dan kato da gora da dansanda duk sunansu daya
.
A guje yan matan suka nufi gida yayin da motar taja birki gab da mu, wata kura ta turnuke tamkar a fagen fama , suk kuwa ba su bata lokaci ba wajen durowa, kai kace wasu kwararrun sojoji ne da suka sami horo
"Yawwa shine, ga motar nan" lateef kenan wanda yake daure da ankwa, ala dole wai shi bakaniken mota ne,
Dajin haka sai nayi fitar burgu, ni ma gidan liman din na shiga,
"Ku tare shi, kar ku bari ya sha"
Zancen wani gabjeje kenan daga yan kato da goran, saidai ya makaro domin tuni na tsunduma aciki
"Ku ceceni zasu kasheni" wannan shine abin da nake fada. Banyi wata wata ba na nufi wani lungu dana ke zaton na ban daki ne, bayan dana yi fatali da wata kwaryar nono na kuma firgita agwagi, abinda ya sanya matan dake gidan fara salallami, iya kacin iya wata nake makyarkyata da kuma kumfar baki, harshena kuma yana furta na banu na lalace
.
Hakan sai ya sanya matan kasancewa cikin rudani bisa rashin sanin abinda ya firgitani, a wannan hali liman ya ba zamo cikin gidan da sauri, akwai gayyar yan kato da gora biyar biye dashi, na tabbata iznin shigowa suke nema, na fara kwalla ihu, ina shirin kama katanga, biyu ne daga cikin yan kato da goran suka rike min kafafu, jawo ni sukayi na fado kafin wani ya dubi fuskata ya yarfa min biyar, wani irin radadi gami da zogo suka keta fuskata naji kamar ance masu su dakata , to amma sai naci gaba da jurewa, ........
WAIWAI TOH FAH
YAU UMAR DAKANSA
YA YAYIMO KATON DUTSEN RIGIMA
DON TOSHE DUK WANI RAMI DA ZAI KAWO CIKAS A TSAKANINSA DA FARIDA
.
Nidinne dai shuraih Usman
Inkiya 99%
Kuyi like na shafinmu www.facebook.com/hausaebooksTARAR ARADU
Littafi na Uku 3
Umar lawan Abdul
Typing Shuraih Usman
Page 3
.
.
Na marairaice "tawace baba"
Bai kara komai ba sai ya tafi ya rabu dani na dan tsaua jim sannan na nufi cikin gida
.
A wajen mahaifiyata farin ciki na tarar da kyakkyawar maraba, ta gabatar min da abinci da kuma fura, Na fito wajen lateef gayyatarsa nayi muka shiga cikin dakin da aka ce nawa ne nida laraba, na ajiye masa abincin ni kuma na koma gefe guda.
"To taso muci mana"
Nayi tsaki "bai da muhalli a ciki na"
Hakika bai kamata nayi haka ba, ko don gudun kar ya zargi wani abu musamman saboda bambancin kabila dake tsakaninmu ga kuma dukiyarsa da muka taho da ita, Amma ina! Shi sam bai kawo haka arai ba tuni yaci tuwo yasha fura, daga bisani yaja fulo ya tuntsure, anan yabar ni ina ta kulle kulle arai har safe,
.
Tun da sassafe lateef ya hau tabe tabe ! Ba wani gyara ne na gaske ba, juyen baikin mai ne da yan abubuwan daba a rasa ba, wajen karfe dayan rana ya kammala, na sallame shi ya tafi, bayan da nace ina zuba idanu, wani lamarin da mahaifina ya tuhume ni akai shine ganin na kwance Number plate(Lamba) na ajiye, wannan ma ya sanya masa shakku a zuciya, na shiga gida na sami mahaifiyata, izini na nema akan ina so mu gana da amaryata, ban sami matsala ba, kai tsaye ta aika gidan ta sanar da su, aka ajiye karfe hudu a matsayin lokacin daya kamata na je, wanka na yi na yi fess dani sannan na hau mota na shiga zagaya gari, duk inda na bi sai abini da kallo, wai su abin mamaki ne saurayi kamata da mota mallakin kansa, ni abin har ya kan bani da riya, ba wata motar kirki bace, irin tsohuwar yayin nan ce da ake yiwa lakabi ajalin tafiya(tab
.
