da baka iya Gane yanayin da yake ciki yace"asibiti za a kaita ai"
Mikewa yarima Ahmed yayi yace"eh asibiti na tuna asibiti za a kaita"
Duk inda fadawa sukayi da mai martaba ya koma fada zasu ji da komai ki yayi be damu da yarima aliyu dake kwance ba yafi damuwa da nimbras din domin ta taka rawar gani in badan ita ba da ya rasa tillo d'an sa mafi soyuwa a zuciyarsa
Yarima ya mike ya d'auketa ya rungumeta a jikinsa ai sai yaji jikinta yayi wani mugun sanyi hakan yasa ya sake kallon fuskarta kawai sai ya Kara matseta a jikinshi,zuciyarsa ciwo yake Masa he can't believe that this small girl save his life .....daga yau rayuwarsa ta Zama nata sai inda tayi dashi fatansa Allah yasa ta rayu
Tafiya ya dingayi,gimbiya Zenabu ko kuka take tana a taimaketa jakkadiya ko lura da Jamila ta mutu yasa ta zauna ta zubawa Jamila Ido hawaye na bin kuncinta
Tafiya yarima yake da sauri dukda ya gan ambulance ya paka be kallesu ba ya cigaba da tafiya har ya Kai gun motarsa Yana kokarin budewa nafeesa ta karaso da gudu
Tace"miye Haka baby zaka wani d'auki slave miye Haka prince ba girmaka bane,,,miye tayi da ka wani dame kanka aikinta tayi na kula da Kai Kuma fa a karkashin mu take sai me dan ta mutu a d'auko wata Mana
Ya ajiye nimbras ya juyo ya kalleta da jajayen idanunshi daya firgita ta,yace"in kyaleta ta mutu Baki gan abinda tayi ba??Ina Zaki gani nafeesat tunda babu soyyaya tsakaninmu dake yau na gane Baki kauna na da kina kaunata da kin fi shiga tashin hankali na halin da yariyar Nan ke ciki,saboda da zaki dube ta da kallon Wanda tayi saving life din mijinki zakiyi but da yike Baki Sona shine in manceta toh in ke Baki d'auki rayuwata da muhimmanci ba ni nasan sacrifice da yariyar Nan tayi min and har abada bazan manceta ba"
Nafeesat tace"understand me, she is just trying to trick you nasan ko mutuwa tayi bazamu bar familyn dinta Haka ba we will comp....."
Bata karasa ba wani guard ya karaso da car key Yana kokarin shiga motar ya jasu yarima ya ture shi ya Shiga a sittin ya ja motar Wanda bazai iya tuna Randa yayi driving da kansa ba Kai dudu a rayuwarsa zai iya kirga so nawa yayi driving
Sai dai fa gidan ba hanya fita Kuma saboda go slow ya hanashi sata a ambulance da tuni aka saka yarima aliyu da Jamila da alamu sun nuna ta mutu
Horn yake kamar mahaukaci but babban holdup ne a gidan saboda bakin dake kokarin fita kowa burinshi ya bar gidan
Ya buga steering cike da haushi dai'dai karasowar ummi ta buga glass
Tace" ga ambulance can an bude second gate babu holdup dan an Hana kowa bi"
Da sauri ya fito daga motar ko kullewa beyi ba ya Bude Baya ya dauki nimbras,abin mamaki skin dinta is gradually turning green
Cikin tashin hankali yace"ummi kalli jikinta"
Ummi tace"muje son da alamu poison din ya Gama spreading a jikinta ya tab'a hanjinta
Shidai sauri yake ba takalmi kafarsa ya karasa empty ambulance da Mai martaba ya turo already sun Bude su ake jira
Shiga yayi ya rungumeta Gam a jikinta duk inda aka so ya ajiyeta a Fara bata first aid ki yayi sai cewa yake holdon zarah karki min Haka please"ummi tace*at least ka ajiyeta Mana su Bata taimakon gaggawa may be a sa Mata oxygen "
