Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 7
kaga ko yanxu fa masu aikin gidana danake baka labari bankarasa maka ba kwanakin baya maryam da rahma. Eh anyi haka ba wadanda kace min akauyen kungu suke ba kakarsu ce takawo maka su kanema musu aiki? Yawwa abokina anyi haka kuwa hmm ai gidana na kawosu nakori wadancan tunda sukam sungama isata saina sake xubi malam ai inasamin komi yadda nake so musamman rahma 'yar duma dumata waii ba amagana inaji da ita domin tana farantamin sosai 'yar jar uwa ga salo da iyayi tamkar wata wayayyiya aini kaganni ko futa banayi da wuri sai maman suhail tafara futa office tohm saina fara barje gumi na sannan nayi wanka nima nafita office, Dariya sukeyi sosai Ai alej nura kana sha aninka kai yanxu baxakadaina iskancin nan nakaba saikasamu yaran mutane kaita suburbuda Duka yakai ma Alhaji sanam yanacewa Ay karkasoma cewa komi shiri ar ka ko alahira mai lasisi ce domin kuwa kayiwa Allah shishshigi dayawa kakuma hada gona biyu guri daya bayan Allah dakansa yaharamta aikata hakan ka kuka dakanka xina kodayaushe Allah xai iya shiryana mikewa Alhaji sanam yayi Tohm gayamin magana tunda naxo gidnka Aa ba.......... Cak Alhaji nura yatsaya da maganar sa yana kallon maman suhail data shigo hannunta rike da wuka har biyu fuskarta jage jage da hawaye alamun taci kukan tagaji Xai magana tadaga. Masa hannu πŸ’›πŸ’›πŸ’›πŸ’›πŸ’›πŸ’› Hajia aina tare da Alhaji uba bisa falo tagama xayyane masa kome game da ismat baiji dadi ba kuma hankalin sa yatashi domin kuwa yanajin sunan yagane wanene sbda shine tsohon mijin jamila kanwar sa wanda suka rabu yanxu tayi aure yaranta uku, awani gidan, Xandau mataki akansa hajia sai yagane bai dawaye xankai karar sa koto ranar monday sai anfitar ma da yarinya hakkinta Kwarai makuwa hakan yayi dai dai amma yanxu inaso da nadauki yarinyar muje gurin mamanta sbda kullum kukanta daya ina mamanta ni tausayinta hanani sakat yake wlh Umm tohm aibakomi xaku iya xuwa amma kutafi da sojeji uku atare daku sbda gudun faruwar wani abu Tohm shikenan Alhaji hakan xa ayi Yamike tare da gyara xaman hulansa Yajikin Mihran kuwa na shiga wajen nasa bayanan ko har yafara futane Mikewa tayi rike da jakansa akafadanta Eh jiki Allahamdulillahi yafita ne wurin imran sbda sucigaba da shirye shirye lokacin dayashigo kakoma bacci Alhj uba yayi murmushi tare da cewa Kai ikon Allah kenan yanxu har komi ya wuce kenan aidani daga bikin xanyi amma tunda yasamu lfy sai ayidin Allah yasa albarka Amin alhaji ai gobe ne xa akai lefe nace tunda dama anfadawa gidan su yarinyar Toh toh bashakka ai yayi kinga juma ah sai adaura aure kawai Eh Tohm yayi bari nawuce office ko Tai murmushi tana binsa abaya kamar yadda yabukata. Ismat nasamun kulawa sosai awurin hajia aina balaifi tadan saki jikinta amma rama kam tayi kamar me jinya sbda tunanin yau daban nagobe daban ga kuka idan tafara hajia bata iya rarrashinta Mihran ne yashigo falon time din hajia nata kwallawa ismat kira tafuta xasu tafi gidan maman nata Hajia na ina kuma xuwa haka dayamma sakaliya Tai dariya Unguwa xani da ni da yarinya ta tunda kai nakusa aurar dakai nan da kwana five kayi gidan kaka duk da acikin guri daya muke amma ai kagirma Ya sunkuyar dakai yana murmushi Hum nifa baxan girma ba hajia wannan yarinyantaki nibantaba ganin taba Anya ba 'yar tsana bace Tai mai dakuwa dai dai lokacin da ismat tafuto hannunta rike da hijabi tana kokarin sawa, Cak ta tsaya shima yayi fasta kafin tafara motsawa ahankali takaraso gaban halia Umma (dayake haka take