Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 5
dan rainanta ma kamar hannunsa ya koma har wanka wani xubin shike mata. Lokacin da xata shiga primary shi yatara yasai mata jaka da takalmi daukanta ma yai sukaje ta xabo abinta tun daga lokacinduk rintsi tare suke tafiya sai ya goyata a keke yasauketa sannan ya wuce. Yanayin yadda fadya ke shiga tafi sauran yan gidan sa ointa domin domin komai farhan yasani na yayi kanwata basai gidan yadauka ba mairo ta mallake yaro yaxama bawanta ita da yayanta. Xuciya nasan mai kyautata mata yanayin yadda farhan kema fadya yasanya ahankali tafara jin sansa tun tana daukan abin wasa sai wayar gari tai xuciyarta cike taf da kaunarsa sanda ko kanta ba lallai tanaima ba yayinda shi ko kadan hankalinsa bai kai nanba shi yadauketa ne a matsayin kanwa ta uwa daya uba daya. Kanwata Na F.A.Ya'u Awani bangaren Fara diya ce ga Alhaji Hamza wani hamshakin dan kasuwa wanda kusan duk wani wanda ya kwan ya tashi da an ambaci sunansa yasan da xamansa. Alhaji hamxa haifaffen kanone shine na biyar a family dinsu wanda ya kasance da tun auransa Allah vai bashi haihuwa ba shekararsu ta takwas da aure Allah ya basu da namiji saidai yaron yana da shekara daya da watanni Allah yai masa rasuwa tun daga lokacin haihuwa ta bude saidai babu wanda ya xauna Fara itace ta hudu wanda itama tunda suka haifeta take laulayi kala kla dan itama din sun fara cire rai da ita. San duniya daga uwar har uban sun dauka sun dorama Fara duk abinda take so shi ne suke mata yarinya ce ba kwaba batasan ta nema ace babu ba kullum akwai tasani gata ko yayan shugaban kasa basa nuna mata ba. Duk wani buri na duniya Alhaji hamxa ya dora kan diyar tasa burinsa tai karatu mai xurfi ya aura mata mai kudi kamarsa yadda baxatai kuka ba. Alhaji hamxa irin mutananne dabasan talaka kai duk wani talaka na unguwar yasan da xaman rashin mutuncinsa sai Allah ya hadashi da mata irinsa wadda ke kara xugashi. Saidai kash sunyi sake saiga diyarsu diyarso daya jal da duk buribsu ya dori kanta ta afka cikin kogin san talaka sunan da sukafi tsana kuma ma talakan dan gidan da duk unguwar babu yasu a talauci. Kanwata Na F.A.Ya'u Dagaske fara ta rasu hakuri xakai summa tafi da ita gida tun daxu nasan yanxu ankaita yafashe da kuka maiyasa ba'atashen naimata kallon karsheba mai yasa baku tashen ankaini da ita ba hakuri xakai haka Allah ya kaddaro ayanxu addu'arka kawai take bukata ba kukaba hakane hawayensa suka karu Allah yajikanki fadya yai miki sakayya da gidan Aljanna yawwa ko kaifa kukan ya isa haka kasan va cikakkiyar lpy ce dakaiba kayi hakuri karka jamakanka illah ka kyaleni nai kukana nikadai nasan rashin da nai ni akama wannan mutuwar eh hakane kowama haka yake fadi anman hakuri shine kasan kukan vaxai dawo da ita va. Acan gida ana tsefe mata kai inda suke jira a gama a hadata dan kaita makwancinta kakarta na gefe tai tagumi ta tsurama gawar ido anya kuwa ba motsi naga takeba baba kenan idonkine dai dan naga tun daxu kike fadin ke baki yarda ta mutuba hakuri xamuyi mu mata addu'a Allah ya jikanta uhum ni nasan idona gaskiya yagani anman tunda kunce haka Allah ya jikanta. Dagaske tana motsi wallahi inji umma hadixa dake tsefe mata kan dasauri umma bilki ta mike bari asamo mota tai waje inda masu jiran afito da gawa suke dako ta fada musu daranta asamo mota dasauri wani makocinsu dake daura alwala ya ijiye butar yai gidansa kankace me ya kawo motarsa kofar gidan abaya akasanyata sai ummanta dake ciki abbanta agaban mota sukai asibiti. Sauran yan uwa suka biyosu