An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
[11/6, 7:22 PM] Oum Hairan&Affan: ME YA JAMIN?
Fauziyya Tasiu Umar
(Oum Hairan)
1-2
Tsugunne a bayan gdan wata matashiyar budurwa ce yar sha shidda zuwa sha bakwai baƙa me matsakaicin tsaho da ɓoyayyen kyau take wankin kayan yara na makaranta tanata rawar sanyi da alamun yanayin hunturun yana kaɗa duk dama Dole ne ya shigeta duba da ko arziƙin rigar sanyi bata samu ba, wani yaro ne qarami da bazai wucce shekara bakwai ba ya fito daga wata ƙofa alamu sun nuna itane ƙofar da zata sadaka da asalin gdan.
Hankalinta nakan wankin da takeyi bata ankare sa tahowar yaron ba saiji tayi ya watsa mata ruwan sanyi a jikinta ta zabura da sauri ta miqe cikin kiɗima take duban yaron idanunta ya kawo ruwa tace “Farook ni ka watsawa ruwa a wannan sanyin ko?" Murgiɗa mata baki yayi yace “an watsa miki ɗin talaka almajira kawai Momy tace kizo ki haɗa mana break in kinƙi kuma ta zaneki"
A sanyaye ta saki aikin da takeyi tana daga rigarta data manne a jikinta ta nufi ƙofar parlourn ta shiga da sallama babu kowa a parlourn sai Muwaddat da jannat ta dubesu dukkansu babu wanda ya samu arziƙin ko wankin idanu ta matsa ta dauki Irfan daketa miƙo mata hannu tana masa murmushi tace “yarinyana ko Pampers baa cire miki ba bari nayi muku wanka sai nabaku abinci Isiya yakaiku makaranta ko?" Ta Faɗi da sigar tambayar yaran Muwaddat ta zunguro baki gaba tace “aa nidai Aunty Anam ki bamu abinci tukunna da yunwa muka tashi"
Saukowar masu gdan ne yasata haɗa nutsuwarta ta durƙusa cikin ladabi tace “barka da fitowa yallabai Hajiya Barka da asuba" baiko kalleta ba yasa kai ya fice a falon Hajiya Salma ce ma ta harareta tace “kinanan kina sakarcin naki na tsiya zaki makarar min da yara ko duba ko Pampers baki cirewa jannat ba saboda ke kin zama mara mutunci to ki makarar dasu sai hankalinki ya kwanta jaka kawai....."
Kalmar ƙarshen ta bugeta sosai ta sunkuyar dakai hakan bai mawa Hajiya Salma ba saida ta saukenta ƙusa a tsakiyar kanta ta rintse idanu hawaye nabin kuncinta inda sabo zuwa yanzu ya kamata ace ta saba da izayar gdannan tunda kusan a cikinta ta rayu tun tana shekara biyar suke tare da mahaifiyarta a wannan gda duk da kasancewar ba'a asalin wannan gidan suke ba mahaifiyarta tana gdansu Aliyu wato mamallakin gdan tanayima iyayensa aiki lkcn da Aliyu yayi aure ne matarsa ta matsa tanason yar aiki shine aka kawo ta gdan nasa matsayin yar aikin gdan yanzu shekara takwas kenan tana aiki a gdan a gabanta duk aka haifi waɗannan yaran Umar Farooq Muwaddat da jannat amma har yanzu yanci yaqi zuwan mata daga megidan har matar gdan har yaran gdan babu wanda take samun sauqi ta gurinsa har garama Salma wani lkcn takan jata suyi hira idan yan mutumcin na kusa.
Ɗaukar yaran tayi suka nufi dakinsu tayi musu wanka tasa musu uniform ta fito ta haɗa musu break ɗin sukaci Farooq nata barna shida Muwaddat babu wanda ta isa hanawa yanzun uwarsu tana dawowa su kitsa mata ƙarya da gaskiya ta hau ta zauna ta zage ubanta daya mutu tun batasan kanta ba ta zage uwarta data qare rayuwarta a bauta don rufa mata asiri sannan idan bai isar mata ba ta gama ta da dukan mutuwa wannan yasa take takatsantsan da lamarin gdan.
