Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Amsa wayar ta samu ta bashi haquri akan bacci ne ya dauketa, basu jima ba sukayi sallama kafin ta sake komawa bacci.

Qarfe goma na safe sautin kidan kwaryar da ake a filin gidan ya tasheta, da farko ta zata ko kunnenta ne beji daidai ba, seda ta kasa kunne sosai sannan ta tabbatar dagaske fa a cikin gidan ne dan ga hayaniyar Mata nan tana jiyowa.

Miqewa tayi zuwa jikin window dan tana dakin ta na saman Bashir ne, labulen ta janye ta leqa da mamaki take kallon Mata masu kidan kwaryar da kuma wadanda suke juyi a fili suna watsa musu kudi.

“Ikon Allah to me akeyi a gidan?”Ta fada a fili, ganin babu me bata amsa yasa ta saki labulen, gadon ta fara gyarawa kafin ta shige toilet tana ci gaba da mamakin abun. Wanka tayo ta shirya cikin wani danyen Lace Baqi da akayiwa kwalliya da Jan Zare ya karbi farar fatarta sosai da sosai ta kashe dauri tareda baza turarenta kafin ta dauki wayarta ta fito daga dakin takalmin qafarta na kwas kwas.

Palour kasan qal dashi Aliyu da Amna na zaune akan Dining suna karyawa duk sunyi wankan su. Gaba daya suka gaisheta tana shirin tambayarsu sauran Ahmad ya bude qofa ya kwaso da gudu Muhammad na bayansa har yana neman faduwa ta tare shi

“Ya haka bana hanaku guje gujen nan ba se kunji ma kanku ciwo ko” ta fada bayan ta tsaida Ahmad din.

“Mami biki akeyi a waje zo ki gani harda masuyin kida da calabash irin na gidan Baba Sarki” Ahmad din ya fada.

“Nima naji kidan tun ina sama ai me yake faruwa a gidan ne?” Tayi tambayar tana kallon Amna da Aliyu dan sune manya.

“Wai suna waccen matar sukeyi” Aliyu ya fada ba tareda ya dago ya kalleta ba.

“Wace matar“ ta tambaya tana tsare shi da ido dukda ta gabe wa yake nufi amma se yaqi ya dago bare ya kalleta kuma yaqi magana se ma kaida kansa gefe da yayi.

“Yayi kyau matar Baban naka ce waccen matar ko Aliyu idan na sake ji se ranka ya baci tabbas” ta fada tana jan kujera ta zauna. Tea ta hada ta debi dankalin da suka soya dan da zafinsa ta hada ta fara ci a ranta tana ayyana kenan bikin suna sukeyi yau, sekace dole su kuwa ai da sun haqura sa hadu a wani karon amma to ita ina ruwanta ma.

Tsaf suka gama cin abincin ta koma cikin palour ta zauna, wayarta ce ta shiga qara Amna dake kusa da ita ta miqa mata. Zahra ce take kiranta Qawarta ce tun ta yarinta tare suka tashi daman sunyi da ita yau din zata zo bayan sun gaisa kuwa take shaida mata tana nan tafe fa gurin qarfe biyu na rana sukayi sallama ta kashe wayar.

A hankali hayaniya ta kaure gidan mata kuwa se shigowa suke kamar ana tunkudo su lokacin har sha biyu tayi ta dena jiyo kidan kwaryar da alama sun tashi ne sedai hayaniyar mata kawai.

Saboda zuwan Zahra yasa ta shiga kitchen, fried rice ta dora ta window kitchen din da yake kallon tsakar gidan take kallon ikon Allah yanda Jama’a ke tururuwa a gidan nasu wasu na shiga wasu na fita. Bata tsinke da lamarinba seda ta ga an wangale get ana shigo da kujeru harda Wata rumfa da kayan decoration ba bata lokaci suka shiga har hadawa kuwa

“Shagali kace abin nayi ne to Allah yasa a tashi lafiya” ta fada a fili tana hada salad dinta, kafin ta gama kuwa har sun gama sauke kaya sun hau shiryawa ga kayan DJ an ajiye daga gefe suma.

