Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 3
abu a kusa da shi ya yi saurin buxe idanunshi ya dubi abinda ya sauka a kusa da shi. Wani farin aljani ne mai kyawun siffa daga cikin jinsi aljanu dudud shekarunsa ba za su gaza xari uku zuwa huxu ba, wannan aljanin ya zamto mai ganiyar quruciya a jikin shi kuma mai ji da sadaukantaka. Yana sauka ya dubi sadauki Ansar yace masa “Ungulaye ba za su ci gangar jikinka ba domin ranar mutuwarka ba yi ba” Yana gama faxar hakan ya yi gaggawar xauko wata buta ya zubawa sadauki Ansar wani ruwan da yake cikin butar a gangar jikinsa nan da nan sadauki Ansar ya soma jin qarfin jikinshi ya soma dawowa jikinshi. Bayan wucewar awanni uku sadauki Ansar ya ji duk wata gajiya da wajen da yake masa ciwo ya daina, ya zamto tamkar wani abu bai tava samunshi ba, ya dubi farin aljaninan da duban girmamawa sannan a hankali yace masa. “Godiya gareka da ka zamto ka taimakaeni ka kuvutar da rayuwata” Sadaukin Ansar yace masa. Shi kuma ya dubi Ansar a hankali yace masa “Sunana aljani zammaru na zamto xaya daga cikin ‘yan qabilar bamu shammat, kuma na zamto daga cikin jinsi aljanu mabiya addinin musulunci na zo ne domin na taimakeka na kuvutar da kai daga halaka, domin duniya tana buqatarka idan ka halaka za a rasa jarumin da zai sasanta rigimar da zata mamaye duka duniya ta sace ruhin sarkin aljanu gamsu” Sadauki Ansar ya dubi Aljani zammaru da matuqar mamaki sannan yace masa. “Ta ya zan sasanta rigimar da dominta aka so hallakani? Ni musulmine babu ruwana da abinda ya shafi kafirai” Ya tabbatar masa. Aljani zammaru ya yi murmushi sannan yace “Akwai matsala babba tun da aka sato ruhin sarki aljanu Gamsu matsalar ita ce sarkin aljanu Gamsu ya zamto adalin sarki mai taimakon talakawa mai kare addinin musulman aljanu duk da cewar ya zamto shi ba ma’abocin musulunci bane, hakan yasa a lokacin da aka sace ruhin na shi duk wani musulmin aljani ya shiga cikin fargaba da tsoro domin sun san za su soma samun tursasawa daga sauran azzaluman sarakunan aljanu, shi yasa na zo gareka domin neman ka taimaki musulmai ‘yan uwanka a sassanta a dawowa da adalin sarki ruhinsa ko ma ci gaba da ibada a cikin kwanciyar hankali ba tare da zullumi ba”. Sadauki Anwar ya yi shiru na tsawon wani lokaci yana tunani daga bisani ya xago da kanshi ya dubi aljani zammaru yace masa. “Na yadda zan nemo wannan ruhin duk inda yake domin mayarwa da sarkin aljanu Gamsu koda hakan yana nufin sai an gabza yaqi, da izinin Allah nasara tana gareni” Ya kammala maganar yana dubansa kafin ya qara da cewar “Yanzu ina za mu riski wanda ya sace wannan ruhin?” Aljani zammaruu ya dube shi sannan ya bashi amsa da cewar. “Wata bokanya ce baqar fata, ta saka wani hatsabibin bawanta shima baqar fata ya sato wannan ruhin, domin haka za mu iya riskarsa a hanya kafin ya qarasa zuwa gareta” Sadauki Ansar ya girgiza kanshi cikin gamsuwa sannan yace wa aljani zammaru “Za mu iya yin gaggawa domin zuwa riskarsa” Yana gama maganar ya yi tsalle ya haye bayan aljani zammaru lokaci xaya shima ya buxe fuka-fukanshi ya tashi da shi sararin samaniya. Suka bi bayan baqar fata bawa Farsu daya sace ruhin sarkin