Daƙyar Allah ya taimaketa suka gama ta goya Jannat suka fito ta bawa Isiya lunch box ɗin yaran suka shiga Mota itakuma ta lulluɓe jannat ta koma ta karasa wankin ta shanya ta shiga ta fara gyaran gdan ɗakin Aliyu ne kawai bata shiga ba saboda yayi mata ƙwaƙƙwaran kashedi akan shigar masa ɗaki tun yana gda ko anan ɗinma da Salma taso sakar mata gyaran ɗakin da ita da Salman yacima mutumci dole tasa ta hqr take gyara masa idan ta dawo daga aikinta.
Tana kammalawa da parlourn ta nufi ɗakinta ta gyara ta kwantar da jannat tayi wanka tasa wata jemammiyar atamfarta domin Salma ta hanata Sanya kaya masu kyau kullum kaganta cikin tsumma zaka ishe da hijjab a jikinta batasan dalilin wannan doka ba.
Sai biyu ta shiga kitchen ta manta bata tambayi masu gdan abinda zasu ci ba ta ɗauki wayarta ta kira number Hajiya Salma saida ta katse ta sake kira sannan ta ɗaga cikin masifa tace “wai Anam ke wacce irin wawuya ce ina aiki zaki dameni...." Cikin ladabi tace “kiyi hqr Hajiya mantawa nayi ban tambaye ki abinda za'a girka muku ba....." Da masifa tace dalla Malama bansani ba ni zaki tambaya bazaki tambayi su Farooq ba to ki girka ubanki....." Qit ta kashe wayar Anam ta tsaye sororo da waya a hannunta tanajin ciwon yanda Hajiya Salma batajin nauyin zaginta yanzu daga tambaya sai cin mutumci?
A saluɓe ta nufi kitchen tana tunanin abinda zata girka lumshe manyan idanunta tayi dabara ta faɗo mata tasan Aliyu yanason tuwon shinkafa miyar taushe aikuwa nandanan ta fita tabawa driver sautun kayan taushe wanda babu a gdan ta koma ta ɗora tuwonta ta malmaleshi a leda ta fara tafasa namanta isasshe tasa masa kayan ƙamshi nandanan ta haɗa komanta sannan taja da baya tayi farfesun naman kaji da yaji Attahiru ta jere musu a dinning ta dauko man shanu soyayye ta narka takai musu dinning ɗin.
Shige daki ta zauna tana game da rakani kashinta jin motar masu gdanne yasata miƙewa ta fito tana riqe da hannun jannat sanye da ƙaton hijjab ɗinta caraf bisa tsautsayi idanunta ya fada cikin na Aliyu tayi saurin janyewa ta rusuna tayi musu Barka da dawowa ya amsa a shaƙe ya buɗe baki yace “hajiya tace kije can gobe Umaimah zatayi birthday akwai ayyuka acan"
Ajiyar zuciya tayi ko banza ta huta da masifar Salmah ta kwana biyu miƙewa tayi ta koma ɗakinta ta haɗa kayanta a yar ƙaramar akwatu ta dauko ta fito ta canza kaya tasa mayafi har sunyi wanka sun dawo dinning ɗin sunacin abinci ta rusuna tace “na shirya zan tafi" dubanta Salmah tayi tace “kwana uku zakiyi ki dawo" jinjina kai tayi Ta miƙe Aliyu dake satar kallonta yace “ki jirani a waje ganinan"
Jinjina kai tayi ta fita ta tsaya jikin motar ya ɗauki sama da 30 minutes sannan ya fito fuskarsa a murtuke ya buɗe motar ya shiga ya zauna ta buɗe gdan baya zata shiga yace “kinsan dake ni drivern babanki ne shiyasa zaki zauna a baya na tuqaki" bataso ake taɓa mata iyaye yanzun zuciyarta take karyewa ta juya jiki a mace ta shiga motar ya figa a guje ya fice daga gdan suka nufi Danladi na Sidi inda family house dinsu Aliyu yake suna zuwa ta buɗe motar ta fice yabi bayanta da kallo da mugun faduwar gaba ganin yanda take motsa jikinta.
Lumshe idanunsa yayi abin yayi masa dadin gani mamaki ya cikasa yaushe yarinyar ta girma haka har ta haɗa kayan ruwa haka? Saurin jan tsaki yayi yana kawar da tunanin ya fito a motar ya nufi cikin gdan a parlourn Ƙasa ya ishe su ita da Mamanta ta kama mata suna morping yana da hotuna Mama ce taga shigowarsa ta rusuna da girmamawa ta gaisheshi ya amsa kamar yanda yake amsawa da gadara ya haye sama Anam ta taɓe baki tace “kamar wani namijin ƙwarai a gda sai yanda akayi dashi" daƙuwa Mama Yabi ta watsa mata tace malafar ubaki ƴar nema koma mene ai yayi miki rana dalilin zaman gdansa gashinan kema ƴar Sakandire ɗin nan da yara sukeyi kin samu kinyi ta kuɗi to ubaki zakice da Haidar?"
