tava
sirrinki,sirrin kuma shi ne za ki iya
mayar da akwatin nan ta zama xan
qarami guri da zaki xaure shi a
qugunki ya kasance dare da rana yana
jikin ki, duk sa’adda kika kaxaita a
cikin xakinki ya zamana cewa kina son
ki karanta littafin al’ajabi sai ki kwance
35
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
gurin ki ajiye shi a gabanki ki xiga
masa jini.
Take gurin zai zama kawai sai
ke kaxai kuma akwatin zata buxe
kanta ki xauko littafin ki karanta da
zarar kin kammala kin mayar da littafin
cikin akwatin za ki ga ta rufe kanta,
kuma ta sake rikixewa ta zama
qaramin gurin.
Haka za ki yi ta yi har ki samu
nasarar kammala karanta littafi a cikin
kwanaki xari uku a da sittin ki sani
cewa daga yau ba ni da sauran alaqa
da ke koda wannan littafi domin dama
nib a waiwar kakanki ce na fi shekara
saba’in ina yi masa bauta bai ‘yanta ni
ba albashir xin ‘yanta shi ne na kare
wanna littafi har izuwa lokacin da
hannunki zai kai kansa, gashi kuwa
yanzu lokacin ya yi.
Da wannan furuci nake yi miki
bankwana yanzu nan zan tafi izuwa
36
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
can qarshen duniya vangaren bangon
arewa zan qarasa sauran rayuwata
tare da mijina wanda tun da aka raba
mu tsawon shekaru yake zaune yana
faman sharar kuka, idan na koma gare
shin a sami ‘yancina babu wani boka
da ya isa ya sake tsare ni na yi masa
bauta, kuma har izuwa qarshen
rayuwata bazan sake rabuwa da mijina
ba, daidai da tsawon kwana xaya”.
Koda gama faxin hakan sai
Aljana jarisa ta yunqura zata tashi
sama, amma sai Nasmirat ta yi wuf ta
roqo fukafukinta guda xaya tace “Ya
za ki tafi baki gaya mini yadda zan
mayar da wannan akwati xan qaramin
guru ba?”
Koda jin wannan tambaya sai
aljana jarisa ta qyalqyale da dariya
tace “Ai na gaya miki tun xazu tun da
dai yanzu kece kaxai a cikin wannan
kogon dutse babu wata halitta mai
37
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
raid a ke ganinki ko sauraronki,kawai
ki buxe littafin ki karanta labarai
bakwai kina kammala wa sai ki mayar
da littafin cikin akwatin ki rufe za ki ga
akwatin da kanta ta rikixe ta zama
gurun.
Gama faxin hakan ke da
wuya sai aljana jarisa ta buxe
fukafukanta ta yi sama tana ta
qyalqyala dariya farin ciki kuma ta
buxe muryarta da qarfi tana faxin na
sami ‘yanci na samu ‘yanci.
Kafin cikin daqiqa biyar aljana
jarisa ta luluqa a cikin gajimare ta vace
vat tamkar bata tava wanzuwa ba a
wajen.
Koda ganin abinda ya faru sai
Nasmirat ta dubi gabas da yamma
kudu da arewa a cikin kogon dutsen
kuma ta kasa kunnuwa har sai data
tabbatar da cewar babu wnai mahaluki
mai rai a cikin kogon sannan ta buxe
38
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
littafin na hikayoyin aljabi ya fara
karanta labarin farko.
Koda ta ji irin tsananin daxin
labarin da kuma abubuwan al’ajabin
dake cikinsa sai ta ji cewa ai idan
kwana zata yi a tsaye tana karanta shi
ba zata gaji ba.
Nan da nan a cikin daqiqa
kaxan ta gama karanta labaru bakwai.
Tana gama karanta labari na
bakwai sai littafin ya rufe kansa,
Nasmirat ta yunqura da nufin ta sake
buxe littafin domin ta ci gaba da
karanta shi amma sai ta ji littafin ya
vame! Tamkar qusa aka kafe shi.
Nan fa ta dage iya qarfinta
domin ta buxe amma sai ta kasa, bisa
dole ta haqura ta mayar da littafin
cikin akwatin.
Faruwa haka keda wuya sai
farar akwatin ta rufe kanta sannan ta
qanqance ta zama guru xaya xan
39
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
qarami cikin farin ciki Nasmirat ta
xauko gurun sannan ta xaure shi a
qugunta sannna ta ruga da gudu ta
fice daga cikin kogon dutsen.
