Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 3
bayan nacire takalmi. Tuni tagama shiryawa tana daure gashin kanta ne da ribbon. Na kalli dressing din nata na doguwar riga mai hade da wandonta,da kuma gyaran mayafi. Hakika sun yimata kyauw Ni kaina sai na tabbatar da cewa farida tafi karfina. Sai kuma na sami zuciyata tana mai rayamin cewa afasa tafiyar kar naje wani ya ganta ya kwacemin ita. Maganarta ta katsemin tunanina "Muje ko umar" Nafito yayin data biyoni. Mahaifiyarta ta kallemu ta jinjina kai gami da cewa "You match each other" Cikin wani harshen dabashi da banbanci dana turawa , nida farida muka kalli juna gami da musayar murmushi. Bisa gaskiya . Gasikaya ne abinda tafada ta dubemu "Kuna da camara ko" Na girgiza kai "Bamu da camara" "Tafiyar taku bata cika ba, a london duk duk inda zamuje da Alhaji da camera muke tafiya haka kuma zaka rinka gani ga duk saurayii da budurwa" Ta mike tsaye "Bari dauko muku tawa" Ta shiga daki bada jimawa ba ta fito. Yar karamar camara ce mai ban sha'awa, ta bude kwalin film ta loda, sannan ta dubemu "Kuzo nafarayi muku kala daya" Muka jeru nida farida muna jiran muga ta dauka, maimakon haka sai ta kama dariya, tafara magana "Karfa nace muku kauyawa, ahaka za'ayi hoton? To ma'anar me yabayar? Kubari kuga yanda za'ayi" Ta nuna mana wata fulawa dake tsakiyar gidan "Ku koma can, kusa fulawar a tsakiya" Muka kamar yadda tafada. Sannan tace "To kai umar tsinki fure ka mika mata ke kuma miko hannu ki karba, ku kumayiwa juna murmushi" Mukayi kamar yadda tafada , sannan hoton, Kyamarar taja film automatically. Ta mikomin kyamarar "To kunga yadda ake hoton soyayya , idan anyi aure kuma akwai wani salon daban,dasannu zan nuna muku shi duk randa aka daura maku aure" Nayi dariya "Mungode mummy" Surukartawa tana burgeni, yadda take bidani ta hanyoyi na musamman babu abin da yadameta tamkar ba suruka ba. "To zamu tafi mummy" Farida tace daita "To adawo lafya" Gab da zamu shiga soro tafara magana " Ina kara tunatar dakufa" Muka waiwayo domin jin abidna zata fada , tayi murmushi " Kun dace da juna " Muka kalli juna nida farida mukayi musayan murmushi. Sannan muka juya gareta gaba daya. Akuma lokaci guda muka hada baki " Thank you mummy" ******** ********** ******** Na bude shagona bayan dana dawo daga koyarwa . Bayan na ajiye takardu sainafara tunanin yin wanka. Na dubi ruwan wankan wanda ni kawai yake jira na watsashi, adai dai lokacinne aka turo kofar cikin gidar "Umar ana waya" Inji matar yayana na dubeta "Wanene yake waya? Ko baba ne?" Ta juya hannu " Ba baba bane yadaice kai yake son yagani" Na jawop kofar shagopn na bita ciki, ina zuwa na dauka na kara akunne "Hello! Wake magana?" "Ina ruwanka koma waye? Kadai kasa kunne da kyau kaji abinda za'afada" "Ina jinka" Nace dashi yacigaba "Karabu da farida tun kafin karasa ranka,karabu da ita tun kafin ta zamto maka cowon ajali" Na gwale ido saboda tsoro , akuma lokaciguda dana fara tambayarsa cikin rawar murya . "Saboda me" Yadaka min tsawa , duk da awayane saida cikina tai kuka "Karabu da ita muddin kai kanason rayuwarka ,inkuma duniya ta isheka sai kafada "Wai me isa" Nakara tambayarsa "Farida bazatayi aure ba har abada" Lafazinnasa yabata min rai bansan sa'an danace "Kar ya kake ba" Ya barke da dariya wadda saida na kauda kan wayar yaci gaba. "Dan samari da karambani kake inakai ina karyata abin da'aka ba ka labarinsa" "Karya kake" Nasake fadi "Farida zatayio aure kuma ni zata aura" " Shikenan babu mamaki amma dai