Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba. Har suka gama suka kira Ammi akan abinda zasu iya bata taci wanda Nurse zasu kawo mata yanzun nan. Sannan ya koma office wajen su Abbi.

Zama yayi yai danyi rubuce rubuce sannan ya dago yace
"Kuyi hakuri dan Allah!"
"Ba komai!"

"A gaskiya Maryam ta shiga hatsari sai dai cikin hukuncin Allah, Allah ya kawar da hatsarin wanda halin da ta shiga wani daga shi yake mutuwa wani ya makance wani ya kurmance wani ya bebance wani kuma ya rasa wani bangare na jikin sa kamar rashin tafiya da sauran su. To yanzu daga can nake naje na duba ta Alhandulillah matsalar tata ba wata babba bace domin kuwa ciwon kadan ne dan naga magana ce ta dauke mata kuma insha Allahu zamu daura ta akan magani da yaddar ubangiji in da rabo sai ta warke amman gaskiya ba a fiya warkewa ba."

"Innalillahi wainna illaihir rajun! Alhamdulillah! Allah mungode maka da wannan jarabawar Allah ka bamu ikon cin wannan jarabawar wannan yarinya Allah bata ikon dauka da cinye ta. Amin!"
Abbi ya fada. Yaa Muhammad yace
"Toh Allah yasa a dace!"

Magunguna ya rubuta sannan ya mike yace
"Zan kawo mata maganin yanzu!"
Mikewa su Abbi sukai sukayi masa godiya suka koma daki inda Nurses suka shiga da ita bandaki Yaya Fadima ta taimaka ta gyara ta suka fito ta zauna akan kujera daya daga cikin nurse din tana hada mata abinci dayar kuma tana matsa mata kafafun ta. Maryam kuwa sai bin yan dakin take da kallo kamar bata san su ba.

Gama hadawa tayi ta karaso ta zauna zata bata abincin kai ta dauke, tace
"Haba My sister ki daure kici ko yaya ne?"

Kai ta girgiza. Yaya Fadima ta amsa tace
"Haba dai Kici kinji kanwata."
Dagowa tayi ta kalli Yaya Fadima sannan ta girgiza ka.

Aisha ce tace
"To me kike so?"
Hawayen dake makale a idon ta ne ya zubo ta daga hannu tai mata nuni da cewar Yaa Haidar shi take son ta gani.

Abbi da ya gane me take nufi ya karaso ya kama hannun ta yace
"Kiyi hakuri kinji Mama nah, Aliyu ya tafi inda ba zai dawo ba."
Kuka ta fashe dashi tana girgiza kanta, Aisha ta rumgume ta tana jijjiga ta.

Ammi ce tace
"Wai Abbi rashin maganar nan fa?"
"Zatayi da yaddar Allah!"

"Toh! Allah ya yadda!"
Haka kememe taki taci abinci, magani ma kin amsa tayi sai allura da akai mata har da ta bacci dan taki ta daina kuka tin da ta tashi kuka kawai take yi wannan yasa sukai mata allura. Kwana ta uku da farfadowa amman sam bata cin abinci sai karin ruwa kuka kuwa shi ya zaman mata abun yi ko da yaushe. Maryam ta rame sosai sai idanu da hanci da suka fito.

In suka zauna ita da Yaa Alkasim tai ta kuka shima sai kukan baya iya lallashin. Kullum cikin nasiha da lallashi su ake a haka ta kwana ashirin a asibiti wanda a lokacin aka sallame su. Lokacin da ta koma gida komai sai ya dawo mata sabo saboda tina yadda suke rayuwa da Yaa Haidar a lokacin baya wanda kullum suna tare.

Tana zaune a falo hannun ta rike da Kur'ani tana karantawa Ammi na kitchen tana hada mata kunu ko zataji dadin bakin ta. Yaa Alkasim da Yaa Abdullah suna zaune a gefen ta.
Da sauri ta dago sai kuma ta mike tana kallon kofa. Yaa Abdullah ne yace
"Menene?"

Kofa ta nufa tana nuna musu da, musu alamun Yaa Haidar ne. Kasa ganewa sukai Yaa Abdullah ya mika mata paper da sauri ta amsa ta rubuta masa
"Muryar Yaa Haidar ne yai sallama wallahi shine!"