aljanu Gamsu. BAQAR FATA BAWA FARSU Yana zaune a bayan aljani a ranshi yana jinjina irin girman siffa da muni da wannan aljanin yake da shi. Suka zo tsakiyar wani teku mai girma da faxi, tun da farsu yake a rayuwarsa bai tava ganin teku mai girma tamkar wannan ba. A hankali ya leqo da kanshi yana kallon ruwan tekun yana cike da al’ajabi. A dai-dai lokacin da suka zo dai-dai tsakiyar tekun a lokacin tamkar walqiya su Gimbiya Lusa suka bayyana a gabansu. Aljanin da yake xauke da Farsu ya dakata da tafiya da yake yi cike da tsoro da fargaba. Ganin ya dakata yasa Farsu ya dawo da hankalinsa gabansa idanunsa suka gane masa su ya girgiza kansa cike da jimami. A hankali su Gimbiya Lusa suka matso daf da juna ta miqe tsaye daga kan aljanin da take kai, tana zuwa dai-dai inda aljanin da Farsu uake kai ta daka wani tsalle ta dawo kanshi. Farsu ya yi gaggawar miqewa domin ganin ganin abinda ya faru, suka tsaya suna kallon-kallo da shi da Gimbiya Lusa. Cikin tsananin hasala tace masa. “Na zo domin amsar ruhin mahaifina sarkin aljanu Gamsu wanda ka sace” farsu ya dubeta a fusace shima yace mata “Amman kin yaudari kanki ‘yar budurwa da kike kiran aljani mahaifinki, kin tava ganin aljani ya haifi mutum? Sannan saboda tsananin ganganci shi ne za ki sadaukar da rayuwarki domin ki halaka kika biyoni domin amsar ruhin” Ya saurara kafin ya qara da cewar. “Yar kyakkyawar budurwa duk kyawun surarki hakan ba zai hanani saka takobi na a tsakiyar siririn wuyanki na raba kanki da kyakkyawan gangar jikinki” Ya gama magana yana mata wani shu’umin murmushi. “Kai baqar fata gafalalle kayi sani cewar ni ce Gimbiya Lusa mai maganin duk wani xan iska! Dan haka ka bani ruhin da ka sato cikin ruwan sanyi ya fiye maka kafin wannan mummunar baqar fuskar taka ta gamu da azabar kaifin takobina wacce bata san komai ba sai shan jinin sadaukai ma su ji da jarumtaka da taurin kai” Cikin murya tsawa-tsawa tace masa. Farsu ya dubeta a fusace cikin daka tsawa yace da ita “Ahir! Xinki da dubana ki gayamun irin waxannan kalaman bana tunanin akwai wani jarumi da zai iya tsoratani da jarumtakarsa ko kalamansa na kurari na baki, balle ke mace mai raunin jarumtaka” Gimbiya Lusa ta girgiza kanta cikin tsananin takaici ta sassauta murya tamkar mai yi masa raxa tace da shi cikin fushi. “Ka yaudari kanka da har kake tunanin gwara na amshi ruhin da tsananin jarumtaka, a yanzu ne za ka san cewar ka yi gagarumin kuskure kuma zaka rabe tsakanin aya da tsakuwa, domin yanzu zan farauce ranka na kuma cilla wannan mummunar gawar taka cikin teku” Tana gama faxa masa ta zare takobinta lokaci xaya ta dubeshi tace “Yau zamu yi gaba da gaba da kai domin sanin bambanci a bayyane yake”. Ta sake yin murmushi. “Ni da kai ABOKAN GABA ne, don haka mu kan iya soma farautar rayukan junanmu” Tana gama maganar ta kai masa wani wawan sara da zumar tsinke zaren da yake sarqe da ruhin cikin zafin nama ya kaucewa saran sannan ya wuce tare da wani hucin iska mai qarfi. Farsu ya dubeta ya girgiza kanshi, sannan ya gyara riqon takobinsa. Suka yi xauki kan junansu lokaci xaya suka gauraya da mummunan artabu a wuri xaya suna musayar kai sara da suka.qara