ba'awannan duniyar ba" Na fusata "Kai makaryaci awannan duniyar kuwa" Yasake dakamin tsawa "To shikenan tun da zaka iya TARAR ARADU DAKA .naga kai mai musune, zamuyi wasa dakai yanda akeyi da dan biri,sannan a karramaka kamar yadda ake karrama kudi" Kafin nasake magana ya ajiye kan wayar. Na dawo shago duk jikina a mace . Babu mutumin nanne da farida tabani labari. Inkuwa hakane hakika ina kan hadari. Sai na kudure azuciyata bazan bawa farida labari ba. Domin hakan zai iya tashin hankalinta harta fara hangen kin yiwuwar aurenmu. Ni kuwa bazanso hakaba. Sannan kuma na kudiri aniyar bazan shaidawa yayana ba. Domin kuwa shaidamasa kamar cinna ma takardar alkawarinmu aurenmu da farida wutane, Domin babu makawa zai rabani da'ita Nikuwa ahalin yuanzu duka biyun sakamako daya zasu bayar, tamkar shida atara da uku ne,da kuma uku atara dashida,kowanne tara kenan To hakama in har kaunar farida zata jamin mutuwa to hakama barinta zaijamin. Domin ahalin yanzu inna rasata ma zuciyata na iya bugawa to kaga da wuya ya kasheka gara dadi ya kasheka to waima da yake cewa zai yi wasa dani..... @mr:-Shuraih 99% Zan cigabaTARAR ARADU Littafina daya (1) Written:- shuraih 99% Page 7 Domin ahalin yanzu inna rasata ma zuciyata na iya bugawa to kaga da wuya ya kasheka gara dadi ya kasheka to waima da yake cewa zai yi wasa dani kamar dani biri yana gani mutane zasu bari a dauramin igiyya a kuguna arinka ja a kasuwa ne? Ashe makenan dubunsa ta cika . $sai najini ina mai murna da wannan matakin dayace zai dauka , To amma karramani dayace zai yifa yadda ake karrama kudi. Nadade ina tunani daga bisani nagane babu wani karamci da kudi suke samu fiye da kashe su, To kasheni za'ayi kenan kwarai kuwa babu tantama kasheni zaiyi kamar yadda ya kashe uku abaya, To amma wannan bai dameni ba dukwanda ya mutu kwanansa ne ya kare. ********* ********** ******** Na dubi farida bayan dana lume acikin kujera "Allah yakaimu ranara daza mukasance kamar haka acikin daki daya a matsayin miji da mata" Tayi murmushi " Amin umar Allah yakarbi addu'arka har yanzu banji kana maganar daurin aureba" Nakai idona gareta "Akwai dalili farida shiyasa kikaga banyi magana ba" Ta maido hankalinta gareni "Wane dalili" "So nake nagama hada lefe" Tarike baki "Wani irin lefe kuma umar" Nakalleta lefe kala nawa kika sani? Aiduk inda kikaji ance lefe akasar hausa ana nufin kayan da mai nemar aure zai kaiwa wadda yake nema" Ta karkada yatsa " Sam karma ka soma don kokayima bana so mummy ma bazata karbaba. Sadaki kawai zaka kawao shima bamai yawa ba" Nayi dariya "Farida arayuwar da akeyi irin na yau duk masoyi yakan nuna kaunar dayake yine ta hanyoyi irinsu lefe. Bawai ina nufin wajibi bane kokuma abin dayake makale da shari'a A'a saidai inda hali akwai bukatar kayi lefe mai yawa domin toshe bakin masu kushewa. Saboda an riga anbata lamarin aure " Tayi tsaki "To kai ina ruwanka da masu kushe kabi hadisi mana daya kecewa mafi albarkacin mace mafi karancin sadakinta" Najin jina kai "Babu shakka farida hakane ni kaina na kanki abubuwa na bidi'a To amma tunda wannan baisabawa shari'a ba nayi aniyar yi miki lefe na ban mamaki. Domin kaucewa wasu kananun maganganu, kisani yanzu duniya ta zuba ido akanki , idan muka yi aure babu lefe , maganar daza ta yi ta yawo shine neman kai ake daka shiyasa ko lefe ban yimiki ba. Ni kuma inaso innuna ma duniya cewa kaunar ki nake jini da tsoka don babbar abinda natsana bai wuci ace ba auren soyayya mukayi ba" Ta bata rai "Tokai ina ruwanka