Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 10
natashin hankali xai iyahaɗiyar xuciya ya mutu,ajemata ledar hannunsa yayi daƙyar ya iyabuɗa bakinsa yayi magana Dik wani avu daxan samu aduniya barin mallakarkine atare dani,rasaki yana nufin tamƙar rasa komai ne arayuwar mahmud.kisa aranki kamar yadda kike arubuce axuciyata kamar yadda kike axane aƙwaƙwalwata, haka kike kwance har yanxu acikin ruhina, allah ne yahaɗamu, .. .... Hawaye yaxiraro masa Banaso yarabamu nawwara,gashi bawata mafita, inaroƙonki daki daina kuka mucigaba da addu ah allah yasassauta mana, Taɗaga kai alaman toh Wannan ledar kibuɗe ciki xakiga kullin ƙyalle bantaɓa buɗewa ko dubawaba domin amanace akabani inbaki baffa,kuma gata loƙacin daya dace inbakiyayi, Dasauri taɗaukiledar tana ƙamƙameta ajikinta tafashe dakuka gwanin tausayi ta tina baffanta da innarta ganin baxai iyajurewa kallonta tana kuka ba yasa yafice yana sharar ƙwallah. Ɗakinta tanufa tanasharar ƙwallah hajia dake ƙoƙarin jona tv tagirgixa kai Nawwara Takira sunanta juyowa tayi tana duban hajia Xo inason xanyi magana dake Tohm tace tanadawowa Bayanta xauna tace Gani hajia. "Yawwa nawwara nikuwa intambayeki anya kuwa kinason aurennan na dr yusrab batakurawa kanki kikeso kiyiba. Nifa banaso ayi abundaxa axo hayaniya dagabaya. Tasunkuyan dakai tana wasa da 'yan yatsun hannunta "Bakomai hajia nixan auri dr yusrab ne domin allah kuma sbd allah zanxauna dashi ba abindaxai faru kawai dai fatana mahaifiyarshi takasance tana sona da 'yan uwanshi,hakan shine xaibani ƙwarin gwiwar samun sauƙin komai, Hajia tai murmushi Ayya karki damu indai dan wannan ne don hajia turai wlh bakida masalada ita macece mai mutumchi tanada kirki sosai.yanxu kinga abundaxami farayi shine inkintsaki saiki maida hankali kan gyaran da akemiki dan allah karki wasa kuma inaso kikira sumayya kifaɗamata ranan monday saitaxo kufita da ita kasuwa akwai abindayakamata kije keda ita kusayo. Aa hajia ni daga wajena bana buƙatar komai bayan abindakikayi dakanki hakama nagode allah yasaka da alkhairi,amma banajin akwai wani taro daxanyi wanne har nake buƙatar wani ƙƴaleƙƴale, baxankomaiba, Hajia takalleta da mamaki duk datasan abundake damunta tabbas batada sukunin sakin jiki dakomai shiyasa take tausayinta tajanyota jikinta Ki kwantar da hankalinki nawwara kuma kiyi haƙuri,insha allahu mahmud da kikarasa yusrab xaimaye miki gurbinsa koma ƴafisa sonki daƙaunarki.da tattalinki, xakidaina wannan xuvar hawaye albarkan annabi (s.a.w.)maxakidaina damunkanki wannan wani jarabawane daga Allah kiƙoƙarin cinyewa saikiga ƙyaƙƙyawan sakamako,kinji,kuma nixanta tayaki addu ah insha Allahu. Tailamo ajikin hajia tana jin nasihar datakemata na shiga jikinta ranta yayi sanyi xuciyarta tarage xafin datakeyi, talalubi hannun hajia tariƙe kam. Ranan monday sumayya taxo sunatareda nawwara bayan maimata gyara tagama mata dilka suka shirya domin tafiya kasuwa liƙaf tasa da safa aƙafarta hannunta ne ƙaɗai awaje yasha gyara yatsun nan sunyi kyau dawani haske fatarta tayiwani laushi da santsi, drivan hajia musa shima saikallonta yake kafin tasaki liƙaf ɗin tana lura taisauri tasaki liƙaf ɗin tana tsaki sumayya ta kalleta Ke kuma sarkin masifa dawa?kike tsaki, Wancan mutumin mana kinga kwa yadda yaxubomani ido . Dariya sumayya tayi Kai naxatama wani abune wlh, ai dole yakalleƙi waikinganki kuwa yadda kika koma? Ai inamaifaɗamiki kalloma sai Dr yasaki agaba Tace uhumm basai yaytayi ba wlh idan naga kallon xaiyawa saina tashi nabasa gu. Humm