Tana bashi ta nufi kofa da sauri Yaa Abdullah da Yaa Alkasin suka mike suka nufi ta suna fadin
"Ba shi bane Maryam gizo take miki!"

Kai ta hau girgizawa tana nuna musu tare da tafiya kamo ta Yaa Alkasim yayi ya rumgume ta yana kuka yace
"Wanda ya mutu baya dawowa Maryam ba Yaa Haidar bane? Haidar ya mutu kuma ba zai dawo ba."

Kuka ta kuma saki tana girgiza kai a haka Aisha ta shigo ta same su, karasowa tayi ta ajiye basket din hannun ta tace
"Menene?"
Yaa Abdullah ne yai mata bayani sai ga Aisha ma na hawaye. Ammi ce ta fito da cup dan ta gamai mata ta gansu a haka.

Ita har ta gaji da wannan kukan nasu kullum haka suke yini kuka a asibiti yau ma sun dawo gida wato zasu cigaba da musu ko?
"Me kuma ya faru?"
Duk suka juyo suka dawo dakin. Yaa Abdullah ya karai wa Ammi bayani. Kai Ammi ta girgiza ta kamo hannu Maryam ta zaunar tace
"Kina da sani fiye da tunani mai tunani kin taba ji inda wanda ya mutu ya dawo?"

Kai ta hau girgizawa. Ammi tace
"To dan me kike cewa shine?"
Paper ta dauka ta fara rubutu tace
"Wallahi Ammi muryar sa naji Ammi dan Allah kuje ku duba min ko shine ya tsaya a waje dan Allah Ammi!"
Ta mika mata Ammi na karantawa idon ta ya kawo ruwa ta dago zatai magana suka jiyo sallamar Mamah.

Amsawa sukai Mamah ta shigo da sauri Maryam ta mike tana nuna mata kofa tana mata da hannu alamar wai taga Yaa Haidar, Mamah tace
"Me take nufi?"

Kan su bata amsa ta dauki memo ta fara rubuta mata tace
"Mamah kinga Yaa Haidar a waje wallahi yanzu yazo yana sallama ni ban da bakin amsawa jin ba a amsa ba ya juya ina jin!"
Amsa Mamah tayi tana karantawa itama idon ta ya kawo kwalla sannan ta rumgume Maryam tana fadin
"Haidar ya mutu Maryam kuma ba zai dawo ba."

Kwacewa tayi a jikin ta, ta sake rubuta mata
"Mamah ke mahaifiyar Yaa Haidar ce kika sani ko Allah ya dawo mana dashi ko kuma zaki ji tsoro in ya dawo ne ni bazan ji tsoron sa ba Ammi dan Allah ku dubo ko shine ya dawo."
Ta bata takardar. amsa Mamah tayi ta karanta. Kai ta girgiza Maryam ta kama hannun ta tana roko. Yaa Abdullah ta kalla tace
"Kaga jeka ka dubo mana ko dai shi din ne?"

Ta fada tana kifta masa ido ya juya ya fita. Mamah tace
"Ya jikin nata Hajiya?"
"Da sauki!"

"Taci abincin kuwa?"
"Ina fa kunu nayo mata na fito na same ta tana wannan maganar!"
Ta mika mata kunun kai ta make. Mamah tace
"In har baki sha ba ko Haidar din ne bazai shigo ba


Da sauri ta amsa ta fara sha sai dai me bata sha rabi ba ta ajiye ta dafe ciki sai kuma ta fara juyi tana kuka, da sauri sukai kan ta wanda ta cigaba da juyi kan su farga har ta suma da sauri Yaa Alkasim ya dauke ta suka tafi asibiti suna zuwa suka aka amshe ta bayani sukai wa doctor ya duba ta ya bata gado kan ta tashi suga halin da take ciki. Bata jima ba ta farka tana ganin Mamah ta fara nuna mata da hannu wai Yaa Haidar din yazo.

Tana gama nuna mata kuma sai ta rike ciki tana kuka dan yadda yake mata ciwo. Doctor yazo ya duba ta ya kara bata magani sannan ya samu ya lafa bayan awa daya yace zasu iya tafiya amman kada ta sha abu mai tsami kila ulcer saboda rashin cin abincin da batayi.