Harabar gidan nasu nada dan girma ba laifi dan a qalla zataci mota biyar zuwa shida saboda filin gefen su da Bashir ya shigo dashi yayi ginin Bangaren Amirah ya ragu sosai shi ya qarawa gurin girma. Tsaf suka gyare ko ina aka jera kujeru can daga gefe ga High-table an shirya se zama kawai ya rage.

Tsaf ta gama girkinta suka jere kayan akan Dining tana shirin shiga daki tayi sallah dan har biyu ta kusa a ka kwankwasa qofa, jafar tacewa yaje ya bude ta dan daka dan taga wanene.

Sadiya da Afiya ne qannen Bashir se Suwaiba diyar qanwar Baban su suka shigo ko wacce da shirgin Jakar kaya a hannunta ga yara na biye dasu. Kada ran kada han take kallonsu har suka qaraso tsakiyar palour suka zube akan kujeru suna wash Allah jij sanyin Ac da qanshin turare na ratsa su.

A kusan tare suka gaisheta, Asma’u da bata dara daga inda take ba ta amsa tana kallonsu da jiran ji da wacce suka zo kuma.

“Ku tashi mu shirya lokaci ya na tafiya dan nasan yanzu zakuga shagali ya kankama fa kuma ni ko wanka ma banyi ba na fito daga gida” inji Sadiya

“Ai bake kadai ba nima banyi wankan ba haka na fito” Suwaiba ta mara wa Sadiyan Baya suka miqe kowacce ta sabi jakarta suka doshi corridor da dakunan suke inda anan Ma’u ta coge. Seta qara gyara tsayuwarta ta yanda ta raba hanyar biyu ba ta yanda wani ze wuce fuskarta na nan a yanayin da bazaka iya fasaltawa ba.

“Bari mu wuce Anty” Sadiyan ta fada
“Zuwa ina?” Asma’u ta tambayeta, se suka kalleta duk su biyun da mamaki, Suwaiba ce tayi qarfin halin cewa
“Wanka zamuyi”.

“To yaushe gidan nan ya zama gidan wanka kuma bani da labari?” Ta fada tana gyara tsayuwarta da jinjinawa rainin hankalin wadannan yaran ta kuwa shirya nuna musu iyakarsu yau dan yanzu ba da bace.

Kallon kallo aka shigayi tsakanin Suwaiba da Sadiya, still Sadiyar ce ta sake magana dan tafi sauran baki tace “ban gane ba Anty wanka fa mukace miki zamuyi anan kine zancen wani gidan wanka kuma ko bamu da damar da zamuyi wanka a gidan dan uwan mu ne?”

“Allah sarki masu Dan uwa dama kuma babu ita kuna iya juyawa kuje wani Gurin tunda bani kadai bace a gidan ko? Ina ga ai kamar a kwai yar uwarku ma kuna iya zuwa gurinta”.

Ba qaramin mamaki ne ya kama su ba da jin kalaman ta, Antyn da ada a dakinta suke duk wata dabdalarsu qarewar wanka har kayan sawa ta kama basu take idan ana wani taro ka zo da kayan da basu kamata ba seta dakko na fita taro ta baka ko yanzu ita Sadiya bata zo da mayafin da zata hada kayan da zata saka ba dan a safiyar nan suka samu labarin taron sunan suka kuma qudiri niyyar se sunzo duk kuwa da gargadin da Dada tayi musu amma sunce baza’ayi babu su ba wallahi.

Sabon Leshinta ta dakko zata saka bata rigada ta siya masa mayafi ba dan ta tamawa bikin Qanwar mijinta ne zata saka saura sati biyu yanzu se kuma ga wannan taron ya taso shiyasa ta dakko tasan bazata rasa mayafi gurin Anty Asma’u ba tunda tana gari qila harda jaka ta samu amma shine take gaya musu wadannan magananganu haka.