gami da tartsatsin haxuwar makamansu ya karaxe sararin saman tekun. Ko wannensu ya himmatu domin ganin ya samu nasara akan abokin gabansa. Gimbiya Lusa ta samu Farus ba yanda ta yi tsamaninsa ba, domin ta same shi dakakken namiji mai tsananin jarumtaka, turjiya gami da zafin nama. Haka shima Farsu ya sami Gimbiya Lusa cikakiyar jaruma mai qarfin damtse da zafin nama wajen kai sara da kare kanta. Jarumar da tafi jarumai da dama qwarewa da sanin salo-salo na yaqi. Haka suka ci gaba da mummunan gwamza yaqi mai tsananin ban mamaki a tsakaninsu, suka wanzu wajen kaiwa junansu miyagun sara da suka da niyar farauce ran juna. Bayan sun xaki dogon lokaci suna wannan fafatawar a lokacin wani abu ya sauka a tsakaninsu. Jin saukar abin shi ne ya tilasta musu dakatawa da yin yaqin su duka suka dubi abun. A lokacin idanun Farsu ya sauka akan Bokanya Namsu uwar gidanshi da ta saka shi aikin idan ya sami nasara zata ‘yanta shi. Ganinta ya saka ya ji wani daxi ya lulluve shi. Bokanya Namsu tace masa cikin sassauta murya. “Maza miqo mun ruhin naga ko wannan qaramar qwaruwar zata iya amsa a wajena, kai yanzu ka kammala aikinka ka gama yi mun bauta don haka na ‘yanta ka” Waxannan kalaman sun matuqar qayatar da zuciyar Farsu. Don haka cikin gaggawa ya miqa hannu ya xauko ruhin daga cikin inda ya adana shi ya dubi Bokanya Namsu itama ta dubi Ruhin. Gambiya Lusa ta dubi ruhin mahaifinta sarkin Aljanu Gamsu. Ba su yi aune ba sai jin dirar wani abu suka kuma ji Yif! Kamar an sauke nannauyan dutse cikin gaggawa suka kai kallonsu idanun Farsu ya kuma ganin wata Bokanya Namsu a tsaye ya dubeta cikin tsananin mamaki yanzu sun zama su biyu ma su kama iri xaya sak kamar an tsaga kara. “Wace ce kenan ta gaskiyar?” Ya tambayi kansa kamar amsar tambayarsa ya ji ance masa. “Ni ce uwar gidanka Bokanya Namsu” Da kakkausar murya tace masa. Xayar itama ta matso gareshi tace masa “Ni ce uwar gidanka Bokanya Namsu”. Farsu ya zuba musu idanu yana kallonsu cikin ruxani ya kasa tantance wace ce ta gaskiyar wace ce ta qarya. A lokacin aljani Zammnaru ya qaraso shima xauke da sadauki Ansar a bayansa shima ya bi ruhin da kallo ya mayar da kallonsa ga Gimbiya Lusa sanna ya haske mata fuska da murmushi lokaci guda kuma cikin tsananin zafin nama ya zare takobi ya kaiwa farsu sara a hannun da yake xauke da Ruhin sarkin Aljanu Gamsu take ruhin ya zame daga hannunsa ya yi qasan teku. Farsu ya juya ya dube shi ya kuma dubi Gimbiya Lusa yace mata “To kyakkyawa ruhin mahaifinki ya faxa cikin teku, ko za ki biyoni cikin tekun mu ci gaba da fafatawa” Yana gama maganar ya sulmiyo daga kan aljanin ya biyo ruhin daya sulmiyo qasan teku. Gimbiya Lusa ta girgiza kanta tunda take a rayuwarta ba ta tava ganin hatsabibin mutum kamar wannan baqar fatar ba. Itama ta daka tsalle ta biyo bayanshi. Ganin haka ne ya sa sadauki Ansar shima ya sulmiyo ya yo qasa shima ya biyo bayan Ruhin sarkin Aljanu Gamsu da ya yo qasan taiku. A cikin tekun sarauniyar aljanun cikin ruwa ta tara mayaqanta suna tsaye suna sauraren qarasowar ruhin sarkin aljanu Gamsu. Tun kamin shekaru xari uku Bokanta ya faxa mata cewar Ruhin zai faxo a nan wurin tun