a motar haya. Batare da wani bata lokaciba likitoci suka bayyana akanta dan bata taimakon da take bukata sunyi darajar saita numfashinta. Likita ya fito abbanta yai gunsa ya ake ciki likita gaskiya tana cikin matsala sosai xuciyarta ce ta kunbura take samun matsala wajan bugawa. Kanwata Na F.A.Ya'u Duda kasantuwar cewar likita ya fada musu halin datake ciki na rayuwa ko mutuwa hakan baisanya su farin ciki da godema Allah ba da yai bata mutuba. Dan Allah da gaske kake ko da wasa wallahi da gaske nake fadya bata mutuba ynx haka tana asibitinnan saidai batasan inda kanta yakeba mekake sanyi xuwa gunta xan mana kace tana asibitinnan eh nace kuma batasan inda kanta yakeba baxasu barka ka gantaba sun hana kowa shiga pls ka koma kaxauna kasan ba lpy ce dakaiba. Gaskiya abin nata ya wuce tunaninmu aiki xa'a mata aiki doctor eh bakuma anan ba india ya xaro ido india eh hakan yasa nake sanar muku kutanadi at list two million koma da rabi million fa doctor ina kake tunanin xamu samu wannan kudin ya watsa hannu gami da tabe baki taya xan sani kuyi gaggawar kawowa dan komai xai iya faruwa in aka samu jinkiri. Allah sarki fadya Allah ya jikanki haba malan ya kake da saurin karaya haba mairo inban karayaba to mai xanyi kina kallo duk wasu yan kadarorina nasaida lokacin dashen kodar farhan kinajin yadda mukai da yaya danai mgn cewa yai ai nine ubansa tunda tun yana yaro yasallamamin shi suma sauran kina kallo kowa naima mgn sai yace babu to inaga naje ga maganar million eh hakane amman Allah yana tare damu saikaga ya fito mana da mafita inda bamuyu xatoba kaidai muyi tamata addu'a ya kada kai eh kema kince wani abu. Fara kina xuwa sch kuwa eh mn anya kuwa tai dan murmushi kayi shuru kasan bansan kana yawan mgn baka gama warwareba eh kyace nai shuru mana tunda kina gwangwani yawwa daxu da kikaje dakin kanwarmu ya kikaga jikin nata tai shiru dan tuno yadda ta ganta saida tai mata kwalla bakiji mai naceba tadanyi kamar batajiba maikace nasan kinji anman bari na maimaita yakikaga jikin kanwarmu ah jiki da sauki duda tana bacci harna tawo hakane kitashi ki tafi kar kiyi dare aikasan yau lecture har six munada kona kai mgriba babu abinda mum xata xata pls indai vaso kike nai fishiba ki tashi ki tafi to shikenan kar ai fushivdani Allah ya kara sauki ta mike ta fice. Kanwata Na F.A.Ya'u Wai yanxu da gaske haka munaji muna kallo fara xata auri wannan matsiyacin kedai bari muga lokacin dana bata muga wane xata xaba mu iyayenta ko shi tai dariya Allah ya nuna mana saidai kinsan wani wani abu karta kuma hadani da inna kaka ka kyaleni da ita indai ni na haifeta baxata kuma xuwa kai mgnar nan gun hajiya kakaba. Tun kwanciyar farhan a asibiti fara tai hijira xuwa makaranta domin inta fito da xummar agida ta tafi sch asibiti take tawowa direct kullum tana gunsa koya ya motsa xata mike tanai masa sannu komai ta samu duk yan kudinta anan yake karewa indai annemi wani abu indai tananan toko ita xata biya bakyashi ko wani shayi sai yayi da gaske take iya tafiya intana xaune tausayinta yakeji sosai burinsa aduniya bai wuce fadya ta warke ba ya nuna mata so ya nuna mata gata irin wanda babu wata diya daxatace ta sameshi danshi sai yanxu yagano shima din yadade yana santa. Yanxu doctor babu wata mafita dai ta aikinnan ehto akwai magani saidai shima yanada tsada bai kuma cika yiba aiki yafi dan inakai sa'a aka dace shikenan yawwa doctor mai xaisanya abamu maganin mu gwada ko Allah xaisa mudace tunda nasan shi vaxai kai kudin aikinba ok shi ya biyoni office sai a rubuta muku. Kanwata