Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ai naje duba safna duk bamu haduba Dr hanna tace ok Allah ya kaimu bye Ahj Saddam tin bayan futar dansa yarikice yashiga wani hali kusan wuni yayi yanata saka da warwara dana sani da nadama kawai yake yana fadin dama dai dama dai da duk haka bata FARUBA Allah yasa zai amfanar kuma ya gamsar daku LUV U ALL 07033524044 [1/31, 8:40 AM] SARATU: _*🍂BIYU BABU…!🍂*_         _SAMU DA RASHI…_                🍂🍂🍂                  🍂🍂                      🍂       _*AɭKAɭAMƖŊ✍:Saɾatų mųŋχaɭɩ*_            _*(AMSAR💕)*_         _watpadd @ Ssaratu75…_ *ɖҽɖɩcatҽɖ tɷ:AUNTY ZALY MMN AHMAD YOLA*     *🅿_____3*   _*Sadaukarwar page din farko nakune FADHILA NURADDIN and SIS HAFNAN,you are indeed a gift to evry1 dat meet you and I'm glad dat i met u,Allah yabar zaman tare💕*_ 🌲🥀💦💦💦💦🥀🥀 💦💦💦🌲 ____________📖AHJ SADDAM Dan asalalin gwaram ne, mahaifinsa malam Abbas Wanda akafi sani da MlmAbashea, Mahay fiyarsa safiya, Wadda ita kadai ce matarsa Suna da yaya 3hyhuwar ta tafari yan biyune duk Mata Sai na3 Wato Saddam amma ana kiransa da gambo Allah yayiwa iyayen sadam da yayyensa rasuwa, a wata rana tasanadin  wutar lantarki wato Nefa Wanda hakan yasa suka rasa rasuwar su, kasan cewar twins din dakin su yana kallon na iyayen, duk acikin palon Saddam wanda nasa dakin yana farkon shigowa stakar gida Hakan yasa Allah yaja kwanansa Lokacin shekararsa 11 Yayan mahyfinsa wato baffa Akilu shiya taho dashi birnir kano ranar sadakar arbain Baffa Akilu mutum ne mai mutukar kulada yara daga kan bare zuwa jininsa Baffa Akilu yana daga cikin mutanen da Allah ya jarabta da rashin Aure Baffa Akilu ya kasance akarkashin wani uban gidansa dake a kasuwar kwari mai arxiki daidai kwargwado ga karamci da tausayi wato Alhj Alkasim Ahj alkasim yayi mutuqar murna ganin mlm Akilu tafe da dansa Wanda shiya bashi shawarar ya daukoshi koba komai yaringa taima kamasa Babu irin nasihar da Alhj Alkasim baya yiwa mlm Akilu akan yaje yasamu hutu yakai lokacin da xaihuta Amma inaaa Mlm Akilu yace yafiso ko mutuwa taxo tariskeshi yana kan Neman halak Ahj Alqasim ya kara yiwa mlm Akilu ta a xiyya Yakuma yiwa gambo wato Saddam Take yaji yaron yashiga ransa hakan yasa yamasa nasiha mai sosa rai Kasan cewar Ahj Alkasim bashida da namiji Hakan yasa yaja Saddam ajiki yadauki duk wata dawai niyar karatunsa da komai narayuwa Domin kullum burinsa ya kyau tatawa nakasa dashi, bare yanxu daya samu maraya, gani yake yayi babbar sa'a Hakan yasa yabawa Ahj Akilu bq Surunga kwana shida dansa Saddam Daxarar Saddam yataso daga schll zaisa uniform yashiga Cikin gida ya karbi abinci Matar Alhj Alkasim kullum saita masa gori Kullum da kalar gorinda takemasa Saddam tinyana jinzafi yana kuka harya saba Saddam daya gama cin Abinci xai dauko bag dinsa yatafi islamiyya Daan tashi xai shirya ya dauko kekensa yabi baffa kasuwa Yana taima kawa baffan nasa da shara hada kaya da mikasu ga ragowar shagunan Alhj Alkasim Babu irin tijarar da matar Alhj Alkasim ba tayi masaba akan baxai kawo mata stintattun baki gida ba Amma Alhj Alkasim yayi burus daita kuma yasa takum kumi akan duk wanda wayula kantasu saiya hukun tashi Hakan yasa matarsa ta sanyawa kanta lis lama ta hakura amma taciki