Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 10
tace"bude cikin carbinet dinnan ki dauko min karamin bowl. Budewa Shakeerah tayi ta Ciro taba Ammi,amsa tayi ta cika shi da dambun nama,sannan tace ta dauki jug ta zuba mata kunun ayar da tahada a cikin firij. Duk haka Shakeerah tayi ta dauki Kayan niki-niki ta nufi part din fulani,da alamu bakinnan na falon,kamar ta juya sai dai ta daure da kyar ta nufi cikin farlon. Da sallama tashiga,duk cikansu suka amsa tare da zubama mata idanuwa sosai,kura mata idanu tayi gabanta na faduwa duk da tasan face din sai dai ta rasa inda tasan face din. Karisowa tayi tana murmushi ta nufi wajen fulani,dire Mata jug din da bowl din d ke rufe da murfinshi tayi tace"fulani gashi inji Ammi na,cikin Sauri Hjy kaltume ta Kuma kallon ta,tasan muryan sai dai ta mance wacce tasani da muryan. Shakeerah ta juyo ta gaida duk bakin dake falon,da Murmushi ko wannen su ke amsa was,hjy shamsiyya tace"munji abin arzikin da kikayi 'yan Mata,yabaki miji nagari mai kula dake. Shiru Shakeerah tayi tana me amsawa da ameen a zuciyar ta,hjy shamsiyya tace"kinsan me nakeso dake?girgiza Kai Shakeerah tayi. "Ga amanar fulani nan a hannunki duk Wanda yayi mata ba dai-dai ba kici kaniyar sa kada ki saurarawa kowa ninasaki. Murmushi Shakeerah tayi tace"Aunty aini ko ansa ni ko ba'asani ba,ba'a Isa ataka fulani Ina wajen na kyaleva Koda kuwa kashe ni za'ayi. Dariya ma abun yabawa su Alhj Khamees dariya, Alhj Ahmad yace"hjy shamsiyya adaiyi hudubar arziki Koh? Duk cikan su dariya sukasa hjy shamsiyya tace"Wallahi abun ne daban haushi sai kace Laweezan 'yar gwal ita ba kyau ba ba komai ba,Wallahi bacin zumunci da tuni yadanna mata saki kowa ya huta. Shakeerah tace"Fulani gani. Dafa kanta fulani tayi tace"tashi kitafi Shakeerah Allah ya Miki albarka,kicema Maryam din ina gaisheta da aiki Allah yajikan Muhammadu. "Ameen Shakeerah tafada sannan tamike tatafi. Bayan fitan ta su Alhj kabeer suka Mike Dan zuwa masallaci. Hjy shamsiyya ta dubi su hjy Maryam tace"Inna Maryam gani da shawara. Gaba Daya maida hankali sukayi wajenta don jin shawarar. _I NEED UR COMMENT_ Xahratty ce✍🏽 Lallai Alqalami 🖋️ Yafi takobi🗡️ 💕💕 ❤️ [7/18, 2:05 PM] Xahratty🥰😘: 💐✨ *DIAMOND LADIES* 💐✨ (Daukar Fansa) Story&writing By PATEEMA ZAHRA LAWAL _______✍🏽_______ *TAMBARI WRITER'S ASSOCIATION* 🔱(( Home of Expert and talented writers,da tamvarin mu muke tafe domin kawo gyara da cigaban Al'ummah)) *T.W.A* _________________________ https://www.facebook.com/Tambari-writers-Association-106058867819812/ _________________________ Marubuciya:- _ *A DALILIN 'YAR TSUNTUWA* _ *MIJIN ZAHRA* *ND* *NOW* *DIAMOND LADIES* (Daukar Fansa) *Littafin diamond ladies (Daukar Fansa)na kudi ne duk maiso ya turo katin Naira dari 100 na waya ta wannan number 08060719719,sai nayi adding dinsa a group din* Bismillahir-rahmanir-raheem. *Da sunan Allah mai rahama mai jin kai....