lokacin ta zauna zaman jiran faxowarsa. Ruhin ya faxa cikin ruwan tekun ya zamto tamkar an cilla wani nannauyan dutse mai nauyi lokaci xaya ya yi qasan teku. Sarauniyar aljanun cikin ruwa tana zaune akan karagarta tana jiran faxowar ruhin. Tsayin shekara xari uku kenan tana zaune zaman jiran faxowarsa. A lokacin da bata yi aune ba taji faxowar abu akanta tayi gagawar buxe idanunta ta dubi abin da idanunta suka gane mata abinda ta jima tana zaune zaman jira tsawon shekaru, tabbas Ruhin sarkin aljanu Gamsu ne wani daxi ya mamaye cikin zuciyarta da gaggawa ta miqe cikin azama ta miqa hannunta ta xauki ruhin ta zuba masa idanu tana kallonsa. Ta juya cikin gaggawa ta xagashi sama a gaban idanun jama’arta cikin xaga murya tace musu “Abinda muka jima muna zaman jiran shi yau mun same shi” Duka hankalin dakarun ya tattara akanta suka zuba mata idanuwa suna kallon ruhin sarkin aljanu Gamsu da yake riqe a hannunta sannan lokaci xaya suka ruxe da shewa da kururuwa suna ma su xaga makamansu sama. A lokacin Bawa Farsu ya faxo tsakiyar wurin ya miqe tsaye da matuwar mamaki domin a tsammaninsa zai yi nutsu a cikin ruwa ya yi qasan tekun amma ga matuqar mamakinsa sai ya ga ya faxo tsakiyar wani fili mai yanyame da dakarun aljanu cikin shirin yaqi. Ya zuba musu idanu yana kallonsu suma suka zubo masa idanu aka soma kallon-kallo a tsakaninsu kamar akuya da kura. A lokacin suma su Gimbiya Lusa suka faxo tsakiyar wurin suka miqe tsaye suka zubawa wurin idanu cike da matuqar mamaki. Sarauniyar aljanun cikin ruwa ta dube su cikin mamaki lokaci xaya yanayin fuskarta ya sauya daga farin ciki zuwa vacin rai ta dubi Ruhin sarkin aljanu Gamsu da yake hannunta ta yi murmushi sannan ta buxe wata jaka da take xaure a gefen qugunta ta saka Ruhin a ciki ta mayar ta rufe kafin ta mayar da dubanta zuwa ga su Farsu dake tsaye carko-carko kamar wasu zakaru cikin murya tsawa-tsawa tace musu. “Kai baqar fata wanne irin shisshigine ya kawoka cikin fadata” Farsu ya dubeta cikin nutsuwa kafin ya bata amsa. “Ni ne baqar fata Farsu na zo ne domin amsar Ruhin da yake hannunki domin bai dace da ke ba” Maganarshi ta zamto tamkar sukar kibiya a cikin zuciyar sarauniyar aljanun cikin ruwa, ta yi zaman shekara xari uku tana jiran abu yau ta same shi sannan wasu za su ce sun zo domin su rabata da shi? Ta dube shi sheqeqe. “Babu makawa duk duniya babu wani wanda yake da jarumtar da zai iya amsar wannan Ruhin daga hannuna, idan kuma akwai jarumi to yana iya gwadawa” Cikin izza ta faxa. Gimbiya Lusa ta dubeta sannan cikin xaga murya tace mata “Na yi zaton mutane ne kawai suke son sace ruhin mahaifina sarkin aljanu Gamsu, ashe ba haka bane a cikin duniyar aljanu ma akwai masu buqatar shi, don haka ina mai tabbatar miki cewar za ki zamto aljana ta farko da zan soma sadarwa zuwa ga ajalinta” Jin haka yasa sarauniyar aljanun cikin ruwa ta yi dariya sannan ta nunata da yatsa tace mata. “Duniya ta daxe da wayewa Gimbiya Lusa don haka na gaba ya yi gaba” Gimbniya Lusa itama ta xaga hannu ta nunata. “Babu makawa zan dawo da na gaba baya, domin duk tsohon da bai ji kunyar hawa jaki ba to shima jaki ba zai ji kunyar kayar da shi