Na F.A.Ya'u Cikin ikon Allah maganin yana aiki tunda doctor dakansa yafada musu gashi kunburin datai harta fara sabewa. Sukansu sunfara ganin cigaba dan da kawai sunajin doctorne takan bude ido wani sa in harta dan murmusa. Ai farhan yadda ya takura musu saida adole suka kaishi inda take yana yin yadda yaganta duk tausayinta ya kamashi haushi kansa ya cika masa xuciya dakyar ya tafi dan cewa yai saita farka dakyar suka ce ammata allurar varci yatafi. Dan Allah yaya farhan wata alfarma xaka mun inajinki Aisha daman so nake kataimaka kaban takardar dana kawo maka sabida mai inasan naxamto mai cika alkawari kamarya munyi da fadya kan baxan baka takardarba sai ta mutu intaji na baka vaxata kuma yadda daniba ni nai gaggawa daban bari ankaitaba shikenan Aisha xan baki saidai na manta inda na ajiyeta saboda banma karantaba nayi xaton ko kawai rubutunta ne da tasaba bani inxata fita ina bacci sannan dan Allah kataimaka karka taba nuna mata cewar nabaka pls yaya shikenan naimiki alkawarin ko da wasa baxatasan nasan meta bakiba yawwa yaya na gode. In tambayeki kekinsan maita rubuta a'a tace ta yadda dani in taimaka kar inkaranta yadda tavan haka na baka gashi nima bansan me ta rubutaba mutuwar da aka fadan tasa banbi takantaba muje na duba miki sai in vaki. Aisha taji dadi dataga dagaske bai karantaba dan da auka koma dakin ma saida yadanyi lalube ya dauko mata dan haka takarbi abarta da kwarin gwiwar in fadya ta warke ta bukaci abarta xata iya rantse mata yaya farhan baisan maine ta rubuta ba. Kanwata Na .F.A.Ya'u Jinyar fadya kabaki daya farhan ne da fara duk wani abu da baxau iyaba ita takeyi saidai in batanan sauran yan uwa suyi . Jiki kam yai sauki dan yanxu ma anbasu sallama danshi farhan tuni aka sallameshi . Umma dan Allah inasan xuwa gidansu Aisha ina ba inda xaki dan Allah yaya wallahi baxakiba yadda bakida lpyar nan haba yaya nafa warke anman sai kadinga cewa banda lpy ni banga alamun waraka atare dakeba adalci daya xan miki inje inkirata to yaya nagode . Yawwa Aisha so nake inkuma tambayarki karki gaji dani sai nake ganin kamar kin baima yaya takaeda ta haba fadya saunawa kikesan na rantse miki koso kike na hadiyi alqur'ani hankalinki xai kwanta to yi hakuri maida wukar na yarda suka dan taba hira kafin Aisha ta mike bari naje wanke wanke nake yaya ya tasoni ta rakota kofar gida ita kuma ta dawo gida. Akullum ya xauna bashi da aiki sai tunani yasani tabvas yanasan fara inya barta baimata adalciba to anman yaxai yida kanwarsa wadda yakeda yakinin baida masoyiya kamarta aduniya baijin xai kuma samu kamarta to mai xai hana kahadasu biyu inji zuciyarsa ina ya fada abayyane baxai yiwuba banda burin mata biyu fadya ta shigo rike da kwanon abinci yaya tashi kaci abinci ya dan mike a firgice yaya tunanin mai kake yai wani malalacin murmushi ba tunani nakeba uhum yaya kenan ta fada gami da xaunawa. Kanwata Na F.A.Ya'u Kinajina kinmun shuru sai kace da kurma nake mgn ko suk salon wulakancin ne dan Allah dady kayi hakuri ba cewa nai kiban hakuriba dan hakurinki bashi nake bukataba so nake kiban amsa abvan salim ya daka mata tsawa malama ke muke jira muna da abin yi kina batq mn lokaci. Inaso ki kara sanin wannan damar itace ta karshe da kikeda ita inkin xabi salim shike nufin kin xabi iyayanki inkin xabi farhan shike nufin rabuwarki damu na har abada tadaga kai takallesu daya bayan daya sai hawaye kinga ba kuka muka kiraki kimana ba kiranki mukai ki fada mana wanda kika xaba dadi ina kukan saba muku daxanyi ne nasani van kyauta muku ba ku