* _FREE PAGE_ Page:2️⃣6️⃣--2️⃣7️⃣🖊️ ___________To aini banid matsala sai dai Ammi na but abinda yafi sauki Ummi kizo kiyima Ammi magana muji ba. Shiru Ummi tayi tace"To shikenan babu matsala zanzo insha Allah. Washegari da safe su Shakeerah suka nufi gidan su harda khadee,direct part din fulani suka wuce,a guje taje ta rungume fulani. Itama fulanin Cike da farin ciki tayo gareta tana murna, Shakeerah ta dubi su fauzy tace"Diamond ladies ga fulani na nan,Cike da girmamawa suka gaida fulani,fulani tace"Allah sarki ai inajin labarin ku a wajenta sosai,Suma sukace sunajin labarin ta wajen Shakeerah. Nan suka nufi part din Ammi suka bar Shakeerah Anan da alamu tana son magana da fulani. Duban ta fulani tayi tace"Shakeerah na hala kina da magana danine? Murmushi Shakeerah tayi tace"Eah fulani dama nan Shakeerah ta zauna ta bawa labarun duk abinda ke faruwa. Shiruuuu fulani tayi da alamu ta zurfafa ne a wajen tunani can tadago ta dubi Shakeerah tace"kisani shi din bai tsari da irin mazan da Zaki Aura ba Koh? "Eah nasani inaso in hada iyayen karya ne,Kuma ba son sa nake ba sai dai tahaka ne kawai zamu samu hujjar da zai gamsar a gaban alkali,kuma ni bazan yar da dashi ba,bazanyi rayuwar Aure dashi ba. Fulani tace"Toh shikenan Shakeerah na goyi bayan ki hundred% sai dai yakamata yazama like Auren sirri Koh? Shakeerah tace"Eah fulani kusan hakane,to Amma ba'anan gizo ke sakar ba Ammi kawai nakeji. Shiru fulani tayi tace"kada kidamu zan shawo kanta, Shakeerah tace"yawwa fukani na tnx so much bari naje zamu dawo wajen ki yau za'a baza chapter tayi maganar tana fita Falon a guje, Murmushi fulani tayi tace"tabbas inason hada zuri'ah daku. Sosai Ammi tayi farin cikin ganin su yanda suke zaune suna hira suna ihu lokaci daya tunanin Abba da Aunty saudah suka fado mata a hankali kwalla ya taro a eyes dinta,cikin Sauri ta maidasu a ranta tana me musu addu'ah akan Allah yagafarta musu,tana farin cikin ganin yau Shakeeran ta cikin rayuwar farin ciki ga wani irin kyau da take dashi kaman jinin larabawa. Tasowa Shakeerah tayi tare da kwantar da kanta jikin Ammi tace"Ammi yau part din fulani zamu gudu don acan zamuyi hira, Ammi tace"Toh shikenan ku dawo dai da wuri,da toh suka amsa mata daga nan suka nufi part din fulani. Kwadon zogale fulani tayi musu,gashi anzuba shuger Dan dai-dai yayi Dadi sosai,hadda yankakken dafaffen kwai . Bayan sunga ma ci aka dasa hira,nan su khadee da fauzy suka Bata labarin rayuwar su,sosai fulani ta tausaya musu tasake bawa Shakeerah goyon bayan wannan abun. Washe gari kuwa wajen azahar Ummi tazo ita da sajeeda,sosai Ammi ta karbeta hannu bibbiyu,nan itama fulani tashigo, Anan suka bawa Ammi labarin abinda ke faruwa,sannan suka ce ta'amin ce da bukatan Shakeerah domin hakan shine mafita. Kada wuya Ammi tayi Cike da damuwa tace"Amma kukunsan hatsarin shi meyasa sai ta haka ne za'a hukunta shi? tayi maganar voice dinta na cracking. Ammi tace"Saboda ita din jajir tacciya ce,Kuma Yana mata so mai tsanani,sannan tana da wayau sai dai duk wuya insha Allah zata dawo batare da wani Abu yashiga tsakanin su ba. Still voice din Ammi cracking yake a hankali tace"Toh shikenan ina matukar son ta banason na rasata kaman yarda na rasa mahaifinta da 'yar uwar ta, Amma zan cigaba da yimata addu'ah har Allah yabata nasara. Gaba daya suka amsa da Ameen. Su Shakeerah sunyi farin ciki sosai da amincewar Ammi sai dai gabadaya Ammi ta canza mata face tarage yimata walwala,a dalilin hakan ba karamin tashi hankalin Shakeerah yayi ba,wata rana ana saura 3days su Kuma school ta Shiga dakin Ammi da sallama tashiga dakin, Ammi tana gyara