Kafin wani lokaci labari ya game ko'ina Umar ya sayi mota, aka rinka zuwa yiwa iyayena barka, sai dai abinda basu sani ba gab barka take da komawa jaje, meyi wuwa awoyi biyu nan gaba
.
Karfe hudu shaura na durfafi gidan liman , bayanda nayi sallar la'asar, kafin n kara sa, shi ma ya fito daga masallaci yana zaune a wani katon buzu yana jan carbi naje na durkusa gwiwa biyu na gada shi, ya amsa gami da shi min albarka, wai har yarom kirki yake kirana, na tashi zuwa gindin mota ta bayan da muka kammala
.
Na harde hannaye a kirji, gami da jingina sosai da motar daidai nake kallon mutane taamkar wani dan birni mai ji da kansa a taron kauyawa
.
A karo na tara na kai idona ga kofat gidan liman , babu abinda nake son gani illa fitowar laraba yarinyar da aka ce da ita ake shirin daura mana aure gobe, koda yake fuskarta bata nuna komai ba, amma amma adadin majalisun tattaunawa dake zuciyata har sun wuce kirge, wadda nafi jin haushi itace mai cewa idan bayeraben ya gaza aiwatar da shirin yaya zanyi.?
.
Shakka babu wannan tunani ne dana ke wwadai da shi, koda a mafarki kuwa ba zan so ya wakana ba, duk kuwa da cewa aiwatar da shirin wani tashin hankali ne babba, amma a wajena tashin hankalin shirin yafi rashin masoyiyata, a wani sashin kuma tafarfasa zuciyata take yi tana kuna, ba don komai ba, sai don abubuwan uku da ahalin yanzu suke tare da ni, Na farko tsana ta da ganin yarinyar dana aika ayo min kiranta, araina zan fi son kallon abu mafi muni fiye da kallon fuskarta, ba don komai ba sai don kasancewarta mai son mallake wani matsayi dana alkawartawa farida shi, hali na biyu kuwa zulumi da jimamin abinda zai biyo bayan shirin danayi, ko tantama babu zai zamo bacin rai da bakin ciki mai girma ga iyayena, zan tafi na barsu cikin tashin hankalin da ban san abinda ya kamata na kwatanta shi da shi ba, tun da na gano haka kuwa kamata yayi na fasa sai dai ina, zuciyar ta yi nisa ban da tunanin mallakar farida bata tuna komai
.
A gefe guda kuwa rashin sanin halin da farida ke ciki ne ke dagula min lissafi, ko ba komai dai na tabbata tana jin jiki, in haka ne kuwa dole ne nayi gaggawar komawa kusa da ita, a cikin wannan hali na hango 'yan mata biyu fitowa daga gidan liman
Fuskar daya na iya gani ma'abociyar tsage 'yan baka da uku-uku dayar kuwa ta rufe fuskarta da farin mayafi, abun d ya tabbatar min da cewa itace wadda ake so na aura, tsayuwarsu a kusa dani ta sanya wani abu yuko min arai, na tsane su iya tsana tamkar na rufe su da duka naji araina, dayar ce ta fara gayar dani, karfin hali nayi na amsa batare da nuna wani abu a fuska ba
.
Daga bisani ta juya ga dayar "laraba baku gaisa ba"
"Ina wuninka" ta maganar ne cikin murya mara kara
Na amsa "lafiya lau" daga haka ban kara komai ba
Batare dana shirya ba , dayar ta janye mayafin da yarinyar ta rufe fuskarta, hakan yabani damar ganin abinda fuskarta ta kunsa,
Doguwa ce ma'abociyar dogon hanci da dan karamin baki idanunta dara dara farare da suka wadatu da gashin gira, idan aka cire hassada mai wannan siffar ita ake kira da kyakkyawa, irin kyawun da duk wanda matarsa ta zama haka bazai rinka nisa da ita ba kuma na sani hikimar mahaifina kenan ta nema min aurenta, sai dai hikimar bata amfanar ba , domin ina tare da wadda ta dame ta ta sahnye, kyakkyawar da idan tana nan duk wata mai kyau ta kan dusashe
.