kinga nawwara yakamata ki aje komai ki basa kulawa tunda kin amince xaki auresa baikamata ki ɗauki masa wani rayuwa dabanba dole kije dasabuwar yanayi dakuma niyyar ibadaxaki kikuma manta da maganar modibbo tunda shi dr time ɗin hs your husbnd kingane Tagirgixa kai idanunta cike daƙwallah tasa hannunta abayanta tana harɗesu taja tatsaya jikin motar Kinsanya xuciyata acikin wani sabon tunanin dabansan menene sakamakon ƙarshensaba, gaskiyar lamarin kuwa sumayya xuciyata kullalliyar ƙoface wadda bawanda take jirayaxo gareta face modibbo, Sumayya taxaro ido Mekike nufi kuma da auren dr yusrab nawwara karki fa cutarda xuciyar datake sonki dagangan akan ahlin da basa maraba dake, Shine dalilin daya dakatar dani daga xuwa rayuwar modibbo,domin baxantaɓa auren namijin da mahaifiyansa bata sonaba komi son da inkemasa xanbarsa kuma naƙƴale rayuwansa duka, amma tayaya kike tsammanin xan iya kankare soyayyar dataginu tindaga wani loƙaci xuwa yanxu? Hawaye suka fara silalowa daga gurbin idanunta Nayi iya ƙoƙarina nakasa amma dan allah kisani a addu anki daxaran kinsallah bana fidda rabo darahman ubangiji tunda ina raye. Shikenan bakomai allah yataimake. Amin Suka shiga yajamotan, Xaune take tana daddannan waya kausar tashigo tana jan akatinta jikin ammu tafaɗa tana murmushi Angaida yarinyata harkinfito? Taɗaga kai Eh inaso naje da wuri kinga nima ammin ƙunshi hajia tace yanxu maiƙunshin xataxo tayima amaryan, Toh shikenan nima ai xanxo amma sai ranan laraban Kausar taɗan xame daga jikinta tana xaunawa Ammu amma xaki kai amaryan kema ko? Eh xankaita tunda batafiyar dare bane da la asar kikace xa atafikantan. Tohm bari naje Taima ammu sallama tanufi maimuna dake xaune ko kallonsu bataiba amma tanajin maganar dasuke amma bata fahimchi maganar auren dasukeba domin gidan hajia waxa a aurar kuma, Anty nixantafi saikuma bayan kwana biyu Me akeyi agidan hajiar Tai murmushi Bikin anty nawwara ake Tashi taƴi dasauri tana mamaki Touu agidan hajia kuma akacemiki? Wayafaɗamiki? Aa anty bakisaniba toh kwa bikinta ake hajiyace tafaɗamin kuma itama nawwara tanakirana mugaisa har pic ɗin angon nagani Maimuna ta harareta ganin wani murnada ximuɗi da kausar take Hum wanene angon Wannan babban likitan kashin wanda yake magana agidan tv n arewa 24 DR YUSRAB YAKUB Tsaye maimunatu ta miƙe tana dafe ƙirjinta Ammu tai tsaki Kausar tamiƙe Anty lafiya kuwa ? Tureta tayi tawuce samada gudu Kausar tayima ammu sallama tafita pking spce tasamu drva yana ganinta yashiga maxauninsa itama baya tabuɗe taxauna tukunna yaja suka fice, cikin loƙacin dabaxa ace maitsayiba yakaita, hajia tajidaɗin ganinta don haka dasauri tarumgumi jikartata "'yar albarkata har kin ƙaraso? Taɗane hajia tana dariya (dayake kausar dama akwai fara ah kawa gonar audiga) "bikinamu hajjo kinga aibama xaunaba, Hajia taƙƴalƙyale da dariya "yayi ja ira saiki shiga ciki ai suna ciki itada sumayya Ehu tasaki tana faɗawa jikin nawwara "wayyo anty amarya kinganki kuwa ? Sumayya tafashe da dariya nawwara tai murmushi Ke aibakyajin magana kausar saikace kinga wata baturiya wannan ehun Hhh wlh nikam karki sagemin gwiwa kibarni kawai nagama yabonki domin nadaɗe banga amaryan data haɗu ba gyara yakarɓrta kamar hakaba, kinyi haske sosai. Faɗamata dai ni nafaɗa tagwaɓi bakina Sumayya tace tana dariya Nawwara takallesu Tohm naji amma ku sai kunfini haɗuwa loƙacin daxa amaku donhaka dan allah kudaina xigani. Suduka sukai dariya nawara tai farinciki sosai da yadda kausar ke ƙaunarta da nunamata kulawa