Ya dube ummi yace"ko me za ayi ayi tana jikina ummi saboda ni take wanan condition din "
Dr Dake ciki ya Kama hanunta ya girgiza Kai Dan babu alamun rai a tattare da ita
Haka dai Suka Isa babban hospital da yike royal hospital ne akwai kwararu aka Shiga da ita likitoci ne birjik akanta yarima na tsaye kansu
Har Suka Gama abinda suke ganin ya dace Amma poison din be bar spreading ba Dan zuwa yanzu ta bushe kamas kamar ice
Daya daga cikin Dr din ya cire facemask dinshi da handglove hakan yasa yarima zuwa gunsa yace"tell me she is alive tell me she will be fine"
Dr ya dukar da Kai yace"iam sorry she is dead"
Wani shako sa yarima yayi yace"karya kake my zarah is not death I have big plans for her bazata mutu ba sai tasan alakar dake tsakaninmu...please Dr revive her she is my life "
Niko nace wani alaka ce yarima
Kokarin janye Dr ake yaki hakan yasa Dr Jiddah fita ta kira ummi
Ummi na shigowa ta wanka me Mari kawai sai ya zube da guiwowinsa ya kurawa nimbras Ido
Ummi ta rasa inda zata sa kanta is like yarima is going crazy kawai sai ta fashe da kuka tana d'aga wayar kawu daya shigo wayarta
Yace"subhannallah me ke faruwa"
Ta kwashe labarin komai ta bashi,ai wani ihu kawu ya fasa yace"labaras din ta mutu??"
Tace"Haka likitoci Suka ce"
Yace"ba ke ne da kuka ba nine da kuka Ni Dana d'auko Yar mutane tundaga Sudan"
. Yanke wayar ummi tayi Jin ana fama da yarima daya Kai bakinsa kunni nimbras ko me yake fad'a Mata oho Dr na cewa wanan dangerous snake ne poison dinshi ya mamaye jikinta zai iya affecting kowa balle she is not breathing muma sai munyi kitting jikin mu ka bar wurin please"
Dr Jiddah na kallon na'urar dake jone da nimbras ta saki wani irin ihu......tace"the heartbeat is rising 5%
Ja baya yarima yayi Yana Jin jiri ya zubawa na'urar Ido kamar inda sauran likitocin sukayi da mamaki a fuskarsu
Dr Jiddah tace"this is a miracle"
Yarima ya Kama hanun nimbras yace"thank you for coming back to me"
Likitoci sunyi iya kokarinsu but jikin nimbras sake rikicewa yake in ka cire nasaran heart beat da aka samu babu wani cigaba
Yarima be motsa ba zuwa dare kafar nimbras fatar ta fara d'ayewa Kamar wacce aka zubawa ruwan zafi
Ko abinci yaki yarda yasa a Baki sallah kawai ke fitar dashi,Yana zaune news din mutuwar Jamila ya riskesu but aliyu na Raye Yana coma itako Jamila daman a take ta mutu
Da misalin 2am sai ga kawu ya iso asibitin a halin daya gan nimbras abin ya tsorata shi yayi ta kallonta
Cikin damuwa yace"ko zamu Kira jannah ya'ta expect ce a wanan cases din "
Yarima ahmed yace"what are we waiting for kawu ko waye za a Kira a Kira ko me suke so za a basu Koda Zan Basu abinda na mallaka a duniya nidai in gan zarah ta mike"
Kawu yace"hmmm har kasan sunanta"
Kiran jannah akayi tace"toh zata Fara shiri
Washe gari mama ta Zo da A'med dake kuka ,yarima ya amshesa Amma yaki shiru duk yaron ya fita hayyacinsa ko abinci Baya ci
Ajiye sa yayi a jijin nimbras da na'urori ke jone a jikinta har oxygen,A'med ya hau jikinta Yana dariya hakan yasa yarima rungume kawu abin tausayi gashi idanunshi a bushe kawu yayi ta buga bayansa