ba. Da mai jini a jika shi ne wanda zamani yake tafiya da shi, don haka ke mai tashe ce ni kuma mai zamani, saboda haka za ki bani ta lumana ko kuwa sai kin ga jinin sadaukanki yana malala tamkar magunar ruwa” Maganar ta zamto tamkar ta watsawa sarauniyar aljanun cikin ruwa wuta a zuciyarta cike da fusata ta dubeta. “Lallai za ki yi nadamar wannan furucin naki, domin sai na ladaftar dake bisa kuskuren da kika yi” Tana rufe baki ta dubi yawan dakarunta da suke mamaye da wajen cikin isa da qasaita tace mu musu “Maza ku yi mun maganin waxannan qananin halitar” tana rufe bakinta dakarun suka zaburo a fusace makamansu a zare za su yi sukuwar sallah akan su. Hausa qarasowa zuwa garesu suna tsaye suna kallonsu, sai da ya zamto baifi sauran taku goma ba sannan Ansar ya daka musu tsawa, wanda hakan ya haddasa musu tsawa waj e xaya lokaci guda yace wa sarauniyar aljanun cikin ruwa. “Kin yi babban kuskure wurin turo dakarunki domin su yaqe mu, don haka ki saurara kiga yadda za mu qare da su kafin mu qaraso gareki” Yana gama maganar ya zare takobinsa sannan cikin azama ta bazata ya yi xauki garesu, ganin tahowarsa yasa suma dakarun suka kuma zaburowa suka gamu a tsakiya kasuwar yaqi da saye da sayarwa rayuka ta soma ci mutuwa ta soma shawagi tana farauce ruhin aljanun cikin ruwa. Masifa irin ta yaqi ta dunga sauka a wurin kai sara da kai suka ya yawaita zubar jini da malalarsa ya wanzu a wurin qasan tekun ya hautsine wanda hakan yasa ruwan tekun ya soma tambal-tambal tamkar zai malalo cikin duniya. Bawa Farsu ya zamo tamkar wata annoba ta wuta a cikin tsakiyar gonar auduga domin duk wurin da ya sa kai sai dfai ka ga kawuna suna yawo a sama tamkar tsuntsaye, jikuna suna zubewa qasa babu kawuna haka itama Gimbiya Lusa ta wanzu tana saukar musu da azabar yaqi. Kafin wani lokaci sun yiwa rundunar fata-fata sai tsirarun xaixaikun dakarun suka rage ganin sun zama tsiraru ya saka sauran suka yadda makamansu suka yi mubaya’a. ganin haka ya sa ran sarauniyar aljanun cikin ruwa ya matuqar dugunzuma ta dube su cikin tsawa tace musu “Qasqanci ya tabbata a gareku halaka ta zama dole a gareku” Tana gama maganar ta zare takobinta dake xaure a xamarata sannan lokaci xaya ta tunkaresu da zumar ta yaqe su ganin irin wannan tahowar da ta yi ya sa bawa Farsu ya taryeta tun kafin ta qaraso suka yi wata muguwar haxuwa takubbansu suka gamu a wuri xaya, wata qara mai qarfi ta cika wurin sannan wata wuta ta buga ta yi sama, suka soma musayar sara da suka a tsakaninsu zuwa tsawon lokaci, ganin lokaci yana tafiya a banza ya sa bawa Farsu ya tunzura ya qara qaimi wurin kai sara da suka gareta can ya xauki numnfashinta ya kai mata wani kaitattacen sara a wuya da zumar tsinke mata kai. Ganin tahowar saran ya sa sarauniyar aljanun cikin ruwa yin qoqarin kaucewa domin kar saran ya sameta amman ta makara domin sai da saran ya sameta kaxan a wuyanta. Ba don wata sarqa da take rateye a wuyanta ba wacce saran ya tsaya akanta, amman banda haka da saran ya yi tasiri akanta da tuni wani labarin ake yi ba nata ba. Sarqa ta zamo daga wuyanta ta sulmiyo ta yo qasa. Bawa Farsu ya ga tahowarta ya miqa hannunsa ya taryota