A zahiri na san yadda ake hira da masoyi sai dai ban san yadda ake hira da mutumin da bai da kima a rai ba, shiru nayi ina sake saken wani batun da bam, abinda na tabbatar zai jefawa 'yan matan shakku a rai, kuma a lokacin na tabbata fuskata ta nuna damuwar dana ke ciki
Kamar an watso su sai gasu suna nufo mu da gudu-gudu, bakake wuluk da su kamar tawagar tururuwa, gayyar irin yan kungiyar nan ne vigilante group (kato da gora) suna cikin motarsu kirar hyundai samfurin pick up (a kori kura) duk da cewa na san su wakilai ne na tashin hankali, wadanda. Lokacin dauke suke da manyan kwandunan takaici, sai na kasance cikin farin cikin zuwansu, ko shakka bana yi a yau din nan maganar auren zata ruguje, sai dai na tabbata duk wani mutunci da kima dana ke da su zasu bi hadarin kaka
.
Na kai idona ga nahiyar da liman yake zaune yana aikin jan carbi, nayi farin ciki dana ga cewa shima yaga zuwansu, ba shi kadai ba hatta ilahirin jama'ar dake rukunin hankalinsu yana kansu baya ga wata gayyar 'yan bin kwakwaf da sukaa biyo su da gudu ban yi mamaki ba a kauye dan kato da gora da dansanda duk sunansu daya
.
A guje yan matan suka nufi gida yayin da motar taja birki gab da mu, wata kura ta turnuke tamkar a fagen fama , suk kuwa ba su bata lokaci ba wajen durowa, kai kace wasu kwararrun sojoji ne da suka sami horo
"Yawwa shine, ga motar nan" lateef kenan wanda yake daure da ankwa, ala dole wai shi bakaniken mota ne,
Dajin haka sai nayi fitar burgu, ni ma gidan liman din na shiga,
"Ku tare shi, kar ku bari ya sha"
Zancen wani gabjeje kenan daga yan kato da goran, saidai ya makaro domin tuni na tsunduma aciki
"Ku ceceni zasu kasheni" wannan shine abin da nake fada. Banyi wata wata ba na nufi wani lungu dana ke zaton na ban daki ne, bayan dana yi fatali da wata kwaryar nono na kuma firgita agwagi, abinda ya sanya matan dake gidan fara salallami, iya kacin iya wata nake makyarkyata da kuma kumfar baki, harshena kuma yana furta na banu na lalace
.
Hakan sai ya sanya matan kasancewa cikin rudani bisa rashin sanin abinda ya firgitani, a wannan hali liman ya ba zamo cikin gidan da sauri, akwai gayyar yan kato da gora biyar biye dashi, na tabbata iznin shigowa suke nema, na fara kwalla ihu, ina shirin kama katanga, biyu ne daga cikin yan kato da goran suka rike min kafafu, jawo ni sukayi na fado kafin wani ya dubi fuskata ya yarfa min biyar, wani irin radadi gami da zogo suka keta fuskata naji kamar ance masu su dakata , to amma sai naci gaba da jurewa, ........
WAIWAI TOH FAH
YAU UMAR DAKANSA
YA YAYIMO KATON DUTSEN RIGIMA
DON TOSHE DUK WANI RAMI DA ZAI KAWO CIKAS A TSAKANINSA DA FARIDA
.
Nidinne dai shuraih Usman
Inkiya 99%
Kuyi like na shafinmu www.facebook.com/hausaebooksTARAR ARADU
Littafi na Uku 3
Umar lawan Abdul
Typing Shuraih Usman
Page 4
.
.
