You Cannot Download this book untill you login but you can read it .
Login Register
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
ο»Ώπͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺ
*A WANI GARI*
πͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺ
*Story and writing*
*BY*
*Leemart Yar pilloh*π²
*Page* 1_2
*Ψ¨Ψ³Ω Ψ§ΩΩΩ Ψ§ΩΨ±ΨΩ Ω Ψ§ΩΨ±ΨΩΩ *
*____________________________________________*
Β©π
*AL'UMMA WRITER'S ASSO...* βπ»
_Aβ’ Wβ’ Aβ’_
_{{Al'umma writers_
_Kungiya daya tamkar da dubu farin cikin mu mu fadakar da Al'umma domin su farfado sugane gsky al'umma sai dan Al'umma Allah ya bamu ikon fadakar da Al'umma}}_
https://www.facebook.com/Alumma-Writers-Association-101394218126525/?referrer=whatsapp
*_________________________________________*
*Bismillahir'rahamanir'rahim*
```Duk kan yabo da godiya sun tab'bata ga Allah ubangijin talikai Wanda shi yabani ikon Fara wannan littafin lafiya kuma Ina rokon Allah yanda yabani ikon Fara shi lafiya yabani ikon gamasa lafiya Kuma Ina fatar wannan littafin zai karbu agareku FANS dan akwai abun Al ajabi acikinsa```π€
"Zaune suke itada iyayen'ta suna'cin rogon da suka dafa ba kajin motsin komai saina taunar'da mahaifiyar'ta takeyi kasan'cewar'ta me raunin hankali
Cikeda tausayin'ta baban marcy yad'ago yazuba mata idanu idanunshi ne yaciko da hawaye tsayin shekara ashirin kenan take famada wannan lalurar tun basu haifi mersy ba ko yaushe zata warke oho
'Daga robar burkutunshi yayi ya tuttulawa cikinsa yasaki wata uwar gyatsa me cikeda d'oya.
Da sauri mersy tarufe hancinta zuciyarta na tashi. I
Wani wawan dundu ya zuba mata abayanta
"Ni kike toshewa hanci??
Saurin mi'kewa tayi Dan tasan yanzu yana iya kaimata duka.
Bayan bukkarsu taje ta d'ebo ruwa a raminda sukayi Dan zuba ruwan cikin 'bawon kwakwa mai d'an zurfi ta zubashi tadawo wajen uwar tata .
Ahankali take bata ruwan tagama tawanke mata hannu sannan ta matsar da ita gefe takwanta
Itakuma tawuce wajen tanufi gidansu 'kawarta yemmi a bakin 'kofar suka had'u da ita tafawa sukayi had'eda Jan hannun juna suka nufi jeji
Gani nayi kawai suna ta ratsa tsakanin kwakwa batareda wani yayiwa d'an uwansa magana ba
Abakin wata 'korama Naga sunyada zango sunzauna alokacinne suka sake ajiyar zuciya atare
Yemmi ce tad'ago ta kalleta
Kinsanme 'kawata??
" a'a saikin fad'a.
"Cikine dani"
Wani kyakykyawan murmushi mersy tasaki Daga baya kuma idanunta yaciko da hawaye
Natayaki murna sosai da sosai kice wannan shekarar za'ayi aurenki zaki huta zaki tafi kibarni shikenan iyayenki zasu zama 'yantattu acikin garinnan.
Ta'karashe maganar idanunta cikeda hawaye
Dafa kafad'arta Yemmi tayi sannan tace.
"Ki kwantar da hankalinki mersy kema zakiyi aure zaku zama 'yan tattu kuma mahaifiyarki zata samu lafiya"
Murmushin takaici mersy tayi tad'an 'batarda zancen ta hanyar cewa.
Cikin waye ne kuma watanshi nawa??