Dakin ta Ammi ta kai ta, ta kwantar da ita amman duk bayan mintina sai ta tambayi
"Ina Yaa Haidar a kira mata shi."

Abbi yai mata rubutu amman abun sai dada gaba yake ba zaka taba ganin idon Maryam ba hawaye ba. Kullum cikin kuka. Kowa tausayin ta yake da kwantar mata da hankali dan yadda suka san tsakanin ta da Yaa Haidar dole ta shiga damuwa. Ta dada ramewa dan ba bacci ba cin abinci.




Tin daga ranar duk abinda zata ci sai ta amayar dashi, duk ta rame kullum suna cikin yawon asibiti.

Mamah ce zaune Maryam kwance a kan cinyar ta. Mamah tace
"Gobe zamu tafi Umrah Amman sati biyu zamuyi mu dawo zan roka miki Allah ya baki lafiya Maryam!"

Hawaye ne ya zubo Mata. Mamah tasa hannu ta goge mata. Ammi ce ta shigo ta zauna tana fadin
"Kukan ake ne?"

"Hmmm Hajiya gobe fa ne tafiyar!"
"To Allah ya kaiku lafiya Amin!"

"Amin ga amanar Maryam nan dan Allah a kular mana da ita."
"Insha Allahu."

Daga nan suka cigaba da hirar wanda kullum hirar dai ta Aliyu ce. Maryam na kwance tana jin su amman ba bakin magana.

Sai yamma Mamah ta tafi. Tana shiga ta hadu da Ummah zata fito kallon ta, ta tsaya yi tace
"Iska na wahal da me kayan kara, duk abinki ba zaki sake haihuwa ba Kuma yarinya ba zasu baki ita ba sai bibiyar su kike to zanyi maganin abun. Kuma ke da ake cewa mai haihuwa tinda kika haifi yara biyu kin kuma? Bama wannan ba yanzu ina yaran daya ya shiga duniya daya ya mutu kinga biyu babu daya kike da wacce bata taba haihuwar ba."

Kai Mamah ta dauke tayi cikin kawai. Ummah tai dariya tace
"Sai naga bayan ki da shegiyar yarinyar nan Maryam!"
Ta fita a gidan fuska ba walwala.

Washe gari dasu Mamah zasu tafi ta shiga yin sallama ta samu Maryam a bandaki tana ta amai tausayin ta bata bayan ta gama ta kama ta ta dawo ta zaunar da ita.

Ammi ta gyara wajen Mamah tace
"Amman ni da an koma asibiti wannan aman yai yawa ayi test da aune aune gaskiya."
"Wallahi ni har na gaji da zaryar asibiti kusan wata kenan ana fama da abu fa."

"To ya zamuyi, ai sauki sai a sannu yake zuwa da sannu zamu samu nasara."
"Shikenan gobe na fadawa Alhaji muje."
"Allah kaimu."
Anan Mamah ta zauna har sai da Abbah ya shigo ya duba Maryam sannan Yaa Alkasim ya tafi kai su Airport

Ranar kwana sukai Maryam amai dan da ta sha ko ruwa ne sai ta dawo dashi. Akan ta yan gidan suka kwana gaba daya sun tausaya mata. Ai kuwa ana dawo daga sallah asuba suka tafi asibiti amsar ta akai aka saka mata ruwa dan jiki ta yayi mugu weak bayan an saka mata ruwa wata nurse ta shigo ta dibi jinin ta dan yin test.

Dakin cike da yan uwan ta ita kuwa tana ramuwar bacci da bata samu tana yi. Wajen karfe sha biyu Nurse din ta shigo da file a hannun ta, bude na farko tayi tace
"Jinin ta ya hau dole a kula da ita dan yarinya ce bai kamata ace jinin ta ya kai har haka ba."

Ta dauki dayan file din tace
"Mun mata na malaria da typhoid all are negative!"
Ta dauki dayan file din ta bude sai ta saki murmushi tace
"Oh congratulation tana dauke da ciki ashe shiyasa take ta wahala har haka!"