ya riqeta a cikin tafin hannunsa ya yi zamiya yana kallonta. Ita ma ta dube shi na wani lokaci, a tsawon rayuwarta yau ita ce ranar farko da wani sadauki ya tava wanzuwa a gabanta tsawon lokaci har ya ke qoqarin samun nasara akanta, a rayuwarta bata xaukar wani tsawon lokaci suna fafatawa da wani sadauki, sai ta farauce rayuwarsa amma ga mamakinta sai ga baqar fata ya zamar mata ciwon ido. Suka zubawa junansu idanu suna kallon juna bawa Farsu ya dubi sarauniyar aljanun cikin ruwa ya dubi sarqa da take riqe a hannunsa ya xagata sama ya nuna mata ita ta bi sarqa da kallo cike da mamaki da baqin cikin ganin ya qwace ta daga gareta annurin da ya yi saura akan fuskarta ya soma narkewa daga kan fuskarta. Tana gama kallon sarqa da Bawa Farsu ya xaga mata akan fuskarta sai ta juya ta dubi hanya sosai sannan tace masa “Wannan sarqa da ka xagata akan idanuna dole na gudu tunda ka xagata na ganta da idanuna, domin sirrin tsafin dake jikinta, amman ba don haka ba da yau sai na halakar da ruhinka, don haka ka jirani a haxuwa ta gaba da za mu yi”. Tana qarasa faxar haka ta dubi hanya ya falfala da wani azababben gudu kafin su farga har ta vace musu daga gani. Bawa Farsu ya bi sarqa da kallo cike da mamaki ya juya ta zuwa ga su Gimbiya Lusa da sadauki Ansar ya fuskance su sosai yana kallonsu cike da mamaki ita kuma sarqa sai qyalqyali take tana xaukar idanu Gimbiya Lusa ta miqa hannu zata amsa Bawa Farsu yace mata. “Dakata” Ga matuqar mamakinsa sai yaga ta qame tamkar gunki ya dubeta sosai ya yi murmushi ya nuna sadauki Ansar da ita shima yace masa “Qame!” Take Ansar ya maqale shi ma tamkar busashen itace. Bawa Farsu ya dube shi a qame kamar busasun itatuwa ya qyalqyale da dariya cike da gamsuwa ya matsa gaban Gimbiya Lusa ya shafi fuskarta a hankali yace mata. “Qaramar mara kunya”. ** Bokanya Namsu ta dubu xayar da take tsaye a kusa da ita da duban matuqar mamaki mai matuqar yawa domin ganin matuqar kama da su ka yi da junansu. Ta yi murmushi akan faffaxar fuskarta sannan cikin murya fushi tace. “Ka yi mana asara biyu, dukkanmu mun rasa abin don haka kakan iya dawowa sufaffarka ta ainahi kafin na halakaka bisa wannan zunibin da ka aikata mun” tana gama maganar tana duban xayar da ke tsaye a gabanta, aka yi wata dariya mai xauke da isgilanci sannan cikin taqama aka ce mata “BOKA SHARBANGA shi kaxai ne wanda ya kamata ya mallaki ruhin sarkin Aljanu Gamsu domin na fi kowa sanin muhimmancinsa a duniyar mutane, domin haka kafin ki halakani ni yanzu zan salwantar da ruhinki domin ke kaxaice bokanya da za ki iya bani matsala a cikin lamarina’. Ya gama maganar yana mai yin wata girgiza tamkar tsuntswa nan take duk kayan da suke sanye a jikinsa suka zube a qasa, ya komo ainahin surarshi ta ainahi, wato namiji basamuden qato mai mummunan kama ya dubi Bokaya Namsu ya yi murmushi. Ta dubeshi itama cikin tsananin fushi mai tarin yawa tace masa. “A yau bokanya xaya a tsakiyar mazaje zata daka maka gumba a hannunka, ta nuna maka cewar akwai bambanci tsakanin aya da tsakuwa” Ta gama maganar tata tana mai miqa hannunta cikin gashin kanta ta zaro wani xan guntun itace ta cilla masa shi, take wuta ta