"Wata biyu kenan kuma Daniel ne yaron sarki"
Ah kice ke jinkirinki yabaki Abu me kyau kunzama manya,amma yakamata ace kinfad'a asan da zaman cikin, tunda kings yanzu matanshi biyarne bansan mata nawa zai aura wannan shekararba,Ni wallahi banason wannan halaiya tamutanen garinnan shiyasa kika na'ki amincewa da kowa bare ayimin cikin nayi aure su suna ganin ba'kin jinine dani hmm.
Tagumi Yemmi tayi sannan tace.
"Nifa ajikina inajin ayanayin rayuwarmu ba rayuwa me kyau mukeba kiduba kigani yadda ake Abu kamar dabbobi agarinnan kwata kwata shekararmu shabiyarne amma anbar iyayenmu abayan gari anharamta mana cin komai sai rogo anhanamu shiga gari sailokacin bikin shekara,hmm abinnan yana bani haushi sosai"
Hmm.
Ni yadda suke Tara matane yake bani takaici kiga namiji da mata samada goma kuma basajin kunyar kusantar matansu ako ina ko agaban yaransune saikiga yara 'kanana suna neman junansu amma saima ace kaga yara masu kwazo.
Ta 'karasa fad'a hawaye nabin fuskarta na tausayin ahalinta Dan tasan akwai duhu sosai cikin rayuwarsu.
Ihunda sukajine yasasu mi'kewa da sauri suka nufi bakin gari tunda anhanasu shiga cikin
Megarin suka gani yana ri'keda jariri sabon haihuwa yanausa daji tsirara yaron yake sai tsala uban kuka yake jikinsa duk jini ko cibiya ba'a yanke masaba yayinda mutanen garin suka biyosa abaya sunata ihu wasuna kuka suna jifan jaririn yayinda sarkin kuma yaketa sauri kuma afusace.
Fashewa da kuka sukayi suka ru'kun'kume juna cikin tausayawa wannan jaririn Domin sunsan zuwa z'ayi a yaddashi a rami yagama kukansa ya mutu ya ru'be domin haka sukeyiwa duk jaririrn da uwarsa ta mutu wajen haihuwarsa acewarsu 'kashin tsiyace dashi sun chanfa wannan abin sosai.
Sunanan tsaye suka ga dawowarsu tabbas dasunada halin taimakawa dasun taimaki wannan jaririn amma babu yadda zasuyi.
Bukkarsu Yemmi suka nufa suka zauna saidai kukanda Yemmi takeyi yawuce hankali.
Bakomai take tunawaba sai yadda takeda ciki yanzu kenan idanta mutu shikenan haka za'ayiwa jininta tabbas tana cikin tsaka mai wuya
Tunaninsu yakusan zuwa d'aya da mersy haka sukacigaba da kukansu har sukagaji sukayi shiru
Saidare mersy takoma gida sanin cewa ba inda mahaifinta yakezuwa kodayaushe yana zaune agidane
Tana zuwa takwanta a bukkarta Dan tasan sunyi bacci itamma bata dade da kwanciyaba baccin yadauketa cikeda mugayen mafarkai irin Wanda tasabayi
Come and plxxx
*_Leemart Yar pilloh_*
πͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺ
*A WANI GARI*
πͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺ
*Ψ¨Ψ³Ω Ψ§ΩΩΩ Ψ§ΩΨ±ΨΩ Ω Ψ§ΩΨ±ΨΩΩ *
*____________________________________________*
Β©π
*AL'UMMA WRITER'S ASSO...* βπ»
_Aβ’ Wβ’ Aβ’_
_{{Al'umma writers_
_Kungiya daya tamkar da dubu farin cikin mu mu fadakar da Al'umma domin su farfado sugane gsky al'umma sai dan Al'umma Allah ya bamu ikon fadakar da Al'umma}}_
https://www.facebook.com/Alumma-Writers-Association-101394218126525/?referrer=whatsap
*_________________________________________*
*story and writing*
*BY*
*Leemart Yar pilloh*π²
*page 2_3*
*_Biamillahir'rahamanir'rahim_*
A firgice ta farka daga baccin datake idanunta ga'ba daya duhu take gani gata dai kaamar me bacci amma ba baccin bane rintse idanuwanta tayi hawaye na zubowa kan piskarta akowanne dare haka take kasancewa bata iya bacci amma daga ta tashi mantawa take da abinda tagani amafarkin.