*Ai ban san ana bibiyar labarin nan nawa har haka ba, amman shine fisabilillahi ba dan comment bare vote, facebook ne kadai masu yin kokarin yin comment da liking, haba to zan daina nima na koma na kwanta. Gaskiya ku gyara in ba haka ba to nima posting sai naga dama.*


*Allah ya jikan musulmai Allah ya kyautata namu zuwan yasa muyi kyakyawan karshe. Amin*




*Antty*
Maryam Suleiman

ο»Ώο»Ώο»ΏπŸ’—πŸ’— *MATAR HAIDAR* πŸ’—πŸ’—
Page 28

By
*MARYAM S INDABAWA*
HAJOW


*Bismillahir Rahmanir Rahmin*


Dai dai farkawar Maryam wanda taji abinda Nurse din ta fada. Dummmmmm haka dakin ya koma babu wani abu da yake motsi na wani dan lokaci. Kallon kallo suka fara yiwa juna. Maryam kuwa zuciyar ta kamar ta fito daga kirjin ta dan yadda take bugawa da tsalle. A wannan lokacin da za'a sake auna jinin ta ba karamin hawa ya sake yi ba saboda tsananin firgicin da ta tsinci kanta a ciki.


Takardar hannun nurse din Yaya Zainab ta fizga tana karantawa jikinta ya hau rawa. Yaya Ummulkursum ta karbi takardar suka hada kai ita da Yaya Fadima da Yaa Abdullah suka karanta. Gaba dayansu takadar suka saki ta fadi kasa fuskar su cike da tsoro da fargaba.

Ammi dake gefe ta zaro ido tana tambayarsu me suka gani a takardar. Kasa magana sukai. Yaa Alkasim kuwa ko kallon takardar baiyi ba ya fita wurin likitan ya nufa ya samu Yaa Muhammad suna tattaunawa akan ciwon Maryam da rashin maganar har yanzu. Kamar wanda aka jeho haka ya shiga office din ransa ya gama baci. Yaa Muhammad ya mike da sauri yana fadin
"Menene ko jikin Maryam din ne?"
"Ina fa ba gwara jikin ta ba da abinda suka ce tana dashi. Wata mahaukaciyar nurse ce take fadin wai ciki ne da ita!"

Ya maida kan sa kan Doctor yace
"Ka taso muje ka duba ta da kan ka, dan ni ban yadda da aikin ta ba ko canjen result akai."
"Is ok ka kwantar da hankalin ka kaji zan kara duba ta, na gani kaji!"

"Is better!"
Ya biyo bayan sa, suka nufi dakin gaba dayan su. A tare suka koma dakin wanda yayi shiru kamar ruwa ya cinye mutanen cikinsa. Karar fanka kawai ake ji sai jefi jefi wannan ya kalli wannan. Suna shigowa likitan ya dauki result din ya karanta.

Kallon Yaa Alkasim yayi yace
"Ba an daura mata aure ba, mijin ya rasu?"
"Yes!"

"So shine me?"
"Kaga ka kara gwada min ita kawai."

Sirinji ya dauko a cikin aljihun lab coat din sa sannan ya karasa wajen gado inda Maryam ke kwance komai ya tsaya mata cak. Jinin ta ya dauka sannan ya fita da kansa ya shiga lab ya kara yin gwajin. Sai da yayi sau uku yana bashi result iri daya dan haka ya dawo dakin. Kowa yasa ya fita sannan ya karasa wajen gadon inda Maryam dake jin duk abinda ke faruwa take.

Ido ta bude wanda ya rine yai jajir, Paper ya bata yace
"Zan miki tambayoyi kinji kanwata?"
Kai ta gyada!

"Wata nawa da auren ku?"
Shiru tayi tana nazari kan ta ya kulle wanne zata fada to wannen ne dai dai in ta fadi wancan me iyayen su zasu ce.

"Kanwata!"
Ta dago ta kalli shi.
"Fada min kinji?"

A paper ta rubuta sannan ta mika masa. Amsa yayi ya gani yace
"Are you sure?"
Kai ta gyada yace
"When last did you saw your period?"

Abinda tin dazu kwakwalwarta ta kulle babu wani tunani da take iya yi sai yanzu ta dawo hayyacinta da taji wannan tambayar. Hankali a tashi dan zata ce tin kan su fara exam da tayi wani period marar ta tai ciwo har ta dawo gida bata karayin wani ba. Shin me hakan ke nufi kenan?