kama itacen ta soma ci ganga-ganga lokaci xaya aljanin da suke kai ya kurma wani ihu mai tunzura zuciya sannan lokaci xaya wutar ya narkashi ya narke tamkar ruwa, ya riqa xiga yana zagwanyewa lokaci guda wutar ta doshi Boka sharbanga. Bokanya Namsu ta miqe ta yi sama tamkar wata tsuntsuwa ta tsaya akan iska ta bi wutar da kallo tana da tabbacin ta gama halaka boka sharbanga. Wutar tana zuwa wurin da boka sharbanga yake tsaye ya narke ya zama ruwa wutar ta ratsa ta cikinsa, wuta da ruwa suka bada wata qara sannan lokaci xaya wutar ta mutu boka sharbanga ya yi dariya yana kallonta yace mata. “Ke qaramar mara kunya maza bisa kanki” Yana rufe bakinsa ya yi wata fitar burtu ya tasar mata yana zuwa kusa da ita suka sake tashi a sama kamar tsuntsaye, nan take ya buxe qirjinsa suka taso suka qaxa qirji da qirji nan take suka yi baya kamar an watsa yakuwa a cikin teku, suka sake tasowa juna a guje suka yi suka yiwa juna karo kamar raguna suka yi baya taga-taga. Wajen da suka yi gware take ya fashe jini ya soma zuba boka sharbanga ya miqa hannunsa sama take wata takobi ta bayyana ya yi xauki akan bokanya Namsu kafin ya qarasa gareta itama ta miqa hannu cikin iska, lokaci guda wata takobi ta bayyana a hannunta itama tayi xauki kansa suka yi wata gamuwa mai muni suka soma kaiwa junansu sara da suka ko wanne yana qoqarin farauce rayuwar xan uwansa duk wanda ya sari wani a cikinsu sai dai kaji kamar wani qarfe da qarfe ne suka gamu a waje guda. Haka suka tafiyar da tsawon lokaci suna faman fafatawa a tsakaninsu ba tare da wani a cikinsu ya sami nasara akan xan uwansa ba, can suna cikin wannan gumurzun sai Boka sharbanga ya faki numfashin bokanya Namsu ya zaro wata farar hoda daga cikin jakarsa ta bokanci ya watsa mata. Hodar tana sauka a jikinta nan take ta soma jin jikinta duk ya saki, ta saki makamin da yake hannunta sannan lokaci guda ta zube a qasa, ya dubeta a wulaqance sannan ya qyalqyale da dariya. “Wanda ya fiki himma ya riga ya sha kanki, don haka yanzunnan zan halaka ki”. Yana gama maganar shi ya buxe jakar bokancinsa ya xauko wata wuqa da aka yi da qashin haqarqarin mutum ua xago da idanunshi ya kalleta gami da qyaqyacewa da dariya kafin ya sake cewa da ita. “Duk duniya babu wani mai sihiri da wannan wuqar ba zata huda shi ba, don haka yanzunnan zan halakar da ruhinki, ki zamto tamkar ba a tava yinki na doron qasa ba” Yana gama maganar tashi lokaci xaya ya xaga wuqar a sama ya dubi qirjinta daidai inda zai luma wuqar sannan yace mata. “Sai wata rana ABOKIYAR GABATA, Bokanya Namsu” Yana gama maganar ya nufi qirjinta cikin sauri da zumar soka wuqar a gaban qirjinta. ** Sarauniyar aljanun cikin ruwa ta wanzu tsawon lokaci tana tafiya babu qaqautawa ita da kanta tana da masaniyar duk duniya babu wani mahaluki da yake da gaggawar da zai iya biyo bayanta har ya cimmata don haka ganin ta yi nisa da wurin su bawa Farsu sai ta rage gaggawar da take yi ta samu wuri ta tsaya. A hankali ta miqa hannunta ta shafi wuyanta cike da takaici da baqin ciki domin rasa sarqarta da ta yi. Duk duniya babu abinda tafi qauna a rayuwarta kamar sarqa domin duk wani sirri nata ya ta’allaqa a