“Ku nake jira zan rufe qofata lokacin sallah ya kwace mun” suka ji muryarta ta dawo dasu daga suman mamakin da sukayi, har Suwaiba ta budi baki zatayi magana Afiya da tun farko bata ce komai ba ta dakatar dasu da cewa

“Sadiya ku muje mana ko bakiji me tace bane”
Dukyanda suka so su sake magana kuwa ta hanasu haka suka tattaru kayansu sukayi waje Sadiya da Suwaiba na kumfar bakin bazasu yarda ba su zata wulaqanta suda gidan dan uwansu ai se sun kira yayan suji idan shi ya bata sabon lasisin wulaqanta su.

Oho bata ma san sunayi ba dan suna fita Jafar ya tura qofar ya rufe dan bata buduwa ta waje dole seta ciki suka ci gaba da kallonsu ita kuma ta shiga daki ta tada sallah. Tana dakin Jafar ya shiga da sallama

“Mami ga Umman su Jawad tazo”(Zahra qawarta)
“toh gani nan zuwa” ta fada ya juy ya fita. Daurin ta ta gyara da fuskar ta ta fito fuska a washe suka rungune juna ita da Zahran da murnar yaushe gamo dan an dade ba’a hadu ba kafin suka zube akan Two sitter ta shiga yiwa Zahra tsiyar qiba.

“Kai matar nan gaskiya wayo kikewa Yah Sayyadi ji yanda kike narka qibar kamar wata Aisha Buhari 😂😂🤐”
“To ya za’ayi barni nayi qibata kowa ya ganni yasan ina jin dadi tunda jikin yaqi zama irin naku jikin models” Zahra ta fada da sigar shaqiyanci suka kwashe da dariya tareda kashe wa, Sallamar da akayi ta katsew Ma’u maganar da tasoyi.

Rahma ce matar Amiru qanin Bashir bayanta kuma Kamila ce itama qanwar su Bashir dince da me aikinta dauke da danta dagaje dagaje dashi ga ledar kaya a hannun Kamilan. Da sauri Kamilan ta shigo dan seda Rahma ta matsa gefe ta bata hanya ta dire ledar a kan centre Table ta na cewa Me aikinta “maza Usaina ki gyara masa jikinsa ga kaya nan ki saka masa nima yanzu zan zo na yi wanka na shirya” ta juya ta fice ita kuwa Usaina ta qaraso ciki tana gaishe su da niyyar ajiye yaron Asma’u tayi saurin dakatar da ita.

“Dauki kayan maza ki bita” ta fada tana nuna mata hanya, ba musu kuwa Usaina ta kinkimi leda da yaron tayi waje harda ja musu qofa se sannan Rahma ta sama ma kanta gurin zama.

“Keda mutanen naki kuma yau Maman Aliyu” Rahma ta fada tana dariya.
“Da kenan Maman Nasir ai sun shani na warke kuma yanzu, kunga ku tashi kuje sama ina zuwa”. Zahra da Rahma suka miqe zuwa sama qaramin palour Ma’u da take sauke manyan baqinta.

Kallon Jafar da Abdallah dake kallo tareda Jawad Dan Zahra tayi tace “ina su Ahmad?”

Jafar ne ya amsa mata yace “Yaya ya fita, yah Amna da Farida ma sun tafi gidan su Amina Shehu sunce sun gaya miki tareda su Ahmad din”

“Eh na tuna, kana jina duk bugub da za’ayi ko waye karka kuskura ka bude kofar nan”.

“Tam Mami” ya amsa mata yana daukar Handle din Game din da suka kunna.