na ciki Dan tasan halin Ahj astaye yake babu wanda ya isa yastallaka dokarsa Tana mutukar kyamar Saddam Ba tason taga yayan ta suna nuna kulawarsu akansa ko suce agidansu yake Musamman yadda taga umma tana shish shige masa Musamman idan takasa yin assignment tadinga binsa tana magiya Hakan ba karamin dadi yakewa Alhj Alkasim ba Saddam yataso cikin yanayin rayuwa ta abin tausayi Duk wanda yaganshi kobai san tarihin saba xaiji kawai yau yaga kalar tausayi Duk da yashaku da yayan Ahj Alkasim Kasan cewar schll dinsu daya haka islamiyya Tohh A kwana atashi Bayan wasu shekaru Baffa yasa Saddam Agaba yana masa nasiha akan yayiwa Allah yanemo matar aure Baffa yastufa sosai dan takai baya iya zuwa kasuwa Saboda yanayin girma da larura tayau da gobe Saddam yatau sayawa baffa yasan kullum zancensa kenan Saddam karna mutu banga auren kaba Toh baffa insha Allah acikin shekarar nan xan nemo mata Saddam kasuwanci yayi nisa shida Alhj Alkasim musam man yanda kowan nensu yake nuna stanstar kulawa tamkar uba da da A wata jama'a Alhj Alkasim yayi sallama a gidansa Ba tareda yajira amsaba yashiga kamar yadda yasaba Alhj sannu daxuwa Yawwa Alhj Alkasim yafada atakaice Ungonan Yamikawa matarsa invitation card Tace tohh na auren waye? Alhj Alkasim yace na auren yata umma Masifa da bala i aranar ba sauki Har Alhj Alkasim yagaji daji yadau key yana nufin futa Lalle ma Ahj to wai yaron ubansa waye agarinnan Alhj Alkasim yace badan kowa bane amma yayi karatu Karatumme Mutane dubu nawane su kayi karatu amma basuyi arxikiba tayita sukar balai San ranta Candai data nisa Sai tasas sauko damurya tace Ahj kaifa kadau alqawari yayan ka sai sunyi kararu maizurfi sannan kayi musu aure sannan yaranka ba kalar talaka bane Cikin stawa Alhj Alkasim yace ya isheki Jabriyya Nasan nayi alqawari amma yanxu na janyeshi daga kan umma Kuma wllh ashirye nake Da duk wacca naga kanta yana rawa saina daste karatun nayi mata aure Idan yaso intaje gidan mijin tacire kan Alhj Alkasim afusace yadau key dinsa Yana isa bakin kofa yaci Karo da yayan sa Baba sannu Barka da gida Yawwa sannunku kundawo lfy Ai ba sukai ga bashi amsaba sai jisukai tauuu sauti yagau raye falon Jabriyya tadauke umma da mari tacilla mata invitation tace waye zubair? Kirasa wanda xaki kula sai mastiyaci dan masiyata Umma wadda ayashe take akasa stabar karfin marin  Dakyar tayi yinkurin dagowa tace meya yimiki Jabriyya tace ubanki ne xai daura miki aure dashi rana ita yau Amugun tashin hankali umma tamike tace waaahh da zubayr Atake taxube agaban Alhj Alkasim Babana wai xubayr xaka auramin Insha Allah fadar Ahj Alkasim Wayyo Allah babana wllh sau biyu muka taba haduwa Dan Allah Abba kataima kamin wllh Abba bana sansa Alhj Alkasim ya rusuna yadago ta yace umma Kaf cikin samarin dakike tarawa babu Wanda yake da niyyar aurenki duk nabi daya bayan daya naji tabakinsu mayau darane Zubair kadaine yace min yanada niyya kuma yayi shirin aure Umma muddin nabarki akan kicigaba da karatu to tabbas xaki kaucewa tarbiyyata Da duk wani burina Na shiga Aljannah adalilin Ku yaya mata da Allah yabani Umma tadago kai araunane Tace to Abba indai wannan ne burinka to dan Allah Abba karka aura min zubayr Wllh dana auri zubayr gara ka auran