Mama zata d'auki A'med ya Hana yace"a kyalesa"
Da misalin 8am sai ga nafeesat ta Zo asibitin tana wa yarima kallon banza babu addu'ar dake ranta Kamar taji news din mutuwar nimbras shiyasa jiya da taji Mai martaba na cewa a d'auko me gawan macijin zaiyi amfani wajen Mata magani ta Riga Wanda aka aika zuwa ta dauke ta b'oye "
Yarima ya d'auki A'med dakewa nafeesa dariya ta sharesa Yana jijjigasa ya fita domin zuwa Kiran dr"
Nafeesa na ganin ya fita tace"kawu can imagine zubda kima da yarima yayi ya wani tada hankalinshi akan baiwa Wanda in mutuwa tayi dukiya kawai za a bawa familynta suyi ta godiya Ni Ina mamakin wanan abin ko akwai wani Abu ne ta daban tsakaninsu da ban sani ba?zai iya yiwuwa talauci ne ya ishesu Suka turo yariyar Dan suyi sacrificing dinta suyi kudi kasan fa talakawar Nan ba abinda bazasu iya ba ka gan inta mutu a Basu dukiya in ba Haka ba Taya tayi tasan an aika maciji ya sari yarima kasan kuwa ta Zo ta sanar min na Kore ta saidai in itace ta kawo macijin ta fake da taji conversation din wasu "
Da mamaki gami da takaici kawu ke kallon nafeesat yarima ya shigo yace"ta fad'a Miki my life is in danger kikayi watsi da maganar rayuwata nafeesat "sai Kuma yayi murmushi takaici ya koma kusa da nimbras da zuwa yanzu abin ba a cewa komai Dr ya shigo ya dubata
Sai 11pm jannah ta sauka garin Sudan aka tura mota airport d'auko ta ko gida Bata je ba balle hutawa yariya ce karama da Bazata wuce 22 ba Amma babbar likita ce Yar kawu ce ta farko
Kitting kanta tayi ta Shiga d'akin ta Fara duba nimbras tace"a gaskiya dole sai an kawu macijin daya sareta an Kai lap anyi test a gano irin poison dinsa da Kuma treatment da za ayi Masa babu wata hanya sai wanan poison din ya Gama bin jikinta"
Yarima ya mike zubur yace"ai Yana gun taron ya Kira Mai martaba but news din daya ji yasa shi zaman dirshen domin ance an zaga gidan kap babu wanan macijin shi yasan ai sai an Kai macijin shiyasa ya tura a d'auko but an rasa Wanda ya dauka"
Nafeesa ta saki wani murmushi tace"in ma Baki mutu ba zan karasaki I just hate you for no reason"
Kawu yace"akwai matsala babba "
Mai martaba ne ya sake Kira yace"a dawo da ita gida ayi na gargajiya
Kawu ya fita yayiwa likita bayani akayi processing discharge dinsu aka maidata gida
Gida aka Kaita aka ware Mata part d'aya local physician ta Zo
Duk tsaye sukayi suna kallonta ta had'a maganin gargajiya
Ta d'ago Kanta ta zuba Mata a baki
Wani amai ta farayi kore daga karshe Kuma sai jini ya Fara fita a bakinta
Yarima yace"ya ake ciki"
Ta girgiza Kai tana kallon aman da tayi cike da damuwa tace" wanan poison din beson bacci saidai ta kasance idanunta a bude Kuma bazai yiwu ba saboda Bata ma hayyancinta
Tari nimbras ta Fara yayi kanta da sauri
Kawu dai na gefe cike da damuwa yana mamaki mutum da ransa a ce Kar yayi bacci
Kiran sallah magrib yasa yace"muje muyi sallah"yarima ya bishi Suka tafi massalaci
Physician ta kalli ummi da tayi jugum tace"masalaha d'aya ne a d'auko macijin ko a samo dai'dai irinsa "
Ummi tace"an duba gidan nan babushi Ina za a samu irinsa???"