Kitchen ta shiga ta hado ruwa da lemo da tarkacen kayan motsa baki a Babban Try Jawad ne ya karba dan yafi Jafar din girma ya kai saman ita kuma ta dibar musu Abinci da sauran kayan da zasu buqata duk ta basu suka kai, da kanta ta murzawa kofar key ta kuma sake jan kunnensu akan karsu bude mata qofa kafin ta haye saman suka hade da su Zahra aka shiga hirar duniya da abinda ze amfane su ba tareda sun koda taso da zancen Abinda ke faruwa a cikin gidan ba.

A dakin me jego fa tuni abubuwa sun dauki Harami, tana zaune ta ci Ado da wata danyar shadda data sha aiki su Sadiya suka shiga palour suna kumfar Baki da zage zagen abinda Ma’u tayi musu, anan palour aka maida magana basu dasa Aya ba Me aikin Kamila Ma ta dawo tana miqawa Kamilar ledar kayansu.

“Kan bala’i lallai matar nan au kema koroki tayi?” Kamilan ta fada.
“Ta koromu ma bare wata me aikin ki ai wallahi bari a tashi taron nan bata ci banza ba se mun nuna mata nan gidan dan uwan mune muna da ikon yin yanda muka ga dama a ciki, ke Amirah bamu muqullin dakin Yaya naji kofar a kulle take”. Cewar Sadiya.

“Nan fa daya yaya sadiya key din dakin mijin nawa zan baku kema kin san baze yuwu ba” Amirah ta fada tana yatsina fuska, tab waima ta basu key wallahi bazata bayar ba kuwa.

“Oh kema diban Albarkar zaki mana dakin dan uwan mu fa mukace ki bude mana mu shiga mu shirya tunda kinga dai nan ko ina da mutane” Kamila ta karba se kuwa Amirah ta miqe tana sabar yarta da take ta nan nan da ita ga kuma key din a hannunta dan kayan da zata saka dana rabo duk suna ciki bata kuma yarda ta bawa kowa ba banda Ummi se Anty Aisha su kadai ta yarda suka shiga dakin.

“Bafa zan bayar ba Yaya Kamila idan kun matsu da wankan ku shiga na dakin baqi dan na kulle toilet din dakina ma kar a batamin ko ga wani nan ai a kofar daki kuyi amfani dashi” ta shige dakin ta ta barsu sototo baki a bude tsabar mamaki.


Mura ce take damuna wallahi kuyi manaji da wannan 🙏🙏🙏🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)

Page 18

Taro yayi taro dan kafin la’asar gida ya cika ya batse da mata kala kala se an bulowa suke. Tuni mata sun zazzauna kan kujerun da aka shirya an wangale get duk inda ka duba qawayen Amirah ne yan gayu sunci kwalliya da kuma manyan Mata Qawayan Addah data gayyoto daga gefe DJ nata sakin duma wasu na tattakawa wasu kuma suna cin abinci dan tuni an fara rabo.

Shinkafa gata nan kala kala, soyayyoyar taliya, dambu, Alala ga dabgen kaji da na naman Sa ga Fura me kyau da aka zuzzuba a kofuna Zobo dasu kunan Aya da lemon robobi dai kaya masha Allah an tanadi komai harda gurasa suka siyo daga kano akayi bandashe me kyau se rububinta kuwa akeyi.

Wuraren Uku na tana su Ma’u na tsaka da Hira Jafar ya kwankwasa kofar palour da suke ciki, seda aka bashi izini sannan ya shiga ya tsaya daga bakin kofa yana cewa
“Mami ana ta Knocking na tambayi waye wai Anty Aisha ce ta gidan su Anty Amirah shine nace bari nazo na gaya miki kafin na bude”.

“Tam jeka ina zuwa” ta fada ya juya yai tafiyarsa. Kamar bazataje ba sedai kuma ta miqe dan Ko ba komai tana ganin girman Anty Aisha amma fa batajin yau akwai wanda zata bari ya shigo mata daki a cikinsu. Sun saba in ana hidima azo a yi mata kaca kaca da guri a tafi a barta da gyara to an dena bakuma za’a sake ba.

