Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da farar t shirt mai gajeren hannu da blue din jeans, ganinshi yasata komawa ta kwanta, cikin sauri yakarasa gareta,

"Ayya amaryar daren jiya, sorry, tashi ahankali muje kiyi wanka kizo kiyi ramuwar sallar safe" yakarashe maganar cikin tsokana,

Shiru tayi masa tasoma kokarin tashi,

"Kabani towel to"

Yana guntse dariyar da ta taho masa yamiko mata, kallonshi tayi ganin yanda yaketa kawar da fuska alamun son yin dariya,

"Wai menene? Ai Kaine abin dariya baniba ya yusleem"

Sai lokacin yasamu damar yin dariyar,

"Nifa ba dake nakeba"

Shiru tayi tasauka tanufi toilet tana takawa sannu sannu,

"Inzo...?" Yace da ita yana murmushi,

"A'a" tafada tana turo baki, bedsheet din gadon ya cire da zummar yabar na kasan domin guda biyu yashimfida amma duk guda biyun sunyi staining nan yaciresu gaba daya,

Yana kokarin shiga toilet din tabude tafito, ganinshi rikeda zannuwan gado yasata dauke kai tayi gaba shikuma yashiga ciki, dakanshi yawanke wurin da ya baci din sannan yafito dasu da niyyar yaje yasasu acikin washing machine,

Dakin yadawo lokacin ta idar da salla tana goge kanta da towel,

"Ina kwana?" Tafada batareda ta kalleshi ba,

Zuwa yayi ya durkusa agabanta,

"Lafiya lau baby, ya wankan safe?"

Rabuwa tayi dashi taci gaba da abinda takeyi shikuma sai faman murmushi yake bakinsa yaki rufuwa ya gonar auduga,

"Inata magana kin rabu dani..." Yafada cikeda tsokana,

"Nifa bacci nakeji gaskiya"

Jin abinda tace yasashi sunkutarta zuwa kan bed ya kwantar da ita yana cewa,

"Kibari mana kisha tea, naga kamar harda yunwa bayan baccin ko?"

Daga mishi kai tayi nan yasauka yafita zuwa kitchen, mintuna kadan yahado mata tea mai kauri da wainar kwai yakawo mata lokacin har baccin yafara daukarta sama sama,

Tashinta yayi yabata tasha tea din sannan takoma ta kwanta, gefenta ya raba ya kwanta shima bayan ya rungumeta,

"Kaifa bazaka sha tea dinba?" Ta bukata idanuwanta arufe,

"Ni na koshi, abu daya kawai nake bukata.."

Bata sake bi takansa ba tayi baccinta, shima ganin haka yasashi yin baccin bawai dan yasoba.

Wuni sukayi suna barci sukuwa su Mami basu nemesu ba,

Karfe 1 saura suka tashi, wanka suka yi suka fesa kwalliya, ita wata maroon din atamfa tasa dinkin doguwar riga shikuma yasha kananan kaya sai kamshi suke,

Part din Mami suka nufa bayan sunyi salla, suna tafe yana rikeda ita suna yar hirarsu har suka shiga, su mamin dukkaninsu suna zaune suna kokarin yin launch,

Zama sukayi suma akayi dasu bayan sun gama suka koma part dinsu, Hafsat ce tace masa yakamata suje su sake gano jikin Hafsat mori, baiyi musu ba yayarda suka dauki surayya suka tafi, saida suka fara biyawa ta kings center suka yimata siyayyar kayan dubiya sannan sukaje asibitin,

Tana zaune akan gado tana waya da barrister aiman bayan fitar mahaifiyarta hajiya, ganinsu yasa tafadada murmushinta ta ajiye wayar tana yimusu sannu da zuwa,

Cikeda sakin fuska dukkaninsu suka gaisa da juna suka dubata, sun kai kimanin mintuna 30 sannan suka tafi bayan sun ajiye mata kayan dubiyar da suka Kawo mata,

Gidan Ummi suka wuce daga asibitin domin gaidasu, lokacin da sukaje sun tarar da ummin itada amal suna aiki a kitchen nan Ummi tashiga yiwa yusleem fada tana cewa daga tafiyarsu jiya shine zai biye Hafsat sudawo yau,

Har magrib suna gidan saida sukayi salla sannan suka tafi gida, a part din Mami suka yada zango suka bude babin hira har karfe 9 nadare sai lokacin suka koma part dinsu.

Yana zaune agefen gadon dake cikin bedroom dinta tafito daga wanka tana daure da towel saida gabanta yafadi lokacin data ganshi,

Tagefen ido yarinka kallonta yana murmushi har ta kammala shiryawa, jawota yayi yadora akan cinyarshi,

"Zo kigani.."