tamkar ƙanwarta hata wankinkai kausarce tahaɗo mayukan wankekai da shampoo kalakala tawankemata kai yayikyau sosai sannan taimata wankin ƙafa ƙarfe huɗu mai ƙunshin taxo sumayya tanacan itama tana wankin ƙafa amarya xa afarayiwa. .............................................................. Game da maimunatu kuwa tanashiga ɗaki tasaka hannu aka, "menene yake shirin faruwa dani dik wanda nakeso shine yakesonta ko itace take bibiyata, dr yusrab ɗan gidan alhaji yakub nera chab Tachiji yatsan hannunta Lallai nayi sakachi amma yaxama dole naɗau mataki akan wannan al amarin wannan 'yarƙauyen bata isa taci tuwo akainaba xannuna mata nawa irin ƙarfin Taɗau keyy tafita Kaitsaye gidansu nancy tapaka motar ta tafito Mameen nancy dama batanan falon bakowa sai kayan kallo da ke yi ɗakin nancy tafaɗa tana kuka dasauri taƙarasa inda tahangenta tare da riƙe kafaɗarta tafashe dakuka cikin tashin hankali nancy dake gabam mirror axaune tana make up,ta aje soson shafa powdern tana karkato da hankalinta kanta Menene yasameki maimuna,nasan ko menene wannan baƙaramin abu bane tunda hawayenki suka kai daxuba tabbas babban abune Yakamata kuma kimin bayani sai musam abinyi domin kukan bashine xaimaganin damuwarba Taɗago kanta fuskarnan tai jaxur tadubi nancy "narasa yayaxanyi najidaɗin rayuwata nancƴ komai taɓarɓarewa yake abubuwa nadagulewa.wannan yarinyar bibiyata take tana kashen farinciki Wacece Nancy ta tanbaya ranta aɓace Nawwara yarinyar datakemani aiki dah Tohh ina ɗan uwan natakuma bataredashi sukeva Bansan komai akaiba nima naji kausar namaganar da ammu ne. Kuma kinji sosai dakyau dr yusrab ne xata aura Tamatse ƙwallar dake xuba aidanunta Naji sosai nancy domin har hotonsa kausar ta nunamin Kutmeleesin nima xangoyi bayanki akan kowanne matakine kiɗauka akanta wlh Wanne mataki kuwa bayan jibi ɗaurin auren nariga danayi sakacin dayarinyar can taga lagona,ba abindayaragemin kamar naɗaufansa narikita raƴuwarta tarasa menene yake mata daɗi arayuwa har baƙinciki yaxama sila na mutuwarta Nancy ta gyara xamanta ranta aɓace itama domin itama tanason dr yusrab tasha sauraronsa dakallonsa agidan tv amma ganin yadda maimuna ta fita tafiya asonshi ƴasa tahaƙura takƴalemata batama nunamata cewa ta taɓa jinsonsaba sbd yadda nancy ke son maimna haka itama takesonta abotace tinsuna yara sintaso atare sunshaƙu baɗankaɗan ba. Maimuna yakamata musan abinyi duk da loƙaci yaƙure baxamurasa mafitaba Maimina ta sauke ajiyan xuciya Hum bayanxuva dole mujira bayan bikin amma dik yadda xanyi baxantaba bari ta mallakeshiba amma tayaya kiban shawara Yawwa kinsan minene kuwa xa ayi nancy tafaɗa tana murmushi Maimuna ta janyota saikinfaɗa Tajawo kunnenta xo kiji Dariya naga suduka sunfashe da ita harda kwanciya sannan maimuna tadubi nancy Kai amma ke kam baƙaramar 'yar iskabace nancy shiyasa kullum ƙara alfahari nike dake wlh banaƙunchi saikin kawo mana mafita hakan xa ayi amma kinsan kausarfa tasan banashiri da nawwara xata xargi wani abu Hmm halina dake tsoro m.saraki um um ƙanwarkice ke bakinsan yadda xaki da ita tabi setiba, Tohm shikenan xanƙoƙari amma kema ki amsomin toh saƙon gobe xanje gidan hajiar baxanshigaba xankira kausarɗinkawai. Nancy tai dariya Xakisha mamaki wlh wata ƙila ranan da aka kaitan xa tadawo. Hhhhhhhhh Ke muguwace kur anin allah suka ƙara fashewa da dariya kafin sufaɗakuma hiran duniyarsu. .......................................................................... Gameda ango kuwa dama yayiginin gidansa 'yan gyarar rakine waɗanda ba