afadi duka abinda za'afadi magana zata warwaremana aurene" "Jini farida na rantse da Allah indai ina da iko sai nayi miki akwati biyar" Ta mike tsaye "Kasan kuwa abin da kake fada? Ni yar gidan wata shugaban kasace daza'a yimin akwati biyar" Nayi murmushi "Kinfi yargidan ko wane shugaban kasa a wurina babu kamar ki aduniya. Farida ki shaida ina yimiki kaunar dazan iya bada sadaki da raina" Ta girgiza kai "Gaskiya umar banyadda kayimin akwati biyar ba" Na mike tsaye "Bakin Alkalami yabushe farida " ******* ********* ********* Na zage rubutu da cak , yaran anaji shida sun nutsu, Inajin dadin yadda yara ke bani hankalinsu izan ina bada assignment. Najuyo na dubesu adaidai lokacin dana kare rubutu. Ian shirin fara bayaninewani yaro ya durkusa agabana. "Sir principle yana magana" Nayio mamakoin abinda zai sa principle kirana awannan lokaci. Hakika yakan kiarani fiye da kowani malami wani loakcin kira mai ma'ana wani lokacin kuma hayaniya kawai. Na ratsa yara kai tsaye kuma na nufi kofa . "Gani yallabai" Nafada aloakcin danake kokarrinn zama akan kujera hannuna furtutu da garin cak. Yadago daga barin rubutun dayake ,ina iya hango idanunsa kadan kadan ta cikin bakin gilashin daya makala. Fuskarsa kuma ta nunamincewa yana so ya gabatar da wani bayani dayake dauke dashi muhimmi " Wato umar nakirakane saboda wata matsala data dade tana faruwa nasha ji da kunnena kuma andade ana kawo min kara, wani irin turancine kake koyar dayara abin ko ka'ida babu? Ya zakarinka koyar dayara turanci broka , ko anfada maka nan kasuwar sabon garice? Gaskiya bazai yiwu mu tafi dakaiba mai cigaba muke nema bawai mai kawo ci baya ba. Saboda haka daga yanzu.........." Yayi shiru baiyi magana ba na cika da mamaki wainine nake koyarda turanci broka . Wannan zacene mara tushe shi kansa pricinple din baikaini iya yturanci ba. Nakan fitar da kalma bayan kalma yadda kasan baturen gaske Wanda hakan yasa ake min lakabi da toni blayer. Amma duk gashi ana kokarin kiransa a matsayin broka. Na dubi principle "Yallabai wayanda suka kawo maka koken sun gabatar maka da shidace" Yadaka min tsawa " Wata shaida tunda nima naji da kunnena" Ya watsomin takardu "Tuni mun rika mun mika matalarka a ma'aikatan ilimi kuma sun bamu madadinka, kana iya hangowa ta window gashi can atsaye" Nawai waya domin ganin wanda ake kira madadina wani mutum ne mai yawan suma da gashin baki. Najuwo ga principle fuskata cike da alamun karaya......... ... TOFA UMAR YaFARA SHIGA @mr:- Shuraih 99% To be con......... Keep followin..... TARAR ARADU Littafina daya (1) Written:- shuraih 99% Page 8 Fuskata cike da alamun karaya "Don Allah yallabai ka taimakeni" "To wane tai mako kuma zanyi ma? Kai dana fadamak maganar har taje ma'aikatar ilmi. Katashi kawai kabani waje kaine kajawo wakanka" Nayi tsawon minti biyu awajen banko motsa ba. Daga bisani sai na tattara takarduna na dube shi "To shikenan yallabai Allah ya taimaka" Bai amasa maganar tawaba na fito daga ofis din cike da mamakin wannan lamari. $hakika zancene mara tushe ballantana makama. Kuma lallai anzalunceni ayanda aiki yake wuya. Ballantana kuma a wannan lokaci danake kokarin mallakar masoyiyata farida. Hawaye yazubo min daga idona lokacin danake kokarin barin ginin ofis din. Ahaka nanufi wajen babur dina saidai na yanke shawarar na tura shi waje tukuna. Domin tashinsa anan ciki zai iya juyo da hankalin kowa nikuma banaso aga tafiyata. Nafara turawa ahankali "Mallam umar ina zuwa hakane" Tambayar mai gadi lokacin danake