Kanta tahad'a da gwuiwarta tabbas akwai duhu da ya mamaye rayuwarsu tanaji ajikinta tamkar akwai wani duhu daya mamaye rayuwarsu itada yan garinsu.
Wannan wane irin rayuwane Babanta kawai zata iya tambaya yabata amsa amma shi kullum cikin maye yake dukda bata ta'ba ganin shi da wata maceba matarshi d'ayace kuma bataga alamun yanabin wasuba amma shid'in tamkar ta'ba'b'be yake ko mahaifin Yemi maatansa biyar ne kuma shi da matannashi suna cikin gari yayinda itakuma Yemi da mahaifiyarta aka korosu waje har sai sunyi ciki.
Itakuma haka kawai tana tsoron mu'amala da mazan garin Sam basa wanka ga wari ga d'oyi dukda baiwar da 'karamin garin nasu yakedashi
Tunda take bata ta'ba ganin wasu mutaneba bayan su kai itakam azatonta sukad'aine suke rayuwa aduniya babu wasu halittun sai irin wad'anda suke gani aduk lokacin da suka yi nisa adaji itada Yemmi
Tayi nisa acikin tunaninta taji ihun mamanta aduk lokacinda taji hakan tasan gari ya Waye da sauri tanufi d'akin shige mahaifinta tagani ya ri'ke hannun maman yana bata ruwa a 'bawon kwakwa tana zuwa ta kar'bo ruwan taci gaba da bata shi kuma ya mi'ke yad'auko rogo yakawo mata
Sai'da taci ta 'Koshi sannan tayi shiru dama indai kaji kukanta to yunwa takeji
Ajiyar zuciya Marcy taja sannan takoma gefe tahad'e kanta da gwuiwarta cikeda tausayin mahaifiyarta ta
Kallonta mahaifinta yayi san'nan ya kad'ai kai yafita ya barsu su kad'ai tadad'e azaune shiru ita d'aya Dan mahaifiyar tata batamagana ita tunda suke tarema bata ta'ba jin maganartaba
Said a gari yawashe sosai sannan ta fito waje batajin yunwa Sam shiyasa tazauna abakin bukkarsu tanajiran fitowar Yemi
Bata dad'e awajenba taga fitowarta
Akusada ita tazauna tana murmushi
A'a manyan masu ciki ya akayine sai yanzu akatashi ko?
"Wallahi kinganni bacci naketayi Ni yunwa ma nakeji gashi mama tace zamu shiga cikin gari yau mugayawa sarki inada ciki "
Ta'karasa tana ta'be baki
Nikam da zan baki shawara da sainace kiyi ha'kuri kar agaya masu tukunna abari sai ranar bikin shekara kafinnan yafito kowa yaganki da abinki koya kikace??
"Amma kinkawo shawara me kyau 'kawata amma kinsan menene?
A'a saekin fad'a.
" Ni tunani nake idanna mutu wajen haihuwa shikenan jinina saidai ya salwanta abinnan yanamin ciwo sosai fiyeda zatonki 'kawata"
Hawaye masu zafi suka biyo fiskarta
Murmushi Marcy tayi sannan race.
Nayi miki Al'kawarin muddin ina jininki bazaije ramin yara ba namiki wannan Al'kawarin.
Murmushi kawai Yemi tayi amma tasan wannan Abu ne da bazaiyiwuba domin basusan INA ramin yaran yakeba kaf garin sarkine kawai da d'ai d'aikun jama'a sukasan wajen
"Dakike maganar haka kinsan ramin be??
Atareda ta kalletaba tace.