arasaba suka rage baiba kuma cikin kwana bakwai aka kammala komai, kusa da gidan iyayensa yake domin gida huɗune tsakaninsa da gidansu,masha allah gidane babba harda sama yaykyau sosai ankuma kashema ginin kuɗi, domin yaune akaje akayijere harda kausar da sumayya da kawar hajia da makwafta tamkar bikin da akaɗaɗe ana shiryasa inkaga yadda mutane ke xuwa gidan hajia allah sanya alkhairi duk da hajia dama mai jama ahce sosai sbd kirkinta ga ƙyauta sam batada ƙyashi ko hassada kuma gatausayin marayu da marasa ƙarfi, tana talfawa mutane dadama dagidajen marayu. Sumayya tayi santin gidan nawwara sosai ɗakinda nawwara keciki anayimata siracen turareta shiga tasameta hartagama siracen tanaxaune tana shafa ruwan turare. Irin wanda bayan yayi awa biyu ajikinki xakije kiwanka daruwan ɗumi, "kaiiii masha allah nawwara ki godemawa allah dayabaki dr yusrab sannan ki godewa hajia da irin ƙaunar datake nunamiki kai yawwa naga al amura ni summyy. Nawwara tai murmushi ta tana ƙasa dakai tareda dangwale tiraren tagoga awuyanta, Hakane allahamdulillahi akullum inaƙara godewa allah da ni imominsa gareni sumayya tabbas hajia tamin komai har bansan dami xansakamataba domin taji irin wannan abindanake ji araina idan nadubeta tabbas abindatakemin ko 'yarta tacikinta tamawa xatajinjina mata allah yaja daran hajia sista Sumayya tace Amin ai addu ah koni xanɗau ɗamarar yimawa hajia kodayaushe domin taibajinta nawwara saikinje kinga ɗakinki kinga yadda akaxuba miki kaya fitinannon kaya wlh najidaɗi komai litegreen gafentin gidan milk and darkgreen allahumma arxiƙuna irinshi. Nawwara ta harareta nawasa Kai kai sumayya kinfiye xuxuta abu allah....... saikuma taishuru Yakikai shuru ko daga wannan har nafasa miki kai toh karki bari yafashe domin daima jibin naganki aciki xakiga tsokana kinsanfa ni sainajira ango yashigo. Nawwara ta dafe ƙirjinta tana bin sumayya da kallo. Baxakisamu tukuiciba sumayya da ma dama ace nida modibbona xa aɗaura mana aure jibi dama ummah ki amince da aurenmu danafi kowa farinciki loƙacin ne xantabbata amarƴa kamar kowacce lo.......................... Ya isa Sumayya tadakatar da ita ranta abace Kinaɓatamin rai ƙwarai nawwara,bansanke axxalima bace saiyanxu,sokike lallai saikin tabbatar min dawani ɓoyayyen abundake xuciyarki,tohm kinga indai wannan cutar ne baxa ayita daniba xanbar gidan bikinnan baxaki ƙaraganina ba harsai kinfasa cutar wannan bawan allah daxakikaiwa bikinciki gida,zaki kai soƴayyar wani har cikin gidansa menene ribar auren nasa dake? dasauri tai ƙofar fita tana mai jinɗacin abin danawwara take ƙoƙarinyi Sam bataso tayaudari yusrab bawan allahne baya da niyyar yaudara acikin al amarinsa Dagudu nawwara tariƙeta tabaya tana kuka "Karkimin haka dan allah kinsan damuwata balaifina bane kitayani addu ah amma baxanfasa auren dr yusrab ba domin yamin halacci yasoni ayadda nake dashi da ahlinsa basu gujeniba tabbas irinsune ahlin danake ta burin naraƴu cikinsu tin abaya amma xuciyata tanaso tafi ƙarfina,akan modibbo bana banbance fari da baƙi, why? Sumayya baƙaramin tausayamata tayiba donhaka suka riƙe juna kowacce na kuka,akarasa mararrashin wani har sukagaji sukayi shuru, Bayan sallan isha i Dr yusrab yaxo gidan hajia falon baki akamasa iso kafin sumayya takaimasa amaryan tasa,nawwara sanye take cikin doguwar riga saiwani katon hijabi data saka har yanajanƙasa tanemi kujera ɗaya dake nesa dashi taxauna sumayya ce sukagaisa dashi harda yar fira tabarkwanci sukayi sannan sumayya ta tafi tabasu waje duk da