Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 8
tana aiki tana kuka gaba daya ta kunna gas din sabida karta bata lokaci suyi mata taron dangi cikin kan kani lokaci ta gama ta ajiye a dinning Durkusawa tai nagama ta fada cikin isa ummie tace wallahi in har naci naji ba yanda nake so ba daga Ke har shegen dan naki sai kun gane kuren ku Bata ce komai ba tashiga daki ta zauna ta rafka uban tagumi Allah ka kawo min sauki a wannan rayuwa in mutuwa ce alkhaeri Allah ka dauke ni in kuma wani laifin nai kake jarrabta ta to ya ubangiji ka yafe min Jitai ana kwalla mata kira ke daman sunan da suke kiran ta dashi Ke nan cikin hanzari ta fito suna dining haka ake girki a gidan ubanki a kawo ba wani abu ne sanyi khalisat ta fada cikin gadara Komawa tai ta hada pineapple with coconut juice da ruwan kankara ta hada dan kar ace be sanyi ba cikin wani babban jug tayi ta kawo ta juya zata tafi Ke zo nan Bata Ankara ba taji an watsa mata ruwan lemon gaba daya a jikin ta wani sanyi ne ya ratsata kuka ta fara yi tana wai me nai muku kuke min haka kun mai dani kamar wata baiwar ku Au tambayar mu kike lallai har yanxu baki gama huruwa ba tunda bakin ki be mutu ba binta ce ta karasa kwara mata sauran lemon bace ki bamu waje kan na galabaitar da Ke jaka kawai Ke ba kina tun kawo kin haihu ba Sai dai ki kuma haifar wani a bola ummie ta fada ni wallahi nagaji da ganin ta a gidan wallh daman kun Bari ya Kore ta khalisat ta fada To ae ba yanxu ba ki Bari lokaci yana nan tafe wadda da kanta zata gudu Dariya sukai gaba daya sannan suka tafa Wani azababban zazzabine ya rufe ta ga ciwon kai take jikin ta ya dau zafi ta fara kakkarwa sabida jigatar da tayi ba Hutu kullum haka take fama rarrafawa tai ta daukko paracetamol a drawer ta sha ta kwanta ko zata Ji relief Haka suhailat take rayuwa cikin kunci da masifa iri iri in su basu dake ta ba to zasu shirya mata makircin da admas din zai dake ta Suhailat ce goye da sultan tana moping dib parlon da gayya suke bata shi tanayi suna batawa binta ce ta fito da underwears din ta tari guda Ke maza ungo jeki wanke min su tas Saura naga badai dai ba kuma ki san yanda zaki wane Karki min mugunta ki tala min su To bari na gama ki gama me lallai Ke wai ban gaya miki in nasaki aiki duk abinda kike ki ajeye kiyi min ba a salube ta karba ta tafi laundry na gidan Ta zazzagewa wani karni ya doki hancin ta amai ne ya tawo mata nan ta dinga kwararawa ya salam yanxu panties din wannan yar iskar zan wanke na yar lesbian innalillahi wa'inna ilaihir raju'un duk da a washing machine zata yi amma tana kyankyamin taba su Sai da ta wanke su tas sannan ta kai mata cikin fargaba kar tace basu yi ba......... By marsal💞[30/04 3:41 pm] Ya Ummi: *👟NAMIJIN GASKE👟* 2⃣7⃣ *By 2besties💞* _salma ali wadah_ ↓ _maryam yarmama_ *(marsal)* ®online hausa writter ⚫shiga toilet ki shanya su sannan ki wanke min shi tas in kin gama ki gyaran daki sannan ki niken wannan kayan Saura kuma naga an sacen dan an saba Ba gyara kwata kwata a toilet din kamar bana mace ba nan ta wanke shi ta gyara dakin tas sannan ta fito jikin ta duk yayi tsami Sabida gajiya Shi kuwa namijn gaske gaba daya baya jin dadi gidan sam wani duk rahar da yake da ya shigo zai Ji yai masa zafi ga wani irin tsanar suhailat da yake Ji shi ya rasa mene dalilin Wayar sa ce ta fara ringin kamar bazai dauka ba sai ya dauka dadyn sa ne Jiki ba kwari ya dauka hello dady son wau me yake damun ka ne