Tace"masalaha d'aya ne a Kira sarkin macizai ayi busa sarewa ko algaita duk wani macijin dake rayuwa a kasar nan zasu Zo gunsa in an dace da me irin poison zai Zo ya janye poison din jikinta Amma nidai ban tab'a ganin irin poison din Nan ba
Ummi ta fita domin zuwa yin sallah sanan ta sanar da Mai martaba
Tana fita nafeesat ta shigo ta kalli physician ta ajiye Mata ledar cike da gula gulai
Physician ta kalli nafeesat cikin rashin fahimta
Nafeesat ta juya Mata baya tace"so Nike ki kashe ta in ma fiye da wanan dukiyar kike so Zan Baki nidai a rabata da duniya "
Physician tayi shiru hakan yasa nafeesat ta juyo ta fuskanceta tace"na ji kinyi shiru "
Physician tayi murmushi tace"in Zaki ninka min dukiyar nan biyar me zai hana"
Nafeesat tace"akan biyan bukata ta zan iya bada ko nawa ne ki aiwatar zan biyaki"
Physician tace"toh in hakane yariyar Nan bazata gan wayewar garin gobe ba
Nafeesat ta
This is the last free page for payment vip 500 regular 300 via 2378022567
Aisha Mohammed
Zeinith bank in Kuma katine mtn for vtu ga number 08148088368
For more information via watsaap line 09090112846
Maman Nur
[8/21, 11:28 PM] MAMAN NOORUL HUDAH Writer: ππππππ
*_YARIMA AHMED_*
ππππππ
_By maman noorul_
_Hudah_
_Paid book_
π
Ώ2οΈβ£3οΈβ£-2οΈβ£4οΈβ£
Bismillahir Rahmanir Rahim
Tace"Ina son mu koma ne"be kalleta ba idanunshi na Kan A'med dake Masa murmushi ta Kai hanun zata daukeshi ya gan zoben hanunta sake kallon zoben yayi zuciyarta na bugawa ya Kama hanun Yana kallo tsoro ne ya kamata har jikinta na rawa
Cikin larabci yace"waye ya Baki?"
Tace"kakata "
Zaiyi magana sai ya gan he is been foolish him yasan wanan ba nashi bane but waye ya buga dublicate din?dole ya Kira kawu ya dawo me da zobensa Kar ya d'auka bashi yayi Dan ya gan ya saka kwanaki
Ta d'auki ahmed ta Goya zata wuce,yace"ai sai ki jira a kawo maganinsa " Bata San Sanda ta zauna kan gadonsa ba yana kallonta Yana ganin karfin halinta
Ta dade zaune tana dafe da ciki sai ya Lura cikine ke Mata ciwo Amma be ce komai ba
Dawowar Fahad yasa ta mike tana mikewa ya Lura da jinin daya b'ata inda ta zauna
Ya zaro Ido, da sauri ya tashi ya kare ta inda Fahad bazai gani ba ya amsa maganin yace"you can go"
Zaiyi magana ya daka me tsawa yace"you can go nace"Fahad ya fita Yana mamaki
Duba dosage din yayi ya mata bayani da larabci ta amsa ta wuce ya kalli bedsheets din daya b'ace sai Kuma yayi tunanin in wani ganta Haka fah
Binta yayi Yana sauri a stairs ya ganta ya Kama hijabinta ta juya tana kallonshi
Yace"kalli jikinki ya b'ace da jini "
Dubawa tayi Aiko tana gani ta saki ihuuuuu dan Bata tab'a gani ba har ta jawo hankalin mutane ya Kama hanunta sukayi ciki tare har rawar jiki take
Suna Shiga ya Mata wani kallo cikin larabci yace"don't tell me Baki San menene wanan ba ta girgiza me Kai alamun ah'ah tana kuka sai ta bashi tausayi ya kwantar da murya ya Fara Mata bayanin yace"I guess this is your first time ta dukar da Kai ya Fara Mata explanation dukda shima he don't know much about jinin but iya Wanda ya sani ya fad'a Mata
Ya rasa Wanda zai Kira a kawo me pad mama ladi ne ta zo zuciyarshi ya kirata a waya cikin ladabi ta gaishesa ya fad'a Mata tace"toh nimbras din ta dawo Daman Bata karya ba
Ya katse wayar ya dube ta be ce komai ba ya fita ya hado Mata tea he don't know why he has a strong feeling about her Wanda besan ko na miye ba