dama nawwara dik maganar sukeyi batasa musu bakiba da ido kawai take binsu tamkar kurma, sumayya kuwa itakanta tayaba da Dr yusrab domin yahaɗu aganinta ma haryafi modibbo nesa bakusaba amma nawwara xataiwasa da damarta,yabirgeta sosai yadda yake komainasa anitse,magana ma kowacce amahallinta take xuwa gwanin sha awa, allah yabarku tare,tafaɗa aranta. Dr yusrab dai dogone samɓal mai ɗan kaurin jiki basosaiba tareda doguwar fuskar maiɗaukeda dogon hanchi da kyawawan idanu masu haske,fatarsa kalace maikyau baƙi mai siminti tamkar jikin tarwaɗa,yakasance mai kyan diri domin 'yanmata dayawa sunfirtamasa soyayƴa,yanaƙi Wannan shine dr ataƙaice Hankalinsa nakanta fitar sumayya yasa yaƙara tattaro hankalinsa kanta.murmushi kawai yakeganin yadda take wani haɗe jiki acikin hijabi,tamkar wata mara gaskiya.tamasa kyau sosai tamkar ya sace ta yatafi yakeji fuskarta yaƙaraƙyau sosai saiwani sheƙe take,gawani asirtaccen ƙamshi dayake tashi ajikinta wanda tunfarkon shigowarta yaji tamkar karyadaina shaƙa,. Amarya ta ango barka da wannan loƙaci? Nawwara tace Yawwa barkada dare. Yayi murmushi Ngde,yakuma shirye shiryen biki.inafatan dai ƙuɗin nan sun isheku gimbiyana? Tace Eh sunmayi yawa ai bari nakawoma ragowan tamiƙe dasauri sabd duk yatsaretada idanuwansa tarasa mimaxatayi,sotake kawai tabar wajensa Aa kibarshi haba k.......... Dasauri yatarota tafaɗa ƙirjinsa duka, ƙasan hijabin tatake batasaniba garin sauri tatashi. Ya allah yafurta dasauri yanamaida hannunsa yarifeta da jikinsa,Bakiɗaya tarikice sai cuku cukun ƙwacewa take, Yasaketa ta tashi dasauri tana jada baya harta kaida jikin kujera ƙasa taxube hannunta tasa abaki tareda fashewa dakuka Duk yadamu bayason damuwarta "kiyi haƙuri kidaina kuka bada gangan hakan yafaruba faɗuwa kikatafi xaki shine na........ Taɗaga masa hannu Kadaina bani haƙuri Yakalleta Toh mekikeyiwa kuka? Tamiƙe tana tangaɗi tamkar wacce tasha wani abu namaye Nima bansaniba kawai naga nima ina kuka kayi haƙuri yusrab dan allah bari nashiga gida, Yusrab yace Bangane ba har yanxu abindakike nufi nawwara bakida lafiyane? Taɗaga kai tanacewa Naji kaina yanaɗanmin ciwo kuma banagani sosai sbd jiwa nakeji Tashi yayi yaƙarasa inda tajingina da garu idanunta arufe Toh muje asibiti kawai Tace Aa Yace Kinga yaxaki kwanta baƙyajindaɗi baxaiyuwuba idan nabarki tamkar nayi wasa da lafiyarkine donhaka kixo muje kawai Bakiɗaya kanta ciwo yake bata jinkomai sai xugin dagefen kanta kema shima bajin abindayake cewa takeba Yaƙaraso inda take Nawwara! Nawwara!!nawwara!!! Shuru yaji gakuma idanunta arufe bakiɗaya yarikice yafara jijjiga hannunta saigani yaytafaɗa kan kujera yif tamkar mara numfashi dasauri yayayibeta yana jijjigata amma kaɗan kaɗan take iyaganinsa duk dabatasan itama indakanta yakeba Wayarsa ya lalubo jikinsa narawa yakira numbn hajia saigatakuwa tashigo dasauri tana rarraba ido canta hangota jikin dr yusrab bata komotsi tanaƙarasawa tarumgumota jikinta tan\a hawaye Menene yasameta Dr Shima idanuwansa tamkar maishirin kuka yace Hajia munacikin hira kawai naji tace kanta naciwo saikuma naga tamaƙale waje ɗaya Toh bari mukaita asubiti 'yar wajen kanwarta takiro dayake duk sunxo biki sinacikin gida Dan danan saigata tashigo malama suwaiba kenan Tana shigowa tace hajia lafiya Kingadai yadda yarinyar nan takoma dandanan suwaiba kamata muje musata mota akaita asubiti Suwaiba tace Subhanallahi menene yasameta baɗaxu naganta sina hirada ƙawartaba. Takama hannuta suna ƙoƙarin ɗagata suwaiba tace ba asubiti xamuba