kiranta) Kinsan sa mihran ne fa shine wanda nabaki labarinsa umma waye shi awurinki Hajia aina takalleta tana kallon sa Kaman ya dama mihran nawa shine wanda kike ban labari Hajia ta hakane wannan itace ismat saidai bansan meyahada ta dagidanmu ba tunda babu wata halaka tsakanina da ita itadakanta tace narabu da ita hajia ta karki saurareta karki mata itace silar ciwon danki wanda nasha fama tadawo takuma famani toh karya kike wlh domin kuwa tuni nagama wancakalar dake daga jikina ganinki ba abundaxai karan bakuma xai rageniba hajia ki kyaleta karki taba saurarinta Rikeshi hajia tayi ganin xaifadi tana xaunan dashi akujera tafara kiran kima kima daya daga cikin sojojin dake gidan kenan Kakira min alhaji jikin MIHRAN xaitashi Dasauri kima yaxaro wayarsa dake aljihu yafara kiran alhaji uba Ismat kam bakidaya kanta ya kulle sama sama take kallonsu Alhaji uba yayi sallama arude yashigo tare da tallafo mihran jikinsa yana shafa fuskarsa Karka karaya dah na dan Allah karkabari kamutu kabarni mihran bani dakowa saikai dan Allah karka mutu alhaji yafara sharar kwalla Dauko min magungunansa hajia xuciyarsa nabugawa dasauri dasauri Dakinsa tashiga tadebo alhaji ne yashiga basa yana shafa kansa Hajia menene yafaru me yatada masa da hankali haka ko kinmanta abinda likita yafadamana ne akan kar asake arinka bata masa rai ko yarinka ganin abindaxai tada masa da hankali Itama hankalin ta atashe tafara kora masa bayani duk abin daya faru kaf yanxun Ransa abace yadago idaninsa jaxur yaxuba akan ismat dake rakube da bangu kirjinta sai lugude yake ga wasu xafafan hawaye dake bin kuncinta Keeeww Yadaka mata tsawa wacce tasa ismat xabura bashiri saiga futsari sannu ahankali yafara xirarowa kasa sai matse cinyoyinta take amma ina sai daya futo yajika mata xani Wannan ce dama wacce ta wulakanta min dah ke wacece kinsan waye kuwa Mihran dahar xaki shiga rayuwarsa ki damalmala kifuta sumul kinci albarkar sa wancan lokacin nakyaleki amma yanxu saikin kuka dakanki xaki xagi ita kanta kaddarar data shigo dake ahlin Uba dawud Jikinta yahau rawa da tsuma kafin Alhaji uba yakuma magana tasuma awajen saigani sikai tafadi sharaf batako motsi Hajiya aina xataje wajenta Alhaji uba yagalma ta harara Lokacin da dahna yafadi amashin gefen gari bawanda yagansa saida bugun xuciyarsa yakai mixanin karshe donhaka koda xata karasa ne bamai ceton ta agidana wama yasani ko labarin kanxon kurege tabamu sbda miyarda da ita taxo ahlin mune sbda tashiga jikinmu tasamu Mihran akaro nabiyu tunda yanxu tasan waye shi matsalar talaka kenan Hajia ai inafada miki, Hakane amma ina neman alfarma agurinka Alhaji tunda jikin nasa yalafa har yasamu bacci kiyi hakuri mana basaika hukunta yarinyar nan ba mukyaleta ma kawai tatafi dan Allah Humm yakalleta Kima Yafado falon yana kamewa Ys sir Samo ruwa kaxubawa wannan yarinyar idan tafarfado katasa keyarta tabar min gida kuma koda a unguwar nan kuka sake ganinta kadanko ta kumita ixaya wacce xata xama ko labarin mu taji saitayi kuka Angama sir Sama Alhaji uba yahaye hajiya na biye dashi Kima yafice anjima kadan yadawo hanninsa rike da gorar ruwa yabude yafara bulbuleta ajikin Ismat Atsorace tafarfado tana sakin wani kuka Dan Allah Alhaji kuyi hakuri dan Allah xantafi xan..... Kima yadaka mata tsawa Ba shiri ta mike jikinta narawa ganin falon bakowa ne yasa tadan samu rilif kima ne yatasa keyarta har sai data bar unguwar yadawo. ......................................................... Muna fukai axxalumai macuta tantiran maxinata maciya amana wlh