yafemun na xabi farhan momi ta mike da hargagi xata daketa ya daga mata hanni batta ta riga ta gama nunan ni bata daukeni uba ta canja uba to wallahi ki sani yadda kika sanyama idonki toka haka xan rufe nawa idon in manta ni na haifeki xan manta inada ya dama can bansaka ran rayuwarki ba da bansameki ba am doing ok so when kin xabi ki rabu damu i will still be happy fiye dama kina nan. Na vaki sati daya shi uban da uwar da kika canja yaxo ya biya sadakinki kibarmin gida bana bukatar komai nasa kamar yadda kaeyasanya rai da xanyi miki wani abu ke kika ga xaki iya inkina da kudin yima kanki sai kiyi ta mike shikenan dady nagode tabar dakin. Alhaji wannan hukuncin dakai shine dai dai tunda ta nuna ita bata haifuba inji baban salim yakalleshi bai ce komai va yabar dakin danshi kadai yasan dacin da ransa ke masa Abban salim yai wata dariya ta mugunta gami da jan dansa subar giddakin. Kanwata Na F.A.Ya'u Tana kwance akan gado tana jiyo motsin momi ta rufe idonta kamar mai vacci tashi muyi mgn nasan ba bacci kikeba tai shuru bakiji mai nace bane ki tashi muyi mgn nace ko badake nake bane ahankula ta mike ta xauna. Wallahi fara kin bani mamaki da har kika iya xabar namiji akan iyayanki so nake kifadan wane irin dadi yake baki da har tafiye miki iyayanki tai shuru koda yake baxaki fada ba anman ni nasani kun gama lalacewarku a waje shiyasa kika kasa rabuwa dashi wallahi momi ba haka bane to in ba haka bane yane eyhe. Ta fashe da kuka momi dan Allah kifadan gaskiya ke kika haifeni awwa lallai kin rika wato kokwanton kasantuwarmu iyayanki kike ma wato kin manta irin gatan da muka baki a vaya ko ba haka bane momi ina mamakin yadda kudi ya fiye miki farin cikina alhalin nasan ko wacce uwa na fifita farin cikin danta kan komai bama kudi ba vaxaki ganeba abinda yanzu nake miki shine xai dawwa mar miki da farin cikinki na har abada yanxu sone ke janki dakinyi aure xaki fuskanci mai muke hango miki momi ni aguna kudi ko dukiya bashine farin ciki ba dalla ni yimun shuru naxo in fada miki indai har ni nahaifeki nakuma isa dake kije kisamu babanki kice kin janye aurenki da wannan matsiyacin kinajina ko fuu ta fice tabar dakin. Kanwata Na F.A.Ya'u Fadya an warware dan yanxi harta koma sch kullum ummanta cikin mata nasiha take kan ta dena sanyama ranta damuwa kodan lpyarta yayinda farhan ya ninka kulawarsa akanta ko ya yaga tai shuru ya dinga janta da wasa kenan harsai yaga ta ware. Tana iya kokarinta wajen cire farhan aranta duda tasan abune mai wuya so daya ne ta kuma riga ta vashi ta yanke shwarar cema muhd ya fito watakil intaga angana mgnr aurenta ta hakura ko yaya ne ta soshi . Gavaki daya gidan an sauyama fara danko gaisuwarta basa amsawa ba ruwansu da mai take ciki lpyrta ko rashin lpyrta taci abinci ko bataciva saidai taurarriyar xuciyarta kasa bata shawarar sauya ra'ayi tanajin xata iya jure komai akan farhan indai xata aureshi. Yau da wuri ta shirya dan vata dabwayar farhan dan ta sanar dashi yadda sukai da dadin nata koda taje gidan sun gaisa da umma cikin sakin fuska dan sun saba sosai ta nuna mata dakinsa suna ciki suna hira shida fadya ta shiga suka gaisa kafin fadya ta mike dan varin dakin ina xaki ki xauna mana ba wani abu bane inji fara ta koma ta xauna nan ta fada masa komai yai shuru baice komai ba ta tsaya tana kallonsa dan tagano hakikanin halinda naganar tasanyashi wato farin ciki ko bakin ciki saidai ta kasa fuskanta shurun yai yawa fadya tace yaya baka ce komaiba ya mike ina xuwa yabar dakin Kanwata Na F.A.Ya'u Ina zuwa fadya ta mike