kayan wadrope din ta,Babu yabo Babu fallasa ta amsa batare data kalli inda Shakeerah take,cikin sanyin jiki Shakeerah tajuya domin fita dakin tsayawa tayi tare da juyowa four eyes sukayi da Ammi,kwallah ne suka tsiyayo ma Shakeerah da gudu taje ta rungume Ammi tana mae fashewa da kuka tace"Kiya hakuri Ammi indai saboda Auren Daddyn khadee kike fushi dani to wallahi ni na hakura da maganar,dama ban sanar mai ba. Tausayi Shakeerah taba Ammi a hankali tafara shafa bayanta tana bubbuga wa tace"ba fushi nake dake ba sai dai tausayi kike bani sosai Shakeerah saboda inda zaki dosa akwai tsananin risk sai dai zan cigaba da yimiki addu'ah kuma inaso kafin ki koma school ki Kira shi a waya ki ce iyayen ki sun amince sai dai idan kun koma school ki maida hankali wajen karatun ki kinji?cikin Sauri Shakeerah tace"Toh Ammi habu matsala,ya zanyi da karatu na? Shiru Ammi tayi tace"yanda Kika gano abin da kka cema kawayen ki na Auren shi yanzu ma keda kanki Zaki natsu kiyi tunanin abinyi. Cikin sanyin jiki Shakeerah tace"Toh shikenan Ammi,tabbas tafara karaya da lamarin. Ammi tace"Shakeerah ta kisa ma zuciyar ki wannan lamarin anci nasara angama,ke mai taimako ne irin Abban ki,kada ki manta da wasiyyar da Abban ki ya bar Miki akan files din nan. "Ina sane dashi Ammi sai dai ina neman jarumin namiji mai Amana shi zanyi aikin dashi. Ammi tace"Toh shikenan ubangiji ya shige miki gaba a dukkan lamuran ki kinji? Ameen Ammi na. Gabadaya suke bedroom din Shakeerah suna kallon Shirin jamai raja da akeyi a Arewa24,wayar Shakeerah ne yayi kara,dauko wayar tayi tare da duban screen din number Daddy ne domin ko saving batayi ba,dagowa tayi ta dube su fauzy tace"diamond ladies chowan mu ne(tsohon mu ne,wato Daddy), "Ahayye nanaye suka saka shewa gaba dayansu. Hannu Shakeerah tasa a mouth tace"Shiiiiiiiiii Bari nayi picking muji me zaice. Juyawa ball eyes dinta tayi kamar yana gabanta tayi picking"Hello papi nah,wani ajiyan zuciya Daddy yayi yace"Oh my shakee baee wallahi I really love yhu,ke bugun numfashi na ce,yakike? Murmushi Shakeerah tayi tace"Ina lafiya papi kaifah? "Lpy nake my shakee,burina kawai na gammu nida ke a room guda. Wani Murmushin mugunta Shakeerah tasaki tace"karka damu papi, Aure zamuyi wanda sai na barma tarihi ni kaina ina mamakin yanda na fada tarkon son ka. Cikin sanyin murya Daddy yace"Koh My shakee? To meyasa haryanzu kinki bani damar na turo,dafe Kai Shakeerah tayi tace"Oh my papi am sorry na manta mom tace katuro magabatan ka,kwance Daddy yake but Jin abinda tace yasashi durowa daga kan gado yace"da gaske kike my shakee? "Yes papi am serious ai Babu wasa tsakanin mu. Daddy yace haka ne,to Amma my shakee inaso ayi kwanan nan ne saboda wallahi na matsu da indinga ganin ki kusa dani,yayi mgnr cikin sanyin murya. "Kada kadamu papi ai Shakeerah takace kai kadai,to ya maganar school dina,babu damuwa sai a canza miki Koh baby na? Cikin muryan shagwaba kamar yana gabanta tace"A'ah papi yanzu haka an maidani kasu ba nacema A.B.U nake ba? Daddy yace"Eah. Shakeerah tace"toh yanzu ancanza mun school,kawai idan kazo mayi maganar. Daddy yace"shikenan baby na amma wallahi banaso kina nisa Dani Sam, Shakeerah tace"Ai hakuri zakayi. Can dai Daddy yace"My shakee kinsan bansan Auren nan yawuce 