Saddam Abbb takarashe maganar cikin shashshekar kuka takuma kamkame hannun uban dan Allah Abbbbaaaa Umma bata ankara ba takarajin wani wawan Marin daya gigi tata batasan lokacin da tayi loww tafada jikin Abba ba Abinka da yan hutu bata taba sanin xabin mariba Alhj Alkasim ya lura yar tasa tasuma yan uwanta kuwa tasneem da yaya duk sun raxana astaye Hawayene kawai ke sintiri afuskarsu Alhj Alkasim Wanda tun marin datai mata na farko xuciyarsa takai kolo luwa amma ganin yayansa agurin yahanashi aikata komai Danshi mutumne da bayason yayan sa suga sa insa tsakaninsu ganin yaya mata ne gidan wani xasu Kuma koda maxnane aixasuyi aure Kuma duk abin da sukaga iyayen su sunayi shi zasuyi Alhj Alkasim yamika hannunsa kan center table yadau ko water bottle Ahankali Umma tafara sauke ajiyar xuciya Alhj Alkasim yace ummata kiyi hakuri kinji nariga nagama magana da iyayen zubair bai kamata naxama karamin mutum ba Tabdijan Nana tace tanata faman huci tanata sintirin kai kawo a falon Wllh umma ko xaki mutu baxaki auri Saddam ba yaronda bamu san dangin saba aiduk kansu bagwara barayi ne kawai na uwar stintau Alhj Alkasim yace nana idan kika sake furta kalma daya Toh kinfada abakin auren ki Yajiyo yace umma ina kaunar Saddam kuma nikaina nayi tunani ba adadi akan nabashi daya daga cikin yayana Toh amma danayi naxari saina ga wllh duk kanku ba wadda ta dace da auren Saddam Saboda inhar xan aura masa daya daga cikin ku Toh hakika xai kaiku ga halaka Nina hango abinda baxaki taba hango waba Kuma nasan abinda baki saniba ninake tare dashi nasan halinsa ciki da bai Auren ki dashi baxai taba kaiki ga samun Aljanna ba Dan haka dan Allah kiyi hakuri kiyarda da babanki baxai miki xaben tumun dare ba Umma ina kaunar ku ina fata da burin Allah ys kuza memin sadaka tujjariya Da sauri yatashi yanufi dakin jabriyya Yana shiga yatarar tanata hada jaka Alhj Alkasim yace Kinyi akan gaba Kibar gidannan har saina nemeki Ya futa ahasale Alhj Alhj ana magana ya akai Ahj baffa Akilu ne yake magana Ahj Alkasim to muje Suka gaisa da baffa cikin mutum tajuna kamar yadda suka Saba Alhj Alkasim yace baffa inasanar dakai daurin auren yata umma ranar jama'a maixuwa insha Allah Baffa yace habba Alhj amma ai Alhj Alkasim yakatse maganar baffa Yace tabbas nasan xakayi tambaya dan nasan kaima kasan kudurina akan yayana Toh amma kai kanka nasha gaya maka matsalolin umma Baffa yace hakane Alhj to amma da fatan ba wanda bataso xaka bata ba dan tinda ga nan nake jiyo kukanta Ahj Alkasim yace E tabbas Baffa yanisa yace nikaina kullum saina yiwa Saddam fadan ya nemo matar aure Indai yara sunkai lokaci aiyin auren yafi alkyri Saidai kuma idan Allah bai kawo ba Amma Alhj maixai hana kayi hakuri kabata xabin nata Atake Alhj Alkasim yamike yace baffa ai wani baya auren matar wani Matar mutum kabarinsa fatan dai Allah yahada kowa da rabon alkyri Baffa yace Amin Toh Alhj Allah adawo lafiya Allah yakiyaye Umma haryanxu tana yashe agun sautin kukanta kwai ne ketashi Yan uwanta sunyi rarrashin har sungaji Jabriyya wanda tini tadau hanyar gidan boka qurzumus Bayanta ajiye kayanta agidan dan yayarta dasuke uba daya Saddam yashigo da sallama Baffa ya amsa ya kasuwa Alhamdllh inji Saddam Imm baffa kasan