Bata kuma cewa komai ba Umaimah ta fito da wata ƙawarta tana ganinta tace “yawwa Anam ki shiga ɗakina ki gyaramin ki shiryamin wardrobe ɗina kayan sun hargitse" amsawa tayi da to cikin ladabi ta nufi saman tayi sallama Hajiya Muniba tana zaune hakimce a parlourn gaban Anam ya fadi.
Ta rusuna ta gaisheta ta amsa mata a wulaqance tace “lfy" cikin in...Ina tace “Hajiya Umaimah ce tace nazo na gyara mata ɗakinta" jinjina kai tayi ta nuna mata hanya ta miƙe taci uwar ɗammara da mayafin ta nufi ɗakin na Umaimah ta soma gyarawa bayan ta gama ta fito har yanzu suna zaune a parlourn sabanin ɗazu yanzu harda Granny ta ƙwama uban glass tana ganinta sukayi murmushi a tare tace “ƴar nema jikar na samu kinje kin ɓuya luf abinki Haidar ya boyeki baku Abuja baku Kano zonan naji fatar ki ko tayi laushi"
Dariya tayi da tasa fararen haƙoranta da suka jeru reras da kyakkyawar wushiyar suka bayyana dimple ɗinta ya lotsa tace “Granny tawa bari nazo nayi miki tausar Tailand" Alh Ma'aru dake gefe yayi murmushi yace “Anam ta Granny nifa Ina tunanin Granny zan dawowa dake su Aliyu sa nemi wata" riƙe baki Granny tayi tace “hooooo Ni Mairamu rufamin asiri da wannan ƴar ƙaniyar ɗiyar tun tana mitsitsiyarta ma azaba take ganamin balle yanzu dubi yanda take wani haɓaka kamar amsawa tsiro taki yo dubi iyayen nonuwa da ɗuwaiwaka idan ta zauneni ai saidai na farka a kabari"
_whattsAp number 09013718241_
*Oum Hairan*
[11/6, 7:22 PM] Oum Hairan&Affan: ME YA JAMIN?
Fauziyya Tasiu Umar
(Oum Hairan)
3-4
Wata baƙar kunya ce ta kama Anam tayi ƙasa da kanta cikin tsananin jin kunya sumsum ta fice Alh Ma'aru yana mata dariya yana cewa “Anam badai kunya ba Hajiya kin bawa yar dakin naki kunya" itadai ƙasa ta sauka taci gaba da taya Mama Yabi aikin da takeyi suna gaf da gamawa Aliyu da Alh Ma'aru suka fito sukayi musu adawo lfy sannan sukaci gaba da ayyukansu basu suka gama ba sai bayan Magrib Anam ta shige ɗakin Mama Yabi tayi alwala tayi sallah ta miƙe a katifa Mama Yabi ce ta shigo masu da abinci ta tashi sukaci suna taba hirar su ta ƴa da uwar suna dariya can Anam ta haɗe rai ta koma kalar tausayi Mama ta dubeta tace tunda kika zo na fahimci damuwa a yanayinki meye ne yake faruwa?" Ƙwalƙwal tayi da ido tace “Allah mama na gaji da masifar Hajiya Salma kullum saita zageki ta zagi ubana da banma sanshi ba ga ƴaƴanta rashin kunya babu kwaɓa kamar ƴaƴan Allah bani musamman Farooq da Muwaddat ji suke kamar zasu iya cin abinci akaina"
Jinjina kai Mama Yabi tayi ta zubawa ƴartata ido tare da sauke numfashi tace “zuwa yanzu ya kamata ace kin saba da waɗannan ƙananun abubuwan Anam ya mutum zaiyi da yanda Ubangiji ya tsara masa rayuwarsa ne saidai ya gode masa kawai in yaƙi kuma ya godewa azabarsa don Allah ki koyi haƙuri da yanayin rayuwa komai zai wucce insha Allahu watarana sai kiga labari kike badawa"