2weeks koh? Yatsine face Shakeerah tayi tace"nima papi banason bikin yawuce haka. Dariya ya kyalkyale dashi kamar wani yaro yace"wayyo Allah I love yhu my shakee bae. Shakeera tace"me too Bari naje mom na Kira na,daganan na fada mata abinda kace. Cikin Sauri Daddy yace"Toh toh toh my love maza kije kinji. Ok bye my papi. Kashe wayar yayi a tare suka kyalkyale da dariya,khadee tace"Oh ni Daddy na ya afka cikin tarkon mu,Allah ya cigaba da doramu bisa kansa, fauzy tace"kuma inda zamu godema Allah wallahi son Allah da annabi yake mata bada sha'awa ko wani Abu ba. Tabe baki Shakeerah tayi tace"kanshi akeji ni school dina nake tunani sai dai nayi alkawari *AUREN WATA HUDU* zanyi. Diddilo idanuwa sukayi a tare suka furta wata hudu? Shakeerah tace"Da yardan Allah,bijahi rasulillah S.A.W. "Fakattttt kingama magana, fauzy ta fada. Sosai da zasu koma school Ammi ta hada musu abubuwa wannan Karan hadda tsakin fate domin duk cikansu su mayun fate ne,sannan ita da fulani suka sake jama Shakeerah kunne. Sai da suka biya ta tudun wada suka dauki khadee sannan suka wuce, Shakeerah wata mata ta samu hjyr kanta,sai dai rayuwa tasa ta natsu sosai,tunda ta kamu da cutar HIV ta koma ga Allah anan garin kaduna,ta roketa akan zasu dauke ta ta musu hayan cewa itace mom nata,da yske matar akwai kudi sai dai bata taba haihuwa ba. Ana haka Daddy ya sanar da Shakeerah cewa yana nan zuwa ranar Saturday domin yaga mom nata,babu damuwa Shakeerah tace masa. Cikin hukun cin Allah Ranar lahado yayi Daddy yakira Shakeerah yace gashinan a kd. Shiryawa tayi cikin wani fitinanniyar kwalliya, sari ta Sanya sak kaman yanda 'yan indiya suke sawa sai dai rigan irin mai cibiyar nan ne a rufe ruffff tasaki gashinta har gadon baya Banda kamshi babu abinda take,hell shoe tasaka mai mugun tsini. Sashi yayi ta kwantance,a takaice dai sai da Daddy ya wahala sannan ya iso gidan hjy harira,gida ne hadadde Wanda daga gani an narka dukiya,duk da ginin gidan irin na kusoshin da da din Nan ne,sai dai ko rabin na Daddy baiyi ba. Koda ya iso sai da yatsaya ya kare ma gidan kallo sannan ya tabe mouth yace"babu lefi 'yar babban gida ne,gsky shakee ta tahada komai. Karar bude gate yaji,cikin Sauri ya dubi inda yaji karar a tunanin shi Shakeerah ce,sai dai Mai gadi ne ya gaishe shi sannan yace"hjyr tace yashigo. Shiga sukayi cikin gidan wani part aka kaishi da alamu shine part din baki,Cike da izza yake tafiya,tunanin abin duniya Yake,yasaka wannan ya kwance wannan,gashi a kungiyar su ana gab da bashi green card a dalilin rashin kaso jinin shi,domin ogan su Mr Patrick ya tabbatar da cewa sai ya karar da kwayayan shi a duniya tukuna,ga rashin mutane,dole ana bukatan a rana yadinga homosex sau biyar a kungiyar su. Bismillah yaji anfada cikin Sauri yadawo da hankalin shi kan megadin yace"ok tnx . Zama yayi ba'a dauki lokaci ba fauzy tashigo hannun ta da tire bakin ta dauke da sallama sai wata a bayanta da alamu 'yar aiki ce domin ita basket ne a hannun ta. Cikin Murmushi yake dunan fauzy yace"A'ah fauzy kece?dariya tayi tace"barka Daddy,inayini? "Lapy Lou yakuke ya mom din naku? Fauzy tace"lafiya lou. "Kun dawo lafiya? "Alhamdulillah lafiya Lou Daddy,bari nakira maka ita. "Ok tnx Daddy yafada. Ba'adauki wani dogon lokaci ba