Alhaji ka cuceni kalalatawa kanka rayuwa kuma wlh yau tunda naji irin badakalar dakuke aikatawa bamaifita adakin nan duk saina kasheku narage wa duniya mugun iri, kai yanxu Alhaji sanam jakancin naka da dabbanci har ya wuce tunani ka auri uwa sannan kaxo ka auri 'yarta inna nillahi wa inna ilaihir raji un, Allah yayimana tsari daku kuncika shedanu saina kashe ku wlh tayi kukan kura taikansu da wukaken nan dagudu Alhaji sanam yaguce takasan hannunta Alhaji nura wanda yasaki kara yana sunkuyawa yarike dukkan hannayenta yamatse Inaaa Atika baki isa ki kasheni ba wlh ina kallonki kawai baki tsaya kinsaurari xance ba xaki yanke hukunci Karya kake Alhaji komi xaka fadamin bayan wanda najiku kuna yine wlh kasakeni nace kasake ni nakashe ka koni kasheni Alhaji baxan aminta da wannan abin kunyar taka ba baxan iya kallon idanin suhail da rudwan nafada musu kai uwansu maxina ci bane baxan iyaba Tafashe da kuka tana xamewa kasa wukaken duk suka fadi Dan Allah Atika kitsaya kisaurare ni kirufamin asiri dani da abokina wlh sharrin shaitan ne kuma insha Allahu baxa mukuma maimaitawa ba kiyi hakuri kingani mijinki ne yaranmu sungirma ga 'yarmu halima gidan aure suhail da rudwan xasu tsaneni mutkar sukaji xancan nan at....... Dakata Alhaji wlh baxakataba samun rufin asiri ba mutkar daga wurina ne tunda karasa daga wurin Allah rahma cikine da ita maryam mahaka amma da banyarda ba koda likita yafadamin sbda yadda naga kame warsu ashe munafukaine nisuke hakewa wlh baxankara koda minti daya agidanka ba Alhaji har dawata dadiro ma agefe tab lallai ina maitabbatar maka na tsaneka tamike dagudu tafuta tana kuka, Rahma da maryam wadanda ke kokarin guduwa sbda jin tashin hankalin dayafaru harsunje bakin get atika dafuto kenan daga wajen Alhaji nura tararakasu da gudu tana xaginsu uwaka ubaka Shegu tsinannu karuwai dama can ko agidan iyayen naku kun lalace insha Allahu saikun nadamar aikata xina 'yan iska shidanu. Ganin sun fice daga gidan duka yasa ta dawo dakinta tana kuka tana hada kaya Rahma garin gudu tafadi wani dutse kato bakinta ydaka takwalla kara hakoranta wajen shidane suka xubo atake ko shurawa bata kumayi ba, ganin haka maryam yasa tatsuguna tatabata taji shuru alamun ta mutu wayar hannunta taxare xata gudu ashe batasani ba wasu 'yan kwamati sunhangota dasauri suka karaso suka chaf keta kai tsaye wurin 'yan sanda suka kaita ....................................................... Hussaina ganin biki yamatso sosai yanxu saura kwana uku daurin aure yasa tashirya taxo wurin maman Ismat akan taji ko Ismat nakiran gida awaya afadamata bikinta don ita bata samun layinta idan takira kullum kuma saita kira, Mama taji dadin ganin Hussaina sbda yanxu tagane Hussaina ba munafukar kawa bace yanxu idan taganta saitaji kamar taga Ismat ne Hussaina ce kenan agidan Wlh mama ina kwana Lfy kalau Hussaina yakuma hidim dimin biki ainima goben xanshigo miya Umhum mama naxone akan maganar Ismat wai dan Allah har yanxu bakyajinta ko awayane? Mama tai shuru kamar maiyin wani tunani Hakane hussaina wlh kinga tunbana damuwa har abinyaxo kuma yana damuna yanxu ko abinci bana iya ci yadda yakamata duk vanajin dadin komi tsoro nadaya shine karsakacina da amana yaxama babban kuskuren daxanyi aduniya Subhanallahi mama wai har yanxu bata taba xuwa gida ba gaskiya mama nima banji dadi ba kuma wannan abin yayi girman dayanxu baikamata ayi shuru ba, xansamu abbana nace musu adaga auren nan yadda xa ayi yanxu kenan domin yaxamar min dole na nunawa duniya Ismat kawace tagari xan