Daga wannan rana kullum da
daddare sai Nasmirat ta shiga cikin
wani shago kasuwa wanda babu wani
a cikinsa ta kulle kanta ta kwance
wannan guru daga qugunta ta ajiye shi
a gabanta sannan tasa zabira ta xan
yanki xanyatsanta ta xigawa gurin jini.
Take yake zama wannan farar
akwatin ya buxe ita kuma sai ta xauko
littafi hikayoyin al’ajabi ta karance
labarai bakwai a cikinsa. Tana gamawa
sai ta mayar da littafin cikin akwatin
kuwa sai ta zama guru, Nasmirat ta
xauke abinta tax aura shi a qugunta.
40
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
BABI NA HUXU
Yau kwana bakwai ke nan
Nasmirat tana yin wannan abun cikin
sirri ba tare da kowa ya gani ba, ko ya
ji hatta mahaifinta nata kuwa amma
kawai ranar daya tava hannunta ya ji
alamun yanka ya tambaye ta yadda
aka yi ta sami wannan raunika sai tace
da shi ai ta je aikin aikatau ne a wani
gidan attajiri aka sata ferayar kabewa
shi ne ta samu wannan raunika.
Koda jin haka sai makaho
marhat yayi ajiyar zuciya, cikin alamun
rashin gamsuwa amma sai ya yi shiru
bai sake tanka mata ba.
41
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
A wanna rana ta bakwai ne
aka je aka xauko Nasmirat da
mahaifinta aka kai su cikin wannan
qerarren gida da shirin cewa kashe
gari za a yi bikin aurenta da sarki Ram.
A can gidan sarki Ram kuwa
tuni an fara shirye-shiryen bikin
aurensa ana ta shirya abinci da za a ci
gobe manya baqi kuwa tuni sun fara
hallara
daga
sauran
qasashen
makwabtaka
birni
da
qauye,
hadimai,barori da kuyangi kuwa sai kai
kawo suke yi suna ta yin ayyuka nag
yare-gyare ado da shirya qawa a
wurare da yake na cikin gidan sarautar.
Su kuwa matan sarki Ram su
goma sha xaya sun taru gaba xayansu
a cikin xakin uwargidansu suna
shiryawa kansu wata ‘yar qaramar
walima sai ciye-ciye da shaye-shaye
suke yi, suna ta qyalqyala dariya
42
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
mugunta suna cewa za su ga yanda
wannan budurwa zata iya tsallake
kaifin takobin sarki Ram yaya suma
suka kasance matan sarki na tsawon
shekaru sun haqura da zuwa turakarsa
sai kamar budurwa yar shekara sha
takwas ce zata iya da shi?
Me ta sani a rayuwar duniya
ma bare ta bashi labarum da za su
kwantar masa da hankali su hana shi
hauka.
A can vangaren turakar sarki
kuma a wannan rana wani abin
mamaki ne ya faru, domin a ranar
gaba xaya ciwon sarki bai tashi ba ko
sau xaya ba, kuma sai ya kasance a
cikin tsananin farin ciki ya yi ta rabon
kuxi da kayayyaki ya zamana cewa
babu abinda yake son a faxa masa
face a ambaci sunan amaryarsa
Nasmirat, shi kansa Boka Aulad
makusancin sarki Ram sai da ya yi
43
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
matuqar mamakin yadda aka yi sarki
Ram bai yi cutarsa ta hauka ba a
wannan rana, kuma har sai da dare ya
raba sarki Ram bai daina nishaxi da
farin ciki ba, babu shiri a lokacin Boka
Aulad yasa aka baiwa sarki Ram
maganin barci yasha sannan ya vingire
akan gado ya kama sharar barci hard
a minshari rabon da sarki Ram ya sami
irin wannan barci mai nauyi tun kafin
ya haxu da lalurar wannan cuta.
Kashe gari kuwa da sassafe
aka fara shagalin biki gaba xaya birnin
ya ruxe da kaxe-kaxe gami da bushebushe sarakuna da ‘ya ‘yansu attajirai
da masu faxa aji suka yi ta tururwa
izuwa cikin birnin suna rinqa shiga
gidan sarautar,masana tarihin birnin
said a suka tabbatar da cewa ba a
tava yin gagarumin taro da ya kai na
bikin auren sarki Ram da Nasmirat ba,
44
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
tun daga farkon kafuwar qasar kuwa
izuwa yanzu.