kokarin fita" " zanje nagabatar dawani uzurine" "To adawo lafiya" Ya maido amsa naci gaba da turawa , saida nayi nisa da ginin makarantar sannan na tasheshi. Nahau zuciyata na mai matukar tafarfasa saboda wannan al'amari ahaka na karasa gida cikin rashin kuzari. ********* ********** ********** Nan fa aiyuka suka yimin yawa kullum inafama da matsaloli guda biyu Neman aiki da kuma zaman banza. Aduk sanda nake zaune nakan debe kewa da littatafan hausa na(umar lawan) Kamar su LINZAMiN DAN ADAM' BABBAR MADAFA SaURA KiRIS Kai dama wasu masu dama. Kwanaki suka cigaba da karfa karfa. Akalla ko wacce ta maimaita sau takwas. Wato wata biyu kenan. Amma har yanzu banga wata alama dazata bani karfin guiwa akan samun aiki ba. Na ziyarci kanfaninuwa da ma'aikatu amma shiru kake ji Kai kace wani arnen dajine yaje neman aiki da takaradan tsire . Tuni yan kudaden dake hannuna sun tafi karaye. Wannan ya tilasta min canja salo. Idan wajen dazanje ba mummuman nisane dashi ba nakan daba sayyada. Badon kamai ba sai don tsadar man fetur . Wanda kudin rabin galan sun isheni sati uku ina gwaguya. Da lamari yakai yakawo sai nadaina zuwa ko'ina, Daga gida sai gidansu farida. Ahalin yanzu ina gindin babur dina ba ko'ina zani ba sai gidansu farida. Na tashi babur din bayan dana sha fama. Nahau na nufi goron dutse. Bada jimawaba na'isa gidan Tun kafin na sauka farida tafito domin tarata. Muka rankaya cikin gida . Muka gaisa da babarmu wadda ayanzu sai ka rantse ni ta haifa ba farida ba. Muka zarce falon shakatawa na zabi kujera daya na zauna. Farida ta zauna akan hannun kujerar idanuwanta kyar akaina . Kullum nazo haka take taraiyarayata takasa tsaye takasa zaune. Itace ta zauna ahaguna, Ta dawo dama ta tsaya akaina , ta zauna agabana kaidai abubuwa da bam- da bam nikaina nasan farida tana kaunata irin kaunar da bantaba zaton zata yiminba ta dubeni bayan data ajiye min tataccen lemo "Umar dan Allah ina roko agareka" Na kalleta bayan dana zuki ruwan lemon "Inajinki" Taci gaba "Kaje ka kawo sadaki sai adaura mana aure izan ma baka da kudi bari na baka" Na kalleta a firgice "Farida bari ma wannan zance ni da yanzu bana aiki yaya za'ai nayi maganar aure? Dame zan rikeki farida" Tayi dariya "Kaji ka da wani zance to menene amfanin albashina? Albashina ya ishemu Wajan zama kuwa dama basai nafada ba, mummy ta koma sama sai ta barmana nan kasa idan kuma bakason zama da'ita sai nakama mana haya.$ To me kuma yarage? Ballantana kasan mummy ba'irin sauran mata bane. Kaima kagani dakanka " Nagirgiza kai "Duk naji jawabinki amma ban karbi rokonkiba. Ki kuma tuna nayi miki alkawarin akwati biyar kuma bazan saba ba " Ta dakatar dani "Bari wannan zancen umar aicewa kayi idan kana da hali. Kuma baka dashi yanzu kaga ba saba alkawri kayiba" Nayi dariya "Ai halin danake nufi farida shine rai da lafiya , ahalin yanzu ban rasa ko dayaba" Ta daure fuska " Nidai inhar nizakayiwa to banaso, mummy ma kuma bazata karbaba " Nayi dariya "To mummy din taki ce ke kadai" Ta kalleni "Naji batawabace nikadai ba kuma bari ganin kafini gata agunta dakayi magana sai tace haka za'ayi bama ta sauraron zancena, to wallahi akan wannan bazata goyama bayaba. Kawai saita goyi bayanka akan abin dzaka takura? To akan wannan kam gakucan da mummy arana" Na mike tsaye "To zaki gani nasan yadda zanyi na shawo kanta" Itama ta tashi "Barima zato bazata taba yarda ba" ****** ************ ******* Zama yayi zama tuni kudaden hannuna sun gama karewa . Wannan ya tilastamin saida akwalar