A guje na shige babbar rigar liman ina neman ceto" ka ceceni liman , idan suka tafi dani kasheni zasu yi"
.
Da nasan haka ce zata faru da ban kwatanta shiga rigar ba, wani rin dundu yayi min da naji tamkar zan amayar da kayan cikina
.
Yafara fada cikin bambami da daga murya "mutumin banza suma kashe ka din mana, wacce tsiya barawo zai tsinana idan an kyale shi? Ni dai Allah ya ceceni da ban riga na aura maka 'ya ba , ace kamata ya aurawa barawo 'ya"
.
Wani sabon salallami ya fito daga bakin wata mata"lailaha illallahu, dama barawo ne malam"
"Barawo ne mana motar mutane ya sato, masu ita ne suka zo masa da 'yan sanda, bakanikensa ne ya tona shi"
"Amma Allah wadaranka" inji wata 'yar tsohuwa, ko rara daya biyu banayi mahaifiyar liman ce, sai dai ba zanso addu'arta ta karbu ba
.
Cikin halin riko na sai na dubu ta taru 'yan bangar suka nufi waje dani, kafata ko takalmi babu tuni na watsar da su, cincirindon da jama'a sukai a waje yayi matukar girgizani, da ganin fitowarmu suka dauki hayaniya, kowa yana fadin abinda yake ganin yayi daidai da shi, cikin motar aka watsa ni, batare da saurarawa ba aka nufi nahiyar gida dani
.
Tarar da mahaifina zugum a soro yana hawaye ya rikitani, na tabbata bakin cikin abinda ke faruwa ne yake cinsa, naji tamkar na tashi drama din na dakatar da ita na kuma fayyace gaskiya, sai dai xuciyata bazata bari ba, ita take jagoranta ta, yayin da ita kuma so yake sarrafa ta, abinda yafi hakan tashin hankali shine samun mahaifiyata tayi zaman dirshen a tsakar gida, kuka ,karaji da kururuwa duk tana yinsu, wannan ya sanya na tsani kai na, bakin cin takaici da damuwa duk suka baibayeni, na amincewa raina na fayyace komai domin samawa iyayena kwanciyar hankali, babu shakka hakan shine zai fi
.
Da wannan tunani na fara kokarin banbare wandona dake rike a hannun wani kato , shi kuwa sai ya kara dakume ni a zatonsa wani salon ne na kara kyautata drama din
"Sakar ni malam" na fada afusace
Ba sakin nawa yayi ba, matse ni yayi iya kacin matsewa gami da yarfa min biyar yana huci, tamkar na rama naji yayin da zogi ya ratsani, to amma sai nayi ta maza na kasance cikin halin daure fuskata hawaye ya zubo min dana kara nazarin halin da mahaifiyata take ciki, ba zan iya kiyasta bakin cikin da take ciki ba na dai tabbata tana tattare da damuwa.
.
"Dauko lambar mu tafi" wani kato ya daka min tsawa, bana bukatar shiga wani waje hannu na tura cikin rumbu na fito da ita, abinda ya sanya yan kato da goran kara tasa keyata, gab da zamu shige soro na kara waiwayowa na dubi mahaifiyata, kafin kuma na tarar da mahaifina a soro, lissafi duk ya dagule , ina ma zuciyata zatayi min alfarma na fayyace komai, sai dai ina ba zata yi min ba, soyayya dake cike da ita ta baibaye ta, wanda hakan ke sauyata gargadi ne cewa farida kubuce min zata yi
******
Ina zaune shiru cikin tariyo abinda ya wakana akauyenmu , a lokacin da su kuma yan kato da goran ke tariyo abubuwan dariya, sai dai atare dani banga abun daya isa ya sanya ni dariya alokacin ba, na rinka tuno halin tashin hankalin dana bar iyayena aciki, na sani izan ba sa'a ba na bar abun da za' aita goranta wa zuri'armu har a nade kasa, wannan itace dabi'ar zaman kauye, barawon Albasa ma akan haana jikansa diya, ballantana kuma ni aka ce barawon motane
Toh ya kukejin littafin (Shuraih Usman)
.