Bisa al’adar auren a qasar
Hindu a wannan lokacin dole ne ango
da amarya su tsaya a gaban
masoyansu ‘yan uwansu da dukkan
zuri’arsu a kwara musu ruwan madarar
shanu akansu sannan kowannensu ya
zo gaban gunkin da suke bautawa ya
yi sujjada ya dangwali wani jan zabibi
da xanyatsansa na hagu yayi fashin
goshi a kansa da goshin gunkin,
sannan kuma ango ya shafawa
amaryarsa jan zabibin akan goshinta,
hakan na faruwa sun tabbata miji da
mata kuma sun sami albarkar gunki.
Bayan taro y agama cika, duk
inda mutum ya hanga gabas da
yamma kudu da arewa sai dai yaga
kowannan bil’adama rubutu batutu
babu masaka tsinke, a cikin tsakiyar
filin gidan sarautar ne aka yi wannan
45
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
gangami sai ga sarki Ram tare da
amaryarsa sun fito daga cikin gidan
sarautar sun fito daga cikin gidan
sarauta.
Dukkaninsu sun cava ado na
gaban kwatance suna tafiya a kan
wani jan kishi wanda ya nufo wajen da
gunki yake, dakaru da kuyangi na take
musu baya.
Koda ganin fitowar sarki da
amaryarsa sai mutane suka ruxe da
shewa suka kama yi musu jinjina gami
da kirari.
Sai da sarki Ram da amaryasa
Nasmirat suka yi taku sittin sannan
suka iso gaban gunki suka tsaya
tsayuwarsu keda wuya sai aka zo da
madarar guda biyu a cikin gorar ruwa
aka kwararaa sarki da Nasmirat a
kansu suka jiqe sharkaf kaico, kaji
wata al’adar banza duk wannan
46
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
kwalliya da ma’auratan suka yi an
vatata.
Nan take sarki Ram ya
dangwali jan zabibi ya yiwa kan fashin
goshin kuma ya yiwa gunki ya koma
gefe xaya ya tsaya.
Ita ma Nasmirat sai ta
dangwali zabibin ta shafawa kanta a
goshin.
Koda ta durfafi gunki da nufin
ta shafa masa zabibin akan goshinsa
sai kawai aka ji an zabga wata irin
tsawa mai qarfin gaske mai tsananin
ban tsoro wacce ta razana kowa
alhalin babu alamar hadari a garin.
Ita kanta Nasmirat bata san
sa’adda ta faxi qas saboda tsananin
firgita da tayi, amma sai ta miqe tsaye
zumbur taje ta shafawa gunki zabibin
sannnan ta shafawa kanta.
Koda ganin haka sai murna ta
kama sarki Ram don haka sai shima ya
47
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
dangwali zabibin ya shafawa Nasmirat
a goshinta suka rungume juna a
lokacin da jama’a suka kaure da shewa
gami da tafi alamar aure ya tabbata a
lokacin da jama’a suka kaure da
wannan shewa ana ta murna gaba
xaya bokayen qasar kuwa hankalinsu a
dugunzume
yake
bisa
wannan
muguwar tsawa da aka tafka.
A lokacin da Nasimarat ta je
zata shafawa abin bautarsu zabibi a
goshi.
Hakan bai tava faruwa ba
kuma yana yi musu nuni ne da cewa
lallai akwai wani babban sauyi da yake
shirin zuwa, amma ta hannu wannan
budurwa amarya sarki.
Nan da nan Bokayen suka bar
filin gidan sarautar gaba xayansu suka
tafi izuwa can wani xakin bauta dake
bayan gari suka kulle qofarsa.
48
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
49
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
BABI NA BIYAR
Boka
Aulad
shi
ne
shugabansu don haka sai ya dube su
gaba xayansu yace da su “Abin da
nake so da ku shi ne kowannenku yayi
mana bincike yanzu a cikin madubin
tsafinsa ya gano mana ma’anar
wannan tsawa mai ban tsoro da aka
tafka sakamakon zuwan Nasmirat
gaban abin bautarmu da nufin shafa
masa zabibi bisa al’adar aure.
