kuma kowa ke saka ran shine magajin sarautar masarautar.
Ita dai Samha tana tsaye tana kallonsa harya kammala wayar da Momma ya kashe.
Had'e fuskarsa yayi yana hararta, “to maganatu miya faru kuma? kike kwalan kira tundaga wata uwa duniya?, wai sai yaushene zakiyi hankali Samha?”.
Baki ta tunziro gaba, idonta harya cika da gwalla “amma dai Uncle aina fara yin hankalin ko, kumafa wani Abu Nazo na nuna maka, naje Sashenka wannan sarkin k'ofar yawanice kana wajen mai martaba”.
Kansa kawai ya girgiza yana kallonta, saida takai aya sannan yace “to aini inada abunyi, yanzuma ba wai sauraren naki zan zauna yiba, dan nan ba India bane, ba'a ganina available ko yaushe OK?”.
Harya juya zai tafi tarik'o hannunsa tana daddaga k'afafu idonta na zubar da hawaye.
Kansa ya dafe domin sanin fitinar Samha, tace,
“please Uncle Sam 2munutes to”.
Juyowa yayi tamkar zai maketa, saikuma komi ya tuna ya fasa, d'an cije lips d'insa yayi yana hararta, “ke wai wace irin fitinanniyace ne?, Uwarmi to zaki fad'amin?”.
Dariya tayi tana share hawayenta dan ganin tasami nasara, wayarta ta daddana sannan ta mik'a masa.
Nanma Harar tata yayi kafin ya kar6a, itace yagani a photo da 'yammata biyu masu kama d'aya, kamarma yarinyar dasuke shirin auren contract, harya yatsina fusaka zaice suwaye? saikuma yatuna. d'an murmushi basarwa ya saki kafin ya kalli Samha da ta tsaresa da idanu. “Uncle ina aunty Munaya anan? ”.
Wayar yamik'a mata yay gaba abinsa yana fad'in titsiye zakimin ma kenan? an fad'a miki bazan ganeta baneba?”.
Baki ta turo tana k'unk'uni, “waikai Uncle Sam bazaka ta6a canjawa baneba? kai kenan kullum sai jan ajin tsiya, shiyya sama ALLAH yayoka jinin sarauta wlhy, Aunty Munaya kin bani da wannan mijin naki mai k'asaitar tsiya, aiko wlhy tunda kace haka saina had'a maka mugunta gobe a wajen dinner ”.
Ta tuntsire da dariya saboda tuno mizata shirya masa.
★★★★★
*Rana bata k'arya........*⛹🏻♀
Yau mun wayi gari safiyar d'aurin aure, gida yakuma d'inkewa da jama'ar dukda d'aurin Auren na Azhar ne bayan sakkowa masallacin juma'a.
Tun jiya banida lafiya, amma na hana su Ayusher fad'ama kowa, sai Magani suka samo min nasha, itama dai Munubiya duk sukuku take, babu abinda ke damummu sai jimamin rabuwa da juna, dan itama kusan zazza6inne ma ta kwana dashi, sai dai dayake nawa ya had'a da damuwa saina fita nuna jin jiki.
Jama'ar gidanmu dai a harmutse suka kwana, wasuma ko barcin basu sami damar yiba saboda ciwon hasada dake cin zukatansu, gashi gida d'inke da jama'ar babu damar matsawa koda nan da canne sai an gane, bare sufita neman mafitar tarwatsa Auren, waddama suke d'an samin tallafinta kwad'ayinta yasaka canja shek'a (innaro🤣), dan jiya da suke zuba tijara shigowa tayi tamisu tas, harma tana Neman tone musu asiri gaban tawagar 'yan biki, badan gwaggo Safiyya ta lalla6a taba ba'asan inda jarabar innaro zata tsayaba kam.
Ko karyawa ban iya tashi nayiba bare aje maganar wanka, ina kwance cikin bargo sai shar6ar kuka nakeyi babu wanda yasani.