Bansaniba amma ko a inama yake zan nemoshi ayau dinnan .
Mi'kewa tsaye tayi tace
Tashi kirakani muduba kawai ramin nakeson gani da tsayin girmansa domin ko ba jininkiba inason nayi taimako ko bayauba nasan jaririn jiya tuni ya mutu taho muje.
Tayi gaba abinta batareda tsoron komaiba
Adole itama Yemi tabi bayanta amma jikinta a sanyaye ne sosai
Suna tafiya suna waiwaye lungu da sa'ko dubawa suke amma har suka gaji basuga ramin ba abin ya matu'kar daure musu kai haka sukaji suka dawo
Amma Marcy tayi Al'kawarin saita nemo ramin yara ko a in a yake
Ahaka suka rabu akan cewa gobe zasu koma
*Cikin gari*
Ba abinda kakeji sai kad'e kad'e da Raye Raye yayinda bad'ala ya yi yawa wannan duk bikin mutuwar da akayi jiyace wadda akayarda jaririn domin d'aya daga cikin yaran wazirin garince y'ar shekara 11 ta rasu wajen haihuwa bushe bushe kawai akeyi
Wannan damar Baban Marcy yayi amfani da ita wajen shiga garin ya samo musu nama domin sundad'e basuciba duk Dan y'arshi tayi shekara 15 batayi cikiba.
Sai dare yadawo ya kira Yemi da Mamanta suka had'u suka ci tare sukasha ruwa
Bayan sungama ne Marcy ta cewa Babanta
Baba meyasa muke rayuwa haka ne?
Waye yayimu?
Meyasa ake kashe jarirai?
Kuma meyasa duk yaronda aka Haifa ranar bikin shekara ake dafa namansa kowa yaci?
Kallonta yayi batareda yace komaiba yami'ke yanufi bukkarsu Dan baida abinda zaice mata amma shida kanshi yana tsoron y'ar tashi dukda yanada buri a 'kasan ranshi yabar abin zuwa lokaci koda zai rasa ransa sai yarinyarsa tabar garin nan dukda har yau yana binciken inda zaisamu hanyar barin garin da su
Sam Marcy bataji dadin shirun baban nataba amma dai zata bishi ahankali harzuwa lokacinda zai gaya mata da kanshi dukansu mi'kewa sukayi itama takama hannun mamanta takaita bukka sannan tawuce nata bukkan
Wash
Comments and share plx
*_Leemart Yar pilloh_*
[4/16, 2:55 PM] Leemarh Phillo: πͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺ
*A WANI GARI*
πͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺ
*NA*
*_Leemart Yar pillohπ²_*
*Ψ¨Ψ³Ω Ψ§ΩΩΩ Ψ§ΩΨ±ΨΩ Ω Ψ§ΩΨ±ΨΩΩ *
*____________________________________________*
Β©π
*AL'UMMA WRITER'S ASSO...* βπ»
_Aβ’ Wβ’ Aβ’_
_{{Al'umma writers_
_Kungiya daya tamkar da dubu farin cikin mu mu fadakar da Al'umma domin su farfado sugane gsky al'umma sai dan Al'umma Allah ya bamu ikon fadakar da Al'umma}}_
https://www.facebook.com/Alumma-Writers-Association-101394218126525/?referrer=whatsapp
*_________________________________________*
*_page 4_5_*
*_INA matuqar alfahari dake wannan page din nakine kiyi yadda kikeso dashi kijuyashi son ranki qaunarki ajinina take ina matuqar alfahari dake ta musanman kina nunamin qauna fiyeda xaton me tunani Allah yabarmu tare my LEEMART PINKY_*ππ
*Bismillahir'rahamanir'rahim*
Tunda tashige bukkar'ta take faman tunani gaba d'aya bacci ya 'kauracewa idanun'ta ha'ki'kanin gaskiya wannan abin ba'karamin damun'ta yakeba amma ita talura kaf mutanen garinsu ba abinda yadame'su da hakan ,
Abu na'biyu shine yadda ake tsangwa'mar'ta fiyema'da yadda ake yiwa Yemi tunda tare aka korosu bakin gari lokacin'da sukayi shekara 12 ba ciki,
Mutanen garinsu munana'ne haka zalika ba'ka'ke 'kirin kuma basa saka komai ajikin'su sai ganye bata ta'ba ganin suna bautar wani abuba rayuwar'su kara zube take.