Koda jin wannan umarni sai
gaba xaya bokayen suka fiddo
madubinsu na tsafi suka duqufa shima
Boka Aulad xin ba a barshi a baya ba
sai ya taya su jim kaxan sai kowa ya
xago kai suka rinqa kallon-kallo a
junansu cikin matuqar al’ajabi aka rasa
wanda zai ce qala har shi kansa Boka
Aulad xin.
50
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
Daga can sai boka Aulad ya
dube su yace.
“Na sani cewa duk abu guda
muka gani a cikin bincikenmu don
haka ba sai na tambayi xayanku ba.
Tabbas wannan bil al’ajabi ne
baba kuma abin tsoro don haka ya
zama wajibi musan matakan da zamu
xauka, wannan tsawa da aka tafka
ashe ba komai bace face gargaxi a
gare mu gaba xayan mutanen Hindu
cewar mai girma abin bautarmu bai yi
amana da wannan auren ba na sarki
saboda ita wannan yarinya Nasmirat
tana da wani babban sirri wanda nan
gaba zata kai ga samun babban
matsayi da xaukaka a birninmu. Ga
dukkan alamu ma sai ta mulke mu ta
zama sarauniyarmu idan kuma hakan
ta faru, mun tafka babban abin kunya
da ba a tava yin kamarsa ba.
51
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
Ko ina a duniya ace ‘yar
almajiri mara cikaken asali ta zama
sarauniyar mu ya zama dole mu hana
sarki yin taraiya da wannan amarya
tasa a wannan daren na yau, kuma
musan hanyar da za mu bi mu
hallakata a sirrance batare da kowa ya
sani ba”.
Koda boka Aulad ya zo nan a
zancensa sai babban Boka na birnin
Kashmir ya miqe tsaye ya dube shi
cikin alamun girmamawa kuma ya
risina masa yace “Ya shugabana to
yanzu ya za mu yi da wannan cuta ta
sarki tunda ka san cewa abu ne
mawuyanci mu sake samun budurwar
da zata iya sai da ranta ta aure shi?”
Koda jin wannan tambaya sai
Boka Aulad ya ja numfashi ya ajiye
sannan yace “Ai har abada jarumai
basa qarewa a cikin duniya sai mu
lalubo wata, ina son ku barni mini
52
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
komai a hannuna zan san abin da zan
yi.
A yau xin nan zan kawar da
wannan amarya ta sarki cire silin gashi
daga cikin tandun mai yafi wannan
aikin sauqi a wajena, tunda kun sani
cewa babu wani mahaluki daya fini
samun aminci a wajen sarki”.
Koda jin wannan batun sai
farin ciki ya lulluve dukanin bokayen
suka kama yiwa Boka Aulad jinjina
cikin farin ciki gami da samun nutsuwa.
A can filin gidan sarauta kuwa
bayan an gama xaura aure sarakai da
manya baqi suna zuwa su taya shi
murna, kuma suna bashi kyaututtuka a
lokacin da amaryarsa ke tsaye daf da
shi, sai ya lura babu boka Aulad a filin
gaba xaya.
Koda ya sake hangawa ko ina
sai yaga ashe gaba xaya bokayen
qasar ma basa nan, nan take hankalin
53
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
sarki Ram ya dugunzuma ainun ya
aiyana a cikin ransa cewar lallai Boka
Aulad yaci amanarsa kuma akwai wata
maqarqashiya da yake shirin tafka
masa, shi da sauran bokayen.
Nan take sarki Ram ya kirawo
sarkin yaqinsa yace da shi, maza kasa
a rakani izuwa turakata kuma daga
yau kada a sake barin kowa ya shigo
inda nake ko a inda amaryata take
koda kuwa Boka Aulad ne, kai kaxai
na yarda da ka shigo turakar mu yi
magana.
Sarkin yaqi ya risina ya ce “An
gama ya shugabana”.
Nan take sarki Ram ya kama
hannun amaryasa Nasmirat suka nufi
cikin gidan sarauta dakaru sama da
miliyan xaya na mutane da aljanu na
take masa baya.
A daidai wannan lokacin ne
Bola Aulad da sauran bokayen suka
54
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
dawo filin fadar koda Boka Aulad ya
hango sarki da amaryarsa za su shige
cikin gidan sarautar sai ya rugo da
gudu ya nufi inda sarki ya ke da nufin
ya shiga.