Ahaka gwaggo Safiyya tashigo kiranmu nida Munubiya, da k'yar su Ameera suka samu natashi zaune ina tangad'i, gaba d'aya nayi wujiga-wujiga dani, da taimakon Munubiya dake rik'e da hannuna muka iso gidan innaro inda su Abba suke jiranmu.
Gaba d'ayanmu ne amaren aka had'a, abin mamaki saiga innaro ta kamani ta zaunar tanamin sannu, harda lallashina wai na kwantar da hankalina.
Kowa zuba mana idanu kuwa yayi, su Fiddausi sai jan tsaki suke a zukatansu sunajin wata tsanar innaro aransu.
Itakam bama tasan sunayiba, sai nannan takeyi damu nida Munubiya.
Nasiha mai ratsa jiki da 6argo sukai mana sosai, muhimmancin aure da hak'uri, biyya da tsoron ALLAH, kare hak'in miji da k'yautatama danginsa da iyayensa, k'arfafa zaman lafiya a tsakani da rik'e sirrin miji, banda biyema k'awayen banza sukaika su baroka, musamman ma da dukanmu zamu cigaba da zuwa makaranta.
Gaba d'ayanmu kowa hawaye yakeyi, musamman mani danakejin tausayin kaina dana iyayena dabasu San auren shekara d'aya nake shirin yiba nadawo garesu.
Munci kuka sannan aka sallamomu, tunda muka dawo sai aunty salamah ta saka mu agaba dole mukayi wanka, da k'yar muka amince aka mana simple kwalliya, muka saka dakakken leshin da mama Rabi'a tasa aka d'inka mana cikin kayan biki dasuka mana itada innarmu, less d'in blue ne da fararen bet ajikinsa, sai aka nad'a mana d'an kwalima blue, munyi k'yau harma bansan yazan musalta ba, nan su Ayusher suka hau zuba mana pictures. lokacin 12 tama wuce, masallacin anguwarmu daza'a d'aura auren yagama cika dank'am da jama'a, dayake bashida nisa da k'ofar gidanmu.
Cikin gidanmu kam ai ba'a magana, dan babu masaka tsinke, sai hayaniya kakeji wani bayajin zancen wani, rabin hirar jama'a kuwa duk akan zancen lefe nane da Wanda zan aura, wad'anda suka gani suna bama wad'anda basu ganiba labari.
Su siyama dai koma ganinsu ba ayi, dan suna taya iyayensu kishi da hassada, aunty Ramla da aunty Raihana sai aunty Hauwa'u ne kawai suka shigo sukaima innarmu murna har d'akinmu, amma aunty khaleesa ko k'eyarta bamu ganiba, kuma tunda safe tazo gidan daga ita har zarah, matar yaa hameed ma mama hanata zuwa tayi, dukda tanaso tazo tama innarmu murna amma surukarta takasa ta tsare, gashi bama dad'in zaman 6angaren takejiba, saboda 'yan ubanci na dangin miji da aketa nuna mata, itama matar yaa Naseer tashigo, dan har picture mukayi da ita, amma matar yaa Shafi'u ma bata shigoba.
Hakan duk bai dameniba, dan ni yanzu basune agabana ba, damuwata tarkon dana saka kaina na auren contract shike cazan tunani a halin yanzun, Wanda ko munubiya nakasa sanarma gaskiya lamarin.