nemota adik inda tashiga indai har daddy yatabbatar mana suna Nigeria Mama na sharar hawaye tace Aaa aa hussaina karki soma dosar abvanki dawannan maganar akan me wannan abin kinga ki kwantar da hankalinki shi komi ahankali ake binsa sai yatafi yadda akeso kikyalemin komi ahannuna insha Allahu kobayan andaura auren naki ne xakiji komi ake ciki tawuri na, tunda kinga ai ko shima daddyn nata yanxu ransa yabaci yace yanxu auren xaikashe kawai dakansa yatabbatar min da hakan kuma jiya saimu jira muga yadda xa ayin ko, Hussaina ranta abace take jijjigakai sbda yanxu kuma tafara xargin daddy domin kuwa yafikama da marar gaskiya Allah dai ma yasa baxuwa yayi yasayar da itaba Shikennan mama Allah yasa muji alkhairi nixan koma amma ace bikina xa ayi babu Ismat wannan wacce irin musifa ce haka bamu taba tsammanin haka arayuwar muba mama muntsara yadda komi xaitafar mana ashe baxamu cika mafarkanmu ba Allah sarki Ismat mama tasha fadamin cewa mihran shine cikon mafarkinta nikuma xahirin mafarkinta idan tarasa mu koda da rana daya ne xatayi kukan da bai da maraba da yanke kauna. Hawaye yasilalo aidanun hussaina kafin tacigaba da magana Mama yau kusan wata biyar kenan rabon danaganta taganni tanacan karkashin wanda bamu da tabbas din akwaishi ko waye, bamusan wanne hali take ba amma Allah yasani kuma yanatare da ita Allah kabayyana mana ita dan girman ixxarka da buwayar ka ya Allah Kafin hussaina takuma magana saiji tayi anfado jikin ta ansaki kuka mai karfi Mama dasauri tamike Ismat!! Hussaina ma xare jikinta take anata tana kiran Ismat kuma mama!? Jikin maman takoma tana kara sakin wani sabon kukan mai cike datashin hankali da kuma dacin abinda daddy yayi musu wanda yake taso mata daga kasan xuciya yanaxuwa wuyanta, tabbas wannan bakincikin xai iya xama ajalinta Ismat Allahamdulillahi Allah Ismat kindawo Allah shine abingodiya amma dai yasakeki ko Daga kai Ismat din tayi tana sakin maman taxauna hussaina tamatso tana rike hannun ta Ismat nayi masifar kewarki wata rayuwa tashiga tsakaninmu bansan kaddarar ma xata yanke haka da wuriba sai Allah yakawo mana karshenta da wuri tohm allahamdulillahi Batayi magana ba saibinsu dakallo kawai take amma bata iya kallon idanin mama saidai takalli hannunta dik lokacin datai kokarin hada idanu da ita sai taji wani sabon kukan yataso mata Nagode hussaina mama bari nashiga ciki Kafin tashiga hussaina tai musu sallama tatafi Alhaji sanam ne yafado falon gamamkinsa naganin Ismat Amma dayake dan duniya ne nagarari sai yawaske yafara tamke fuska sannu ahankali yatsuke fuskarsa tam. Xai wuce dakinsa mama tace Alhaji baka ga Ismat bane daxu tashigo Allah dai yataimake mu ta gudo dabamusan yayaxamiyi da wannan aure ba Yadan ja birki Hum hakan datayi yayi dai dai ai yanxu haka dakikaganni daga wajensa nake ashe sundawo Nigeria baifadamana ba amma tunda abin nasa ba mutumci dole xanraba auren baxata koma ba Yawwa alhaji hakan yayi ma Ismat dasauri takallesa sabda mamakin yadda taga ya wani waske suna hada ido yakara tamke fuska tare da jifanta da kallon gargadi yana kama kunnensa daya kafin ya dora hannun sa alebansa sannan yawuce dakinsa yanaji aransa sam baxata fadawa mamanta abindaya faru ba yasan wacece Ismat da kunya sannan ga xirfin ciki. Yau kwanan ta uku agida amma mama tarasa menene yasauyamata Ismat gabaki daya yanxu bata sakin jiki da ita kullum saikuka da xaman daki batason futowa falo kokadan saikaxo gidan kafuta bakasan tana nan ba Alhaji sanam cikin wadannan kwanakin duk afirgice yake daxaran yakoma gefe