Kwatsam sai Boka Aulad yaga
sarkin yaqi ya sha gabansa cikin fushi
Boka Aulad ya dube shi yace “Wane
irin shirme ne haka zaka zo kasha
gabana alhalin kasan cewa sarki baya
son na gusa daga kusa da shi daidai
da tsawon rabin sa’a”.
Koda jin haka sai sarkin yaqi
ya yi xan guntun murmushi yace.
“Ai wannan da ne, yanzu nan
sarki ya bani umarnin cewa kada na
sake barin kowa ya je inda yake, koda
kuwa kai ne”.
Koda jin haka sai ran Boka
Aulad ya vaci ainun ya dakawa sarkin
yaqi tsawa yace “Wai shin ni kakan ka
55
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
ne har da zaka zo mini da maganar
wasa”.
Da jin haka sai sarkin yaqi ya
turvune fuskarsa yace “Na tava yi
maka wasa ne? ko kuwa zan yi wa
sarki qarya ne saboda kawai biyan
wata buqata tawa? Inda sarki bai
sauya ra’ayinsa ba ai babu yadda za a
yi ya tafi ya barka. Ni ina ganin sarki
yana zarginka da wani laifi don haka
kasan hanyar da zaka bi ka gyara
tsakaninka da shi”.
Koda sarkin yaqi ya zo nan a
zancensa sai hankali Boka Aulad ya
dugunzuma ainun fiye da koyaushe ya
dubi sarkin yaqi cikin alamun matuqar
damuwa yace.
“Dole ne naga sarki yanzu
domin na hana shi Tarawa da wannan
amaryar tasa domin kuwa akwai
babbar matsala, abin da nake so da
56
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
kai shi ne ka yi min jagora izuwa ga
sarki yanzu nan kafin lokaci ya qure”.
Sarkin yaqi ya girgiza kai yace.
“Ba zan iya ba, domin ni ma
idan na kaika gare shi zan iya rasa
matsayina gaba xaya”.
Koda jin haka sai Boka Aulad
ya dakawa sarkin yaqi tsawa, a karo
na biyu yace.
‘Shin ka manta ne cewa ni da
kai duk munyi rantsuwa da girman
abin bautarmu cewa zamu sallama
rayuwarmu da komai na mu domin mu
kare wannan gidan sarauta na mu da
qasar gaba xaya.
Na rantse da girman iyayena
idan ban hana sarki taraiya da wannan
amarya tasa ba sai mulkin ya suvuce
masa gaba xaya domin ita amaryarce
zata haye karagarsa kuma ajalinsa a
hannunta yake, ta yaya muna ji muna
gani za mu bar ‘yar almajiri mara
57
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
cikakken asali zata zo ta karvi mulkin
qasar nan dare xaya?
Sa’adda Boka Aulad ya zo nan
a zancensa sai hankalin sarkin yaqi ya
dugunzuma ainun ya yi shiru yana
tunani da nazari har izuwa tsawon yan
daqiqu ya rasa abin da zai ce daga can
sai ya xago kai ya dubi Boka Aulad
yace.
“Tabbas dole ne na baka
haxin kai xari bisa xari domin ganin
mun ceci rayuwar sarki da kuma
darajar qasar nan ta kowane hali,
amma ka sani cewa tsalle xaya shi ke
jefa mutum a cikin rijiya, gaggawa a
cikin wannan al’amari a gare ni yana
da matuqar haxari, ka tuna cewa kai
fa boka ne wanda babu kamarsa a
qasar nan don haka ka yi amfani da
qarfin
sihirinka
wajen
magance
wannan matsala”.
58
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
Boka Aulad ya yi ajiyar zuciya
cikin alamun takaici yace “Ai in da zan
iya yin hakan da tuni na yi ba sai na
tuntuve ka ba, ai idan ka ji makaho
yace a yi wasan jifa to lallai ya taka
hoge, ka tuna cewa duk faxin qasar
nan ba a sami budurwa da ta amince
za ta auri sarki ba a cikin wannan
larura tasa face Nasmirat kasan kuma
lallai akwai abinda ta taka.
Bisa wannan binciken da na yi
a kanta na gano cewa akwai wani
babban sihirin tsafi a jikinta wanda
duk wanda ya tunkareta da nufin ya
hallakata mutuwa zai yi, maganinta
kawai shi ne sarki ya fasa aurenta
kuma ya nisanta da ita.