gaba daya baka zuwa gidan kuma in ba'a kira ka ba baka kira dady wallahi aiki ne yai min yawa to kai dai dinga sassautawa kan ka Kar ka sa marwa kanka wata matsalan to dady ina jika na sai da yai jim sannan yace yana gida shi gaba daya ya ma manta dashi Ka boye su bare su zo mu gansu dady ban son su dinga fita sabida kar a kwaso masa gajiya ya fada dan ya gaji ma da zance yaron ko maganr sa shi da uwar sa ba yaso to ka gaishe su zasu Ji dady ya kashe wayar Ta gama aiki tana daki tana ma sultan wasa wayar ta taji tana vibrate dan badamar tasa ta a ringin su binta suce tana hada musu munafunci dauka ta cikin jin dadi Hajiya hussaina ce ta kira ta yar uwa ta ya kike lafiya Hajiya wasu kwalla ta share wai har yanxu basu daina yi miki abubuwa ba Wallahi Hajiya sai addu'a dan kullu sabbabin azaba suke fito min dasu yanxu ban isa nayi nisa da sultan ba sai suyi masa wani abun Ko imani basu dashi bare suyi tunani wannan da be san me duniyar take ciki b To ki kara haquri na san kina yi sannan ki dage wajen addu'a Allah yana jin ki kuma yana kallon su Sannan zan sa a dinga yi miki addu'a to nagode Hajiya zan turo miki da kudi ki dinga yi min sadaka dasu Kinga ni ba halin fita to ya za'ae kimin transfer din ta waya zan miki sai ki turo min da account number dn ki Ki bari Nasa ae miki aa Hajiya wai ba raina abinda kike min nake ba kawai ina so ayi addu'a sosai Sannan kisa a dinga yimin sauka in an gama sai a yi abinci sadaka Allah ya yayemin wannan masifar to shikkenan Ke ma kin dage da addu'a sosai sai kiga Allah ya karya duk wani sharrin da sukai miki Sukai sallama sannan ta tura mata ba dare ba rana haka take addu'a ko aiki take yi bata daina addu'a Su binta kuwa suna nan suna sake sabon shiri domin yanxu ko makirci suka hada mata su fada masa baya dukan ta sai dai yace to Ke kinji ki gyara Da yamma tana waje tana bawa flowers ruwa sultan yaba bayan ta yana faman kuka ajiye wa tai ta fara jijjiga shi amma ya ki daina kukan Namijn gaske ne gefe yana karanta newspaper tunda sultan ya fara kuka ya tsaya yana kallon su kamar ya kure ta sai kuma ya kasa taso wa yai ya karaso inda take jijjiga sultan Matsawa tai kirjin ta na dukan tara tara kawo shi taji ya fada gaban ta ne ya wani mugun faduwa na shiga uku ta fada a ranta kawo shi mana ta sake maimaita mata A tsorace ta mika masa shi ya karbe shi ya koma garden Allah yasa ba wani abu zai masa ba Wasa ya fara masa kan kace me yaro ya fara dariya kamar me tana dafa gefe tana kallon sa kamar ba shi ba suna hada ido ya daka mata tsawa back to your business Jiki na bari ta cigaba da aikin ta wani sanyi taji yana ratsa ranta Allah nagode ma dan rabon da ta dauki dan tun yana jariri Khalisat ce ta fito da niyar zuwa wajen namijn gaske tsayawa tai saroro me zan gani Adams Kasan me ka dauka kuwa kallon rashin fahimta yai mata me kike nufi nuna sultan tai wanda yake wasa da hannun sa Naga ka dau wannan to ba dana bane ba zaro ido tai lallai aikin su ya fara warware wa tana wannan tunani taji yana cewa shima yana da hakki akaina kuma ya kamata ace nasan halin da yake ciki domin.....katse shi tai Kaga Adams bana son dogon zance waya ce danka bane tashi tai a fusace ta shiga cikin gida........ By marsal💞 [30/04 3:41 pm] Ya Ummi: *👟NAMIJIN GASKE👟* 2⃣8⃣ *by 2besties* _salma Ali wadah_ ↓ _maryam yarmama_ *(marsal)* ®online hausa writter ☆adams yaci gaba da yiwa sultan wasa ,sultan sai dariya yake Bintace tafito tana yamutse fuska tace dear waimeye haka? Adams yace kamarya?badana bane akwai wani da acikinnan kamarsa? Binta ta murguda baki tace kaidai kasani,yanzu muzakawa gorin haihuwa kukan munafurci tafashe dashi Yayinda khalisat tafito tana huci tace wallahi bazaiyuba dole in kashe dannan kowa yarasa Da karfi ta warci sultan ahannun adams ta tika dakasa,kara ya saki numfashinsa ya dauke Itama suhailat ta dora hannu aka ta kurma uban ihu nashiga uku,dana kun kashemin dana innalillahi wa,innahiraihi raji,un Adams rai abace ya kalli khalisat yace kin kyauta kin kashemin dana Harararsa khalisat tayi tace and so what kuma nakashe banza Ran suhailat ya bace tayi kukan kura tayo kan khalisat tadinga kai mata bugu idonta ya rufe, Binta tanaganin haka tayi shashinta da gudu Namijin gaske yana zuwa ya daddage ya fesawa suhailat mari pas kyawawa guda uku yace ke a matsayinki na yar aiki harkin isa ki dukarmin matata inkyaleki Suhailat tace adams wannan wani irin zaluncine nagaji dazaman gidannan ka sauwakemin nagaji kuma sai ubangiji Allah yasakamin Momyn adams ce tashigo tare da hajiya hassana Momyn adams tace to Dama ance komin nisan jifa kasa zai dawo gashi yau nagani da idona na sheda,suhailat jeki sako mayafinki mutafi kingama zaman aure agidannan Adams yace momy yaushe kikazo? Harara tadakamai tace ina zakasani kana tare da shedan ta kasani daga yau bani bakai ka nemi wata uwar badainiba,kaida suhailat har abada kunyi nesa kuma zansa jami,an tsaro da cameras sosai agidanmu ko an ganka na yarje akama ka Hajiya hassana ta dauki sultan dayake tsakanin raida mutuwa ta dorasa akafadarta tana zubar da hawaye,itama suhailat tafito sanye da hijjabi tana zubar da kwallah dauke da akwati a hannunta Momy tace aje musu akwatin anan in Allah ya yarda keda gidannan har abada Aje akwatin suhailat tayi ta kalli namijin gaske tana karajin kaunarsa da sonsa tamkar ajininta ,bin bayan su umma tayi hawaye nafita a idonta By Marsal [30/04 3:41 pm] Ya Ummi: *👟NAMIJIN GASKE👟* 2⃣9⃣ _salma ali wadah_ ↓ _maryam yarmama_ *(marsal)* ®online hausa writter _this page is dedicated to our fans,thank you for ur support and ur love,we gave u around of love in our heart_ Asibiti aka nufa da sultan akasamai drip,suhailat tayi kuka harta godewa Allah dataga wahalar dasultan yakesha Ga hannunsa ya karye abin tausayi Hajiya hassana sai tausarta take,mutane yan gaisuwa suka fara cika a asibitin,momyn suhailat ce tashigo tare da dadynta Suhailat taruga aguje ta rungumi momy tana momy sunason kasheni zasu kasheni zasu haukatani sun rabani da mijina momy mainayi musu Kuka momy tasata kalli suhailat data rame tayi baki ba lallema adinga ganetaba . Dady yace suhailat haka suka zamarmin dake?lalle azzalumai ne dole in dau mataki Tarin sultan yakatse musu hanzari,da gudu suhailat ta nufi wajen,tana dan matsamai kirji,dago hannu sultan yayi yana wa suhailat murmushi,barcine ya kwashesa Yayinda suhailat taji gabanta yayi mugun haduwa,dagudu tawuce su momy taja wata doctor tana doctor pls kizo ki duban yarona kar ya mutu Dagudu suka shiga dakin yayinda doctor din ta auna sultan girgiza kai tayu jiki asanyaye tayi yake tace ki kwantar da hankalinki yana baccine. Girgiza kai suhailat tayi tana a a ban yardaba jikina ya bani kamar dana ya mutu Momyn adams da jikinsa yayi sanyi tace haba suhailat ki kwantar da hankalinki Momy ta dakawa momyn adams,harara tace tayaya zata kwantar da hankalinka bayan