Har kuwa ta sauka qasan Anty Aisha na tsaye a bakin qofar. Dan kadan Ma’u ta bude qofa taja ta tsaya Anty Aisha data taho da niyyar shigowa ganin ta tare qofar se jikinta yayi sanyi. Gaisawa sukayi ta tambayi Anty Aishan ya taro tace lafiya lau se sukayi shiru gaba daya kafin Aishan tayi qarfin halin cewa

“Daman nace ne bari nazo ki bada abunda za’a zubo muku abincine”

“Lah ai kubarshi ma wlh nayi abinci da yake ina da baqi”. Asma’u ta tareta kafin ta fara qoqarin juyawa tunda maganar kenan se Antyn ta katseta tana cewa

“Am nace dan Allah in ba damuwa ko zamu dan kawo wasu baqin mu su dan zauna anan can din ya cika wallahi”

“Ai haka taro yake daman se haquri ba lallai mutum ya samu yanda yake so ba, se suyi haquri su zauna tunda abun nadan lokaci ne” garam ta rufo qofarta tabar Anty Aisha da baki a bude.

Data koma saman ma tambayarta sukayi ya akayi
“Wai baqi zasu kawomun nan”
“Kika ce me?” Suka hada baki gurin tambayarta, se tayi yar dariya kafin tace.

“Me zance kuwa in banda karsu zo, nifa na yanke alaqa se wadda ta zama dole ba se an san cikin ka ba sannan za’a maka yankan bayan? To muje baya baya kowa yayi ya tasa dan ba qara”. Cewar Asma’un

“Allah ya rufa asiri dai amma dangin mijin nan naku basuda kunya wlh” cewar Zahra.

“Waa ai ni baza’a fara wannan wasan dani bama wallahi ni naga qoqarin Maman Aliyu da batai musu hauka dan order ba wallahi ai sam mutanen nan basu san mutunchi ba” Rahma ta fada, ita dai Ma’u shiru tayi bata ce musu komai ba. Bazasu gane ba duk yanda za’a musu bayani idan ba kansu ta fada ba. Hirar su suka ci gaba dayi har aka kira la’asar suka tashi dan yin sallah.

Yan suna kuwa Qarfe hudu daidai Aka sanar da fitowar Me Jego Hajia Amirah da ta cancada kwalliya da wani dan ubansun Leshi Dark blue da adon light Blue din zare dayayi bala’in karbar farar fatarta. Tayi kyau harta gaji komai Hassadar mutum dole ya yaba anyi mata lafiyayyar Fitted gown dinki ya fita ko ina das.

Ga Goggoron da aka daura mata ya zauna das ya qara qawata kyakykywar fuskarta hannu da qafa ya dau Ja da Baqin qunshi ga Danqareriyar sarqar gwal a wuyanta da zobuna harda awarwaro Allah kadai yasan ina suka samo su. Rungume take da yarta da akayiwa Kwalliya cikin daya daga cikin rigunan Ma’u fara harda shawl din dan shima farine ta nadeta a ciki Qawayen ta na take mata baya suka shigo filin tuni DJ ya ware wusu WARRR.

Seda suka rakata har mazauninta aka dauki hotuna sannan kowa ya nemi gurin zama. Bayan kowa ya nutsa DJ Fele da takanas suka dakkoshi tun daga Kano ya nemi da wata ta fito ta bude taro da bayanin maraba, Hajiya Hassana daya daga qawayen Addah ce ta fita ta fara jawabi kamar haka.

“Dafarko munawa kowa da kowa barka da zuwa wannan shagalin suna na Yar Gata yarinya haihuwar dangi, muna fatan yanda aka fara taro lafiya a tashi lafiya kowa kuma ya koma gidansa lafiya. Muna qarawa yiwa kowa barka da zuwa” aka dauki tafi raf raf.