Tun da ba zamu iya tava
Nasmirat ba ai za mu iya raba sarki da
ita, ni yanzu ba ni da sauran aminci
sarki kai kuwa kana da shi, ka yi
amfani da wannan dama a yau xin nan
59
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
kafin sarki ya shiga xakin amaryarsa
kasa a sace shi a sirrance mu fitar da
daga cikin gidan sarautar gaba xaya,
mu kaishi can gidana na bayan gari
mu voye shi.
A sannan ne zamu yi tunanin
hanyar da zamu bi mu fitar da
Nasmirat daga cikin gidan sarautar
gaba xaya a cikin ruwan sanyi”.
Lokacin da Boka Aulad ya zo
nan a zancensa sai hankalin sarkin
yaqi ya qara dugunzuma ya shiga cikin
halin wasi-wasi,zullumi, fargaba da
zargi kawai sai ya xago kai ya dubi
Boka Aulad cikin alamun rashin yadda
yace.
“Duk waxannan abubuwan da
ka shirya mini yanzu sunyi kama da
hanyoyin da ake bi a shirya juyin mulki,
da wace hujja zan yi amfani na gamsu
cewa ba juyin mulki kake shirin yiwa
sarki ba?”
60
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
Boka Aulad ya dakawa sarkin
yaqi tsawa a karo na uku yace “Yau
shekara ta arba’in ina bauta a wannan
gidan na sarauta na yi bauta ga
mahaifin sarki Ram da kakansa duk
tsawon waxannan shekarun ba a tava
kamani da laifin cin amanarsu ba, duk
abinda nake nema na jin daxi duniya
ina da shi a can fada ta ina da dukiya
mai tsananin yawan da ban san iyakar
adadin yawanta ba, ina da matan aure
guda tamanin da xaya, ina da ‘ya ‘ya
arba’in da biyu fadata ta ginu kuma ta
qawatu fiye da wannan wacce muke
ciki ina da fadawa kuyangi,barori da
dakarun tsaro waxanda suka ninka na
wannan fadar sau uku, a kan wane
dalili zan yi sha’awar wannan fada ko
karagar cikinta?”.
Koda sarkin yaqi ya ji
waxannan tambayoyi da Boka Aulad
ya yi masa sai jikinsa ya yi sanyi
61
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
matuqa ya rasa abin da zai ce daga
can sai ya xaga kai ya dubi Boka Aulad
yace.
“Kafin dare yayi akai amarya
xakin angonta zan san abin da zan yi
akai kuma zan nemeka na sanar da kai
komai”.
Koda jin haka sai Boka Aulad
yayi doguwar ajiyar zuciya, sannan
yace “Lallai ka tabbatar da cewa ka yi
duk motsinka kafin a kai amarya xakin
sarki”.
Koda gama faxin haka sai
Boka Aulad ya juya ya yafito wani
hadiminsa da hannu take hadimin ya
janyo dokin Boka Aulad da sauri ya
kawo masa.
Cikin alamun fushi Boka Aulad
ya kama dokin nasa yah aye ya
zabureshi da gudu ya nufi hanyar fita
daga cikin gidan sarautar gaba xaya,
aikuwa sai wasu dakarun Boka Aulad
62
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
kimanin su arba’in bisa dawakai suka
rufa masa baya.
Koda jama’ar gari suka ga
Boka Aulad ya fice daga ciki gidan
sarautar gaba xaya sai suka cika da
tsananin mamaki saboda an san cewa
dare da rana yana tare da sarki baya
yarda ya yi nisanta da shi,shi ma
sarkin haka fa aka fara tsegumi, kowa
ya riqa faxin albarkacin bakinsa.
63
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
BABI NA SHIDA
Al’amarin sarki Ram kuwa
lokacin daya kama hannun amaryarsa
Nasmirat ya yaja ta izuwa cikin gidan
sarauta bai zame ko ina ba sai cikin
wani babban falo wanda girmansa ya
kai na fadar gidan sarautar. Babu
komai a cikin wannan falo face kujeru
da tebura na cin abinci birjik da yawa
iya ganin mutum.
Suna shigowa cikin wannan
babban falon sai suka yi arba da gaba
xayan sarakunan nahiyar waxanda
suka zo taya sarki Ram murna wannan
aure nas kowane sarki yana tare da
matarsa a zaune ga kayan ciye-ciye
dana shaye-shaye, iri-iri babu adadi
akan teburin amma a saboda girmama
64
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
sarki Ram ko ruwansha babu wanda
ya xauka ya kai bakinsa sai ya iso
tukuna.