Bata da wata sauran kalma data rage da zatayima Mama bayani ta fahimceta dole tasata yin shiru ta kwanta itadai da Dad zai taimaketa kamar yanda ya furta ya dawo da ita gurin Granny tabbas da taji daɗi sosai. Bayan sunyi sallar Isha wani aikin suka dauko ita da Mamanta sukeyin komai cike da kulawa da juna har suka gama wajen 11:30 suka nufi ɗakin Mama suka kwanta sunata yan hirarrakinsu mama tana faɗa mata so takeyi idan lkcn hutunta yayi zataje Gashua ta kwana biyu rabonta da gida Yobe shekara huɗu kenan kallonta Anam tayi tace “amma meye zai hana mu tafi tare Mama nima inason naje naga dangina"
Dafa kanta mama tayi tace “to banda abinki Kharimatu ai zakije ne kinsan yanayin aikina da naki ba ɗaya bane kedai kije kiyita hqr da halin iyayen gdanki watarana zai zama tarihi kinji" ɗaga kai tayi ta fara addu'ar kwanciya bacci badon taso hukuncin na Mama ba sai don ba halinta bane jayayya da mahaifiyarta da wannan bacci ya ɗauke ta da asuba kuwa suka shiga zarafin aikin abincin birthday duk da cewar an bayar da kwangilar wani amma yanayin yanda suke d yawan masifa gasu da ɗabbaƙa bidi'a yasa gidan ya cika ke kya dauka bikin aure sukeyi ko suna Anam Bata samu kantaba sai huɗu da yammaci tun safe dake Allah ya hore mata lfyr aiki kamar engine tayi wankanta ta ɗauki wata lashinta da Umaimah ta bata tasa riga ce doguwa saiya kasance sun fito mata da asalin surar ta da ƙuruciyarta abinka da chocolate color oily skin sai milk ɗin less ɗin yayi mugun haskata tayi kyau na ban mamaki ta fita ta nufi sashin Granny ta sameta ita da Alh Mahdi wa gurin Alh Ma'aru ta rusuna ta gaida shi ya amsa mata da sakin fuska Granny tace.
“Ƴar nema kinzo ki tumurmusani ɗin ne?" Dariya tayi tace “haba My Kakus ƴar tsohuwa yaushe rabonki da tausa irin tawa me daɗi saboda daɗinta fah kikece mata tausar Tailand" kama ƙafarta tayi tana matsawa a hankali Alh Mahdi ya tashi yace “Hajiya Iya tunda kin samu ƴar hira bari naje gurin yaran can da suka cika mana gda da kiɗa kamar ƴaƴan yahudawa"
Fita yayi Hajiya Iya da Anam sukaci gaba da hirarsu Hajiya Iya na korarta ita kuma ta nace taƙi tafiya saida tace “zakici kunnen Uwaki bari na kira miki Mala'ikinki Haidar ai yana gdan naga zuwanshi da iyalinshi ƙila na samu salama kajini da ƴa ƴar kusun uwa tanata murɗemin yatsa......"
Wata ƙara Hajiya Iya ta saki daidai lkcn da Aliyu ya shigo tayi caraf tace “yawwa Haidaruruwa kaɗamin wannan ja'irar yarinyar gurɗemin yatsu take neman yi" kafin ma ya waiwayo kanta tayi wuf ta shige ɗakin Hajiya Iya tana cewa “Granny kefa kikace nayi miki shikenan tunda bakiso bari na gyara miki ɗakinki na jera miki kayanki a wardrobe"
Bata kula da hararar da Aliyun ke watsa mata ba shi yarasa meye tashi batazo ɗaya da yarinyar ba yanda ta nufi ɗakin tana kaɗa jiki yayi mugun ƙular dashi a haukansa gani yake donshi takeyi wanda ita batasan ma da hakan ba tunda bata taɓa samun mai faɗi mata ba. Tana jiyo hirarsu da Granny yau ma kamar kullum Ƙorafi takeyi masa shi yaƙi gaba kullum kaganshi kamar haɗowar hadari bayada fara'a baya da rahama a fuskarsa inda shi kuma yace “nikam Granny kinsamin ido da yawa duk duniya kece kike cemin na ragu kona ƙaru ke kuma ba iya yimin maganin matsala ta zakiyi ba"........