hajia aljanune sama mani xam xam Hajia tadafe ƙirji aljanu Eh sune yanxu kuma xata tashi bi ixinillahi Dr yusrab shima yaxargi hakan ganin yadda dan danan tarikice Hajia tace Wayyo allah na bari nakawo miki dama inadashi Bayantakawo tadubi dr Kaje gida dare nayi dr Ya sunkuyar dakai Aa hajia xanjira naga samun sauƙinta baxan iyatafiyaba wlh. Suwaiba nagama tufa addu o indatagama karantawa tafara yayyafa mata ruwan ajikitashafa mata afuska wata ƙara nawwara tasaki tanaxabura saikuma takoma tafaɗi tana fitar dawani huci Cannn kuma sai sukaji shuru cigabada addu ahn mlm suwaiba tayi tana tofa mata cikin ƙanƙanin loƙacin saigata tabuɗe ido takuma dawo hayyacinta,tana kallon hajia dakeriƙe da ita Dr kuma na tsaye tamkar yafashe dakuka inka kalli fuskansa , Hajia menene yafaru? Hajia tace Bakida lfy ne amma yanxu bakomai muna magana ne akanwani abu Miƙewa tayi tana kallon dr sannan tace Hajia miyasa dr baitafiba Hajia tace Eh nace yatsaya xamiwani maganane Taɗaga kai Barinaje nakwanta Tafice tana mai tunanin lfy kuwa taganta kwance tsakaninsu Bayanfitarta dr yayiwa su hajia sallama yatafi. ............................................................................ Yau tAkama talata kumaranan party masha allah amarya tayi kyau sosai dominduk wanda yaganta saiyatofa albarkachinbakinsa. Kausar tanacikin ƙawayen sumayya waɗanda tagayyato anata gyare gyaren kwalliya domin fita xa ayi prtyn wayar kausar ta shiga ƙara tana dubawataga maikiran ɗagawa tai kafin can tace Tohm inaxuwa Takashe tareda ficewa ƙarasawa tayi inda maimuna ta fKa mota tana juranta Anty maimakon ki ƙarasa saikuma kitsaya ananki kirana? Mai muna tai murmushi. Eh aikema kinsan yaddahajia ke fushini baxanshigoba Kausar tace Hum hakane amma anty kinsan illar gaba menene amfanin wannan gabar taku ni aganina nawwara batacancanci haka daga uwar ɗakinta amatsayinta na mai biyayya ba, Maimuna ta kwantar da murya Hakane maganarki kausar shiyasa nake sonki sbd kintinatar dani akan abin dayashigemin duhu dama kuma nayi wannan tunanin shiyasa makikaganni naxo yanxu domin nagyara kuskurena Murmushi kausar tayi tana maijindaɗi. Yawwa anty yanxu saikishigo xankira hajia da nawwara kuxauna asulhunta ko kai amma anty najidaɗi sosai wlh Wani murmushi maimuna tayi tare da kanne ido bayan tafaki idon kausar Aa bayanxu ba wannan saibayanbiki xanje hargidan ita nawwara hajia kuma jibi xanxo nabata haƙuri amma yanxu hajia batagama hucewaba ba xata saurareniba Anty hajia tanadasauƙin kai baxataƙi amsar haƙurinkiba. Kausar baxan iyashigaba domin komai xai iyafaruwa in hajia taganni yanxu . Shikenan anty Maimuna tagyara tsaiwarta tana ɗauko wani kwali tamiƙawa kausar Amsa tayi tace antƴ namaye kuma wannan Nawwara xaki baiwa shi amma amatsayinkece kikabata gift na aure Taiƙasa dakanta hawaye naƙoƙarin xubowa daga idaniyarta Kausar nayi nadama har xuciyata ta bani shawarar nayiwa nawwara alkhairi amma idan nace xanfuskanceta nabata xargine xaishiga xuciyarta hakama hajia sbd ƙiyayya dana nunamata abaya .yanxu nayi nadama wlh,akwai wasu kayama danasa nancy tasiyomata intaje dibai,wannanɗin ki bata kitabbatar kuma kinbata,nasan inkika ce daga garekine koxatafi sakin rai tai amfani dashi, yanadakyau turare shiyasa naxaɓi nakawo mata. Jijjuya kwalin kausar tafarayi tana murmushi. "Wow anty wannan turaren baƙaramin ƙamshi xaiba daga ganinsa shikenan xanbata kuma kin kyauta abin alkhaiein yanadakyau kuma najidaɗin sauya tunaninki dakikayi akan anty nawwara yanxu bari nakoma xami fitane party. Ok saikun dawo .tashige motarta taja kausar takoma gidan bikin cikin jakar ta tasa turaren domin yanxu amarya nacikin mutane batada loƙaci, tanajira xuwa dare tabata. 