Lateef ya danka masu kudin aikinsu naira dubu biyar, suka watse suna godiya, suka bar mu mu biyu ni dashi,
Ya dubeni "ina fata komai yayi yanda ake so"
Na gyada kai "komai yayi lateef sai dai kuma ina mai jimamin abubuwan da suka faru, ko tantama bana yi iyayena suna cikin bakin ciki"
.
Ya girgiza kai cikin jimami daga bisani ya kara matsowa kusa dani
"Umar na shawarce ka da wani abu mana"
"Wani abu kemar me fa"
Ya sunkuyar da kai "ka gafarce ni bisa abin da zan fada a gani na ka hakura da farida zai fi sauki"
Na kura masa ido kawai a kuma lokaci guda hawaye ya fara gangarowa daga kumatuna nasa hannu na share sannan na mike tsaye
"Lateef da ace zuciyata zata iya jure haka , da tuni na aiwatar da shi, sai dai ina! Ba zayta jure ba tun farkon gani na da farida ta rigaya ta mallake ni, bana aiwatar da komai sai abinda zan faranta ranta, kuma kasan wani abu a halin yanzun ba auren tane abin daya fi damuna ba, burina shine na tsamo ta daga kangin rayuwar data ke ciki, na daura niyya kuma zan cigaba da fafutaka iya raina, ko bani ba farida zata auri wanda ranta ke so, ta dandani dadin rayuwar aure ita da mijinta?" Na sunkuyo kusa da fuskarsa "ka shaida lateef na rantse da Allah na bayar da rayuwata fansa ga murmushin fuskar masoyiyata"(ina masoyan gaskiyan suke)
(Ga ni nan Shuraih Usman
.
Ya jinjina kai gami da kuramin idanu, daga bisani ya ajiye wani ingarman numfashi
"Lallai umar kayi nisa, ba kumaa zaka taba jin kira ba, saidai duk da haka ina da wata shawarar, ka mika rahoton hannun 'yan sanda zasu taimaka wajen zakulo duk abinda ke faruwa"
Na girgiza kai "bazan yi haka ba lateef , irin wannan binciken yana bukatar hanya ko kudi, ni kuwa hanya ta zuwa masallaci kawai, ka sani kudi kuwa bana bukatar cewa da kai komai"
.
Ya mike tsye gami da dafa kafadata "Umar nima bani da kudin amma ina da hanya kuma hanya wadda take da karfi, yaya zaka yi idan nace kanina inspector ne? Da taimakon Allah da jajurcewa ta muka samu yakai matsayin, sa'arda yana karatu ko naira daya ya kashe, nine na bashi ita, to zan taimaka maka zan tuntube shi da batun, kuma zai yi duk abinda ake so batare da ka kashe koda naira daya ba"
.
A wannan lokaci danake cikin tashin hankali abune mai wuya na iya yin murmushi, saidai na jibgewa lateef kundi-kundi na godiya, yayi murmushi 'kar ka damu Allah ne ya hada mu, bamu san irin amfanar juna da zamuyi ba arayuwa"
*****
Ban tsaya yin komai ba in banda wanka , haka na nufi asibiti yunwa na kwakular cikina, tunda na saka kafata a ginin asibitin tunane tunane suke ta tsere a raina, mafi muni shine mai cewa mai yiwu wa farida ta rigamu gidan gaskiya
A inda na bar mummy jiya, yau ma anan na tarar da ita bata canza kaya ba, ban kuma ga alamar tayi wanka ba, canji daya dana iya gani shine yau tafi jiya rama, ta dago kai sa'ar da na tsaya a kanta ba gaisuwa ce agabanmu ba mai jiki na fara tambayarta,
.
Ta kwantar dakai "to ina iya cewa da sauki tunda dai shi ake nema, amma ni tun jiya har yanzu ban ganta ba, kowa na tuntuba sai yace na dai saurara wai ana cigaba da kokari , umar ina zaton ma mutuwa tayi suke boye mun"
Hawaye ya zubo a fuskata, shiru nayi cikin rashin sanin me zance da alama fitar da rai da farida ne, ya mantar da mummy tambayata yanda na karke da iyayena, to ana ta kai waya ke ta kaya?.