an zalunceta Momyn adam tace haba hajara haba hajara ina matsayin yayarki yar uwarki zaki dinga gasamin magana Momy tace dole ingayamiki magana iya san raina saboda duk abunda yafaru kece sanadi ke kika matsa ayi aurannan,gashi sunaso. Su nakasamin yata Kuka momyn adams tasa nagode hajara ba laifinki bane nagode Dadyn suhailat yace haba kuyi shuru mana kisawa zuciyarku hakuri,kekuma doctor ki gayamana gaskiya in mutuwa yayi musani Doctor tace alhaji sai hakuri rai yayi halinsa Sakin baki suhailat tayi tana kukan zuci daga bisani tasaki ihu tayi kan sultan ta kankamesa gam gam tana sultan_sultan _sultan karka tafi ka barni ina sonka sultan Hassanace da momyn adams suke riketa dabata baki;amma ina kuka take tana ta sumbatu da kuka da fadin sunan sultan By Marsal[30/04 3:41 pm] Ya Ummi: *👟NAMIJIN GASKE👟* 3⃣0⃣ *By 2besties💞* _salma ali wadah_ ↓ _maryam yarmama_ *(marsal)* ®online hausa writter Wani likita ne ya shigo tare da nurses sukace su basu waje ina sam taki saki gadon da sultan yake da kyar aka ban bare ta daga jikin gadon suka tura shi suka fita Wani kuka tasa ki tare da zubewa kasa a sume nan itama aka dauke ta Cikin ikon Allah likitoci suka taru akan sultan suka ceto ransa da kyar turo shi sukai suka kaishi dakin da suhailat take A hankali ta fara bude idon ta abinda ya faru ne ya fara dawo mata da sauri ta tashi Hajiya hassana ne da mome suka yo kan ta suna mata sannu Ina sultan yake dan Allah kuce be mutu ba kuka ta saki mome ce ta rike ta tana bata haquri Hannun ta taja har bakin gadon da sultan yake wani farin ciki ne ya ishe ta ganin sultan yana bacci hankali kwance an dorai masa kansa da bandages daukan sa tai ta rungume shi tana kuka tashi yai daga baccin yana mata dariya nan itama ta fara dariyar farin ciki Nan likita ya shigo ya basu sallama gidan su suhailat dake abuja suka huce ita kuma Hajiya hassan tayi gidan ta Binta ce da su ummie farin ciki ya ishe su shegiya ana cen ana kukan mutuwa yanxu sai mugu dan da za'a dauka ae masa wasa Ni wallh ba abinda ya batan rai irin wa ae shima yana da haqqi akai na yanxu kinga sai ya nemi wani me haqqin khalisat ta fada Dariya suka kwashe sannan suka tafa to yanxu Mene abinyi ku matso kuji nan suka hadu binta ta rada musu wata maganar dariya suka kuma saki gaba dayan su Kulawa sosai Momeen suhailat take basu ita da sultan nan take suka warware sukai kyau kamar basu ba, Dadyn Adams ne zaune shi da momen sa alhaji ni wallh abinda yaron nan yake sam baya kyautawa ya fifita matan sa akan suhailat ga abubuwan da suke mata yanxu da wuya iyayen ta su bari ta komo Duk yadda muke da mahaifiyar ta amma sai da ta kusa fadan magana Gaskiya be kyauta ta ba waya dady ya daukko ya danna kiran sa yana zaune jugum ya rasa abinda Ke damun da sauri ya dauka cikin fada dady ya fara magana Kai wane irin yaro ne mara jin magana kai maza maza kazo ina son ganin ka kan raina ya gama baci Tab ko wane laifi naiwa dady nasan ba karami bane a hanzar ce ya shirya ya fito ko takan su khalisat be biba By marsal [30/04 3:41 pm] Ya Ummi: *👟NAMIJIN GASKE👟* 3⃣1⃣ *By 2besties💞* _salma ali wadah_ ↓ _maryam yarmama_ *(marsal)* ®online hausa writter A 36o yake gudu cikin kan kanin lokaci ya isa gidan a parlon dady ya tarar da su durkusawa yai har kasa ya gaida mome amma ko kallon arziki be samu ba dady kuwa da kyar ya amsa Lallai Adams basai kayi haka zaka nuna mana Cesar ka girma ba dagowa yai da sauri wani mugun