*_1:30pm_*
Masallacin yagama cika taban mamaki, tuni tawagar gidan Sarki sun iso tun bayan gama sallar juma'a, d'aurin aurene daya tara manyan mutane ta dalilin gidan sarauta, manyan sarakunan k'asarnan da 'yan siyasa, governors senators attajirai na gida dana k'etare, talakawan gari da tawagar iyaye da dangin sauran angunan, abokan su abbanmu danasu yayunmu, abokan anguna da abokan arzik'i, dangin iyayenmu mata danasu abbanmu, kowa ya hallara, bakajin komai sai kad'e-kad'e da bushe bushe irinna gidan sarauta. president da Kansa ya iso wannan waje bisa gayyatar papi, bansan yanda zan musalta muku irin cikarda anguwarmu tayiba aranar, bama zaka iya gane taka maimai inane ake d'aurin aurenba. Su Kansu masarautar su Galadima sunsha mamaki, basuyi zaton auren Na Galadima zai tara jama'a manyan mutane hakaba, dubi da yanda ba d'iyar wata hamshak'iyar masarautar zai auraba. basu San abin ba anan yakeba wai *d'uwawu yafi fuska k'yawun gani*🙊🤥😜😂 inji masu iya magana......................✍🏼
Amin afuwa, mu had'u tomorrow danjin yanda d'aurin aurenba zai kaya⛹🏻♀⛹🏻♀⛹🏻♀.
Barkanmu da dawowa😄✋🏻🤝🏻
*_ya ALLAH ma gafartama iyayenmu_*😭👏🏻
*_Typing📲_*
*_HASKE WRITERS ASSO...💡_*
_(Home of expert and perfect writer's)_
*_♦RAINA KAMA......!!♦_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
👉🏻2⃣0⃣
.........A cikinmu Fauziyya ce babba, dan haka aka fara d'aura auren ta, daga nan sai ni da Munubiya, an fara d'aura na Hassana Auwal fharuk (munubiya) da yaa marwan Ibraheem, sannan ni Hussaina Auwal fharuk (Munaya) da Muhammad Sameer Saifudden Abubakar (Galadima), saikuma Safara'u, sai Haleematu, Fiddausice k'arshe.
Ana gama d'aurin auren busar algaitu suka fara tashi, sarkin marok'a yafara zuba kirari wa Ango Galadima sarkin gobe a masarautar gagara badau.
Maganar k'yawun da Anguna sukayi ma 6ata lokacine, kowanne yafito angonsa sak abin kallo da birgewar kowa, duk miskilancin yaa Marwan saigashi yana washe hakwara tamkar gonar audiga😁.
🤥ance anguna basa kuka ranar aurensu, to kuwa yau saiga Galadima na share hawaye, dukda auren contract yayi nakuma shekara 1 kacal, saiyajisa wani iri daban, ya kuma zama babban mutum, tuno Abie dayayi yasaka hawaye fitowa daga idanunsa, bazai iya tuna tsawon lokacin dayayi kuka na k'arsheba, amma saigashi yau yanayi acikin d'umbin jama'a, akuma ranar d'aurin auren da ya rad'ama suna na (wucin gadi).
Papi ne yad'an bugi kafad'arsa yana murmushin jin dad'i shima, dajin wata k'aunar jikan nasa ta musamman.
Aikam masu videos da photuna ansamu abinyi, hakama masu d'auka awaya ba'a magana.
Kafin kace mi social media ta d'auka, lungu da sak'o hotunan d'auren aurenne suketa yawo, musamman da jama'a ketajin wai wadda aka bugasu a jarida yana kissing ce ya aura, wayyo ALLAH abin magana yasamu a yanar gizo, kowane polder na charts ka shiga zancen kenan dai.
Daga wajen d'aurin aure tawagar gidan su Galadima k'aton hall d'in da aka tanada domin cin abincin bak'i suka nufa, duk wani maiji da kansa zaka sameshi awajenne, Galadima har kansa yafara ciwo saboda yawan magana ta amsa gaisuwar jama'a da murna da yakeyi.
Ana tsaka da cin abincin Momma ta kirashi, dama shi ba ma abincin yakeciba, zaune kawai yake yana juya spoon a plate, wayarsa yaciro daga aljuhun gaban rigar milk d'in shaddarsa, dan tuni yacire malum-malun d'in tana hannun Harun.