abin mamaki Yanxu inakan hanya umma takirani Baffa yace inajin ka Saddam yace yana ta kuka wai Alhj ya kori Mamansu kuma next Friday xai daura mata aure da wani ita kuma tace garani Baffa kaga shikkenan nahuta Neman wata Daman nadade nima inason ta kadan kadan amma dana tuna mamansu sai naji nastaneta Baffa yace nasan xa arina dan yanxu nan Alhj yafuta daga dakin nan Bayan danaji hayaniya da koke koke daga cikin gidan sai naga yafuto Afusace baffa yaga yawa Saddam duk yadda sukayi da Alhj Ya kara da cewa Saddam nikaina badan halin matar saba Dani zance masa ina Neman Auren yarsa To tabbas ninasan da abinda Alhj ya hango akanka tabbas akwai Saddam shawarata kacire umma aranka da rayuwarka Domin nayiwa Alhj shagube ne akan yabarta taxabi Wanda take so bance masa kaiba kaistaye Saboda nima baxanso ka hada jini da yayan Alhj Alkasim Saddam, umma ba xata taba xamowa mace ta alkyri a rayu warkaba sai dai tazamo maka matar kaddara Saboda umma idonta ya bude sosai tuntana karama Sannan uwa uba tarbiyyar mahayfi yarta yayi mutukar tasiri arayuwarsu Dan haka kayi hakuri da ita Koda kuwa bayan raina Dama dai ace ""...... .. Tohh fahh...... AMSAR 07033524044 [1/31, 8:42 AM] SARATU: _*🍂BIYU BABU…!🍂*_         _SAMU DA RASHI…_                🍂🍂🍂                  🍂🍂                      🍂       _*AɭKAɭAMƖŊ✍:Saɾatų mųŋχaɭɩ*_            _*(AMSAR💕)*_         _watpadd @ Ssaratu75…_ *ɖҽɖɩcatҽɖ tɷ:Aunty zaly yola mmn Ahmad*     *🅿_____4*   _*Sadaukarwar page din nan nakine FARIDA AUWAL Cike da fata da addu'a Allah ya tabbatar mk da Alkyri Allah yasa kicimma burukanki💕*_ 🌿🌾🌿🌿🌿🌿🌿🌾🌿🌾🌾 ____________📖Baffa yaci gaba da cewa Dama dai ace acikinsu akwai wacca ta gado halin Alhjne to da sauki amma duk da haka tasirin uwa yana iya canxa da a kowane lokaci Sani shi kadai ne ya iya xaman hakuri da jabriyya aduk sanda tayo yaji Itama jabriyya ananne kadai take sakewa dan tashiga tafuta yadda take so Tayi nisa matuqa wajan nemarwa yatta mafuta Ta kowane irin hali Taje gun wannan matsafi taje gun wancan boka Gaba dayansu sun Tabbatar mata da cewar Aure bazai tabbataba Hakan yasa tasakar musu makudan kudade dan cimma burinta Alhj Alkasim yariga yagama sanin halin matarsa Muddin suka samu sabani har takai tahada kayanta da niyyar yaji to tabbas akwai shirin kulla sharri aranta Hakan yasa tun aranar data tafi ya kudiri niyyar sai yaga bayan asirinta awannan karan Ta hanyar azkar da sallolin dare addu'oin kariya daga sharrin sihiri da shaidanu RANA BATA QARYA Saidai uwar ya taji kunya Ayaune babban masallacin juma'a dake zoo road wato masallacin murtala ramat Ya cika da iyayen yaya da waliyyansu Naa ibi yanabi daki daki har akaxo kan iyayen zubair dana Amar yarsa UMMA KALTUM Sautin da umma tajiyo na maroka shiya tabbatar mata da tafaru takare Aikuwa tasaki wani irin ihu Mecike daban tausayi Da gudu yan uwanta suka shigo Sister lfy Umma kiyi hakuri kidauka kaddarane auren ki da zubayr Afusace umma tace kaddara ta galla musu harara kume yasa bata fada kankuba Kawai danni baba yast Kafin takarasa wayarta tadau ruri Tana dubawa taga umman suce takira Araunane umma ta daga tace Hajja daman Abba baya sona Hmmm uwa uwace Harta manta marin da tasha😀 Jabriyya tace ai kisa ranki a inuwa