kallo mome ta watsa masa Mome menayi au baka sani ba to bari kaji duk irin abunda kake wa suhailat ya dawo kunne na wato sabida rashin adalci shiru tai batare da ta karasa ba Mome kiyi haquri ba laifi na bane to laifin wane ni kaina mome ba'a son raina nake haka ba wllh amma ae laifin suhailat din rufe min baki shashasha wanda ya kasa rike gidan sa dady ya fada Yanxu sabida rashi mutunci irin naka tunda ta baro gidan ka baka taba zuwa dubata ita da yaron da yasami hadari ko bayan komene kai ka ja Kuyi haquri in Allah ya yarda zanje haquri ya basu sannan ya tashi ya fita Hmmmm alhaji yaron nan sai an hada masa da addu'a lamarin ya girmama to Allah ya sawwake Daga gidan su gidan su suhailat ya nufa jiki ba kwari dan yasan Momeen suhailat ba wasa sallama yai a dakile mome ta amsa ko gaisuwar da kyar ta amsa ya jikin sultan ban sani tsohon mara kunya Mome dan Allah kiyi haquri wallahi ba laifi na bane eheee lallai ba laifin ka bane shine zaku taru kai da matan ka ku kashe min 'yata da jikana ko to wllh da wani abun ya same su da sai munyi shari'a da kai ae ni ban san kai yaron banza ne ba sai yanxu Mome dab Allah kiyi haquri ina sultan din yake au ina ma magana kai mara kunya ko sai ka tashi kaje inda yake ka dauko shi Ita kuwa suhailat tana tsaye wanda tun shigowar sa take kyau ya kara yi mata nan taji son sa na kuma nunkuwa a ranta kamar baza ta fito ba gudun kar yai mata hulakanci a gaban mom yasa ta daure ta fito dauke da sultan A sanyaye ta gaisheshi dagowa yai kai sai da gaban sa ya fadi ganin irin kyaun da tai masa fuska a sake ya amsa nan ta mika masa sultan Tab wadda take fadan ma dan ita ta fito wajen mijin ta ba tare da wata damuwa lallai ma suhailat din nan momy ta tashi rai bace Yana ma sultan wasa yana satar kallon ta duk wani abu da yake Ji game da ita ya daina sai ma wani son ta da karu a zuciyar sa Da kyar ya bada sultan dan sam be gaji da kallon sa shi da uwar sa ba gani yake kamar ya sace ta su gudu Yana fita mome ta fito kodai wallah anyi mara zuciya duk irin abinda yake miki amma har wani rawar kafar fitowa kike ko duk wannan abin dan na kwato miki encin ki nake mome wllh sam ba laifin sa bane Sharrin matan sa ne ni kaina nasan irin son da yake min baya musu to shikke Allah ya kyauta amma ko sani ba inda zaki koma da sauri ta dago kallon da momy tai mata ne yasa ya sauke kanta da sauri Shi kuwa Adams nan ya maida gidan su suhailat wajen zuwan sa duk da ba wata magana da take shiga tsakanin su da suhailat amma suna satar kallon junan in sunyi kuskuren hada ido sai su sakar ma junan su murmushi Ko daga aiki ya dawo baya koma gidan da wuri sai ya biya wajen suhailat nan su khalisat suka kasa gane kan sa A dakin khalisat suke zaune anya kuwa bakwa ganin kamar aikin nan ya warware dan ina zargin haka ko bacci bayayi sosai Nifa jiya ina bincike ya wayar sa bayan ya shiga wanka pictures din sa nagani shida shegen dan da be mutu ba wata uwar ashar binta ta saki zai taba yihuwa ba wallahi Nan take ta kira wayar kawarta naja'atu Ke ba lapiya ba wallh gaba daya aikin nan ya warware to ku kuma kawo kudi a kuma sabon aiki Karki damu wannan karon fa bazamu sassauta mata ba me kankat za'ae shikke nan karku damu Shi kuwa Adams zuwan da yake yi yasa wata soyayya ta kuma kulluwa a ran su gidan su ya zarce wajen mome tana zaune da remote a hannun ta ah son ya akai Sosa keya yayi cike da kunya to yau kuma ni ake jin kunya gaskiya wannan