Wannan wace irin rayuwa'ce?? yaushe chanji zaizo musu ajikinta tanajin tamkar ba'akan daidai suke ba itada su.
Tayi zurfi cikin tunanin'ta duk'da sanin dare yayi sosai amma bata kashe wutar icen data kunna'ba
Kamar amafar'ki taga wutar tamutu wani irin sanyine yake ratsa mata jikinta take tafara rawar sanyi ahankali ta zame kan ganyenda take kwanciya jin tana 'ko'karin fad'uwa
Ahakan taji tamkar antsaya akanta jitayi anmatse bakin'ta antsiyaya mata wani irin ruwa me uban wari tundaga nan bata sake sanin inda kanta yakeba
*****
Ahankali suke saukowa a matakalar jirgin hannun'su sar'ke Dana juna
Su hudune maza uku mace d'aya kuma daga duk'kan alamu itace 'karamar'su ganin yadda tawani langwa'be kai a kafadar babban.
Kana ganin su kasan jini d'aya ne ganin yadda suke matu'kar kama duk'kansu shigar mutumcine ajikinsu kuma a nutse suke
Suna gama sauko'wa naga sunnufi wani had'ad'd'en mota mace da namiji ne agaba yayinda sauran biyu suke abaya aguje ya finciki kan motar suka fita daga cikin jirgin.
Alhaji wai haryanzu yarannan basu 'karasoba kodai tafiyar mota sukayine ??
Murmushi kawai yayi kafin yayi magana sukaji dirin motarsu alamun harma sun shigo.
Mi'kewa yayi domin tarban zaratan yarannashi
Da sauri na tsakiyan ya rungumeshi yana fad'in.
Oyoyo Abbana"
Cikin matsanan'cin farin ciki Abban ya 'kara rungumeshi
Ummi ce tace.
To dai yakamata kasakeshi haka ko ai saikasa jikinshi yayi ciwo"
Sakinshi yayi tareda Jan hannun shi yanufi cikin gidan dashi
Macen'ce ta tsaya bubbuga 'kafafu ganin duk sunwuce sunbarta
Babbanne yadawo da baya yazuba mata rankwashi Wanda saidayasa hawaye cika mata idanu
Harararshi tayi 'kasa 'kasa tana fad'in"ba'kin mugu kawai mutum sai shegen ba'kin zalunci ya iya"
Dawowa yayi da baya
Mekikace?
Ya'ke tayi tana washe ha'kora tace.
Cewa nayi kayi ha'kuri"
Girgiza kai yayi yawuce ciki,daga bayanta taji anshe'ke da dariya tasan aikin ya Usman ne
Turo baki tayi tajuya ta wuce bin bayanta shima yayi yana jinjina rigima irinta Ayshart
A babban falon gaba d'aya suka yada zango suka shiga fira dama basa tareda yunwa saboda ba doguwar tafiya sukayiba.
A.A family kenan wato Abubakar Aliyu family.
Family me cikeda qaunar juna da tarbiyya duk'da akwai 'kullin'da ya 'kullesu amma rayuwa suke yadda Allah ya tsara musu cikeda godiyar Allah.
