauna ina tariyo maganganun da yaya Faruk ya zauna ya na fad’a min, kenan maganar Anisa ta zama gaske da tace yaya Faruk na matsa mana ne saboda ni, ya akayi tayi saurin gano cewa yaya Faruk so na yake yi amma ni ban gano haka ba.

Har yanzu maganganun shi suna min yawo a zuciya ta, ban san kuma dalilin da yasa na kasa gasgata maganganun shi a raina ba duk da nasan har zuciyar shi yake fad’a min.

Abin da bazan iya tantancewa ba shine ni dai a zuciya ta ba ta yi marhabun da maganar yaya Faruk ba, hakan na nufin kenan bana son shi?

Wata zuciyar ce ta gargad’e ni da cewa "kar kiyi saurin yanke hukunci dan ba a yanzu bane zaki samo amsar ki".

Ni kaina nasan yaya Faruk ya kai namiji da duk macen da ta ganshi za tayi fatan ya so ta, ya had’a duk abin da mace ke buk’ata, sannan ya na da ilimi, kud’i, kyau, duk da muna takun sak’a dashi, hakan ba zai hana fad’ar cewa yana da kyawawan halaye, matsalar shi ita ce fad’a da miskilanci.
A ra’ayi na shine ba na ra’ayin namiji so rude, na fi buk’atar namiji friendly kamar yaya Khalil.

Zuciya ta ce ta bani shawarar kar in fad’a ma Anisa wannan maganar, dan duk yadda takai ga complaining d’in abin da yaya Faruk ke mana, ba za taso in yi rejecting d’in shi ba, fad’a ma ta na nufin kamar maganar taje kunnen family ne.
Shawara d’aya na yanke shine in yi watsi da maganar da yazo min in ci gaba da harka ta, in yaso in ya tambaye ni in ce ban gama shawara ba.

Da wannan shawarar na samu mafita, na manta da wani batun yaya Faruk.



WANENE YAYA FARUK?

Yaya Faruk d’a ne ga Engineer Yusuf wagini, mahaifin shi ma’aikaci ne a NNPC dake marabar rido a kaduna, sannan yana da kamfanin sai da motoci da suka yi had’in gwiwa da k’anin shi Ibrahim. Mahaifin Faruk wa ne ga mahifin su Fatima.

Mahaifyar shi Hajiya Rukaiyya ‘yar asalin cikin katsina ce, mahaifiyar shi business woman ce da take saro kaya daga Dubai take kawowa gida Nigeria.
Yaya Faruk ya ci sunan kakan mu ne Umar, shi yasa ake kiran sa da Faruk.
Mahaifin yaya Faruk shahararren mai kud’i ne.

Yaya Faruk d’an kimanin shekara 32 kuma shine babba a family, ya ba ma yaya Aminu ratar shekara d’aya, sai suka taso kan su d’aya kuma abokai ne.

Tun da aka haifi yaya Faruk sai da aka d’auki wasu shekaru sannan Momi ta sake haihuwa amma sai yaron bai zo da rai ba, daga nan sai da Momi ta sake d’iban wasu shekarun sannan ta haifi Anisa, dan har su Momi sun cire rai da sake haihuwa.

Yaya Faruk tun yana k’arami yake da sha’awar aikin soja har yau da yake matsayin Bregadier.

Yaya Faruk mutum ne wanda Magana bai dame shi ba, baya shiga abin da ba ruwan shi, akwai shi da miskilanci sannan ga wanda ya fahimce ci yana da dad’in zama da kuma kyauta, Shi mutum ne mai son zumunci.

Yaya Faruk irin classic d’in mazan nan ne da ake ce musu one in town, yana da kyau wanda yake d’aukar hankalin ‘yan mata, kalar skin d’in shi normal fari ne wanda bai yi yawa can ba, gashi da dogon hanci, dogo ne amma ba can ba, yanayin jikin shi irin giant ne, yana da farin jinin ‘yan mata da kuma mutane, sai dai shi ‘yan matan ba sa gaban sa illah Fatima da yake ganin yayi gamdakatar da soyayyar ta.



CI GABAN LABARIN

A can ‘bangaren yaya Faruk kuwa tun da ya koma gida yaji ya samu relief a zuciyar shi, ko ba komai yau ya samu ya amayar da abin dake cikin zuciyar shi na wasu shekaru.

Sai dai zuciyar shi ke kai kawo akan yanayin Fatima da ya fad’a mata maganar, bai ga wata alama na farin ciki ko bak’in ciki ba, yanzu ba zai iya yanke hukuncin cewa tayi na’am dashi ba ko akasin hakan.

Idan Fatima tayi accepting d’in shi yasan ya samu farin cikin da ya dad’e yana buri, kenan idan tak’i accepting d’in shi yana nufin zai samu akasin farin ciki kenan, rasa Fatima a gurin shi yana nufin rasa jin dad’in shi ne, shi kan shi bai san lokacin da son Fatima ya mishi dabaibayi.

Baya fatan hakan ta kasance gare shi saboda bai san halin da zai shiga ba in ya rasa ta.

Yana cikin wannan tunanin ne wayar shi ta fara haske tana d’auke wa, hakan na nufin kira ne ya shigo wayar saboda a silent yasa ta.

Sunan Ogan shi yaga yayi appearing a jikin screen d’in wayar.

Da azama ya d’auka ya mik’a gaisuwa yana jiran jin abin da Ogan zai ce mai tun da ya kira shi a wannan lokacin.

Sanar dashi yayi akan ya ajiye duk abin da yake yi ya tawo Abuja gobe, akwai wani aiki da za ayi kuma a ciki har dashi a ciki.

Cikin ladabi ya amsa mishi da insha Allah yana nan tawo wa.

Yana gama receiving d’in call d’in ya wurga wayar can gefen gado, ya dunk’ule hannun shi ya kai ma d’ayan hannun naushi kamar hannun ne ya masa laifi.

Wani irin takaici ne ya kama shi a lokaci guda, yana ganin yanzu ne ya kamata ya

Please Login or Register in order to submit comment