baburdina. Na turashi inda akeyimin gyara nace asanyamasa ganye. Haka kuwa akayi. To ashe aiki aka samamin bansani ba Saida nashafe wata guda cur harda kwana shida amma kullum naje sai yace ba'azo an tayaba dana lura sai naga nima in naje har nadawo ko kuda ban taba gani ya sauka akai ba . TOFA GA BABUR INA MAI SAYA SAIYA TUNTUBENI @mr:- shuraih 99%TARAR ARADU Littafina daya (1) Written:- shuraih 99% Page 9 Saida nashafe wata guda cur harda kwana shida amma kullum naje sai yace ba'azo an tayaba dana lura sai naga nima in naje har nadawo ko kuda ban taba gani ya sauka akai ba . Wannan ya sanyani yake shawarar na bari sai sati-sati narika zuwa. Ina nan ahaka atsakiyar sati nabiyu wanda har nafara cin bashi saiga wani yaro har gida "Wai kazo anzo sayen baburrinka" Nan danan na zari takalma . Don tsabar sauri kamar na tsahi sama. Duk da cewa yaron da gudu ya koma amma duk kusan tare muka isa. Wani dattijone rigarsa duk dauda yayi furtutu dashi. Da gani sana'arsa bazata wuce saida harawar dabbobi ba na sunkuya na gaidashi "Kaine me wannan babur din" " Nine baba " Na amsa masa "To nasaya naira dubu uku" Kaina yasara jin kudin tamakar za'asiyi mataccen keke "Haba baba kadai fadi gaskiyar abinda kasaya" Ya kalleni "Kai yaro dattijo kamata baya ciniki da tayi inka sayar to inbaka sayar ba nakara gaba" "Kadai kara baba" Nasake cewa dashi, sai kawai yakada kai yatafi hakika ba zai kara ba. Na tuna da dadewar baburdin awajen kotayawa ba'ayi ba. Kuma lallai innabari dattijonnan yatafi balallaine asiyaba, sai kawai nabishi dagudu ina cewa "Dakata baba" Baiko saurareni ba ganinhaka yasanyani shan gabansa "Ansiyar maka baba" Ya kalleni fuska a turbune yacoi gaba da tafiyarsa, Nan nashiga hadashi Allah da annabi da kyar na samu yadawo yabiya . Na baiwa mai gyaran dari uku yaron daya kirani kuwa naira hamsin. Sauran kudin nayi aniyar in na biya bashi sai in ajiye in rika gutsura ahankali. ***** ************ ******** Nayi tagumi sakamakon wannan tsaka mai wuya dana shiga al'amarine da banga alamun karewarsaba "Salamu alaikum" Akafada daga kofar shagon muryar yaya nane. Na amsa gami da kokarin mikewa ,sai gashi yashigo. Nayi masa sannu dazuwa da kuma barka da yamma . Yasami kujera yazauna "Umar nasamo maka aiki awajen wani mutum akasuwarmu" Sai naji tamkar natsahi narungumeshi tsabar farin ciki, nafara jero godiya kala da bam da bam "Ya'isa ya'isa" Yace dani sa'arda yake dagamin hannu "Tsaya kaji yadda al'amarin yake" "To yaya" Nafada sa'arda na kara matsowa . "Kasaida hankalinka sosai ayaransa na yanzu babu wani cikakken mai ilmi. Shi kuma burinsa akullum yasamu wanda zai taimakamasa wajen harkar oda. To ammam shiru kakeji, duk wanda yasamo daya fara sai cin amana ya biyo baya. Saboda haka inhar kai gaskiya ka gama warkewa" Bakina har kunne saboda tsabar farin ciki Na cigaba da godiya shi kuma yatashi yafita. Na daka wani tsalle nafada kan katifa. Waini umar nine zan zama dan kasuwar kwari. Dama gani dason birni. Kawai sai nafara mafarkin zaune Wai ganinan nasha boyel zan hau mota kawai sai sailulata tayi kara. $dana fiddo sai naji ashe farida ce kecewa "Mai gida kayo sauri kazo muatafi yawon shakatawar" Sai nace "To ganinan zuwa " Kawai sai nabude motata na shiga kai naitayin shirme kala kala tun kafinma naje naga kasuwar. Da dare banyi wani barcin kirki ba saboda tsabar doki. Sau uku ina murda hannun agogona ina kara awa guda guda wai don saboda gari yayi maza ya waye. Sai na tuna ashe saurin ba'a agogo bane. Ahaka