Abubakar shine sunan mahaifinsu sunan mahaifiayarsu Khadija
Yaransu hudu Babban shine Aliyu Wanda yaci sunan kakansu sai me bimai d'an lelen duka gidan kai kayi zatonma shine d'an fari saboda yadda kowa yake ji dashi wato Umar kusan Kansu d'aya da Aliyu Dan wata'kila haihuwar kusa kusa maman su tayi sai mebimasa Usman sai Auta Ayshart
Kubiyoni asannu Dan sanin suwaye familyn A.A
*******.
Bata sake sanin inda kanta yakeba sai washe gari da rana tafarka cikin tsananin zazza'bi da ciwan kai
Ahankali ta lalla'ba ta fito hankalin'ta gaba d'aya yana kan mahaifiyar'ta ba tasan yata kwana'ba duk'da cewa tasan mahaifinta baya matsawa daga kusa da ita saida babban dalili.
Ilai kuwa a bukkar tasameshi yanabawa mamanta magani wani dad'ine ya ziyarceta kusada maman taje ta zauna tad'an kwanto jikinta tana lumshe idanu
Bakida lafiyane ?? Ya'tambaye ta
Shiru tad'an sannan tace eh
Meke damunki??
Ata'kaice tamasa bayani
Baice komaiba ya tashi yafita tasan magani yashiga daji nemo mata danshi bayason yaji ance ba lafiya ko cikin maye yake saiya fita nemo magani.
Itakamma mamaki take dayau taganshi ba cikin mayeba kuma taji dad'in hakan dama ace yadaina kenan
Sai yamma sannan yadawo zuwa lokacin jikinta yayi zafi sosai sai kelaya amai take Yemi ce da mamanta suke kula dasu
Koda yabata maganin me makonsauki sai jiki ya'kara rikicewa fiyeda farko
'Kura mata ido baban yayi daga bisani ya sunkuyar da kai .
Cikeda farinciki maman Yemi tace.
"Bunnah Marcy tayi ciki neko ??
Ahankali ya d'aga mata kai idanunshi cikeda hawaye natausayin y'artashi
Duk'da acikin halin ciwo take hakan baihanata gane zancen'suba .
Hankalinta ne yayi matu'kar tashi domin ita bata ta'ba yin abinda take ganin mutanen garin sunayiba idan sunje gona kuma Yemi tace sai anyi za'ayi ciki ita kam tace datayi irinsa gwanda tamutu abayan gari
Fashewa tayi da matsanancin kuka domin tasan Baban'ta bazaiyi 'karyaba Dan shine babban me bada magani na duka garin mutane har biyosa suke wajen gari shiyasa koya shiga gari ba'a tona masa asiri awajen sarkin.
Cikeda tausayinta Yemi ta rungumeta tana kuka Dan tasan abinda 'kawartata ta tsana kenan arayuwar'ta ace tayi ciki.
*Tofa wannan lukutar jalalan taya za'a warwareshi makaranta kuxo Ku kwance'minshi
Shin wae cikinne da ita idan shine yazatayi toma ataqaece cikin Waye ne inajiran ra'ayinku_*
_taku har kullum me kaunarku_
*_Leemart Yar pilloh_*
[4/16, 8:36 PM] Leemarh Phillo: πͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺ
*A WANI GARI*
πͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺ
*NA*
*_Leemart Yar pilloh_*π²
*Ψ¨Ψ³Ω Ψ§ΩΩΩ Ψ§ΩΨ±ΨΩ Ω Ψ§ΩΨ±ΨΩΩ *
*____________________________________________*
Β©π
*AL'UMMA WRITER'S ASSO...* βπ»
_Aβ’ Wβ’ Aβ’_
_{{Al'umma writers_
_Kungiya daya tamkar da dubu farin cikin mu mu fadakar da Al'umma domin su farfado sugane gsky al'umma sai dan Al'umma Allah ya bamu ikon fadakar da Al'umma}}_
https://www.facebook.com/Alumma-Writers-Association-101394218126525/?referrer=whatsapp
*_________________________________________*
_wannan shafin gaba d'ayansa nakine my dear Allah yasaka da alkhaery Allah yabar xumunci Allah yasa lapiya najiki shiru kiyi ha'kuri kidawo baxan iya jure rashinkiba two days my_ *_Deejarh (larkhi)_* ππππππ
*_page 6_7_*
Tun daga wannan rana Marcy tashiga cikin tsananin tashin hankali da rashin nutsuwa gaba d'aya tarame ta jeme tayi fari fat ko abinci bata iyaci Yemi ce med'an rarrashinta amma babban abin damuwar shine ganin yadda cikinta yake girma har motsi tanaji acikinta dukda na Yemi yafi nata girma takasa yardewa kanta cewa ta aikata abinda ta tsana
Har yau bata daina zuwa ramin yaraba domin tace itafa saita nemoshi aduk inda yake , saidai kullum wahala kawai sukesha basu ta'ba ganin ko rami 'karamiba
Wani lokacinma ita kad'ai take fita batareda Yemi ba kuma cikinta nabata wahala shiyasa take guduwa ta barta.