maganr ba karama bace Mome dan Allah Kije ki bawa Momeen suhailat haquri a dawo min da ita a razane ta tashi rufan asirin bazaka hada mu fadan da bazamu shirya ba agaban ka tace lokaci take jira ka basu takarda ba dani kai da kai laifi kai zaka je bikon matar ka Mome dan Allah ki taimaka wllh ina mutukar son ta tab ba dani ba in na kuma zuwa sabida kana ganin baka sha wuyar dawo da ita ba Kila ma ku hadu ku kashe ta ba inda zani By marsal [30/04 3:41 pm] Ya Ummi: *👟NAMIJIN GASKE👟* 3⃣2⃣ *By 2besties💞* _salma ali wadah_ ↓ _maryam yarmama_ *(marsal)* ®online hausa writter Mome ki taimaka kai tashi ka ban wuri ka dame ni Fita yai ba kwarin jiki ko gida be huce ba ya tafi gidan su suhailat tun kan ya karasa magana mome ta daka masa wata tsawa lallai sai yau na tabbatar baka da kunya Ae kaida suhailat kuma hmmm magana ta kare kuka yake mata sosai kamar wani karamin yaro Kai kamaji London za'a kaita ta karo karatu kaje matan ka sun ishe ka haquri ba irin wanda be bata amma ina fir ta ki haqura Gida ya koma rai bace ido yai ja kamar wani gauta ummie ce ta tawo tana kwarwasa zata taba shi ya hankade ta har sai da ta fadi kasa kallon kallo akai tsakanin binta da khalisat Da ido binta tai mata inkiyar ta bishi tana shiga yana kokarin cire kaya honey wai me yasame ka ne mari ya fara zuba mata sannan ya zaro belt ya fara dukanta ta ko ina da gudu ta fito Binta da ummie kuwa mamaki ne ya hana su guduwa nan ya hada su gaba daya ya fara tafka shegu en iska kun rabani da matata me hankali Wallahi kuka sake muka rabu wallh gaba dayan ku sai kun gwamce baku sanni ba ya shige ya barsu suna kuka Wajen dadyn su ya nufa yana kuka ya fada masa komai sai da yai masa fada sannan ya kira dadyn ta shima kin yarda yai Kamar wani zararre ya zama duk wanda yasan zai fada aji ya fada aje a rarrashi gidan su suhailat amma ina Da kyar mome ta yarda an fara shirye shiryen komarwa ta wani farin ciki ne ya ishe su duk su biyun kullum yana gidan makale da ita Su kuwa su binta kuwa wata tsanar suhailat suka kara satar fita sukai gaba dayan su naja'atu tai musu jagora zuwa wajen boka me kankat Wasu damun kudi suka ajiye masa boka so mike ka haukatar da ita hauka mara warkewa dariya yai yace angama Tun lokacin da akace zata dawo yake kuma kawata mata bangaren ta Cikin dare mome taji ihu tun yana kasa kasa har Taji yayi yawa da gudu ta taho suna rige rige da dady Daga bangaren suhailat suka jiyo suna shiga suka ga suhailat ce take ihu gashinta yai buzu buzu Kuka mome ta saki wayyo na shiga uku me nake gani kardai ace haukace wa kikai ganin surutan da take kuma tana surutai ya tabbatr musu suhailat ta haukace kuka suke yi har dadyn By marsal[30/04 3:41 pm] Ya Ummi: *👟NAMIJIN GASKE👟* 3⃣3⃣ *by 2besties* _Salma ali wadah_ ↓ _maryam yarmama_ *(marsal)* ®online hausa writter Tufafin jikinta suhailat ta yaga tana dariya da kankame momy tana fadin momy gasunan da garwashin wuta zasu konani,gasu da bakin kaya Kuka momy take tana mata tofi Yayinda kanwarta wasila tashigo tana kuka itama Dady ya rige suhailat aka daddaureta da jikin karafunan gadon,sai ihu take momy bata fasa,mata tofiba Dady cikin tausayawa yace saidanace kar ayi aurannan kika matsa gashi ai sunaso su mata lahani Ita dazaman auren nan tagamashi har abada Momy tace,alhaji ko da ace kai zaka yarda mu kara tarayya da iyayen adams a matsayin surukai bazan taba yardaba kalli yanda sukeso su illatamin yata

Chapter 5 of 8