Ganin Momma yasashi mik'ewa yafice daga hall d'in gaba d'aya, can waje yasamu wasu kujeru ya zauna sannan yakirata ta video call, tana d'agawa sai kawai ya fashe mata da kuka ganinta zaune kusada Abie.
daga Momma har Abie d'in sagade sukayi suna kallonsa, saida yayi mai isarsa yasaka handkerchief d'insa ya goge fuska sannan Momma tace “ho d'an nema duk murnar aurence kokuwa shagwa6a ce ta motsa?”.
Tur6une fusaka yayi zai sake wani kukan Momma ta kwashe da dariya irin wadda yadad'e baiga tayiba, Abie ma murmushin sane ya fad'ad'a sosai. saida Momma tayi dariyar mai isarta sannan tace, “Muh'd kafa girma, kai yanzu babban mutumne, nan kuma da wata shekarar kazama baba, amma katasamu gaba kana kuka?”.
Handkerchief yasaka yakuma goge hawayen dasuka taho masa, sannan yace “momma na barka da rana”.
“Barkan ka dai angon d'iyata Munaya, ALLAH ya sanya alkairi yabada zaman lafiya yasa bad'i iyanzu munan muna shagalin sunan jikan mai martaba”. tayi maganar tana kallon Abie daketa zuba murmushi, gira d'aya ta d'aga masa, shikuma ya k'yafta mata idanu.
Dariya Galadima yasaka musu, irin wannan soyayya haka summa manta dashi.
Gyaran murya yayi sannan Momma ta d'ago tana kallonsa, suka saki dariya lokaci d'aya. yayinda Abie ke tayasu da Murmushi.
Galadima ya tsagaita dariyar yana fad'in “my Abie ya jiki?”.
Da idanu Abie ya amsa masa da Alhmdllh, sannan yamasa nuni da ALLAH ya Santa alkairi.
Hannu yasa yarufe fuskarsa alamar jin kunya.
Har aka kammala liyafar cin abincin yana a waje suna hira da parent d'insa, saida papi ya aiko akirasa saboda yanason nunashi wa jama'arsa da basu sanshiba, hakan yabama wasu daga cikin 'yan masarautar su haushi, sai dai basuda yanda zasuyi da wannan tsohon mai k'arfa-k'arfar tsiya da Nuna Isa.
Bayan ya Yanke call d'in yamik'e yabi bayan d'an Aiken, ya iske a hall d'in kuma papi ya had'a wani video call d'in dasu Momma, domin Abie yaga d'umbin jama'ar dasuka halarci d'aurin auren gudan jininsa.
Aiko yaji dad'i sosai harma Momma, harda hawayen farin ciki Abie yayi.
Nandai a kaita zuba masa addu'ar Neman lafiya ga mummunar addu'a ga dukkan masu hannu na shigarsa wannan halin tsawon shekaru, da idanu yake fad'ama Momma magana itakuma tana fad'a musu. Daga nan Galadima yayi jawabin daya ta6a zukatan jama'ar wajen, wasu harda share hawaye, wasu daga cikinsu dasuka San wasu abubuwan daya faru wa tsohon sarki Saifudeen kam duk sai zukatansu suka karye, musamman masu hannu aciki dasuka bada gusunmawa, jin addu'a da alwashin d'ansa Muhammad Sameer dake tabbatar da bazai bar duk mai hannu acikiba, sai dai shima amasa irin na mahaifinsa, hakanne kawai zai iya dakatar dashi.
Abie da Momma Kansu kuka sukeyi daga can suma.
Taron yatashi zukatan wasu cikeda tausayin Galadima da k'udirin taimakonsa, yayinda yasamu k'yaututtuka daga manyan k'asar.