😎tohhh fa kunji wata kutungular shin mai maimunatu ke ƙoƙarin yine? Bari dai muje mugani kucigabada bina inatare daku 😎 Sanye take cikin kaya masu matuƙar kƴau da ƙayatarwa domin baƙaramin ƙuɗi akaxuba akasiya tufafinba, masha allah nawwara tasha ƙyau sosai dikka wanda yaganta awannan loƙacin saiya yaba kƴawun da allah yayimata, Bayan motoce sungama xuwa naɗaukar su xuwa wajen dna, motarda ango ke ciki kausar tabuɗe tasa amarƴa kafin kuma sauran 'yanbiki sushishshiga atafi wajen dna, Kanta aƙasa yake tin dataxauna har akafara tafiya,ko motsinkirki takasa yi. Dr yusrab da yamutu akallon tauratuwartasa sam yakasa mallakar kansa idanuwansa kuwa ko ƙiftawa bayayi daga gareta domin gani ƴake tamkar xataɓace wa ganinsa lallai nawwara kƴautar allah ce xuwa garesa,ahankali ya lumshe kyawawan iɗanuwansa masu kyangani,tare da ƙara ɗorasu akan hannun nawwara dake sarƙe da ɗaya hannun,yasha ƙunshi haɗaɗɗe gwanin sha awa ,baƙaramin ƙyau hannaƴenta sukayiba gawasu awarwaraƴe masu ƙyalli na gwal da hajia tasiyamata sarkan wuyantama nadubu tamanin ne, sai sheƙi awarwaron keyi, hannun dr har rawa yake ya isa ga nata hannun amma kafin yaƙarasa riƙe hannunta wayarsa dake gaban rigarsa tai kuka, tsaki yaja yanaɗaukowa yaga aminace ƙanwarsa tsaki yayi yana ɗaga wayar cikin ƙanƙanin loƙaci yakashe yana matsowa kusa da nawwara fuskarsa cike da farinciki, Amincin allah yatabbata agareki amaryata Batare da ta motsa daga inda takeba tai shuru nawani loƙaci kafin tace Amin, Yasa hannusa cikin nata yana murmushi kin haɗu amaryata tamkar xamu gasar ƙƴau, Tai shuru yasake matse hannunta Koda gasar kƴau xamu natabbata tauraruwata itace xata lashe gasa domin tadabance ita. Taimurmushi tana janye hannunta daga nashi Hunm ngde,ango Mamaki xaiji ko daɗi dajin wannan furicin daga gareta domin. Batakasance maisakin jiki dashiba balle yay tunanin samun wannan daddaɗan sunan daga gareta ANGO Hannunsa duk biyun yasa yarumgumota gabaɗaya tafaɗa jikinsa yana sauke ajiƴar xuciya, Yunƙurin tashi tayi yamaidata tareda kai bakinsa setin kunnenta yana yimata raɗa. Ƙasa tayi dakanta cikin ƙirjinsa tana lafewa tamkar mage tasamu jikin mutum, hannunsa ɗayan yasa yakamo hannunta yana murxawa tare da yabon ƙunshinta, "Drrrrr....... Taimaganar acan ƙasan maƙoshinta shima daƙyar yaji, sbd yadda taja sunan Ganin yadda dik tawani shagwaɓe yasa yaƙara rikicewa tareda axama wajen mannata aƙirjinsa yana lallashinta cikin tattausan lafaxi,maiɗauke da sigogin ƙauna muraran, baƴason komai ƙanƙantar abu yashiga tsakaninsa da nawwara,yanajin tamkar su dauwama ahaka Tanajikinsa alafe har aka ƙarasa wajen dna abokinsa taufiq dake drivan nasu sai tsaki yake kuwa,tinfarkon faruwan abun yanakallon su ta mudibu inya haɗa ido da yusrab saiya kashe masa ido, donhaka ganin har yafaka apaking spce basu daniyar fitowa yasa cikin xafi yajuyo yakallesa yaga yadda yakanainayeta ajikinsa tamkar wacce xa akwace masa yarufe ido kuma tamkar mai bacci Taufiq yakuma jantsaki yana masa magana "Ɗan isaka kawai kaga da allah wani salon iskancin ƙuma toh aisaika fitokasaki yarinyar mutane gobe gobe nan dai xata xama taka duka, Dr yusrab da cikin salonsa na inyaso yabuɗe idanunsa ahankali yanasaukesu akan fuskar taufiq wanda saiharara yake gallamasa jeri jeri, Ɗauke kansa yayi yana laso leɓansa naƙasa. Idanunsa tamkar maijin