aure dai Ahj bai isa yahadaki da mastiya ciba Mai stunstun sama yaci bare yabawa na kasa Umma tarushe da kuka tace wayyo Allah na amfa riga anfa daura auren gasu Baba nan sun dawo takuma rushewa da ihu tana tirje tirje Jabriyya batasan lokacin da danno wasu makudan ashar ba Niii HAJJA niii Alhj zai tozarta Tayi cilli da wayar ta Tamike tanata hucin tiririn takaici Habba hajja yaka mata kidauki duniya da sauki Ina amfanin rashin mika lamura ga Allah da yadda da qaddara mai kyau ko Mara kyau Dakata sani... " Wannan bai shafi shafin rayuwar kaba Ka wanixo da guntat takin wa azinka ko dan labcimma baka stomawa sani yace tab jahilci yafi hauka wuyar magani Sani yasan halin hajja tayi nisa Yana dai kara tinasar daitane kawai saboda hakkin musulunci Sani ya kasance shi kadai ne adanginsu hajja Wanda yake iya danne xuciyarsa yazauna da ita Duk da cewar dangar takarsa da ita tayi nisa amma sanin duk wadanda suka fishi kusanci daita bazasu iya koda kwana daya da ita lafiya ba hakan yasa yake hakuri daita aduk lokacin da tayo yaji Fuwww Hajja tafice tabar sani sororo astaye Bata nufi ko inaba sai gurin boka qurzumus Takwa zazzage masa buhun zagi dacin mutunci Kuma tace dole saiya nemo kudin ta yabata yanxu yanxu Boka yasan halinta staf zata iya toona masa asiri Takuma gayawa duk wadanda tayi masu hanyarsa sudaina xuwa Hakan yasa ya lalo kuda denta yabata Hajja ta fincike tayi gaba Boka qurzumus yaga samu yaga rashi Fadi yake almura bakar bahara😂 Hajja a kan titi taciro wa yarta tahar hada talatsa number yaya Hello Hannatu kina jina Lalle lalle kafin akai umma kitabbata kinsiyo allurar nan tastarin iyali kidirka mata Koda ukuce Hankalin hannatu yatashi Atsorace tace habba hajja wane irin allura planning har guda3takarasa maganar acikin shagwaba Hajja tace aixatafi aiki Dan kostau stayi baxan bari yagifta akan umma ta hyhu agidan stiyaba Kina jina ko Hanna tace Hajja inama laifin ayi mata ta2months Tinda batafa taba hyhu waba wllh akwai mastala Hajja ta daka mata stawa tace saidai kiga mastala akanki mai mugun fata Xakibi umarnina ko kuwa taka rasa maganar acikin bal bali Hanna saida tarazana tace to hajja batajira hajja takara magana ba takaste kiran jikinta duk yayi sanyi 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🌾🌾🌾🌾🌾 Kwana3 Ahj yaware na bikin umma Yan uwan hajja duk dasu akai komai tamkar basu san bata gidanba Sunyiwa umma nasiha sosai akan tabi mijinta kuma katta kuskura tayo irin halin mahyfiyarsu Ahj Alkasim shiyace xai kai umma gidan mijinta da kansa bayan kowa yaje yaga gida anata Addu'a r Alkyri 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🌾🌾🌾🌾🌾🌾🌾 Ahj Alkasim tindaga kofar futowar umma daga gida yake fado mata addu'a tana fada har suka isa mota Suna xuwa kofar gidan zubayr Ahj Alkasim yake tayiwa umma nasiha tamkar yaciri xuciyarsa yabata aro Saboda stabar son tayi aiki da nasiharda yake gaya mata Daga karshe yace umma a yau kuma a yanxu zan gaya miki babban dalilina dayasa nace baxan aura miki Saddam ba Ahj Alkasim yaja numfashi yanisa yace Saboda inhar na aura miki Saddam to tabbas bancika uba mai adalciba Domin kuwa ihar daya daga cikinku ta xama matar sa Tohh lalle xai kaita jahannama Da sauri umma ta dago taqurawa