na hakura saidai naita duba loakci. Akalla dai naduba sau saba'in ahaka akayi assalatu da mukaje masallaci muka dawo sai kawai nashiga wanka . Alhali yayan nawa sai karfe goma yake fita Akalla dai jiran awa hudu nayi Da lokaci yayai muka fita . Rumfar da mukaje katotuwace dabana zaton tana dana biyu. Rumfar kawai dazata fita sai dai na Alhaji saminu da umar lawan yabada labarinta acikin littafinsa "SAURA KIRIS" Mutum biyune aciki kuma duk matasa ne kamarni yayana ya tambayesu Alhaji sukace karfe uku yake fitowa Wannan yasanya ni faduwar gaba "Ai munyi dashi nazo dashi da safe" Yayana yace daso "Ok kudanyi jiransa" Wani acikin yaran yafada Anan muka samu benci muka zauna Nayi taraba idanu ina kallon masu wucewa. Aciki na hango wani mutum yana tafe ana faduwa ana gaisheshi. Farine dogo mai dan kauri. Badomin nasan mai martaba sarkin kano ba to da sai nace shine wannan . To ammma ko babu komai wannan bai kai mai martaba sarkin kano farin jini ba. Amma shima yana dade daidai nasa. Sai naga yana matsowa garemu "Ga shinan" Yayana yafada sai muka mike tsaye domin karramashi. Daya iso sai nayi kamar yadda naga yayana yayi wato muka durkusa har kasa muka gaidashi, "Yaya sunanka dana" Alhaji ya tambaya , na sunkuyar dakaina yayin danake cewa "sunana umar" "Allah sarki" Yace dani "Sunan naka da dadi" Ya hadani dana cikin kantinan yace sununamin abinda zanyi. Aranar wuni nayi ina mimmiko kayayyaki. Da akatashi aka bani dari biyu na hau mota sallama kuma akace sai sati sati. ********** ********** ******** Ahankali kwanaki suka cigaba da zukewa irin zukar da takarda ke yiwa ruwan biro. TO FA ABI YAFARA KYAU GA UMAR KUTAYASHI MURNA SAIDAI BANSAN KO NAN GABA BA @mr shuraih 99% .zan ci gabaTARAR ARADU Littafina daya (1) Written:- shuraih 99% Page 10 ********** ********** ******** Ahankali kwanaki suka cigaba da zukewa irin zukar da takarda ke yiwa ruwan biro. Ahaka nafara kirga makonni Ko kusa bazaka hada samuna na kasuwa dana makaranta ba.$ Bada dadewaba nafara haskaka kantin. Sakamakon iya mu'amala da jama'a da kuma ilimina hatta kantinan makota idan akayi bakon bature ni suke zuwa su kira. Wannan si yasa akafara yimin lakabi da bakin bature. Na shiga ran alhaji matuka sai yafara aikena wurare dabam dabam sai ya zamto kullum da alhaji yafito toni nagama zama . Jeka nan tafi can kai wannan karbo wancan, kai dade sauransu. Amma duk samunnan danake yi dinki daya kawai nayi. Sauran kudadena kuwa nakan kashesune aharakan hada lefena. Wannan yasanya watarana daya daga cikin abokan aikina yake tambayata "Wai kai umar mai kake da kudine?'Ullum kana samu amma ba'agani jikinka" Nayi dariya "Jamil kenan kowanne mutum kasan yanada manufa, abin dayasa kake ganin halka bawai kwalliya kuka fini son yiba. Bukatun kudi danakedasu shiyasa kukaga ina tattalawa" Yarike baki "Kai kuwa wani irin bukatune wayannan dahar sai ka takura kanaka zaka biya? Nagafa ko aure baka dashi" Nakalleshi "To mai aurene kawai yake da manyan bukatu?ka tsaya idan lokaci yayi zaka gni" Dai dai wannan lokaci alhaji yashigo ,wata kyakkaywar sailulace ahannunsa. Ni dai tunda nake bantaba ganin kan waya mai kyawun na Alhaji ba. Wannan yasanya akullum alhaji yana waya nakan bishoi da ido har yagane yanda nake nuna sha'awata da kan wayar wannan yasanya shi yimin karin bayani akan muhimmancin kan wayar. Ya kuma shaidamin naira dubu dari biyu yasiya nayi matukar mamaki da jin haka . Dubu dari biyu ai kudin kyakkyawar motane . Da alhaji yazo ya tsaya akusa damu Sai