Shayi ya had'o ya kawo Mata tsoro ya kamata tana girgiza Kai ta dukar da Kai tace"yallabai kafi karfin ka kawo min tea nice ya dace nayi maka bauta
Hararanta yayi ta amsa da wuri da k'yar ta Sha Rabi ta sauke kofin a bakinta ta mike sai Kuma ta duka ta dafe yatsun kafar shi tace"Allah ya baka tsawon rai ranka dade"
Lumshe Ido yayi ta bar bedroom din a dining ta tattara tsadaden warmers din abinci ta fita dasu
Tana fita yayi ta kallon jinin sai kawai ya kwashe bedsheet din ya tura wardrobe dinsa madadin ya Kai gun kayan wanki
Masarautar ya d'auki hayaniya saboda shirin Mali daola-ba festival jibi kowa sai murna yake saboda gobe za a bada hutun public holiday babban festival ne me cike da nishadin
A hanya ta sake had'uwa da wacce ta gan tana shuwa d'azu sai dai Bata mata magana ba tana Allah Allah ne ta Kai bagarensu sai Kare wurin take da hijabi
Shiko bΓ yan ya kwashe bedsheet din ya d'au waya ya Kira kawu
Kamar jira kawu yake ya d'aga da sauri
Yace"yau Kai da kanka ka kirani?"Allah yasa inji alkhairi"
Kai tsaye yace"zobena Nike son ka bani"
Ai kawu kwarewa yayi ta cewa"hellow hellow bana jinka"
Yarima ya yanke Yana murmushi but akan zoben Nan za a jisu
_______________
Gimbiya Zenabu ne zaune da jakkadiya da sauran ya'yanta harda Wanda sukayi aure sun zo festive da amaryar aliyu da yike uwargidansa mulki be gabanta Basu sakota a plan dinsu
Gimbiya Zenabu ta bude basket din ko tsoro babu macijin ya fito duk sun tsorata har aliyu ya saki ihu
Tace"eazy ba abinda zaiyiwa kowa shi Wanda aka aika ma kawai yake tsara toh dai ka ji plan din ko?? ranar taron za a sakesa bayan mun fada Masa inda zashi da Wanda zai Sara Amma ce in muna son aikin yayi kyau a ajiye Masa hoton yarima tundaga yau "
Yarima aliyu da kafafunsa na sama kujera har yanzu yace"me ake jira?"
Jakkadiya ce ta fito da hoton yarima Mai kyau tace"inshallah zamu Gama da case din yarima Kuma baza a zarge mu ba faruwar abin a bainar jama'a zai sa a rasa gane Kan lamarin kasancewar mawaka da rawa zasu Zo daga kasashe daban daban ta Ina za a fara binciken ??"
Aliyu yayi dariya yace"good iam impress "
Sisters dinsa Suka kyalkyale da dariya suka ce bΓ yan shi babu wani a hanyarka ya Zama tarihi ai "
Amarya aliyu gimbiya saratu ta mike tace"Bari in leka wajenta in d'auko rahoto kunsan shashasha ce sultanan ta yarda Dani"
Jakkadiya tayi dariyar gefen Baki ta ajiye hoton a gaban maciji caccaka hoton ya Fara Yi karshe ya koma gefe ya wani irin fasa Kai yayi fushi
Jakkadiya ta karasa tace"shi muke so ka kashe da dafin ka"
Kamar ko Yana ji tace"yarima Aliyu zaka kashe a bainar jama'a....sai ya kwantar da Kai alamun girmamawa
Tafi Aliyu yayi Yana kallon uwar tasa tace"mum you are amazing you are superb,you are curning Allah yayi muguwar mace anan Makira Mara tsoron Allah"wani kallo tayi me ya toshe bakinsa Yana dariya itama dariyar tayi tace"you can said that again akan ku ba abinda bazanyi ba
Yace"mum na gan wata Yar yariyar a gidan Nan tayi min Ina son Ina d'ana"
Wani kallo tayi me jakkadiya tace"karka kuskura domin mahaifinka na kule da Kai har yanzu fa bawai an rufe case din siddika bane Kuma yin haka' zaka b'ata Mana aiki"
Ya Mata kallon raini yace"stay within your limit na baiwa ki daina bani umurni in ba haka ba I will not hetsitate to cut your tongue "
Ta dukar da Kai tace"tuba Nike ranka dade"
Mummy tace"karka kuskura wallahi Kai meyasa idanunka be ganin yarane karka b'ata Mana aiki ban hanaka ba but ka bari sai munyi nasara in ya so you can sleep with ko wace mace kake so mulki zamu shinfida son ranmu ai