tabi bayan farhan haba yaya yaxataxo maka da mgn irin wannan anman ka kasa nuna mata farin cikinka saima katashi kabarta yadan juyo to mai kikesan nanata kinasan inbata goyon baya ne wajen sabama iyayanta to anman yaya da wanne xataji da abinda ake mt agida ko taxo ka nuna ko in kula akalla kamata nasiha dan ta fuskanceka hakane kuma kince wani abu muje. Shikenan ta goge hawayenta bayan gama sauraron dogon bayanin farhan din Allah yai daman nidin ba matarka bace nagode ta fice tana kuka jiyai baxai iya hakura yabarta ta tafi ahakaba da sauri ya bi bayanta tanaji yana kwala mata kira saima sauri data kara saida yadan kara sauri kan ya sha gabanta ruwanda ke hannunsa ya mika mata pls kitaimaka ki wanke fuskarki yakarbi robar bayan ta wanke ya karbi robar ya mika mata hankici ta goge fuskar suna tafe yana kara bata baki kafin suje kofar gidansu harya yasamu ta gamsu saida ta shiga gida sannan ya juya sai asannan wani zazzafan hawaye ya zubo masa dan sanin ya gama rasa Fara. Zaune suke suna kallo tazo asalube ta zauna arakube can gefe babu wanda ya daga ido cikinsu ya kalleta balle su nuna alamar sun san da ita a hankula tace dad gurinka naxo to ingurina kikaxo baki iya mgn daman abba so nake infada maka nafasa auran Farhan inasan auran duk wanda kuka ban to inkin fasa auran farhan saimai ta daga ido a tsorace dad dan inasan yimuku biyayya biyayya ai lokacin yagama ficeki kin riga kin bata wayanki tun afarko. Kanwata Na. F.A.Ya'u Ya tabe baki aimun riga mungama mgn kin san Allah baxan janye mgn ta ba ni baxan kara karan banin zaba miki mijiba kinriga da kin nunan iyakata dan Allah dad kayi hakuri karki ban hakuri inma yaron ne yace baiyasanki to kiyi gaggawar kawo wani kafin juma'a inba hakaba xakibarmin gida nafasa miki ummanta dake gefe tace Amman alhaji ya daga mata hannu karkice dani kala ya mike yabar gun itama dagudu ta tashi tai daki tana kuka yadda dad yai fishi tasan baxai sauya batunsaba. Fadya kenan to yanxu mai kuma kikesan na miki tai murmushi dan kanwa taxo gun yayarta wani abune tai dariya to muje ciki suna shiga Fara ta fada jikin fadya tana kuka adan tsorace tadagota yayarmu lpy fadya nashiga uku kowa ya tsaneni mai ya faru nan ta fada mata duk yadda sukai da dad dinta to ke wane hukunci kika yanke ehto na yanke baxan kawo kowaba in dady ya yanke korata xantafi ta xaro ido to ina xaki bansaniba gaskiya daman kakalece kawai nakeda itama din bansan meyasaba takanas taxo taci mutubcina wai inasan raba mata kan yaya kinga banda nadafa shikenan xan tayaki addu'a insha Allahu Allah xau kawo miki mafita bari naje har kofar gida ta rakata taxo fita ta riko hannunta pls fadya kimin alkawarin baxaki fadawa farhanba me yasa sabida banso yadauka nidin nakasa bin umarninsa nakasa ma iyayena biyayya tai murmushi karkiji komai yayarmu kisa aranki baxaiji ba tai dariya nagode kanwis. Kanwata Na F.A.Ya'u Duk yadda sukai da fara ta fadama ummanta ummanta ta tausaya mata koda babansu yadawo ta fada masa yace shikenan xamuje Allah ma yataimaka sadaki suke bukata kawai kinga sauran sai asai katifa da dan sauran kayan kitchen to gurin xama ai ba matsala bane ita fadya tunda itama sauran kadan tabar gidan sai ta dawo dakin kannenta inyaso dakinta tunda yafi nasa girma sai ya xame musu nasu dakin nasa sai sunaida kitchen tai dari gaskiya hakan yai Allah yasa abokiyar arxikinsa ce yace ameen. Ta daga ido taga tara dai dai tasaukar da ajiyar xuciya watakil dad ya hakura tunda gashi har tara baixo yace tabar masa gida ba. Turo kofar dataji yasanya