domin kuwa bakaramar fargaba ke damunsa ba gashi duk wata hanya daxata hadasa da Ismat gujewa take bata yadda su hadu ko awurin cin abinci yanxu takoma dakinta dayin komai tsoronsa daya karta fadawa mahaifiyarta abindaya faru ahankali idankadubi alhaji yarame kadan Mama ce xaune kusa dashi tana matsa masa kafa Alhaji nifa narasa ganewa yarinyar nan Ismat gabaki daya tachanja tadaina walwala tadaina shiga cikinmu agidan nan ayman kawai take mu ammala dashi kamar dah amma ninarasa kanta bataxama ko hira miya nayi nayi tafadamin menene yake damunta amma taki saitace bakomi kuma kuka take ciki kullumwannan wacce irin rayuwa ce alhaji mutum xairayu dakukane tunda dai ansamu anrabata da shi mugun mijin nata aikomi yawuce Yaja numfashi tare da hamdala sbda bata fadamata komi ba Sai ahankali xata dawo dai dai maman kamal karki rika takura mata da Allah idan tahuce xata koma kamar dah din Ai shikennan Tana cikine Yatambaya Eh tana ciki bafa ta motsawa konan dacan daga dakinta sai dakin mardiyya mai aiki idan fa tashigo tagaisheni da safe baxata dawo ba saikuma wata goben Mikewa yayi yana jinjina kai alamun baiji dadiba Tohhh baridai naje nayi mata magana baikamata kuma abarta atafi ahakanba ai da masala nixanji laifin me mukayi mata harhaka Allah yasa tafada maka kodayake aikun fi kusa Kwance take bisa gado ahannun ta waya ce tana kallon hoton mihran tsaye dakananin kaya sun amshi jikinsa kayan ga wani lafiyayyen murmushi dayake kwance afuskarsa Hawayene ke xarara bakakkautawa sbda tasan yanxu andaura masa aure da wacce yakeso tunda taji lokacin da hajia aina ke fadin saura kwana shida bikin yanxu yakama kenan gobe daurin aurensa kuma dawata ba itaba saitakara fashewa dakuka, Har daddy yashigo batasani ba jin ana murxawa kofar key yasa tamike tana binsa da kallo 'yar guntuwar kwallar dake makale a idaninta tasubuto Bakinta narawa tafara magana Kaji tsoron Allah katina mutuwa lallai babu wanda xai dauwwama aduniyar nan Ki ajiye wa axinki domin kuwa ni banaxo domin yimiki wani abu bane mutkar xaki doru akan sharudana wadanda xansa miki yanxu Tana daga kai tana ja dabaya ganin yadda yake tunkarota Xanbi Tohm xauna Tagirgixa kai alamun aa Fincikota yayi tare da rumgumeta tsamtsam ajikinsa yana shan shanar wuyanta hannunsa yasa yadanke bakinta harsai dayayi mata maxauni da cinyarsa tunkunna yasaki mata baki yafara magana Kixauna karki kokarin tashi domin kuwa mitkar kikayi kokarin tashi xanmiki abindabakya so, Tadaga kai hawaye na sintiri afuskarta kamar bagobe Kidawo da mu ammalarki ta cikin gida kirike abindaya faru matsayin sirri atsakanin mu karki sake koda wasa naji maganar nan abakin wani Takallesa tare da yin wani murmushi nakaso kanka dayawa Alhaji kenan Yaxaro ido What Ismat nine alhaji nifa daddynki ne kodakwa abindanayi miki fyadene balle aurenki nayi kuma har yau banajin hakan amatakin kuskure yanadaga cikin sharadina karki fasa kirana da daddy dik randa kika saba saina maimaita abindana yi miki adubai Bakwa xan iya cigaba da kiranka dawannan sunan ba sbda kai baka cancanta kaxama ubaba Tafashe dakuka Dawannan rayuwar danakeyi dakai da uwata wacce batadamu da halin da 'yarta ke ciki ba wallahi gwara mutuwa tafi sauki Karya kike yadda nake bukatar ki arayuwata awannan hali ko wanine yakashe ki wallahi saina karar masa da dangi donhaka karki wani yunkuri maikama dahaka Fuskarta sharkaf da hawaye takallesa Nadade aduniya na wuce wata uku mutkar bakadakatar da auren da mihran xaiyi ba gobene daurin auren Yaya kike tsammanin hakan xaifaru