Masu hannu aciki kuwa suntafi da nufin sake shiri akan Galadima d'in, domin aganinsu sunyi sake d'an zaki ya girma, kuma Galadima na neman zame musu *RAINA KAMA......*
https://2gnblog.blogspot.com/
★★★.★.★.★★★
Gidanmu kam tunda aka kammala d'aurin aure labari ya shigo gabana yashiga luguden daka, rungume juna mukayi ni da Munubiya muka fashe da kuka mai ban tausayi, Wanda muka saka jama'a dayawa kukan, ciki kuwa harda Innarmu da mama Rabi'a. babu wanda yace mu bari, aka barmu mukayi mai isarmu, dan kowa yasan dolene muyi irin wannan kukan na rabuwa, dan yau babu fashi dolene mu Rabun, abinda baita6a faruwa agaremuba, kullum a gado d'aya muke kwana muke tashi, kowanne aiki tare mukeyin sa, komai namu iri d'ayane, daidai da pants & bra iri d'aya muke sakawa, idan d'aya bashida lafiya saika d'auka muduka bamuda lafiyar, babu abinda ke banbantamu sai hali, amma yau gashi aure zai banbantamu, jinai inama muma mazane tamkar su Aiyaan, yanda babu mai rabamu d'in.
https://2gnblog.blogspot.com/
Haka dai wannan yinin biki akayishi a wani iri, mu cikin damuwar rabuwa, matan gidanmu cikin hassada da bak'in cikin mun fisu.
danma Su Abba sunyi dogon gargad'i akan wlhy duk wacce tasake tada finina a gidan sai dai ta k'arasa bikin a gidan su.
Wannan furucinne yasaka kowa yin likimo, sai dai fa ta ciki na ciki🙊😂.
Hotunama da akayi na family wasu fuskar tasu tamkar kashin farar safiya😖🥴, Innaro kam ai mune nagaban girarta a yau, sai dama-dama takeyi damu, dama komai akayi saitace an kaima Ai'sha dai ko, (😂su innaro anga banza).
Wannan abun datakeyine keta kuma hasala matan gidanmu da 'ya'yansu, itakam ko a ha6ar kallabinta, warkajaminta kawai takeyi na murnar auren jikoki.
Yayinmu mazane kawai babu ruwansu, duk suna cikin farin cikin wannan aure.
Bayan la'asar sakaliya saiga sak'o daga masarata mutane biyu d'auke da akwatina biyu wai sun kawo kayan da zansa awajen dinner ni da Munubiya, sun shirya dinner d'inne mu biyu kawai banda sauran amaren.
Wannan lamari kam ya sosa zukatan mutane da yawa, ni kaina banji dad'in hakanba gaskiya, dan banason su d'auka kamar mun banbanta da sune yanzun, gaskiya da ace inada Number Galadima dana kirashi nace a fasa wlhy, saboda muma anan gidanmu yayunmu sun shirya mana dinner d'in gaba d'ayanmu, duk da ni dama ban saka ran zuwan Galadima ba a wajen.
Gashi kuma gate pass guda 30 kacal suka kawo, alamun basa buk'atar mutane dayawa a wajen kenan, ikuma na nace inhar bada sauran 'yan uwana ba ban zuwa nima d'in.
Lallashin duniya anyi nak'i sauraren kowa, nakafe akan bazan jeba.
Matan gidanmu kam cewa sukayi munafurcine kawai.
Zancensu bai dameniba, nidai ina akan bakana bazanjeba. su Ayusher sun rasa yanda zasuyi dani, dama akwai number Galadima saisu kirasa su sanar masa halin da ake ciki.
Innarmu kam ko k'ala batace daniba, yitaima tamkar batasan mi akeyiba, mama Rabi'a da Aunty Salamah sai fad'a sukemin kamar zasu dokeni, hakama innaro, sai jaraba takemin harda dungure min kai.
cikin ikon ALLAH kuwa ana cikin haka saiga kiran Samha yashigo wayata, Ayusher ta d'auka suka gaisa, azaton Samha nice, saboda muryar Ayusher ma tana kama da tamu. Tace, “Aunty gimbiya ya hidima?”.
Murmushi Ayusher tayi danjin sunan nawa harya canja, tace “ba ita baceba Ayusher ce”.