barchi Kaga da allah malam jeka baruwanka da fitowarmu aa in iskanci yabirgeƙa kaima kaje kayi, Jin abin da Dr yacene yasa taufiq fusata yakwalla masa harara yafice yabasu gu kawai yashige filin dna Sannu ahankali yaɗagota daga jikinsa yana taƙoƙarin haɗa idanuwansu wuri ɗaya amma abin yagagara domin taƙi sam, haka yahaƙura ganin suna ɓata loƙaci yasa yay axamar gyaramata rufewar net ɗin dake lilliɓe da fuskarta sannan yakama hannunta suka fito,wow masha allah fans saikunga waɗannan ma aurata juna don ko hasidin, Dashigowarsu cikin filin hol ɗin akaɗau tafi da murna da farinciki, dandanan mutane akashiga ɗaɗɗaukarsu foto da wayoyi, masu watsa falawa nayi. Anyi pty lfy angama lfy domin ƙarfe tara akatashi.sannan akadawo gida nanma Dr dakyar yarabuda nawwara,tashiga gida tamkar xaicinyeta sbd so. Ita har tsoroma tafaraji wannan wanna irin so yakemata, amma koda ta tambayi xuciyarta saitarasa amsa takamawa donhaka ta tattara tunanin tawatsar,, Game da amina kanwar Dr da kawayenta biyar dasuka halacci ptyn kuwa sinyaba da nawwara ɗari bisa ɗari saiwani abudaya tsayama amina arai shine yadda kowa yake faɗar kamanninta da nawwara har iƙlima ƙawartama tace yanaga kuna bala in kamada amaryar yayanki, amina tace ikon allah kenan ai, daganan tawatsar ita,. Musalin ƙarfe goma akaɗaura auren. Dr yusrab yaƙub da nawwara ibrahim, tare daɗinbin mutanen dasuka halacci ɗaurin auren, suka shaida bayan gabatarda hotinan da gaisuwar sirikai ango sukatafi.amarya kwa tundaga loƙacin da akaɗaura auren taɓalle da kuka har kawo yanxu,ƙarfe takwas nadare kenan datake cikin shirinta natafiya gidanmijinta adirƙushetake gaban hajia tana maixubar. Hawaye tamkar ba gobe,tafaɗa jikin hajia tana kuka ta ƙamƙameta itama hajia yitake tana rarrashinta ahaka tana riƙe da ita ta tashi jin anafaɗin afito da amarya harbakin mota ta isa da ita taibismillah tare da addu o i taxaunar da ita nawwara tariƙe hannun hajia kam saikuka take gwanin tausayi. Haka hajia taxare hannunta daga na nawwara tajuya gida dasauri tana sharar kwallah, Motocin kai amarya suka ɗaga, Kausar da sumayya ma sun sha kuka loƙacin da xa adawo dasu suka ƙamƙame nawwara tanayi suma sunayi sumayyace tafara fita kafin kausar tabita saita tina tadawo turaren dake jakarta taɗauko tadanƙamata wannan tukuichine daga gareni antƴ nawwara ki amfani dashi yanadakyau sosai tafice itama Kafin Dr da abokansa sushigo ta tashi taboye turaren sannan takoma taxauna tana rufe kanta, ba ajimaba kuwa suka shigo taredashi da abokansa uku taufiq da aisar da saddam, sunyi nsiha wa amarya da ango sannan suka yi barkwancinsu daga ƙarshe suka gabatarda kansu wa amarya sannan suka yi addu ah sukatafi binsu dr yayi domin rakiya tana kallon fitarsa ta tashi tasa key abedrom ɗin Kodaya dawo yaduba yaga abindatayi murmushi yayi kawai yafice ɗakinsa shima cikeda gajiyar viki ruwa yawatsa tukunna yakwanta,xuciyarsa cike da tunanin amaryartasa maikyau, .🌱🍯🌱🌱🍯🌱🐝🌱 🌱🍯🌱🌱🍯🌱🌱🌱 🌼🌱 MURNAN SALLAH augst 11,2019🌱🌼 Allahamdulillah Allahamdulillah godiya ƙwarai wa allahn annabi muhammad(s.a.w), bayada haka kuma ni SHAMSIYYA ADAM inataya 'yan uwa da avokan arxiƙi murnan wannan rana mai albarka ta bikin babban sallah.allah yasa aibikin sallah lafiya agama lfy,ubangiji allah yaxaunar manada ƙasar mu lfy yashiryamu shirin addinin muslinci allah kajiƙan kahkata FAƊIMATU (jummai)ka jikan dikkan al unmar musulmai waɗanda suka rigamu gidan gaskiya,amin,👋👋ƴanxu haka munhanyarmu nadawo wa daga sallan idi masha allah inacikin

Chapter 8 of 10