Can na hango Addah bakin nan kamar ze tsage saboda fara’a taci wanka ta saka wata Hadaddiyar Atamfa ta manyan mata ga dauri an cakare se maraba takeyiwa baqin ta ranta fes ganin yanda suka amsa gayyatarta suka zo mata taron da yawa dukda a qurarren lokaci tayi gayyatar.

Suna ya kankama tuni a ka shiga shagali ka’in da na’in, duk yanda Amirah taso kwakwume yar haka seda ta bayar da ita Dangi da qawaye suka ringa daukanta ana ta hotuna. Ba daukan yarinyar yafi damunta ba, sanyi ya riga ya kankama musamman lokacin da yake La’asar sakaliya ga bishiyun tsakar gidan suna ta rangaji suna qara yawan isaka sannan Get ma a wangale yake saboda yawan Jama’a.

A fili fara’a takeyi amma zuciyarta addua take ta ja Allah ya rufa mata asiri a tashi taron nan qalau batare da wani abu ya faru ba dan se a yanzu take jin kamar tayi wauta a lamarin. Haka ta daure zuciyarta ta zage suna ta kwasar rawa ana videon tiktok da qawayenta da kuma daukar hotuna wasuma live suke video amma fa rabin hankalin ta na kan duk inda akayi da yarinyar.

Biki fa yayi baki mata an zage DJ Fele na kada musu ganga suna cin uwar sabada, daga can cikin gida bayan da Amirah ta gama shiryawa zata fito, harta zuwa key din dakin Bashir a jakarta ta tuna da kayan rabon da zasu sallami baqinsu yana ciki. Gudun kar azo a manta har a watse ba’a fito da kayan ba yasa ta danqawa Anty Aisha akan da taga an fara haramar tafiya ta fito da kaya a fara rabo.

Haka kuwa akayi ganin magriba ta doso yasa ta bude daki ta fara fito da kayayyaki tana bawa wadanda suke zaune a palour basu fita gurin kida ba. Kunsan mutanen mu da souvenir nan da nan fa akayo mata caaa yan uwansu ganin kamar zabe take tana raba kayan aiko suka duru dakin Bashir duk yanda Su Ummi suka so su hana be yuwuba tun kuwa kafin aje da nisa a garin kwatar leda wata ta kaiwa Murfin wardrobe naushi, abunka da me qashi daya nan take gilashi ya tarwatse 😂😂😂 mata aka debi salati.

Basu dawo daga wannan tashin hankali ba aka samu yaran biyu daga ciki da suna shiga su kan mirror sukayi ganin kayan wasa suka kuwa shiga watso tsadaddun turarukan Bashir suna fashewa Tush a qasa, babu me jiran a ce masa ya fita sum sum suka fara ficewa daga dakin dan sun san sun tsokalo tsuliyar dodo yau amma dukda haka seda aka samu was masu son zuciyar da suka saci turare suka fita dasu.

Tsilli tsilli Ummi da Anty Aisha sukayi ko wacce ta kasa magana,
“Yanzu Anty yaya zamuyi?” Ummi ta fada tana rarraba ido dan tasan Allah ne kadai ze kwaceta a hannun Yaya Bashir idan yaji harda ita a dakin.

“Ummi nima tunanin da nakeyi kenan, amma kinga samo tsintiya mu tattare tunda me afkuwa ta afku maji da abinda ze biyo baya”. Tayi Na’am da maganar dan haka ta fita ta dakko tsintiya da abin shara suka shiga kwashe kwalabe da gilasan bayan sun gama suka hado kan kayan rabo tas suka dire a palour, dakin Amirah Anty Aisha ta shiga ta nemi guri me kyau da ba wanda ya gani ta ajiye mata muqullin da niyyar idan ta tambayeta ta gaya mata inda yake bata tsaya ba ta hada kan yayanta sukayi gida dan bata san yanda za’a qare ba.