ko kinmanta da abindanayi masa tayaya xankuma iya dakatar da aurensa yanxu Harara takwala masa tare dacewa Tayadda kabi kayi abinda kayimin mana idan kuma bahaka ba wlh saina kashe kaina Dasauri yarufe mata baki Xanyi iya kokarina amma kisani lokacin mutuwar ki baiba indai akan wannan ne Yajanyeta daga cinyarsa tare dayimata kiss agefen fuskarta yadaga mata hannu yafuta Wani sabon kukan tadasa tare dafurta kalmar Wayyo Allah ni Ismat kaico na! πŸ’šπŸ’›πŸ’š Hussaina ce tsaye gaban wanda xata aura me suna kabeer tasha kyau iya kyau kasancewar kwalliyar faty ne ajikinta haka shima amma kwata kwata takasa dago kai takallesa sai boye fuskarta take acikin net din dayake rufe da kanta Hmm haba hussaina kidago ki kalli angon naki mana koda kwa saudaya ne sbda yaune ranar daya dacewa ace kin tantance waye mijin ki agobe! Dasauri tadago tana dubansa da tambaya Mihran! Aa aa mihran banason wasa banaso ina kabeer din? dama kasanshi ne? Miyasa xakafadi wannan maganar? Kayi magana mihran ka kullemin kai ina kabeer? Murmushi mihran yasaki tare da kara rage filin dake tsakaninsu yayinda hussaina ta kara matsawa baya cike da mamakin wannan abu dake shirin faruwa Hussaina nine kabeer mana shine sunana na asali anakiranane da mihran sbda sunan kakana ne, kiyi hakuri da irin boyewar dana miki nayi hakane sbda nasan baxaki taba amincewa daniba mutkar kinsan ninedin shiyasa nayi amfani da fuskar bogi kuma nayi hakane sbda tausayi dakuma sonki daya shigeni lokaci daya baxan juri ganin ki kina xubar hawaye ba akan yaudarar da umar yayi miki shiyasa nakware wa soyayyarki nikaina banxa to ba, kiyi hakuri amma ni wani irin mutum ne wanda baya manta alkhairi ko yaya yake nakan saka shi daxarar nasamu dama kina da hali mekyau nasan wannan dan Allah karki bijirewa aure na sbda kinsan yanxu wanene mijin ki agobe, Sauke ajiyar xuciya tayi idaninta akasa tana sharar kwallah Subhanallahi wannan kuma wanne irin al amarine mihran dama kaine kabeer bansaniba miyasa kasa nakamu da sonka wanda baxan iya cirewa ba yayakake so nayi yanxu sokake yi n a aureka daga baya nagane amana naci tsakanina da Ismat babu wannan wlh baxan iya ba yanxu haka Ismat tadawo gida kuma aurenta ya mutu da wanne ido xankalleta? Dan Allah meyasa kamana haka mihran? Sbda inasonki kuma dama naji hakan akirjina tun lokacin nakasa ganewa sbda Allah haka yaso abin yafaru karki damu idan kuma xaki iya wulakanta ni kema shikennan saiki sanar wa Abba kinjanye baxaki aureni ba Yafara tafiya dasauri tasha gabansa Shikennan shikennan ka koyamin sonka wanda bansan tayaya xanyi musalinsa ba na amince da aurenka amma lallai banji dadin faruwar hakaba mihran Kinga share wannan hawayen dake kwance afuskarki kigyara kwalliyar kafin atafi inkin ki kuma ni nashare miki nagyara miki fuskarki tas Harararsa tayi tana saurin matsawa daga kusa dashi Dariya yayi yana xuba dikkan hannayensa a aljihu yafara tafiya domin barin falon Xamu taho da imran yanxu fa kisauri pls, Ita dai batakara magana ba sai xubewa datayi kan daya daga cikin kujerun dake jere adakin reras gwanin sha awa tanasakin wani xaxxafan huci kafin tayi murmushi wanda nikaina bansan ma anansa ba daga hannu biyu tayi sama tafara addu ah Allahamdulillah Allah kaine abin godiya nadade inason mihran acikin xuciya ta amma Allah baka bani ba saigashi danayi hakuri kabani shi cikin sauki lallai nayidace da jarimin namiji cikakke irin wanda kowacce mace ke fatan mallakar irinsa, Allah kabani damar yin biyayya agaresa iyakar iyawata Allah kacikawa kowa burinsa