babanta ido Cikeda alamar tambaya tana jiran taji dalili Ahj Alkasim yace kwarai kuwa dan tabbas ba wacca acikin ku da xata iya yimasa biyayya ta kuma bishi Musam man Ke Wllh Saidai shii ya biki Saboda yanada sanyi hali Wanda akasari yafi kyau ga halin mace shi dabi arsa da halayarsa daban suke dasauran matasa kamarsa Nikaina inajin zafin rashin samun ya mai irin halin daxan bashi Ahj Alkasim mur yarsa tayi rauni yaci gaba da cewa Shiyasa duk mutuminda yayi sakaci wajan bin sunnar Annabi s a w to xaita tafka asara da dana sani arayuwarsa idan kuma yagane daga baya tofah Lokacin bakin alqalami yabushe Tabbas samarwa yaya uwa tagari musam man mai addini ba qaramar taka sa'a bane arayuwa domin tana mutuqar taka rawar gani wajan tarbiyyar yaya Umma kuyi hakuri nasan narusa rayuwarku bakuyi sa'ar uwaba Allah yagani nayi duk kokarin da xanyi akan nasami mace tagari amma Allah bai banba DESTINY Kenan ba wanda ya isa yacan xashi dan rubutaccen Al amarine daga Allah 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🌾🌾🌾🌾🌾 Ahj Alkasim yace shiyasa Nayi dagaske na jajirce wajan neman sanin waye zubayr domin inada tabbacin insha Allahu zai saita ki hanya madai dai ciya har kikai ga samun Aljannah takar kashin qafarsa Dan haka kikwantar da hankalinki kinji ummata Ya danyi murmushi yace au kema kiyi mana habba Amarya Koda yake saikin shiga gidanki kinga irin qoqarin da mahay finki yayi miki sannan nasan zakiyi dariya Umma ta dago kai araunane don magan ganun Abbanta sun stuma sassan jikinta Tace ngd Abba Ahj Alkasim yayi irin muryarta da take cikin kuka yace nima ngd umma Umma ba tasan sanda takifa kanta acinyar Abba ba tasa dariya Cikin farin ciki Ahj Alkasim ya dagota yace ko kefa daman dariyar nakeson gani Kinga umma barina fada miki halayen mijinki zubayr Kinaji umma Yanada ilimin arabi da boko mutane da yawa sun masa shaidar yana riqo da addini Sallah ajam i bata wuceshi ga mutunta al umma sannan uwa uba yanada jajir cewa E dan tsayayyene Umma ina mai tabbatar miki tinda zubayr ya kasan ce mai kula da ibar Allah to tabbas xaki same shi mai sauke duk kan hakko qinki akan sa dan yasan Allah ne ya dora masa Dan wllh duk Wanda kika samu yana sauke hakkin Allah Toh sauke haqqin mutane baxai taba yimasa wahala ba Saboda yana tare d Allah yazama naAllah Toh anan dai Ahj Alkasim ya shiga da umma yakuma damqa amanar yarsa ahannun sirkinsa Yayi musu Addu'a sosai sannan yayi sallama yamike Umma ta kama hannun Abbanta tace Dan Allah baba ina Neman alfarma Yace fadi ummata inajinki Umma tace baba dan girman Allah baba ka wuce gidan Uncle sani kadawo da hajja dann Kafin taka rasa fada Ahj Alkasim yace karki damu nayi miki Alqawari insha Allah A KWANA A TASHI Maisa ba fade zama sarki Bayan wasu shekaru Ahj SADDAM yaxama hamshaqin mai Arxiki Bayan Allah yayi wa baffansa rasuwa Wanda Ashe karar ne shima Ahj Alkasim Yarasu Hakan yayi sanadiyyar korar karen da hajja ta yiwa Saddam Itama Tasneem ranar sadakar bakwai din Ahj hajja ta dan qawa mahy fiyarta ita Mahyfin tasneem kanine agun Ahj Alkasim su biyu ne kacal agun mahyfi yarsu sai tarin wadanda suke uba daya Mahyfin tasneem yarasu tintana shekara 3 Hakan yasa Alhj Alkasim yayi yunqurin Auren mmn tasneem amma inaa