.
Jama'a sai fa kunyi hakuri kwana biyunnan don ina busy sosai, amma zan ringa kokari koda short ne ina kawo maku
.
Sannan ina taya Abokina Yarima A. Gangariya murna , domin kuwa iyalinsa ta haifa masa da namiji, Allah ya rayashi, ya sa mahaddacin Alqur'ani ne,
Ameen
.
Nidinne dai Shuraih Usman
Daga:- www.facebook.com/hausaebooksTARAR ARADU
Littafi na Uku 3
Umar lawan Abdul
Typing Shuraih Usman
Page 5
.
.
Muna nan tsugunne cikin jimami, wata nurse tazo tayi mana sallama, sannan taci gaba" hajiya an fito da yarki daga dakin na'urori an bata daki mai lamba sha hudu, zo muje ki gani"?
.
Muka mike gaba daya babu wani alamun karfi a jikina tamkar wanda aka wuni laftar masa jiki,
Mummy ta dubi nurse din "a wanne hali take yanzu?"
"Eh to mu karasa din ina ga ana iya cewa da sauki tunda tana iya yin numfashi sama sama"
Tsoro ya kara cika zuciyata, a wannan hali muka isa dakin tsa hannu ta tura kofar ta shiga sannan muka bita abaya,
Kwance tage rigingine idan baka kura ido ba bazaka ga alamun numfashinta ba, tamkar wata gunki ce ko zane
Na girgiza kai cikin tausayawa a kuma lokacin da zubar hawayena ke daduwa
Mummy kuwa tagumi tayi da alama ta gama fidda rai hawaye a fuskarta wani na bin wani
.
Nurse din ta dafa kafaddarta "ki kwantar da hankalinki hajiya me yiwuwa nan da awa biyu zata iya wartsakewa, damuwa ce tayi mata yawa kdan ya rage jininta ya hau, amma Allah ya kiyaye, wata kila gobe iwar haka ma ta iya takawa da kafafunta"
.
Daga ni har mummy babu wanda zancen ya shiga akwai shakku cikin tashin farida a irin wannan dan kankanin lokaci, tana iya yiwuwa tunda su jami'an lafiya ne, suna da sani akanta, tana kuma iya kin yiwuwa jawabin nata ya kare ne a matsayin wani salon kwantar da hankali
Muna nan zaune cikin halin zama mai kama da makoki ga wadanda radadin mutuwar ke cinsu, sai kofa ta bude wani ne dan siriri dogo da ganinsa kasan kwararren likita ne,biye da shi akwai wasu nurse guda biyu
.
Ya dubemu "ku dan bamu dama, zamu dan bata wani taimako'
Muka mike a tsaye tare batare da bata lokaci ba muka nufi waje
Na duba agogona karfe goman dare na juya ga mummy" zan je na dawo in Allah ya yarda nan da minti talatin
Ta gyada kai "to shikenan"
*****
Na san makulli na bude dakina batare da bata lokaci ba nasa kafa ciki ba komai ne ya maido ni illa na kwashe yan tsirarun kudadena da suka rage, aniya ta shine siyawa mummy abinci da su, bayan dana kula cewa itama bata ci komai ba, sai dai ba anan gizo ke sakar ba ko na kai mata ma ba lallai ba ne taci
.
Bayan dana debe sune na fara kokarin ficewa a daidai lokacin ne wata kara ta gauraye ko ina na,cike da mamakin abunda ke iya yin wannan kara, shakka babu agogon bangona bashi da alarm , ban kuma mallaki wani abu mai alarm ba
.