Sunata hirarsu da zolayar juna yanata dariya abinda kullum yake bawa Anam mamaki ko a gdansa ita zata iya rantsewa bata taɓa ganinsa yana dariya ba kullum fuskarsa kamar ta bijimin sa amma Indai ya haɗu da Granny yanzu zakijishi yana ɓaɓɓaka dariya, taɓe baki tayi a ranta tace “miskilin banza da baya iya control na gdansa a fili kuma amsa kiran da Granny take mata tayi ta fito tana goge fuskarta da tsumma ta rusuna tace “gani Kaka" nuna mata kitchen tayi tace “wannan kitifaffen ubangidan naki zaki haɗowa abinci yace anan zaici"
Miƙewa tayi ta nufi kitchen ɗin yana latsa wayar hannunsa ta haɗo sinasir da miyarsa da taji tantaƙwashi da man shanu ta dauko masa lemu me sanyi da ruwa ta jero masa ta nufo inda yake gabanta na faɗuwa ko a gda bata ƙaunar kai masa abinci saboda baayi masa gwaninta.
Tsugunnawa tayi a gabansa mayafin jikinta ya zame daga kanta dake me yauƙi ne ya sauka ƙasa bisa rashin saa rigar irin me buɗaɗɗen wuyan nan ce tudun dukiyar fulaninta duk a waje suke hakan yayi daidai da ɗagowarsa da nufin yi mata masifar daya saba tsautsayi yasa idonsa ya caki ƙirjinta da batama lura da mayafin ya zame ba ya zubawa wannan abu me matuƙar ɗaukar hankalinsa a jikin mace idanu kamar wanda ya warke daga ciwon makanta, hakan yayi daidai da ɗagowarta da nufin neman izinin tashi domin ta gama haɗa masa kawai ta mayar da idanunta a ƙirjinta taga abinda ya shagala da kallo. Ta kuwa firgita ainun a razane ta wawuro mayafinta ta rufe jikinta ko ina na jikinta ya ɗauki rawa tasan yau ta shiga uku har shida gaban shida har tara ma ta shiga.
[11/6, 7:22 PM] Oum Hairan&Affan: ME YA JAMIN?
Fauziyya Tasiu Umar
(Oum Hairan)
5-6
Cikin kiɗima ta ja da baya ta zube a ƙasa tayi knile down tace “kayima girman Allah da darajar Hajiya da Alh kayi hqr wlh tallahi bansan ya zame b......" Ɗaganta hannu yayi ya haɗiye kunyarsa cikin ƙara ji yace “tashi kibani guri mara sanin ciwon kai wato ke nan har kinkai budurwar da zaki rinƙa tallan jikinki a kwararo toni ko jiki zai burgeni me zanyi da wannan baƙar fatar taki wawuya dake bagidajiya"
Itadai Anam har tuntuɓe takeyi saboda sauri sukayi kicibis da Granny ta riƙota da sauri tana cewa “ke marainiyar Allah nutsu kama kanki meye yayi zafi da wannan firgici haka me Haidar ɗin yayi miki?" Toshe bakinta tayi domin batada kalmar magana ta janye ta kwasa a mugun guje ta nufi bayan gdan saida ta fakaici ido sannan ta shiga gdan ta shige ɗakin Mama Yabi cikin Sa'a itanma batanan ta kwanta tana mayar da numfashi tare da yima Allah gdy daya kuɓutar da ita daga cin duka gurinsa tananan kwance har aka gama birthday ɗin kowa ya watse saida ta tabbatar da tafiyar Aliyu da Salma sannan ta fito suka shiga gyaran gdan basu gama ba saida dare ya shiga suka ƙarasa suka kwanta .
Washegari ma aikin ne dasu Hajiya Muniba irin matan nan ne da baayi musu gwaninta komai kayi baka iyaba su gyara nan tace ba hakaba su gyara nan tace a'a daƙyar Allah ya basu ikon gamawa itama wannan rana sunji a jikinsu dan ko abinci basu samu damar ci ba sai Magrib suna cikin cin abincin Umaimah ta shigo ta dubeta tace “Ya Aliyu yace kije ku tafi gobe Monday sunada aiki" wani abu ya tokare mata maƙoshi abincin data zuba a bakinta yaƙi haɗiyuwa a ranta tace “shikenan shi bawa bashi da hutu bashi da ƴanci a rayuwarsa?