"Nifa gaskiya....."

"Kefa gaskiya me?"

Shiru tayi masa tana tutturo baki, daukarta yayi daga ita sai towel din yakaita dakinshi, wasu akwatuna guda biyu shake da kananan kaya da kayan bacci tagani sai sauran kayan shan iska nan tazauna tarinka duba kayan tana yaba kyansu duk da cewar bamasu nauyi bane,

"Haka nake son kullum kirinka saka min su ina hango kayana daga nesa,shiyasa nakawo miki tsarabarsu daga chairo"

Kunya taji maganarshi tabata dan haka tarufe fuskarta,

Da wayo da wayo yasamu ya lallabata har yakai ga cimma muradinshi.


Kullum sai sunje sun dubo Hafsat a asibiti sannan koda yaushe Hafsat da Hafsat mori take yin girki idan zasuje sai su tafi mata dashi dahaka har tafara samun sauki domin karayar dake hannunta ma tawarke,

Ranar alhamis aka sallameta daga asibitin takoma gida,washe gari ranar juma'a da daddare Hafsat tayiwa yusleem wanka,

Sabbin kaya tasaka masa milk colour din shadda mai tsadar gaske inbanda kyalli babu abinda takeyi tafesheshi da turaren silver man sannan tashafa masa farar powder tasa masa lipstick abakinshi bayan tagyara masa girarshi da brush,shidai kallonta yakeyi har tagama,

"Ina zamuje ne?" Ya bukata,

"Zance zakaje wurin Hafsat..."

Murmushi yayi domin bai ganeba,

"Zance kuma?"

"Kwarai kuwa, ya yusleem nasan Hafsat har yanzu tana sonka sannan kuma kasan tayi mana halacci, ni wallahi nayarda kaje ka nemi aurenta kakawota ka hadamu nida ita mu zauna akarkashin inuwarka"

Kallonta yayi cikeda mamaki zaiyi magana tahana taja hannunshi suka fito,

"Idan har kana sona karka yimin gardama kaje kawai"

Baiyi magana ba har tasashi acikin mota, tana ganin fitarsa tashige part din Mami domin bata son tazauna ita kadai shaidan yasamu damar ribatarta,koda taje bata fadawa su mami inda yatafi ba kawai cemusu tayi yaje unguwa.

Har yusleem yaje gidan alh Musa mori zuciyarsa bata gushe daga mamakin matarsa Hafsat ba, wani sabon sonta yakeji yana shigarsa domin yagane bata da mugunta da hassada saboda yanzu ba kowacce macece zata iya yin abinda tayiba, sam kishi bai rufe mata ido yasata manta alkhairin Hafsat mori agareta ba,

A parking space yayi parking yatura daya daga cikin ma'aikatan gidan yakirata, mintuna goma zuwa 12 sai gata sanye da bakar doguwar riga kamar koda yaushe kamshi na faman tashi daga gareta,

Kallon kallon suka shigayi shida ita daga karshe yasaki dan murmushi yace,

"Wannan kallon fa kamar yau kika fara ganina"

Itama murmushin tayi tace,

"To kila hakanne, lafiya naganka da wannan daren?"

"Nazo zance ne wajenki"

Murmushi tayi, "Ko?"

"Kwarai kuwa"

Shiru tadanyi shima yayi shirun zuwa can yace,

"Hafsat nasan abaya nayi miki wasu abubuwa wadanda basu daceba amma ina mai neman yafiyarki sannan ayanzu nashirya aurenki mutukar kin amince"

Murmushi hafsat tayi sannan ta kura masa idanu na tsawon wasu mintuna Wanda har saida shi kansa yaji ya tsargu da kallon,

"Yusleem kenan ai kuma ka makaro domin wani yarigaka,duk da nasan ba yin kanka bane tunda ada baka kaunata"

"Hafsat ai da kikace, ayanzu kinyi min abinda dole zuciyata ta amshi sonki"

Girgiza masa kai tayi,

"Nagode kuma naji dadi amma kayi hakuri bazan iya auranka ba domin nasamu miji daidai dani"

Zai sake magana ta katseshi,

"Nabarka lafiya agaida madam sannan gobe za afara zaman kotu domin saurarar kararku wadda nashigar akan tsohuwar matarka rahina, idan kasamu time zuwanka Nada mutukar amfani"

Tana gama fadin haka tayi gaba tabarshi awurin, ganin tashige cikin gida tabarshi yasashi shiga motarsa yakoma gida,

Bai samu Hafsat a part din mamiba dan haka yawuce part dinsu, acan ya isketa ta caba kwalliya tanata zuba kamshi tazauna zaman jiranshi,

Lokacin da taganshi da fara'a tatashi ta taryeshi tashiga jikinshi ya rungumeta,

"Sannu da zuwa, ka barota lafiya?"