Cikin jimami tace Aunty gimbiyar fa?”.
Labarin komai Ayusher tabata, sannan tace “dan ALLAH ko zaki had'ani da Galadima?”.
Samha tace “babu damuwa bara na dubashi, duk da nasan yana tare da abokansa yanzun”.
Godiya Ayusher Tamata sannan suka yanke wayar akan idan tagansa zata kira”.
Masifa nahau yima Ayusher akan miyasa zatace saita fad'a masa, nidai koma miye babu inda zanje.
Banza Ayusher tamin tamkar batasan inayi da itaba ma.
Kusan muntuna 7 saiga kiran Samha yasake shigowa, Ayusher ta d'aga, maimakon taji muryar Samha saitaji ta Galadima cikin k'asaitar nan tasa da izza.
Nutsuwa Ayusher tayi sosai ta gaisheshi, sannan ta masa bayanin komai.
uffan bai ceba saida ta kai ayar zancenta, lips d'insa yad'an cija kafin yace “had'ani da ita”.
A kunne Ayusher ta sakamin wayar, yayinda kowa yafice daga d'akin aka barni ni kad'ai saikace wata mayya.
Dagani har shi kowa yayi shiru, shi yanajin kansa nima hakance, kusan minti 4 yaji banida niyyar tankawa saiya yi guntun tsoki, “shin ke baki iya gaisuwa bane?”.
Dukda naji ban k'yautaba saina ta6e baki, cikeda dakiya nace, “ina yini”. muryata a dishe take saboda kukan danaketa sha tun jiya.
Bai amsa gaisuwarba yace “wane sak'o kika bada a bani?”.
Saida na tunzuro baki sannan nace “yoni minace abaka?”.
Lips d'insa ya lasa yana fad'in “nikikema wannan abun?”.
Banza namasa danni bansan mina masaba kuma.
Yaja guntun tsoki, “ki kama kanki fa, karkiga auren contract mukayi, akwai sharid'd'a acikinsa, bana buk'atar ganin kowa awajen inba keda sister d'inki ba, haka na tsara, kuma babu mai canjamin ra'ayina, zuwa anjima wadda zata shiryaku zatazo, idan kin gadama karki bari a shiryaki, nikuma zakiga mi zan yi akai..”.
d'if ya katse wayar, cirota nayi daga kunnina ina dubawa tamkar zan ganoshi acikinta. naja tsaki ina fad'in “aikin banza kaje ka koyo R sannan kamin wannan ikon, nifa baka isa takani ba acikin auren contract...... ”
Sauran maganar ta mak'ale a mak'oshina saboda shigowar munubiya.
Zama tayi akusa dani, “sweetheart zan iya neman alfarma a wajenki?”.
Kai na d'aga mata.
Ta gyara zamanta sosai tareda kamo hannayena duka acikin nata. “inason kima mijinki biyyay kiyi yanda yakeso, yanzu hakkin bin dokarsa tarataya a kanki dole inhar bata sa6ama addini ba, kina kaucewa kuwa zaki had'u da fushin ALLAH, tunda yace haka yakeso ayi kiyarda kawai, awa nawane anyi an tashi kowa yakama gabansa”.
Alk'awarin Dana mata yasani amincewa zanje tilas amma badan raina yasoba.
An tsara wad'anda zasuje, dan haka aka damk'ama kowa gate pass d'insa a hannu ya Adana. dukda wasu gani kwaf zasuje kuwa.
Bayan sallar isha'i saiga masu mana shiri sun iso, babbar magana wai d'an sanda yaga gawar soja.
Jama'a ni kaina bamma gaskata cewar nibace ballan tana Ku 'yan kallo, saika rantse kace dama can mud'in jinin sarauta ne, munyi k'yau har mun gaji, gashi dandanan akayi aka gama, har kusan 9pm muna jiransu, gidan yayi tsitt duk wad'anda zasuje dinner sun tafi, wad'anda zasu bimune kawai tare damu muna jiransu Galadima, dan shima yaa marwan d'in baikai ga isowaba.