Mama ce ta taɓa ta tace “ki tashi karkiyi laifi Haidar ba wuya bane fusatashi" miƙewa tayi sarai tasan halinsa ko kayanta bata ɗauka ba ta fita yana zaune cikin mota ta nufi motar gabanta na faɗuwa da kuma matsananciyar kunyarsa ta isa ta buɗe ta shiga bata ko samu arziƙin kallo ba ya gama wayarsa yatada motar suka tafi har sukaje gdan bai tanka mata ba yana parking ta fita yabi bayanta da kallo tare da taɓe baki.
Turus taja ta tsaya saboda ganin yanda parlourn yayi kaca² yaran duk sun ɓatashi da gudu Jannat ta nufota ta ɗauke ta tana juyawa da ita tanayi mata dariya yarinyar ma na dariya daidai lkcn da Salma ta fito Anam bataji tahowarta ba kawai sukayi karo aikuwa ta angajeta bisa tsautsayi ta faɗa kan cup ɗin glass ɗin ɗaya fashe a parlourn aikuwa ta fasa ƙara saboda nitsewar da kwalbar tayi a goshinta jini yayi wata irin tsartuwa ya fallatsa har jikin Aliyu dake tsaye tun lkcn da Anam keyima Jannat wasa.
Da gudu ya ƙara so kanta ya ɗagota gabaɗaya jini ya wanke mata fuska yace “subhanallahi Salma bakida hankali ne wasa fa takewa ƴarki shine zaki ture ta har kiji mata ciwo haka kefa kika dameni naje na ɗaukota yara sun dameki dama abinda kika shirya yi mata kenan?"
Yana mgn yana tare jinin da hannunsa inda ita kuma Anam taketa jijjiga kanta daya ɗaure da wani mugun ciwo, taɓe baki Salma tayi tace “to ko zaka rama matane Aliyu naga alamun kaji ciwon kaima a jikinka" kallon Salman yayi rashin lkcn bata amsa yasashi kama hannun Anam yace “Sannu Kharimatu tashi muje ayi miki dressing na gurin" miƙewa tayi tana layi saboda ba ƙaramin jini ta zubar ba motar yaja a mugun guje suka fice daga gdan suka nufi wani asibitin kuɗi a cikin unguwar ta Yankaba tasha wahala kafin su zare kwalbar sukayi dressing gurin likitan ya dubesa yace “zatayita fama da ciwon kai dole ta rinƙa samun hutu" jinjina kai yayi ya biya su suka fito har yanzu kuka takeyi bawai na zafin ciwon bane a'a tunawa da tayi cewa da mahaifinta yana raye qila duk da haka bata rinƙa faruwa da itaba.
Sau ɗaya yace mata sannu har sukaje gda wani abin mamaki Salma Bata gyara gurin da jinin ya zuba ba balle ta gyara parlourn Suna shiga Anam ta ɗauki tsintsiya zata share parlourn ya dakatar da ita yace “kije ki kwanta kawai" aje tsintsiyar tayi ta nufi ɗakinta ta kwanta nandanan kuwa zazzaɓi ya rufeta me zafin gaske a daren taci wahalar zazzaɓin batayi tunanin zatakai safe ba hakanan dai ta rinƙa addu'o'in da suka sawwaƙa a bakinta har zuwa wayewar gari da safe da wuri ta tashi domin shirya yaran zuwa makaranta ta kamasu tayi musu wanka tanayi tana duba breakfast ɗin data ɗora harta gama ta haɗa masu gdan basu sauko ba ta zauna tana rawar sanyi tana bama yaran abinci zazzaɓi na ƙara ƙarfi sanyin A.C na haɗa ta ita ba abin ta kasheba matar gdan ta nakasata.
Gama sallamar yaran tayi takaisu ga driver ya tafi makaranta dasu hadda jannat dake itama ansata juma'a ne bata zuwa ta dawo a wahalce ta rinƙa gyara gdan ta kusa gama parlourn taji sun sauko ta durƙusa cikin ladabi ta gaishesu Salma ta ɗauke kai sai Aliyu ne yace “ya jikin...." Kafin ta bashi amsa yaga yanda take rawar sanyi yace “ko zazzaɓi kikeyi ne?" Ɗaga masa kai tayi ya matsa ya taɓa jikinta yaji zafi zau ya dubi Salma yace “ki ɗauki key na motarki ki tafi zan Kaita asibiti" wani malolon baƙin ciki ne ya cika zuciyar Salma ta kuwa taso masa da cewa “haba Aliyu wannan ai wulaƙanci ne