Shakeerah btakariso Banda karar takalmin ta Babu abinda ke tashi,Kara ne irin ta glass tunkafin takariso Daddy yaji wani kamshi mai matukar dadi ya ziyarci hancin ta,kufullll ya hadiye wani miyau da kyar,da sallama tashigo falon face nata babu yabo babu fallasa,cikin Sauri Daddy ya mike daga kan kujeran da yake yace"Ur welcome my Shakeerah. Murmushi tayi tare da watsa finger's tace"tnx papi,samun kujerar dake facing dinshi ta zauna,Murmushi Daddy yayi ya samu waje ya zauna yace"My shakee my Queen,jujjuya eyes balls dinta tayi tare da gaishe shi,Cike da farin ciki ya amsa. Fira suka dan taba sannan tahada masa abubuwan motsa baki sannan tamike tace"Bari ta bashi waje kafin ya kammala, cikin Sauri Daddy yace"Haba my shakee tsakani na dake ai babu haka babu 'yar kunya,koma wa tayi ta zauna. Sai da yaci abinci a gabanta yayi dam bb abinda yqke saki sai Santi yace"Wai wayayi girikin nan? "Nice,amsar da tabashi kenan,wani farin ciki yakara Kama shi yace"My shakee waike komai kin hada ne. Dagowa tayi face dinta bb fari'ah cikin fa e din shagwaba tace"pls papi menene meaning din shakeee? Shiru yayi sai can yadage kafada yace"I don't know. "Uhm shine kake kirana dashi?pls kadena kira na dashi har sai randa kasamo meaning din. Ok Darling yanda kikace haka za'ayi,nan suka kara tattaunawa akan mgnr Aure yakuma ce next week za'aturo magabatan shi, Shakeerah ta nuna masa Babu komai Allah yakawo su lfy. "Papi to ya maganar school dina? Daddy yace"na zauna nayi wani tunani gaskiya bazaki cigaba da zuwa ba sai dai ki canza school. A firgice Shakeerah ta mikie daga zaunen da take tace"Nacanza school fa kace? gasky I can't kawai ka kyaleni idan nagama school din ayi Auren......uhm nina ma fasa Auren, ta karishe mgnr tana mummur guda mouth. A gigice yadubeta yace"Haba Darling Sam mgnr fasa Aure bai taso ba don haka na amince, Shakeerah tace"wallahi daga baya kacan za nima sai na canza. "Oya tell me ya yanayin tsare-tsaren school dina zai kasance? Daddy yace"gaskiya Ni ban tsara komai ba. Shakeerah tace"Toh papi nina tsara. "Ok Darling inajinki. "Yawwa duk weekend zan dinga dawowa,dama dakwai gida da mom ta siyamun nan zan dinga Zama. Daddy yace"toh gidan yayi miki bb wani matsala.? Shakeerah tace"yep papi na yayi bb matsala. Nan suka cigaba da hirar su ta masoya daganan Shakeerah taje takira fake mom nan suka zauna suka fara tsare-tsaren komai,godiya sosai Daddy kema fake mom. Itama tace"zata sanar da kawun nan Shakeerah. Da zai tafi yamata ihsani sosai. _I NEED UR COMMENT_ Xahratty ce✍🏽 Lallai Alqalami 🖋️ Yafi takobi 🗡️ 💕💕 ❤️ [7/18, 2:05 PM] Xahratty🥰😘: 💐✨ *DIAMOND LADIES* 💐✨ (Daukar Fansa) Story&writing By PATEEMA ZAHRA LAWAL _______✍🏽_______ *TAMBARI WRITER'S ASSOCIATION* 🔱(( Home of Expert and talented writers,da tamvarin mu muke tafe domin kawo gyara da cigaban Al'ummah)) *T.W.A* _________________________ https://www.facebook.com/Tambari-writers-Association-106058867819812/ _________________________ Marubuciya:- _ *A DALILIN 'YAR TSUNTUWA* _ *MIJIN ZAHRA* *ND* *NOW* *DIAMOND LADIES* (Daukar Fansa) *Littafin diamond ladies (Daukar Fansa)na kudi ne duk maiso ya turo katin Naira dari 100 na waya ta wannan number 08060719719,sai nayi adding dinsa a group din* 👌🏽SADAUKARWA👌🏽 Na Sadaukar da page din nan agreku:- *Zahra Ummu Ayshat* *Saudat(ummu farhana*) *Precious* *Khadija tijjani* *Ayusha* *Fatima mansur* Bismillahir-rahmanir-raheem. *Da sunan Allah mai rahama mai jin kai....