Koda sarakuna da matayensu
suka ga sarki Ram tare da amaryarsa
sun shigo cikin falon sai gaba xayansu
suka miqe tsaye suna kama yi masa
tafi ya yin da waxannan sarakunan
suka yi arba da amaryar Nasmirat a
cikin gagarumin ado da aka cava mata
sai dukkaninsu suka ximauce bisa
ganin irin tsananin kyawun da Allah ya
bata.
Nan fa wasun su suka fara
munafunci da tsegumi ga ‘yan uwansu
sarakuna.
Sarkin birnin kirishna ne ya
dubi sarkin birnin lamras ya yi masa
raxa a kunne yace “Tabbas banga
laifin sarki Ram ba da ya auri wannan
yarinyar ‘yar almajiri saboda ko ni ne
ba zan bari ta wuce ni ba”.
65
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
Koda jin haka sai sarki lamras
ya yi murmushi yace “Amma ba don
kyaunta ya aure ta ba an ce saboda
kawai zata iya bashi labaru ne masu
daxi waxanda za su sa hankalinsa ya
kwanta ya daina hauka da shirme,
abin tambaya a nan shi ne a ina
wannan yarinya zata iya samo labarai
masu daxi, kuma masu ban al’ajabin
da za su iya saita wannan mahaukacin
sarki?”
Koda gama faxin hakan sai ga
sarki Ram tare da amaryarsa sun iso
daf da sarki lamras,kawai sai sarki
Ram ya dubi sarki Lamras yace.
“Na yi murna da ganinka a
wannan biki a zatona ba zaka zo ba
saboda laifin da na yi maka sa’adda
muka haxu a bikin naxin sarautar
birnin sin”.
66
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
Koda jin haka sai sarki lamras
ya kama yaqe gami da murmushin
dole muryarsa na rawa yace.
“Haba ya kai sarkin sarakuna
ai ban isa na qi amsa gaiyatar bikinka
ba”.
Ita kuwa Nasmirat sai ta dube
shi tace “Zaka sha mamaki idan ka ji
irin labarum da zan baiwa sarki daga
daren yau, zaka ji daga bakinsa”.
Koda jin wannan batu sai jikin
sarki lamras ya kama tsuma saboda
tsananin mamaki gami da razana.
Daga nan suka yi gaba abinsu
haka dai aka ci gaba da gudanar
liyafar bikin na su.
Har tsawon wani lokaci kafin
aka kammala sarki Ram da amaryasa
suka wuce cikin.
Da shigarsu sai ta fahimci kan
sarki ya fara ciwo nan da nan
idanunsa suka juye ya fara tangaxi.
67
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
Koda ganin haka sai ta
fahimci cewa lallai ciwon sarki ne zai
tashi a daidai wannan lokacin
maimakon ta ji tsoro ta nisanta da shi
sai ta janyo shi jikinta ta shiga yi masa
raxa a kunne tana mai cewa.
“Ya kai wannan sarki mai
daraja ka yi sani cewa an tava yin
wani gagarumin sarki a birnin kisra
wanda ya shekara xari da ashirin akan
karagar mulki batare da ya tava
fuskantar
wata
matsala
ba
a
rayuwarsa amma a karon banza aka
rabashi da mulki yana ji yana gani da
qarfinsa da lafiyarsa ya dawo bawan
sarkin da ya hau karagar alhalin da shi
sabon sarkin ya kasance bawansa
kuma ko kaxan ba shi da wata alaqa
da gidan sarautar”.
Koda jin wannan batu sai
sarki Ram ya ji kansa ya wattsake take
kuma ya ji kansa ya daina ciwo don
68
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
haka sai ya dubi Nasmirat cikin
tsananin zaquwa yace, ta yaya wannan
al’amari ya faru, maza ki bani wannan
labari yake tauraruwar taurari.
Sa’adda Nasmirat taga sarki
Ram ya zaqu da son jin wannan
labarin sai ta qyalqyale da dariya tace.
“Ai kuwa akwai xinbin darasi
a cikin wannan labarin kuma gashi
yanzu dare ya soma yi, ina ganin har
gari ya waye ba zan iya gama baka shi
ba”.