jikinta. Duk abubuwan duk abubuwan ba su ne vacin ranta ba, babban vacin ranta na rashin samun damar buxe jakar da ta saka ruhin sarkin aljanu Gamsu wanda dole sai ta yi amfani da sarqa ta zata buxe jakar. Wannan abun shi ne abu mai muni da sarauniyar aljanun cikin ruwa ta tava cin karo da shi a tsawon shekarunta da ta yi a duniya. Ta xaga kanta sama ta soma qoqarin tunani da zumar ta tunano hanyar da zata bi domin ganin ta samo mafita akan abinda ya dameta. Abubuwa da yawa suka yi ta zuwar mata cikin ranta, amma duk ba su haska mata tunanin yadda zata dawo da sarqarta ba. Haka sa’o’i masu dama suka wuce tana faman tunane-tunane bayan tsawon lokaci wata dabara ta faxo mata, wannan dabarar ba qaramun faranta mata rai tayi ba, domin ta yi imani itace hanya guda da zata dawo da sarqarta gareta cikin ruwan sanyi. Don haka cikin gaggawa ta miqe tsaye ta lalubi gefen qungunta ta xauko wani madubin tsafi ta dubi kanta a ciki ta yi murmushi sannu a hankali ta soma karanto wasu xalasimai na tsafi tana duban kanta a jikin madubin, bata xauki wani lokaci a haka ba take kamaninta suka soma juyewa zuwa na bil’adama. A hankali ta juya kama zuwa ga surar mace baqar fata mai kyawun gaske, yadda duk wani namiji idan ya kalleta sai ya yi mafarkin kyawunta, ta dubi kanta a jikin madubin har sheqi take yi tamkar ta shafa shuni a jikin fatarta, ga manyan fararen idanu da jan shacin bakinta tayi wa kanta tattausan murmushi a hankali tace. “Wannan surar Gimbiya Zailu na aro, duk duniyar baqaqe babu mai kyawunta zan yaudari baqar fatar nan na amshi sarqata daga hannunsa kafin na halakar da ruhinsa ya zamto na shafe shi daga doron qasa” Ta qarasa magana tana qyaqyacewa da dariya kafin lokaci guda ta nufi wajen teku ta wajen da tana da tabbacin tanan su Bawa Farsu za su fito. Iska teku ta ci gaba da kaxawa a hankali. ** Tsawon lokaci suka xauka a tsaye a wurin bawa farsu yana kallonsu yana yi musu dariya. Kafin ya miqa hannu ya xauki sadauki Ansar ya mayar da shi can wani wuri yua ajiye shi, ya xauko wasu sassa na gawarwaki halittun da suka yi yaqi da su ya xoxxora masa a jikinsa. Ya dawo itama Gimbiya Lusa ya zuba mata idanu yana kallonta ya qare mata kallo a hankali. Ban tava tsayawa na qare miki kallo ba sai yau, ashe daman haka kike da tsantsar kyau, ya saurara yana dubanta ya dubi idanunta da suke a buxe manya da su, farare qal. “Tunda nake a rayuwata ban tava ganin kyawawan qwayar idanuwa kamar naki ba, surarki zata xauki hankalin sarakuna da attajirai ma su ji da kansu” Ya kammala maganar yana dubanta. Ya juya ga sadauki Ansar yace masa “Ka koma yadda kake” Yana faxar haka sai sadauki Ansar ya ci gaba da motsi kamar yadda ya ke a baya, ya tsaya yana duban kansa cike da mamaki ya mayar da kallonsa ga Bawa Farsu yaga yadda ya tsaya a gaban Gimbiya Lusa cikin tsawa yace masa. “Meye haka? Maza ka matsa daga wajenta” Ya juyo yana dubansa fuskarsa xauke da murmushi. “Kana da alaqa da ita ne?” Ya jefa masa tambayar sadauki Ansar shima ya tsare sa da ido. “Wanne sihiri ka samo kake aikatawa a gare mu, don haka ina mai sanar maka lallai kayi gaggawar rabuwa da shi, idan kuma ba haka

Chapter 2 of 3