naduniya amma banda budurwar dake burin mallakar mihran sbda shidin kabawa wacce ta cancanta dashi, Allah kayi salati ga shugaban mu Annabi muhammadu s a w, wanda baida adadi kayi kara karka daina ya Allah, Allahamdulillah. Takankame jakarta akirjinta tana karajin dadin kamshin turaren dake jikin mihran sbda shine yarike mata jakar tadade ahannunsa, ................................................... Dik yadda alhaji sanam yayi yakasa domin kuwa bashi dawata hanya daxai iya samu yahana auren mihran gamama kinsa ma dayaji da hussaina kawar Ismat din xa adaura lallai yayi mamaki domin kuwa yaga abin kamar cin amanane akayiwa Ismat Mama dake xaune kusa da Ismat tana nuna mata ankon misra 'yar kawarta wanda xa ayi bikin nan da wata uku Kinga dai atamfar tafi leshin kyau ko amma yakama miyi duka ukun sbda hajia liima tafi haka agurina Hmmm aini mama boyel din yafimin kyau duk da babikin xaniba kawai kimin shikadai ya isa Mama tamike dagakashin gidin datake tana kallon ta Sbda me Ismat meyasa wai kikeso kirinka batamin raine haba dan Allah misra fa sa arki ce haka lokacin danake hadaku kawance da ita kika rinka wulakanta yarinyar nan taxo gidannan wurinki amma kishare ta ko kima bargidan gabadaya haka harta gaji tadaina xuwa kulaki ma tadaina haba kewai karamar yarinya ce daxanta fama dake akan komai sainayi fama dake toh baki isaba wlh kuma indai kiga kinbatamin rai shine ke naki farincikin ai saiki dage kinji, Hankalin Ismat atashe tafara magana Aa mama kiyi hakuri wlh ba haka bane xani bikin indai hakan xaisa ranki yayi sanyi dama ganinayi abindaya faru tsakanina da ita baya xata kalleni dahakan nasan bankyauta mata ba wlh, Tohm naji ai sai kigyara ahankali ko tunda aikinsan wacece hajiya liima awurina Shikennan mama ya wuce Ranar juma ah akadaura auren hussaina da mihran aikuwa labari karab akunnen Ismat saida tasuma sbda firgici da gigicewa gaba daya daina ganewa tayi kafin idaninta yarufe tadaina ganin komai nadakin sai duhu, tafi awa biyar kwancee ko motsawa batayi ba kafin mama tashigo dakin nata tasameta aikuwa hankali atashe takira daddy awuya tasanar masa tana gursheken kuka kamar ta mutu, babata lokaci sai gashi kuwa yadawo shiyadauketa dakansa yasa amota mama tashiga gidn gaba dama kamal nagoye abayanta, sai hospital. ....................................................... Alhaji nura xuwansa gidan su atika sau biyar amma taki dawowa iyayenta sunyi sunyi da ita amma taki fadar komai saidai kuka, haka suhail da ridwan suke xuwa susata agaba da lallashi amma bata fadawa kowa abindayasa tabar gidan babansu ba, har sun hakura Yaukam alhaji nura yaci alwashin xuwa wurin bokansa yasa shi yarufe mata baki akan maganar dataji sunyi yaxama har ta mutu bawanda xata iyafadawa abindayafaru. ,amarya da ango kam ba amagana in ana sallah amma tsayawa lissafa muku yadda gidan mihran yahadu wlh saikuce wani abunma karya nikeπŸ˜€, nikuma banason akaryatani akan gaskiya ta😁 Haka kuwa alhaji nura yayi kamar yadda yakissifa aransa boka dan duwala yayimasa aiki yadda yake so an bame bakin atika maman suhail, yanxu ko kukan ma datake yawanyi tadaina kuma gabadaya tama manta da abindaya faru domin kuwa alhaji nura ita dakanta tanemosa akan maganar komawarta dakinta yace bakomi koyau idan tashirya xaixo sutafi haka kuwa akayi ranar takoma da daddare, suhail da ridwan nata mamakin sha anin maman nasu. (Toh muje xuwa fa wlh tallahi masu karatu ina mugun mugun kaunarku kudai kucigaba da kasancewa tare dani Shamsiyya Adam in sha Allahu

Chapter 5 of 7