gabanta faduwa mikewa tai alamar bashi waje ya xauna ba xama naxoba maxa ki tashi ki hada kayanki kaya dad eh ba dogon mgn naxo yi dakeba tana kuka tana hada kayanta haka tagama shi yajawo ta agaban mum dinta ya tsaya inxakice mata wani abu ta fashe da kuka tai ciki da gudu ta juya kamar tavi mum dintata saidai kash ba dama. Saida sukaxo bakin falon ya kamo hannunta ya danga mata kudi ga sadakinkinan amman dad yadora hannunsa kan bakinta karki cemun komao daman burin kowanne uba yarsa ta girma ya aurae da ita nima nawa ya cika saidai karki manta yau shi xai xame miki rana ta karshe da xaki taka kafarki a gidana. Kanwata Na F.A.Ya'u. Akofar falon taga umman fadya da wasu mata biyu su suka tafi da ita tanaji tana kallo saida sukaxo kofar gida ta daga ido danma gidansu kallon krshe kuka ya kuma kwace mata. Tun xuwan Fara gidan mutan gidan sukabi sunka addabeta duk wata tsana yimata suke habaici ba irin wanda batasha inka dauke fadya ummanta sai Farhan agunsu kawai take samun farin ciki. Inka sameta a babban gidan to ruwa xata diba shima bata tsayawa wajen cikawa shiyasa sau tari saidai fadya ko kannenta su devo mata inba haka ba da hawaye xata bar gurin. Wata sabuwa duk wani mai xuwa gurin fadya farhan ya koreshi tsirfa kala kala haka yake fito mata da ita kan samari abin har mamaki yake vata abinda ma baimata dava yanxu yi yake na takura ita kanta fara abin yadan fara bata wani tunani na daban. Ni wallahi duk hankaliba ba'a kwance yakeba wai yaronnan ya rasa wayakeso sai yarinyarnan me matar tasa ba kedai bari nima abinda ke dagan hankali kenan har yaushe yai auren gashi babansu yace yaji yagani gaskiya maza sai abarsu dayasan ita yakeso yaje yai auren maganganun da fara take jiyo umma da yayarta nayi kenan rasa mai xatai tayi kuka ko dariya kowanne yaki xuwa sai wani kululun takaici da yaxo mata wuya ta tsaya na takaici. Kanwata Na F.A.Ya'u Ba laifinsa bane laifina da tun farko na kasa ma iyayena biyayya na xabeshi tun farko mai yasa na kasa gano tsantsar soyayyar da yakema kanwarsa har na dage saina aureshi takasa kuka sai takaici kawai da haushin kanta dana farhan da ya cikata yama rasa waxai auro mata sai wadda ta gama sanin sirrinta wayyo kaicona farhan ka cuceni. Umma wai ina yayarmu tana daki na leka tacw batajin dadi kinsan mai ciki sai a hankali bari na leka ta shi tana xaune ta rabka tagumi subhanallahi yayarmu lafiya wani haushi ya kara cikata bansaniba dalla malama barmin daki yayarmu konai miki wani abune wai bakiji nace kifitar min daga daki bane sun sun ta fice tabar dakin aiko tana fita wani kuka yaximata tako fashe da kuka. Yaya wai maikaima yayata ne yai dariya maikikagani na shiga naga tana cikin damuwa ban mata komaiba bari naje nagani lpy muka rabu. Subhanallahi ya fada ganinta tanata sharar kuka fara lpy ya fada yana dagata tako tureshi kasane mugu axxalumi me nai miki haka me ne mekamun lallaima ta fadi aranta wannan mutumin ya raina mata hankali kafita ni kaban waje na tsaneka kasakeni towo mai yakawo maganae saki kasakeni kaje ka auri yar uwarka ta gano inda ta dosa kishine yai murmushi lallaima wannan ya rauna mata hankali dariyama ta bashi to wayace miki da saki atsakaninmu ai aurenmu mutu karaba inkinga kinbaeni saidai inna mutu wallahi baka isaba saika sakeni ka cuceni karabani da kowa nawa yai shuru ni na taba cemun muki ki rabu da wani naki akaina ko na taba cemiki baxan miki kishiya ba eyye lallai to wallahi gidanmu xan tafi to aisaikije in xasu karbeki kin manta yadda kukai dole nan xaki dawo ta

Chapter 3 of 5