A can filin kida kuwa bayan yaran mata sun gama nasu, nan kuma Manyan mata qawayen Addah suka shiga suma su zubda nasu galangalan din. magriba tayi amma haka suka ci gaba da buga ganga mata na rawa. Addah da jikinta har tsuma yake ta shiga zuge jaka da niyyar fito da sababbin kudin data yiwo chanji daman saboda liqi sedai kudi sukace dauke mu inda kika ajiye.

Hankali tashe take sake laluba jakar, da kudin liqi da da wayarta data Amirah data karba ta saka mata a jakar ga uban gudummawar da ta samu ta tabbatar da qila har chanji zasu samu bayan sun biya basussukan da suka ciyo se gashi gaba daya babu su babu alamarsu.

Wata Ashar me maiqo ta janyo ta dire tana zazzare ido kamar ance zata ga kudin ne a qasa, wannan shi ake kira da tashin hankali ba’a saka masa rana. Amirah ta hango da wasu mutum biyu sun nufi cikin gida da sauri ta shiga kwala mata kira amma ina qarar kida bazata bari ta jiyota ba har suka shige se kawai ta nufi get afujajan ta shiga jansa ruf ta rufe gida.

Kwadon yana jiki daman hatta da key din da suka bude basu cire ba tsabar rashin hankali ko kidane yai dadi oho Allah dai ya rufa asiri ba’a samu wani ya zare ba da wannan tayi amfani ta garqame gida tsaf ta jefa muqulli a riga ta nufi gurin gangar DJ gadan gadan tana zuwa kuwa batayi wata wata ba ta fizge wayar inji kida ya dauki dif.

A fusace yaron DJ ya juya da niyyar ganin waye yai musu danyan aikin se ganin uwar biki yayi ta riqe qugu tana kumbura tana sace wa.
“Zoka mayar amma ka kashe kidan ka bani abin magana” Addah ta fada, shikuwa beyi musu ba ya maida waya ya miqa mata lasifiqa ya tsaya yaga ikon Allah dan dai daga yanayinta yasan ba lafiya ba.

Juyawa tayi ta kalli mata da suka qame suna kallonta da jiran jin wani wulaqanci ne yasa aka katse musu cashewa suna cikin Warwarewa.
Addah na haki kamar wadda tayi gudu ta fara magana tana cewa “nidai bazan ja doguwar magana, idan kin san ke kika kwashe mun kudi a jaka kusan dubu dari biyu kika hada da wayata ta dubu saba’in data me jego Me kyamara uku ni ban san kudinta na to ki fito dasu yanzu ko kizo ga jakar can na ajiye kin sanya salin alin ki maidamun komai ciki idan ba haka na rantse da abinda ze kashe ni daga nan se police station dan se an fito mun da kudina ni ba taron farin ciki na tara ba dan azo a sabautani ni ba”.

Hayaniya ce ta tashi a gurin mata suka shiga duka jakun kunan su ai se kuji an yanko salati kafin wata ta dire wata ta dauka kan kace me guri ya rikece da surutan mata da yawa an yashe musu jaka tas suna can basu ankara ba.

Hajia Mariya daya daga cikin qawayen Addah ta zazzage jakarta tas a qasa komai na ciki ya zubo ga tsabar kudi nan da wayarta harda qaton zoban gwal data saka taji ya dame ta duk suna ciki amma babu muqullin motar da tazo da ita. Hannaye biyu ta dora a hannu ta fashe da kuka tana kururuwar ta shiga uku.

“Ni Mariya na shiga uku yau in koma in cewa Alhaji me? Be san na fito ba da safiyar nan Fatu kika azazzaloni se nazo sunan nan na dauko sabuwar motarsa sau daya ya hauta kafin ya tafi

Please Login or Register in order to submit comment