"Lafiya lau baby, tana gaidaki"

"Ina amsawa, ina fata dai kayi nasarar sace zuciyarta da dadadan kalamanka"

Kai yagirgiza alamun a'a nan ta langabar dakai alamun neman karin bayani,bai boye mata komaiba domin Hafsat takasance wani sirri na rayuwarshi kuma ma ayanda ta nuna mishi to bazai iya boye mata komai ba saboda irinsune matan da miji baya iya boye musu sirrinshi, hannunshi takama,

"Ya yusleem wallahi banji dadiba ko kadan amma Allah yasa hakan shi yafi alkhairi"

"Amin" yafada yana jan hancinta.

Washe gari sun sami halattar kotun inda aranar aka gama shari'a aka yankewa Rahina hukunci daidai da laifinta,kwatanta irin godiyar da Hafsat tayiwa Hafsat mori abin ba acewa, tuni suka kulla zumunci mai karfi, haka itama Khadija har yanzu tana ziyartar Hafsat akai akai amma ba kamar da ba.

Soyayya mai wuyar fassarawa yusleem ke nunawa Hafsat wannan dalilinne yasa daga shi har ita suka manta da kowa sai junansu, ita Hafsat yanzu dadin da take ciki yasa tadade da manta wuyar da suka sha abaya sai yanzu tayarda da cewar komai lokacine gashi yanzu tana zaune cikin kwanciyar hankali da jin dadi,

Umarah yusleem yabiya musu shida ita suka tafi tacan suka wuce birnin london domin yawon bude idanu, watansu daya suka dawo, batare da tasaniba ya nemar mata admission a university nan yafara koya mata mota cikin lokaci kankani ta kware dan haka ya tura aka Kawo mata lafiyayyar mota mai numfashi yar yayi ta zamani,

Babu bata lokaci tasoma halattar makaranta inda zata karanci micro biology, kullum tare suke fita da yusleem dasafe tayi driving dinsu zuwa school dinsu idan sunje sai tafito tabashi motar daga nan yawuce office idan tatashi yazo ya dauketa,

Tsakiyar semester dinsu tafara wani bacci mai kashe jiki ga yawan cin abinci da takeyi hakan itada yusleem yabasu damar fahimtar cewar lallai sun samu karuwa, murna dukkaninsu suka shiga nunawa junansu bama yakamar yusleem wanda ya dauki son duniya da tattalinsa ya dora akan ta itada abinda ke cikinta,koda yaushe cikin bata kulawa yake hatta girki shine yake yimata.

Cikinta yanada wata biyar lokacin har ya bayyana suka fara shirye shiryen bikinsu surayya dasu Abdul, khalifa zai auri amal kanwar Hafsat shikuma Abdul zai auri Mimi kawar sury ita kuma surayya zata auri Dr faruk kwararren likitan kwakwalwa, Hafsat ita tayi ruwa da tsaki har aka kammala biki aka kai amare gidajensu,

Agajiye tazauna abakin gado tana nishi saboda gajiyar dake tattare da ita ga kuma ciki, ahankali yusleem wanda ke kwance yatashi zaune ya fara yimata tausa yana danna mata kafafunta,

"Ya yusleem yakamata gobe mukaiwa barrister Hafsat mori da mijinta barrister aiman ziyara kaga mun kwana biyu bamu haduba"

"Duk yadda kikace hakan za ayi gimbiyata"

Murmushi tayi taja karan hancinshi, shima murmushin yayi ya yi mata masauki ajikinshi cikeda so da kauna.



Alhamdulillah


Godiya ga Allah subhanahu wata'ala da yanuna min karshen wannan littafi lafiya, ina addu'ar Allah ya yafe mana kura kuren dake ciki ya taramu acikin ladan gaba daya Allahumma amin. Godiya marar adadi ga dunbin masoyana masu bibiyar labarina akoda yaushe, hakika banda kamarku kuma akoda yaushe da bazarku nake rawa, duk wata masoyiyar ummi A'isha wacce take jinta aranta ko nasanta ko ban santaba to tasa aranta nima ina kaunarta, Yabo da jinjina ga yan kungiyar Haske writers Asso, tabbas kudin nadabanne agareni ina addu'ar Allah yakara hada kanmu yakara mana dunbin basira da fasaha,Masu karatu sai mun hadu acikin labari nagaba idan Allah ya nufa.





*_Ummi Shatu_*👌🏻

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


2 Comments On ALWASHI
avatar
aliyu-1-5-2

1 year ago

Reply

I appreciate it

avatar
aliyu-1-5-2

1 year ago

Reply

I appreciate it

Please Login or Register in order to submit comment