Hajja ta shiga tafuta tace sam Babu macen data isa tai shearing mijinta Hajja bata barta hakaba har saida takuma yin asirin data korata jiharta wato kasar Ghana Wanda acan iyayenta suke Taxo bautar kasa anan kanin Ahj Alkasim yaganta iyeyensu sukaje har Ghana suka nemi aurenta Babu yadda basuyi ba akan Ahj Alkasim ya basu tasneem bayan sadakar arbain amma fafur yaqi ganin ita kadai zai dinga kallo yana tuna dan uwan sa Tole suka hakura duba da cewar dangin uba sunfi su qarfi 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🌾🌾🌾🌾🌾 Ahj Saddam yayi aure harda dansa wanda alokacin yashiga primary schll xaman su fly shida matar sa duk Kansu basu da haya niya so silently Hmmm daman ai sai hali yazo daya ake abota Hajja wacca ahalin yanxu ta fanstama neman inda Saddam yake tamkar wacca tasamu hau Hajja tun bata yarda da jita jitan da takeji na Saddam ya zama mai arxiqi Hardai taxo ta yadda Bayan ta tabbatar daga majiya mai tusheee Kasan cewar yanzu abin duniyar yaja baya sannan gaa donta dana yayan sam basuyi mata albarka ba Kasan cewar da zarar mastala ta kunno kai xata kwasa takaiwa boka yawar Ware mata Sai ana mata nasiha saita tubure Wai ita sam bata xuwa gun bokaye saidai malamai fafur taqi yadda wai ita Allah ma ya stare ta da zuwa gun boka Hmmm lalle jahilci yafi hauka😁 Baya ga irin stist stinewa yan uwan Ahj data dingayi a lokacin rabon gadon Saboda tana jin haushin sun shigo cikin rabo Ahaka dai akai baran baran Daman can saboda Ahj suke daga Mata kafa Dan shine komai nasu arayuwa Hajja ta kashewa umma aure Bayan nan takuma yin nasarar hallaka mijin Hanna Wanda laru rarsa tayi musu kaka gida Hajja ta gano muddin yana darai to tabbas xasu wayi gari a tutar holoqo Saboda kullum ana hanyar asibiti gobe wannan kasa jibi wancan gari Hakan yasa hajja ta hada kai da umma saida su kaga bayansa Wanda sai daga baya suke gayawa Hanna Aikuwa taja dogon tastaki tace kuntai makeni dan wllh sai yanzu nasan bashi da amfani Ni kenan kullum acikin dawai niya Hajja tai shewa tace yawwa yar gari Daman tin farko da kika ga na kafe saikin aure shi aina hango abinda baki saniba Bello bashi da kowa dan cirani ne yazo birni yatara uba uban Arziqi Sai larurar sace take lashe kudin Yanxu kuwa kinga sai muci karenmu babu babbaka suka fada atare suka sheqe da dariya Har uwar fa😏 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🌾🌾🌾🌾 Hajja tai nasarar rufe bakin duk wani makusancin mijin Hanna Dakarsu samu damar sanar da iyayen sa cewar ya rasu Balle axo raba gado abasu abinda ya sawwaqa BELLO yakasance tun yana yaro yake fama da laru rar sikla Wanda iyensa basu da karfi Hardai da suka gaji sai suka turo shi Alma jiranta jihar kano Bello yasha wuya ahaka harya girma har ya samu Sana'a yazama mai arziqi bello koda yayi kudi sam bai damu da iyayen Saba Dan yana tuna irin wulaqancin daya sha arayuwarsa A dalilin Alma jiranta da suka turo shi Bayan sunsan yanada larura Hakan yasa yayi busus dasu Bello ya hadu da Hanna A xaryar asibiti da yake yawan yi dan Neman magani A lokacin yakai kusan shekara 43ba aure Tinda Hanna ta bawa hajja labarin yana sonta Shi kenan hajja tace kurun kus mai abin yazo Hanna taso bijire wa hajja Dan ganin bello ba mijin moro bane amma