Taiwa kan ta tambayar
"Fada min kinji!"
Rubuta masa tayi ya amsa sannan yace
"Kin tabbata?"

Kai ta gyada masa ya jin jina kai yace
"Good"
Fita yayi ya kira Ammi da Abbi sannan ya kalle su yace
"A bisa binciken da nayi da kuma amsar da tambayoyi da nai mata, ya nuna tana da *CIKI* na kusan wata uku."

"Lahaula walaquwwata illabillah........ La'ilaha illalahu Muhammad Rasulillahi Sallalahu alaihi wasalam!"
Ammi ta fada. Mika musu result yayi sannan ya fita.

Amsa Abbi yayi da zuwan sa kenan bai san me yake faruwa ba. Takardar ya karanta sannan ya juya ya fita kawai. Ammi ta bishi da kallo sannan ta kalli Maryam dake fidda numfashi kadan kadan. Hawaye na zubowa a idon ta.

Zuciya ta kuwa bugawa take kawai tsoro, fargaba, farin ciki ta rasa wanne zatayi a duniya. Yaa Alkasim ne ya shigo da sauri yace
"Ammi me ya faru?"
Kai Ammi ta girgiza kawai ta juya ta fita. Karasowa yayi gefen gadon yace
"Maryam menene fada min?"

Hawaye take sai girgiza kai take. Ammi na fita ta kalle su tace
"Ku tashi mu tafi gida!"
Mikewa sukai Yaya Fadima tace
"An sallame ta ne?"

Ammi bata, bata amsa ba kawai ta fice sauran suka bi bayan ta ita kuwa dakin da Maryam take ta koma. Nan ta samu Alkasim yana tambayar Maryam amman sai kuka take. Fita yayi ya koma dakin doctor yace
"Me result din ya nuna?"
"Is positive!"

Ido ya zaro yace
"Impossible!"
Sannan ya fita a dakin da sauri. Ya nufi dakin da Maryam take
"Tashi muje wani asibitin a kara test ban yadda da wannan ba."

"Oh haka suka ce da cikin dai?"
Yaya Fadima ta fada. Kai ya gyada. Kallon Maryam sukai da jikin ta ke ta rawa dan wani zazzabi da ke son kamata. Kan ta sukai suna mata sannu ganin kamar tana firgita yasa ya kira likita allura yai mata bacci ya dauke ta.

Yaya Fadima ce ta kalli Yaa Alkasim tace
"Kai me kake tunani akan wannan lamarin?"
"Bazan taba yadda ba, nasan Maryam ba yar iska bace wama za ace yai mata cikin?"

Ya tambaya sai kuma yace
"Haidar za a ce ni shaidane Maryam da Haidar ba mazina ta bane wallahi ba zasu taba aikata zina ba dan nasan halin su duk su biyu suna da imani da tsoron Allah, Allah ba zai jarabce su da wannan mummunan aikin ba domin suna kiyaye hukuncin Allah nasan ba dai dai bane ba wani ciki da Maryam take dashi shiyasa nace zamu je wani asibitin mu kara dubawa."
Ajiyar zuciya Yaya Fadima ta sauke tace
"Wannan haka ne Yaa Alkasim amman dole mu bari ba yanzu ba kaga halin da take ciki mu bari muga ya jikin nata in yaso sai muje wani asibitin! Amman ya kake ganin su Ammi suka dauki alamarin?"

Kai ya girgiza yace
"Ban sani ba!".
"Cewa tayi duk mu tafi gida fa."

"To abar wa a wajen ita Maryam din?"
"Abinda yake bani tsoro kenan kar su Ammi su kasa fahimtar 'yar su, kar su zarge ta da wani abu."

"Anya kuwa?"
"To ban dai sani ba."
Sukai shiru suna kallon Maryam dake baccin wahala dan da ka kalle ta zaka san ba baccin dadi take ba.




A kofar gida duk sukai parking suka fito kowa cikin tashi hankali da baci rai suka shiga gida wanda fitowar Ummah kenan ta gansu a wannan halin ba karamin dadi taji ba. Falon Ammi duk suka tafi, Yaa Muhammad da Ibrahim sai Yaya Zainab da Ummulkursum zama tayi suma duk suka zauna.