Jitayi andafa kafad'arta ahankali ta d'ago kanta ta zuba mata ido Yemi ce gaba d'aya ta zabge saboda cikinta yakai wata bakwa.
Kina nan kina ta faman sana'ar taki ko???
Ance kirage sakawa kanki damuwa saboda ba'ason me ciki da damuwa kinji ki dinga kwantarda hankalinki banason ganin ki cikin wani hali kinji "
Ta 'karasa tana mata murmushi Wanda kana gani kasan na dolene .
Murmushin 'boye damuwa tayi tace .
Nifa tunani nake gobene bikin shekara bansan iya adadin jarirai nawa za'a yankaba da ace inada yadda da baza'a yanka Dan kowa ba domin suma kamarmu suke dukda rayuwarmu batada maraba data dabbobi
Cikeda mamaki Yemi take kallon 'kawar tata domin idan tayi magana saika rantse ba ita taiba ba'a yanayin fata da kamanni kawai Marcy ta banbanta da suba harda halayya da dabi'a Marcy gaba d'aya komai ba inda ta bar mahaifiyarta a kodayaushe fatanta bai wuce na Allah yasa Marcy tabar garinba dukda su awajensu bawasu al'ummar sai su kad'ai amma zata iya zuwa ta tashi nata jama'ar (anya kuwa to maji magani)
Lafiya kuwa ?taji Marcy tana tambayarta
"Ba komai Ni tunaninama. Shine yadda daga yau mundaina rayuwar wajen gari saidai ciki gobe kowa zaisan munada ciki kuma zamu koma gidan sarki da zama har mu haihu"
Kina nufin za'a rabamu da iyayena??
Kwarai da gaske Dan haka mamana tafad'amin saika haihu saika koma koma gidanku daga nan sai azo ayimaka wanka da ruwan kwakwa a shafa maka jinin kura asamaka rigar kura shikenan saika koma gidan mijinka kuyita zuba soyayya"
Ta 'karasa fad'a fiskarta cikeda murmushi
Kallonta kawai takeyi Dan ita bama tasan wasu al'adunnasuba saboda sundad'e awajen gari suna zaman jiran ciki kamar yadda maman Yemi take cewa.
Mi'kewa tayi tanufi bukkar Mamanta yabar Yemi awajen
Idanda sabo Yemi tasaba da halin Marcy Dan ita wani lokacin muguwar miskilace ,mi'kewa itanma tayi tanufi nasu bukkan ganin rana yana 'ko'karin fad'uwa.
Lokacinda tashiga mahaifiyarta ta bacci takeyi saboda bata dad'e dashan magani ba
Ruwa takeson sha gashi babu aramin da sukesha na gindin bishiyar dabino dole sai sunje 'korama
Tasan kuma Babanta baya zama ba ruwa ad'akin saboda kar mahaifiyarta ta ashi ba ruwa kusa.