* _FREE PAGE_ Page:2️⃣8️⃣--2️⃣9️⃣🖊️ ___________Sosai su Shakeerah suka mai da hankali wajen karatun sa, a gefe daya Kuma Daddy ya turo magabatan sa wajen fake magabatan Shakeerah an tsayar da magana nan da two weeks za'a daura Aure. Daddy yaso ayi event sai dai Shakeerah tace ita Sam bataso bada itaba,kudi yaturomata 10million akan tayi siyayya kuma ta hada ma kanta lefe. Komai shiya siya hatta da kayan daki,domin a dangin Shakeerah bb Wanda yasan da maganar daga Ammi sai fulani Shiyasa bb wani shirye-shirye da ake gudanar wa ta bangaren ta sai dai a gidan hjy harirah. Ana saura sati guda biki 'yan uwan Daddy suka kawo kayan lefe ciki kuwa harda car key,abun ya birge kowa akwati dozin uku gaskiya Daddy yatara dukiyan haram Allah ya kiyashe mu. Ranar wata laraba da daddare Daddy na bacci yaji zoben hannun sa yafara rawa,alamun anason mgn dashi,bude ido yayi, nan kuwa zoben yayi haske sosai sai ga wani mutumi ya bayya na a gaban sa da jajayen kaya,mummuna sosai sai wani baki gashi bb alamun imani a fuskan sa, cikin tsawa yace"Lallai Sani kana nan kana bacci muko muna cikin matsala babba. A firgice Daddy yace"Oga Patrick tuba nakeyi........tsawa ya dakama Daddy"kayimun shiru kaje zaka auro Mana masifa da bala'i a binciken da mukayi wannan yarinyar annoba ce a cikin mu meyasa zaka Aure ta? Cikin Daddy na shaking yace"A'ah oga Shakeerah Bata da matsala kafin na Aure ta sai da nayi bincike kuma an tabbatar mun da Babu abinda zai faru kamar yanda sauran suka faru. "Alhj Sani kanaja da magana nane?da binciken da akamaka da Wanda mukayi wannene gaskiya? Shiru Daddy yayi. Mr Patrick yace"Oh nagane ka Saboda kaga nabaka karamin shugaban kungiya shine kakeso kayi abinda kaga dama?to Bari kaji Muddin ka Aure yarinyar nan aka samu matsala to kayi kuka da kanka badamu ba. Yana gama fadar haka yabace battt,tsaki Daddy yaja yace"kilama kunyi bincike ne kunka da alkhairi shine kukeson rabani da ita,aini da Shakeerah sai dai mutuwa,Yana gama fadar haka ya juya ya cigaba da baccin sa. Shakeerah dasu khadee Suma ta bangaren su sun dage da addu'ah sosai akan Allah yabasu nasara akan Daddy,haka ta bangaren Ammi,fulani da Ummi ma ba'a barsu a Baya ba,a kwana a tashi biki ya kasance saura kwana hudu,Babu wani gyara da Shakeerah taje yi domin ita ba Aure zataje yiba. Hjy sameera hankalinta yatashi Jin Daddy zai Kara Aure tunda ake mata kishiyoyi bata taba Jin irin wani mugun kishi ba sai akan wannan da za'akawo mata,gaban ta na tsanan ta faduwa matuka ta rasa dalilin hakan. Kwatsam su Shakeerah na school chairman din department dinsu yakira su Kan cewa antafi yajin aiki,ba karamin Jin dadi sukayi ba shikenan faduwa tazo dai-dai da zama,Ranar Asabar kuwa aka daura Auren Shakeerah da Daddy duk da Babu taro Amma Sai da Daddy ya turo abokan sa,unguwan du hjy harirah yayi makil da manyan Mutane,ana gama daurin Aure Daddy ya dauki Amaryan shi,dama tunkafin yazo Shakeerah taje sunyi sallama da su Ammi da fulani,sosai suka sake bata shawarwari da ja mata kunne Akan kada ta kuskura ta yarda da Daddy. Irin kukan rabuwar