Ummah parking motar ta tayi ta fito ta nufi cikin gidan bangaren Ammi ta nufa wanda lokacin Yaa Muhammad yace
"Ammi me ke faruwa ne?"
Shiru Ammi tayi can ta dago ta kalle su tace
"Mummunan abu na shirin ya faru damu koma nace ya faru damu... Ace acikin gidan nan za a samu wanda zai yi ciki ba aure."

Tayi shiru dan abun ba karamin tsoro ya bata ba. Yaa Ibrahim yace
"Da gaske cikin ne da Maryam?"
Dummmm haka Ummah taji ta zaro ido da sauri tana fadin
"Ciki ciki! Kuma Maryam?"

"Shine likita ya tabbatar!"
Maganar Ammi ta dawo da ita da tunani da zancen zucin da take da sauri ta juya ta nufi mota hankali a tashe take fadin
"Ciki ciki! Maryam ke da ciki? Garin Yaya wannan jarababben yaron kan ya mutu sai da ya sadu da ita kenan, daga daura aure yaje wajen ta ko me?"

Shiru tayi tana tuna abinda taji Ammi ta fada wai
"Mummunan abu na shirin ya faru damu koma nace ya faru damu... Ace acikin gidan nan za a samu wanda zai yi ciki ba aure"
"To suna so suce cikin ba na Haidar bane ko me ko suna so suce kan ai aure suka tara."

Kai ta girgiza tana fadin
"Nasan wane Aliyu ba zai taba kusantar zina ba kamar yadda nasan Maryam to ya akai abin ya faru. Dole na dauki mataki tin kan Hajiya Binta taji batun nan dan nasan a duniya ba abinda zata so kamar taga jinin Aliyu ko da kuwa shege ne wanda na tabbata da kyar in cikin nan shege ne dole na batar dake Maryam dole na batar dake da dan cikin ki, Binta ba zata taba ganin jinin ta ba ko na dan ta dole na batar da ke kamar yadda na batar da Abubakar daman da tamu dake da tamu da ta Hajiya Amina zan samu na jefi tsuntsu biyu da dutse daya za na batar muku da yarinya na saka muku tsanar ta sannan na batar da jini Hajiya Binta."

Wata dariya tayi tana fadin
"Komai zai zo yadda nake so kuma yadda zan tsara."
Unguwa zata amman sai ta canja hanya ta tafi gidan bokan ta.



*
"Ammi amman kina ganin da gaske cikin ne?"
Yaya Ummulkursum ta fada.
"Nima dai abun ya bani mamaki anya kuwa?"
Yaya Zainab ta fada.

"Likita zai karya ne. zai yi mata sharri ne?"
Ammi ta fada. Kai suka hau girgizawa. Yaa Ibrahim yace
"Ba zai ba amman yakamata mu canja asibiti a kara zuwa wani a tabbatar ko?"

"Haka ne Yaya!"
Yaya Zainab da Ummulkursum suka fada.
"Kai na ya daure na rasa wane tunani zanyi!
"Ammi please ki nutsu ni a gaskiya bana zargin Maryam da aikata zina sai dai in wani tsautsayin ne ko wani abun!"
Yaa Ummulkursum ta fada.
"In wani tsautsayi ne ya hana ta fada mana!"

"Ammi kinsan ta da kunya. Kuma abinda Yaya Ummulkursun ta fada haka ne amman yanzu in cikin ne na wa za a ce?"
Yaya Zainab ta fada.
"Kada ku daurawa bawan Allah dake kabarin sa kwance cikin rahmar Allah. Nasan Aliyu yaro ne mai imani da ilimi da kunya ba zai taba aikata haka ba, ba zai aikata zina ba."

"Ammi ita kuma Maryam din fa?"
Yaa Abdullah ya fada wanda ya jima yana tsaye yana jin tattaunawar tasu. Shiru tayi kawai can ta mike tace
"Bari na gani ko Abbin ku yana ciki!"