naji ashe suna tattaunawa ne da wani mutum mai harkar setlit.zance da akeyima zai kawo setlit ne guda biyar. Kuma duk za a sanyasune a sabon gidan da alhaji yake ginawa. Ni alahaji har mamaki yake bani komai nasa sai ya burgeka.to amma mai zaiyi da wannan sabon gidan alhali ko haihuwa bai taba yiba. Hirar tasu takare akan cewa za'a aikomasa da kudin gobe da rana. (Umar harka fara bani tausayi) Shuraih 99% ********** ************* ******** Ina cikin cin abin ci alhaji yakirani sai yamiko min key din motarsa "Je ka kabude but akwai wata jaka kadaukomin" Nakarfa na tafi da gaggawa Ina dauko jakan saina gane kudine aciki babu tantama sai na baiwa alhaji zan tafi ya tsaidani Ada nayi zaton zasukai miliyan daya ashe dubu dari da hamsinne bako maine yajawo hakan ba sai kasancewarsu yan wazobiya Ya dubeni "Kaga kudinnan kakai wa malam abba mai dishi su" Anan IBB malam abba yake amma naira dari biyu akabani kudin mashin. Nafito na tsaya abakin titi shiru babu wani dan acaba mara fasinja . Wannan yasa na yanke shawarar nafara tattakawa akafa har zuwa loakcin da zansamu dan acaba. Nayi tafiya mai dan nisa . Kawai sainaji anyayimeni nayi sama bansan komaeneneba. Saidai na jini acan gefe guda nayi kokarin namike amma ina juwa ta daukeni dole nakoma na zauna . Sai bayan yan dakiku nayi kiliya .saboda haka na lalubi jakata Amma babu ita kuma babu dalilinta . Tashin hankali shin wai meyafaru danine Bandai san takamaiman abinda ya yayimeniba. Kuma gashi babu mutane a eriyar wajan Na duba jikina babu inda naji ko da kwarzane toni yanzu yazan saka kaina zuwa zanyi wajen alhaji ko kuwa karasawa zanyi inda aka aikeni? Duk biyun dai kusan ma'anarsu daya kusan duk inda naje dai bani da abin fada. Wannan yasa na share waje kawai na zauna (da yafimaka umar lolx shuraih 99%) Ina wajen la'asar tayi.nahada kai da gwuiwa na rasa me yake min dadi. Kawai sanaji ana tabani. Dana daga kai sainaga ashe jamil ne. "Lafiya kazo nan kazauna" Na maida kaina batare dana bashi amasa ba "To kazo alhaji yana kira" Da kamar bazani ba sai wata zuciyarta ce jeka. Na bishi muka rankay zuwa kasuwa. Alahaji ya dubeni "Ya akayine umar nayi waya ance baka kai kudinba" Na sunkuyar da kaina kasa cikin rashin sanin abinda yakamata nafada "Ina kudin suke" Sai naji bakina suna fadin "Sun bata" "Kamar yaya sun bata?" Yatambaya cikin mamaki. Ni kaina nasan bakina yayi gidadanci daya bada wannan amsar. Na bayyana masa duk abinda nasani. Ya dade yana kallona daga bisani ya mike tsaye game da faidn "Allah ya kyauta" ******* ************ ******** Nacigaba da zama akasuwa cikin rashin jin dadi dominkuwa ina fuskantar wani irin kallo daga abokan aikina . Alhaji ma kuma ya canza taku . Ahalin yanzu baya aikena nakai kudi ko kuma na karbo ,nasan bakomai bane ya jawo hakan ba illa bacewar jakar kudi. Wannan yasanya akullum takaicin duniya na damuna . To amma yana iya abin sai hakuri . Bayan dana karya kumallo sai najawo wata bakar jaketna na dora sakamakon sanyi da akatashi da shi. Sai kawai na nufi kasuwa muka ci gaba da hulda kamar yadda muka saba ........ WATA AZAL DIN KUMA Keep following Its shuraih 99% Zan ci gabaTARAR ARADU Littafina daya (1) Written:- shuraih 99% Page 11 Bayan dana karya kumallo sai najawo wata bakar jaketna na dora sakamakon sanyi da akatashi da shi. Sai kawai na nufi kasuwa muka ci gaba da hulda kamar yadda muka saba ........ Da rana ta raba sai kuma zafi ya kori sanyi, Wannan yasanya kowa cire rigar daya kara . Muka rarrataye. Da alamun yau alhaji agajiye yake ,domin kuwa tunda yazo ya dare kujera yake ta gyangyadi abinsa. Sailularsa kashe alarm din yayi domin kar adameshi. Kawai ya dorata ahannun kujera . Bai farkaba sai bayan la'asar shima sai da muka yo sallah sannan na tasheshi Yayi mika da hamma sannan yafara lalube-lalube ba musan kome yake nema ba sai bayan daya rasa sannan ya dubemu "Wai ina sailulata take?" "Ina kuka sanya min sailulata" Duk muka yi shiru,kawai sai muka fara rantse-rantse kowa yana fadin bai gantaba.alhaji yafara salati "Da batan sailular nan gwara batan kudin da'aka sayeta,manya manyan abokan mu'amalata ta taurai suna tuntubatane ta wannan layin,akwai kuma nombobi da dama wanda a sailular kawai na shigar dasu,ciki kuwa harda wani mutumin danakeso na tuntuba in anjima don Allah duk wanda yasan inda take yafada zan bashi dubu hamsin" Babu wanda yayi magana acikinmu. Ahaka alahaji yafita akaba da cigiyar sailular duk kasuwa.amma shiru kakeji. Duk yanda akayi de wanine ya lababo ya saceta. Bayan alhaji yadawo daga sallah sai ya zauna akan kucjera. Ko magana ma bayayi saboda tsabar takaici yananan zaune har kusan sallar magriba. Dif nepa suka dauke wuta ba'aganin komai agurin sai dai in ka kura ido sosai zaka hango irin kwaronnan "makyallu" Koriyar wuta nata fita daga bindinsa Yayi kememe abinsa ajikin bango. Jamilu ya tabo ibrahim "dubi hikimar Allah" Wai duk wannan haske daga bindin kwaro yake Ya jinjina kai "Kadan kenan daga hikimarsa" Alhaji ma ya waiwaya wajen domin yagane ma idanunsa , Jamilu kuwa yace sai ya daukoshi. Adai dai lokacin haske yagama kantin sakamakon generator da'aka tayar, To amma kwaron ya shige cikin kaya wutar kawai ake gani. Dana kura ido sanaga ashe ma rigata ya shiga. Jamilu ya laluba ,sai naga ya hada. Gami da fadin "kai" Ya kuma ja dabaya "Menene?" Ibrahim ya tambaya "Ba kwaro bace ashe sailulace" "Wace irin sailula" kuma na tambaya fuska a yakune "Sailula nawa kasani" Jamil yafada loakcin dayake dauko rigar, Akazo da ita gabanmu aka sanya hannu aikuwa sailular alhajice, wai ashe kyallin danjar sabis muke hangowa Alhaji yai gauron numafashi ya mika hannu ya karba , nikuwa alokacin nawa numfashi ya dauke (nima nawa ya kusan daukewa da kyar na seta hanaklina ,lol Shuraih 99%) Akwai kallon yaya haka ? Da fuskokin mutanen ke dauke dashi bayan kallona na tsayin lokaci da alahaji yayi sai kawai yakada kai ya fita . ******* ************** ********* Ahalin yanzu duk wani amincin dake tsakanina da jama'a akasuwa yakau . Hakan bakaramin kuntata min yakeba Alhaji dai yadena aikena ko'ina izan kuwa nazauna kusa da mutum ko carbi ya fitar sai ya mayar da abinsa aljihu. Wai gudun kar na faki idonsa na dauke. Duk inda na nufa kuwa kaga ana C.I.D na hatta da randa izan zan sha ruwa sai atsareni da ido wai duk karna faki ido na tura modar aljihu (hahaha sai ni masoyi shuraih 99%) Kai abubuwan takaici dabam-dabam Ahaka na cigaba da zama cikin zullumi da bakin ciki . Izan kaga na saki raina to tabbata muna tare da farida don gudun karta gane halin dana keciki. Inanan rakube a cikin kanti sai gwani alhaji ya shigo . Da ganinsa kaga babban mutum akwai wani mutum biye dashi alhaji ya mike tsaye suka gaisa Sannan ya sami waje ya zauna "Alahi agogonne na kawomaka" Yafada lokacin dayake duban mai gidan mu "Yauwa! Ansamo" Alhajinmu ya tambaya "Kwarai kuwa" inji wacan mutumin Lokacin dayake karbar wani dan akwati daga hannun mutumin da suka zo tare, Da bude akwatin sai ga wani walwali, agogone na

Chapter 2 of 3