Ya jinjina Kai but shifa be gamsu ba har yanzu hoton nimbras na yawo a idanunshi
B'angaren gimbiya meryam ko zaune take a bedroom dinta yaranta maza kananu biyu da sa'ad sai Kamal ta zuba musu Ido
Sa'ad shine babba so take yayi mulki kasar Mali but yarima aliyu da yarima Ahmed are standing on his way be wuce 15years ba
Waya ta kunna ta Kira wata number da tayi serving da karima bugu ta d'auka
Tace"karima iam ready had'ani da mahalbin badai ya iya aikin ba wanan festival din blood will flow wallahi "
Karima tace"abinda Nike fad'a Miki kenan kinki ji da Kin Amince da shawara toh da ba Haka ba wallahi toh dai gashi kin bari Abu ya girmama
Tace"nifa yarima Ahmed be tsaya min a rai kamar Aliyu ba saboda shi yarima aliyu karamin al'hakine uwarsa sakarya ce but shi aliyu uwarsa zata iyayin komai Dan d'anta ya gaji sarautar mali
Karima tace"ba wani dai dukansu threat ne to you a Gama dasu kawa ki turo hotunansu a Gama dasu ga dama Nan ranan festival"
Tace"ok yanzu Zan turo hoton Zan Kuma tura Miki kudin"
Karima tace"yanzu na ji Batu
Saratu b'agaren ummi tayi,ummi na tsaye da hadimanta tana musu bayanin inda festive din zai kasance da Shirin da zasuyi anyi decorating part dinta yayi kyau sai ga saratu
Ta gaida ummi cikin ladabi ummi ta amsa fuska sake abinka da Mai farar zuciya tace"ya kuke aliyu be leko Ni kwana biyu ba lafiya dai ko"
Saratu tace"lafiya da yike sai jiya ya dawo daga kasar aiki kike ne?'
Tace"kin San festive ya zo ba hutu "
Saratu ta mike tace"hakane Nima aikin na can na Bari na Zo duba mummy ne nace bari in zo mu gaisa "
Ummi tayi Mata godiya sanan ta bar part din
Sosai mama ladi ta bawa nimbras kulawa ta gyara jikinta ta ci abinci kafin bacci ya dauketa shiko A'med beyi ba Yana gun mama Dan ya Fara sake Mata
da misalin 8:30 nimbras tayi ta Jin kidi a masarautar
Mama ladi tace"ki shirya kije yau duk matan gidan Nan Banda iyayen Amma daga Kan matar yarima zuwa ma'aikata suna babba hall suna rawa ba a Bari namiji yaje Zaki tsince kanki cikin nishad'i maganar majicin yayi crossing ranta mama ta mike tace*Nan Nima zanje ki Zo muje
Mikewa tayi ta bi bayan mama dake goye da A'med dukda bawai ta Gama fahimci maganar mama bane
Tana Shiga hall din ta tarar da makid'a na kidi ana rawa
Ta zauna kusa da Jamila ta gaisheta cikin yarensu
Jamila ta kalleta cikin murna tace"wow kema sudaneese ce"
Tace"eh"ban dade da zuwa ba"
Jamila tace"au Niko mun dade anan mahaifiyata ita ce jakkadiyar uwargidan sarki anan na girma na Sami kaina
Nimbras was so happy mussaman data gan Jamila ta sake Mata
Cikin low voice tace"wanene yarima Ahmed a masarautar Nan?"
Jamila na murmushi idanunta na kan rawar da gimbiya Fatima keyi
Tace"shine Wanda zai gaji sarki Bari in nuna miki hotonsa"
Ta Ciro waya ta Shiga gallery ta nuna masa hotonsa tashi nimbras Tayi bΓ yan ta gan hoton jikinta na rawa
Zatayi magana Jamila ta ruga da gudu ta Shiga fili
Kiran gimbiya nafeesat ake ta fito ta taka Amma gabad'aya Bata Zo taron ba....saratu tace"Dan Allah kushareta sai girman Kai banza a Kira wata a madadinta
Gimbiya Fatima taje ta Kama hanun nimbras ta shigo da ita
Jamila ta Fara ihu da yare tana cewa tayi rawa
Murmushi ya sub'uce Mata aka sa kid'ar Sudan
Nimbras ta Fara rawa abin ya mugun birge mutane Bata dade ba ta koma gefe ta Kama hanun Jamila suka je waje
Tace"akwai matsala fa"ta kwashe