nan da'akeyi Sam Shakeerah batayi ba sukuwa su khadee da fauzy Sunyi kuka kamar ransu zai fita,a dalilin kewar Shakeerah ita kuwa cemusu take suyi hakuri tana nan dawowa soon. Sosai 'yan uwan Daddy suka tarbeta d farin ciki da kauna tunda family house dinsu suka kaita,Bayan sallar isha'i suka dauketa suka kaita gidanta,direct part din hjy Sameera suka nufa da ita,domin Amarya ma tana can. Sun samu hjy Sameera akan kujera tayi daurin kirji ture kaga tsiya Sai karkada kafafuwa take tana taunar chwengum. Sun aje Shakeerah 'yan uwan Daddy zasu gabatar da ita hjy Sameera ta dakatar dasu,kunga kutashi kutafi wannan abun da zaku fada ba yau nasaba jinsa ba don haka nariga na haddace ku ajeta ku tafi,duk da cewa 'yan uwan tane suma,mikewa sukayi suka fita batare dasun tanka ba,don sun San halinta ba kirki tacika ba. Tsaki Hjy sameera taja tace"kekuma munafuka Sai ki bude mana face din naki domin kuwa muba siyan sa zamuyi ba. Daddy ne yayi gyaran murya tare da shigowa,sannu da zuwa Aunty Amarya tamai,batare da ya kalleta ba ya amsa. Bude taro yayi da addu'ah sannan yafara magana kamar haka"Amarya Ina Miki maraba da shigowa gidan ki,Allah yasa kin shigo da kafar dama,pls inaso ki bude face din ki don 'yan uwan ki su ganki kigansu,toh Shakeerah tafada tare da yaye mayafin da ke kanta a hankali. Duk cikan su suka mike tare da tsalle, Hjy sameera tace"haba haba no wonder,dama nasan za'a rina tunda naga tazo gidan nan nasan tuggu aka shirya maka,Yaya tarasu shine aka baka kanwa ka Aura?lallai ne.ita kuwa Aunty Amarya nuna ta take tayi tace"Amma ke maciyiyar Amana ce,daga zuwan ki rannan shine har kintafi da zuciyar shi wajen malaman garin ku?lallai. Ture Aunty Amarya Hjy sameera tayi gefe ta matso har gaban Shakeerah tace"lallai yaro baisan wuta ba sai ya taka,yayarki ma bataci galaba akaina ba wajen kishi balle ke 'yar tatsitsiyar ki dake,wallahi tundaga gobe kifara irgawa cewa kinkawo kanki gidan wahala,domin Babu ke babu samun farin ciki a gidan nan. Tana gama fadar haka ta fice,shidai Daddy shiru yayi Yana tunanin yanda zai yi ya shawo kan matsalar,tsaki Aunty Amarya tayi ta dube Shakeerah tace"munafuka........ Daddy ne yadaga hannu zai mari Aunty Amarya cikin Sauri Shakeerah tarike hannunn shi tace"haba papi na kada kaga lefinta kishi ne yakawo haka,kishin na naka,sannan akan me zaka dake?ita mai danyar jini ma tayi kishi Ina ga wacce tsufa yazomata ta Fadi maganganu na rashin da'a baka hukunta taba sai wannan. Shiru Daddy yayi tare da wucewa fuuuuu ya nufi wani part daban da alamu shine na Shakeerah,duban juna Shakeerah da Aunty Amarya sukayi suka kece da dariya, Aunty Amarya tace"gaskiya Shakeerah plan dinki yana kyau,yanzu mutashi a part din nan kafin tsohuwar nan tadawo tamana rashin M. Tabe baki Shakeerah tayi suka nufi part dinta,zage-zage Aunty Amarya take cikin pretend ta wuce part dinta.tsayawa Shakeerah tayi a kofar Falon batare da tashiga ba, Saboda talura Hjy sameera na leken ta ta window,don haka sai tayi kamar batasan inda zatashiga ba.Wayar ta ne yafara ringing cikin sauri tadauka ganin Daddy ne,hade rai tayi kamar yana gabanta batare da tayi magana ba,a hankali yace"Amarya ta kina Ina? A zafafe tace"gani a waje cikin tantagar yan sanyi Babu Wanda

Chapter 6 of 10