inaaa Hajja ta gano gun morar Hajja tayo kulla kullenta Akasha biki Hanna tahyfi safna ba dadewa Allah yayi wa bello rasuwa Lokacin safna tana basic 1a schll Hanna Hannaatu umma kaltum umma Sautin kwala kiran hajja kenan da takewa yayanta Cikin razani da Al ajabi Tohh tabdi cewar umma bayan ta cabe baki Hanna tace ko lfy hajja take kwala mana irin wannan kiran haka Umma tace hmmm ai in kika bibiya gidan masu kudi ta gano Hanna tace Tashi dai muje kinsan zuzutun hajja Katta shigo taji muna gulmatta Hmmm uwa kenan mai siyan mutunci agun yayanta kuma mai barar dashi har su taka Atare suka yunkura suka futo falo Hajja fly suka fada atare Hajja acikin kambama murya tace yau yau nayi gamo Can kuma sai tasas sauta murya tace wllh wllh baxai yiwuba Can basai ta fashe da kukaba Da farko dariya su hanna suka fara yimata aboye Amma yanxu seriously sun kasa gane kan hajjantasu Toko madai hajja kantane ya kwance Ko kuma dai gidan masu kudin ta gano To dai Kubiyoni AMSAR💕💕 [1/31, 8:50 AM] SARATU: _*🍂BIYU BABU…!🍂*_         _SAMU DA RASHI…_                🍂🍂🍂                  🍂🍂                      🍂       _*AɭKAɭAMƖŊ✍:Saratu munzali*_            _*(AMSAR💕)*_         _watpadd @ Ssaratu75…_ *ɖҽɖɩcatҽɖ tɷ:AUNTY ZALY MMN AHMAD YOLA*     _*Na sadau karmiki da page din nan nakine sukutum AUNTY HAUWA S ZARIYA Mmn Uswan naji dadin tarba da kulawarki gareni jzkllu bi khayr💕*_ ________________________________ *AREWA WRITES ASSOCIATION* _________________________________ *💦{arewa gin shiƙin al'ummah}💦* _________________________________ https://www.facebook.com/104534761033461/posts/104535871033350/?substory_index=0&app=fbl *BISMILLH RAHMANI RAHIM* P_____5 ____📖 Cikin muryar kuka hajja taci gada da cewa"gaskiya duniya akwai butulci"yanzu kamar Saddam ace ya manta ko wa yayi silar arzikinsa ai baici ace ya manta da zuri'ar Ahj Alkasim ba". Haba hajja daman akan maganar wannan solobiyon kiketa kwala mana wanan kiran?,ta karasa maganar tana shirin barin gun. Umma tayi sauri ta riko rigarta tace" haba yaya da dina dake saurin ƙufula ki tsaya muji karashen zancen mana. Hajja tace" umma sakonan zai zo kigane inda nadosa gaba dayan ta tarikice tace" yau na tabbatar damu yan Rakiya ne" Umma tace" Rakiya fa ki kace?, RAKIYA R wa kuma". Kwarai umma mu yan Rakiya ne Gashi nan kiri kiri Saddam ya nunawa duniya cewar Munzama Ƴan Rakiyar masu Arziqi kenan munra kosu duniya ta kuma baye labba da kuka" Umma wanda itama takai bango ta dai daure tace" hajja ai wllh ko yanxu mun godewa Allah,dan munci arziqi babu wani abu damai kudi zainuna mana". Bata karasa faɗi ba taji wuff hajja ta buge bakinta to" ke dallah can har kinsan meye duniya? ai muddin kana darai toka nemeta kamar bazaka mutu ba". Yarinya bakisan kuɗi ba baki san kuma amfanin suba, su kansu masu kuɗin sunfi talaka masifar sansa da zafin Neman sa Shiyasa yawan su basa zakkah basa tausaya na assault. Hanna tamike tsaye tanata layi tace" hajja kemafa daba kuɗin ki ba idan baba yafitar da zakkarsa indai ya baki ki rarrabawa maqota ba kya basu Sai kice gida bai qoshiba. Afusace hajja tace" toh dan ubanki gidan ya qoshine ko kintaba ganin ya bani zakkah koku bai taba bawa ba. Umma wacca tinda aka bigewa baki

Chapter 2 of 15