Sai around 9:15pm sannan mukaji dirar mitoci a k'ofar gidan.
Aunty Mimi ce da kanta tashigo itada wasu bayi guda hud'u, saida ta gaisa dasu innarmu sannan aka mata iso d'akinmu, wani dad'ine ya ratsa zuciyarta, dukda batasan wacece matar k'anin nataba acikinmu, amma muntafi da imaninta, jitai inama natane wad'an nan twins, ALLAH yasa haihuwar farko na haifo musu irinmu.
Daga ni har munubiya rissinawa mukayi muka gaidata cikeda girmamawa, dan munsan a haife ta haifemu, dukda bawai sa'ar innarmu bace, ko mama Rabi'a ma ta girme mata.
Hakan damukayi yamata dad'i kuma mun birgeta, ta kama hannayenmu tana yaba k'yawun damukayi, wasu turarurruka ta fidso kala uku a bag d'inta tashiga feshemu dasu, dukda uban turaren da aunty salamah tamana wanka dasu zance, dan itama haka taita zazaga mana su d'azun, ni saima hawarmin kai sukeyi wlhy.
Wasu alk'yabbu masu azabar k'yau iri d'aya aka saka mana, takalman dake k'afarmu kansu abin kallone.
Aikam bamu fitaba saida tamana hotuna, afaloma saida aka mana muda su innarmu.
A waje muka iske motoci guda uku masu k'yau, da alama sauran motocin sun d'auki jama'a sun tafi.
Saida mukaje jikin motocin sannan aunty Mimi tayi murmushi tana kallonmu, to karnayi abin kunya, wacce ta my k'ani? wacce ta Marwan?.
K'asa mukayi da kanmu saboda kunya, saida ta kuma maimaita tambayar sannan munubiya tayi k'arfin halin nunani, kunyarmu takuma birgeta sosai, hannun munubiya ta kama tana fad'in kece babba ai, zoki fara shiga”. a motar farko ta sakata, sannan tadawo takama hannuna ta sakani a ta biyu.
Rufe k'ofar tayi takoma motar bayanmu tashiga. yayinda kuyangin nan hud'u suma suka shiga motar k'arshe.
Tunda nashigo k'amshin turarensa yadaki hancina, ta gefen ido na saci kallonsa, kishin gid'e yake a kan kujerar motar tamkar yasamu gado (dan bansan yama zan musalta muku tsarin motarba nikam, ammafa komai abin kallone) k'afarsa d'aya a k'asa d'aya akan kujerar, kansa na gab dani, dan dazai zame ko motsawa dolene saiya ta6a jikina, sanye yake cikin wasu Fararen suit masu azabar k'yau, sunyi mugun fidda ainahinsa matsayin cikakken namiji mai aji da gayu, aikin danna wayarsa kawai yakeyi tamkarma baisan na shigo motarba, dan ko sau d'aya bai d'ago ya dubeniba.
Nima basarwa nayi nayi tamkar bansan dawata halitta acikin motarba bayan driver.
Shikuwa tun shigowa ta k'amshin turarena yabigi hancinsa tareda shiga magudanar jininsa, a rayuwa yana matuk'ar k'aunar k'amshi, lumshe idanunsa yayi yana lasar lips, amma jinkai da k'asaita ta hanashi d'agowa yako dubeni.
Itakam munubiya tana shiga bayan aunty Mimi tarufe k'ofar yaa marwan jawota yayi jikinsa, tareda sumbatar gefen kumatunta. ta matse jikinta waje guda saboda tsorata, muryata na rawa ta gaidashi.
Ya amsa yana wani kuma shinshina wuyanta da bata wasu kisses d'in.
Mamaki da al'ajabine suka kamata, anya kuwa wannan yaa marwan d'in nanne mai shegen muskilanci da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 18 Chapter of 90