Da jin haka sai jikin sarki Ram
ya kama tsuma zuciyarsa ta kama
tafarfasa kamar zata qone, kawai sai
ya zare takobinsa ya dakawa Nasmirat
tsawa yace.
“Maza ki ci gaba da ba ni
labarin da kika soma ko kuma yanzun
na sare miki kai”.
Koda jin haka sai Nasmirat ta
dubi sarki Ram cikin alamun tsoro tace.
69
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
“Kwantar da hankalinka ya kai
mijina ai yanzu nan zan ci gaba da
baka wannan labarin” Nasmirat ta yi
doguwar ajiyar numfashi sannan tace.
70
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
BABI NA BAKWAI
Kimanin shekaru xari da huxu
da suka shuxe anyi wani gawurtaccen
sarki a birnin kisira mai suna lafayis,
sarki lafayis ya kasance shahararren
mayaqi kuma babban sadauki mai
tarwatsa maza a filin daga.
Sarki lafayis ya kasance
azzalumin gaske domin bai xauki ran
xan adam a bakin komai ba, zalunci
kwace gami da fyaxe su ne al’adarsa
ta kullum da koyaushe rashin imaninsa
bai tsaya akan mazaje ba, hatta mata
da qananan yara bai qyale ba, sai da
takai cewa gaba xaya qasashen dake
makwabtaka da birnin qisra ana tsoron
sarki lafayis don haka duk qarshen
wata sai kowane sarki ya kawo masa
kuxi da bayi kyauta, domin gudun
71
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
kada a kawo musu harin bazato, ko
ace za a yaqe su.
Haka dai sarki lafayis ya zama
alaqaqai kuma qadangaren bakin tulu
a nahiyar gaba xaya, ya adabi kowa
don haka duk sarkin da ya bashi
wannan cin hanci sai dai wani ba shi
ba, wato dai ataqaice sai da takai
cewa a fakaice sarki lafiyas ne ke
mulki gaba xaya qasashen dake
nahiyar saboda duk umarnin daya
baiwa sarakuna dole su bi kuma duk
abinda ya buqata daga gare su sai sun
kawo masa.
A rayuwar sarki lafayis babu
abinda ya tsana sama da ayi masa
gardama ko kuma ya bayar da umarni
aqi bi, duk wanda ya aikata xaya daga
cikin waxannan laifukan a gare shi to
sai ya kashe shi, ya qarar da dukkan
zuri’arsa domin ya zamo misali ga
wasu haka kuma a rayuwar sarki
72
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
lafayis babu abin da yake so sama da
labaru da abubuwan ban dariya.
Don haka in dai mutum ya iya
barkwanci ko kuma ya iya abin dariya
to lallai zai samu kusanci sosai da sarki
lafayis kuma zai rinqa samun kyautar
dukiya mai yawan gaske.
Wata rana sai sarki lafayis ya
sami labarin wani gari da yake can
qarshen iyakar nahiyarsu da nahiyar
qasashen nasara wanda ake kira da
suna madhuzar.
Shi dai wannan birni na
madhuzar sabon birni ne wanda fatake
suka qiriqire shi asali ma ba a san ko a
qarqashin wacce qasa yake ba, akwai
ni’ima ta ruwa da yabanya a wajen shi
yasa fatake suka zavi wurin amatsayin
masauki rabin mutanen dake zaune a
birnin nasara ne rabin su kuma
larabawa saboda zaman lafiyan da ake
yi tsakanin qabilun biyu da kuma
73
HIKAYOYIN AL’AJABI
MADAKI
harkar cinikaiya sai aure ya rinqa
qulluwa a tsakaninsu suka rinqa
haihuwar kyawawan mata masu
kyawun launin fata gami da kwari da
kuma jarumta mazansu da matansu
duk kyawawa ne na gaban kwatance.
Babban abin da zai xaure wa
mutum kai shi ne babu wani bambanci
kowa yana da ikon yayi irin addininsa
da yake so babu mai hana shi,
shugabanci birnin a qarqashin qabilu
biyu yake babu sarki a garin amma
kowace qabila tana da wakili a
majalisar garin kuma wakilai a
majalisar garin kuma wakilai bakwai
ne sannan duk matsayinsu xaya babu
wanda yafi wani.
Kawai
dai
waxannan
shugabanin su goma sha huxu su ne
suke zartar da doka shari’a