Shawarar dana fara yankewa itace nayi ficewata , amma sai karar taci gaba abinda yasan ya ni canza shawara , na fara yan dube dube domin gano daga inda karar ke fitowa, bayan dan lokaci na fahimci wajen akan katiata ne sai na nufi can ina mai kwadayin ganin ko me ne ne, mamaki ya kama ni yayin da na yi arba da mai yin, na'urar sadarwa ce ta hannu, ni dai ban mallaketa ba kuma baki nake yi ba ballantana nayi zaton wani ne ya manta ta,
Na kasance cikin shawarwarin abunda ya kamata nayi wata zuciyar tace tsallake ka fita,wata kuma tace dauki ka saurari kiran daga nan ma sai ka san ko ta wace
.
Nayi kasadar durkusawa na dauka kirar samsung ce mai kyawun gani, har yanzu bata daina callara kara ba, cikin ganganci da karambani na danna O.K ban bata lokaci ba wajen karata a kunne na
"Hello wane ne"
Aka amsa a daya bangaren "Mala'ikan mutuwane"
Error page error page error page
An samu matsalar fallayen littafin anan amma ga abuinda ya kunsa
.
"Hello wane ne"
Aka amsa a daya bangaren "mala'ikan mutuwane"
Gabana ya buga, hankalina ya tashi sakamakon muryar danaji, ba kokonto tabbas na shaida wannan murya, ba muryan kowa bane illa na mugun mutumin nan daya jefa rayuwata cikin tashin hankali
Mutumin ya cigaba da fadin "kai yaro ka tsorata ne , to gwamma ma ka saduda don kuwa mun riga da mun gama wasan da mukeyi da kai, don haka yau zaka bakunci kiyama dafatan kayi aiki mai kyau, sannan ina shaida maka gwamma kayi zamanka a cikin dakinka domin kuwa anan muka zaba zamu kasheka, amma in kaso kana iya tafiya duk inda zaka, mu kuma zamu bika mu kamoka sannan mu dawo dakai har dakin naka sannan mu hallakak..."
.
Ban tsaya ya karasa maganar ba na datse kiran ta hanyar kashe wayar, sannan nayi cilli da ita ta gwaru da bagon dakina
.
Gabana sai faduwa yake , na fito daga cikin dakin na kulle sannan na nufi hanyar asibiti ,
Ina tafiya ne kawai amma hankalina bashi a jikina, tunane tunane kala kala babu wanda banyi ba acikin zuciyata,
Domin kuwa nasan wannan mutumi bashi da imani kuma baya da tausayi tabbas zai iya aikata abunda ya furta
.
Ina cikin tafiya ko lura da gabana banayi, kwatsam sai ji nayi wani abu ya dake ni akai zan yi ihu amma naji wata basamudiyar hannu tayi caraf ta rufe mani baki,
Koda na lura sai naga wani katon mutum ne ya rungume ni ta baya ya kuma sakayo da hannunsa ya rufe min baki, ina ta wutsil da kafafuwana domin na kwaci kaina daga hannunsa amma yafi karfina, babu irin kokarin da banyi ba , haka wannan mutumin ya dauko wata hankici daga aljihunsa ya sanya a hancina, wani daddan kamshi na sheka daga nan ban san me ya faru dani ba
******
Farkawa nayi a gigice sakamakon ruwan sanyin daya sauka a fuskana, cikin firgici na bude idanuna, ba karamin razana da kidima nayi ba sakamakon yanda na tsinci kaina,
.
Igiyane mai kauri daure a wuyana igiyar an jashi yaje sama aka daurashi a jikin fankan dakina,
Hannuna suma a zagaya da su ta bayana sannan suma aka dauresu tamau
kafafuwana kuwa suna saman wani dan karamin kujera wanda da ba don shiba toh na tabbata da yanzu ina kiyama,
.
Hahhahahahahahah, sautin dariya naji acikin dakin nan idona yakai wajen da nake jin dariya take idona yai arba da wasu girda girdan karti su Uku, dukkansu suna sanye ne da bakaken kaya, jaket, da kuma jeans,
Na tsakiyarsu ya zo gabana "malam umar sai defa kayi hakuri don kuwa yau zan aikaka kiyama