Bincike takeyi sosai dukda cewa babu komai sai tulin magungunan Babanta tana d'aga wani ganye saitaga ruwa fari tas a 'bawon kwakwa da sauri ta d'auko jikinta har rawa yake tana sawa baki taji wani mugun wari ya bugeta tabbas bazata ta'ba mantawa da wannan ruwan ba shine Wanda aka d'ura mata da dare kuma tunda ga ranar bata sake sanin kantaba said a tayi kwanaki kuma tana farkowa tafara ciwonda ya'kijin magani
Da sauri ruwan ya subuce ahannunta jitayi 'kafafunta sun kasa d'aukarta tazube awajen idanunta na fitarda zazzafan hawaye
Gani tayi antsaya akanta tasan mahaifinta ne shiyasa bata 'bata lokaci wajen cewa saita d'ago taga kowaye.
*******
Wai Ni Bros aikin me kakeyine haka kusan wata biyar kenan koda yaushe kana aiki kan computer ninahgaji gaskiya saina fad'awa Abba haba mutum saikace inji dubiba yadda kabi ka rame ka 'kanjame saikace ba kaiba haba kasawa kanka nutsuwa mana please kaji bro" ya'karasa fad'a da muryar rarrashi
Mi'kewa Aliyu yayi yarufe computer yatashi yahau gadon kwantarda umar din yayi a cinyarsa cikeda 'kasaitarsa yace.
Kai 'kanina kacika rikici INA kan aiki nane domin nayi Al'kawarin saina cika wannan burin nawa inakan bincike ne.
Wanne irin aikine wannan haba Bros nidai nafi bu'katar kazauna kahuta kaji ko?
Murmushi Aliyu yayi yace shikenan. D'an lele na aje komai insha Allah kwanta muyi bacci rigimamme kawai ka girma. Bakasan ka girmaba.
Turo baki Umar yayi ya ja blanket ya ruge jikinsa har kansa shima Aliyu kwanciya yayi amma a zuciyarsa yana tuanani yadda zaiyi da Umar ne domin aikinsa na sirrine kuma kwata kwata wata biyu yarage masa amma baicimma komaiba akan aikin saboda abubuwa sunyimai yawa da darenne kawai yakeda lokaci
Nandai yayanke shawarar zai fad'awa Umar din wataKilama yasamu taimakonsa Dan yasan Umar ma ba bayaba Usmanne shashashan nan ya kwanta da 'Kudirin zai fad'awa Dan uwansa aikinda yakeyi tareda Neman had'in kansa wajen tayashi binciken cikin sirri.
*_wae kulli kenan kubiyoni a next page_*
_share and comments plx_
*_Leemart Yar pilloh_*ππππ
[4/18, 11:47 AM] Leemarh Phillo: πͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺ
*A WANI GARI*
πͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺπͺ
*NA*
*_Leemart Yar pilloh_*π²
*Ψ¨Ψ³Ω Ψ§ΩΩΩ Ψ§ΩΨ±ΨΩ Ω Ψ§ΩΨ±ΨΩΩ *
*____________________________________________*
Β©π
*AL'UMMA WRITER'S ASSO...* βπ»
_Aβ’ Wβ’ Aβ’_
_{{Al'umma writers_
_Kungiya daya tamkar da dubu farin cikin mu mu fadakar da Al'umma domin su farfado sugane gsky al'umma sai dan Al'umma Allah ya bamu ikon fadakar da Al'umma}}_
https://www.facebook.com/Alumma-Writers-Association-101394218126525/?referrer=whatsapp
*_________________________________________*
_sadaukarwa ga dukkan a wani gari fans INA matuqar jindadin yadda kuke qaunar wannan littafin love you so much_
*_page 8_9_*
Koda suka tashi da safe Sam baibi takan aikinsa ba saboda yadda yaga Umar yasa mai ido ya kasa ya tsare duk inda yayi hankalinshi nakai shiyasama yayi tamkar bai luraba yashiga cikin garden yazauna yana karanta news paper saidai gaba d'aya hankalinshi baya kai kawai tunanin aikinsa yake.
Jin alamun