Ta mike ta fita suka zauna suna tattaunawa. Matan duk tausayin Maryam ya dada kamasu shi me yake shirin faruwa dasu ne wannan wane irin jarabawace Allah ya basu ikon cinye ta amman suna tsaka mai wuya. Ammi da ta shiga taga Abbi baya nan zama tayi tana tunanin mafita dan kan ta ya kulle gaba daya Maryam na da ciki kai karya ne itama ba zata yadda ba ace tana da ciki. Haka tai ta tunani har aka fara kiran sallah magariba da sauri ta mike ta dauro alwala tazo tayi sallah. Bayan ta idar ne kuma tai addu'a wanda ta dan samu nutsuwa har ta hau tunanin a wane hali Maryam take a lokacin. Mikewa tayi ta shiga bangaren ta, ta samu su Zainab da Ummulkrsum tace
"Ku kira min Abdullah ya kaini asibiti ku kuma kuzo ku tafi gida kunji."

"To Ammi!"
Suna cikin kiran sa ya shigo tace
"Yauwah muje ka kaini asibiti!"
Suka tafi.




*Allah ka yafe mana kasa muyi kyakyawan karshe Amin*



Maryam Suleiman
"Antty*

ο»Ώο»Ώο»ΏπŸ’—πŸ’— *MATAR HAIDAR* πŸ’—πŸ’—
Page 29

By
*MARYAM S INDABAWA*
HAJOW


*Bismillahir Rahmanir Rahmin*


A asibiti Fadima da Yaa Alkasim ne zaune sunyi shiru suna tunanin kowa da abinda yake tunani. shigowar Ammi ne ya sa suka mike da sauri ta kalle su, ta kalli Maryam tace
"Ya jikin nata?"

"Da sauki!"
"Ki tashi Abdullah ya kai ki gida!"
Ta fada tana kallon Zainab.

"Ammi baya gari kuma na nemi alfarmar ya barni na kwana tare da Maryam."
"Shikenan kije gida ni zan kwana da ita."

"A'ah Ammi ni zan kwana kije ki huta dan Allah!"
Zama tayi ta zuba ma Maryam ido tace
"Tin yaushe take baccin?"

"Bayan fitar ku jikin ya tashi shine akai mata allura."
"Shiru Ammi tayi. Yaa Abdullah ya karasa yana kallon kanwar tasa da ta rame sosai tausayi ta bashi dan haka sai ya juya ya fita kawai dan zuciyar sa ba karamin karyewa tayi ba. Sai goma suka tafi suka bar Fadima a wajen ta.

Ammi na komawa gida ta nufi bangaren Abbi wanda dawowar sa kenan. Zama tayi tace
" Kaci abinci ne?"
Dagowa yai ya aika mata da wani kallo wanda ya bata mamaki.

Kasa shiru tayi tace
"Na jima ina jiran ka dan ina so muyi maganar akan Ummi "
Ummi take kiran Maryam wani lokacin saboda sunan mahaifiyar sa ne.

"Ai yar kice duk abinda kika yanke ya dace!"
"Bangane ba Abbi!"

"Kome tayi da sanin ki!"
"Wai kaima ka yadda da tana da cikin?"

"Saboda me bazan yadda, naje asibiti yafi biyar ana min test ana fada min positive. Ke zan fara tambaya cikin waye a jikin ta, kada kice min na Haidar ne!"
"Innalillahi wainna illahir rajiun Yanzu ni kake zargi akan cikin jikin Ummi, zan sani na boye maka shin me ka dauken da Ummi ne? Naga kafi kowa sani na da Ummi kasan halin mu dan me kuma zaka daura mana laifi baka taba kawowa ko fyade akai mata ko wani abu ba....."

"Kinga ko kina son ki kare ta, in fyade ne wata uku dayi bata fada ba a haka tasan tana da ciki aka daura mata aure da yaron nan, Allah yaso baya raye da wane hali zai shiga kinsan dai yadda yake son ta."
"Dan Allah ka daina fadar haka wa ka sani wanda ya taba zuwa zance gun Ummi. Haidar ne kadai mane min ta inma tuhuma za ai shi za a tuhuma."

"Na fada miki kada ku daurawa yaro nan, yana can kwance cikin kabarinsa cikin salama, kada kisa a tashe shi ana tambayar sa dan Allah!"
"Amman Alhaji......."

"Dan Allah Amina ki kyale ni, tashi kije yanzu bana son magana ki kyale ni da abinda nake ji. Wai yau ni a cikin gida

Please Login or Register in order to submit comment