Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 2
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels YARINYAR BABA [01:02 PM, 01-Oct-16] by ZAINAB ELKASEEM *YARINYAR* *BABA* _*Written & Edited*_ _*By Zee Mmn Khady*_ *```Just a short story```* *Page* 1-10 "Gaskiya ni Momy bazani school d'innan ba, kawai sai mutum yaje wannan banzan malamin yari'ka yimashi kallon banza, kamar wata tsiya yafika, Ilham tafad'a tana shagwa6a. Matar data kira da Momy tace "ke ilham banison shashancin banza da wofi, ki maza ki tashi kitafi tun kafin ranki yayi mugun 6aci cikin gidannan. Wasu 'kyawawan yara su biyu mace da namiji 'yan kimanin shekaru bakwai, suka fito sanye cikin uniform d'insu, gwanin ban sha'awa sukace "momy mun shirya, sannan suka maida dubansu ga ilham wacce keta zo6ara baki ita a dole bazata school ba, sukace "aunty ilham dan Allah ki shirya mutafi kinsan idan muka makara uncle zemana duka..... Cikin masifa ta kallesu ta daka masu uwar tsawa "bazaniba nace ku wuce Ku bani wuri idan ba so kuke in 6ata maku rai ba, dan uwarku ni sa'arkuce dazakuce sai kunjera dani kuntafi school..... Saukar wani lafiyyayen mari taji wanda momynta ta shimfid'a mata a kunci, wasu star's tagani suna zagaya mata kai saboda bala'in zafin marin saida ta fasa 'kara. Hakan yayi dai-dai da fitowar dadynsu daga d'akinsa, Ganinsa yasa ilham fad'uwa 'kasa kan kafet d'in dake shimfid'e tsakiyar falon tana kuka "wayyo Allah nashiga ukku dady ka taimakeni.... Da sauri yazo yakamata ya d'agota sannan ya rungumeta jikinsa yana tambayarta "lafiya ilham waye yata6a min ke,? Cikin muryar kuka da shagwa6a take magana "momy ce wai dole sai naje school nikuma nace bazaniba. Haba ilhama danme bazaki school ba ga 'kannenki sun shirya suna jiranki, 'Kara shagwa6ewa tayi tare da 'Kara narkewa jikin dad d'inta tace "ni bazaniba. Cike daso da 'kauna dady ke rarrashinta yace "shikenan tunda baki zuwa je d'akinki ki kwanta ki huta, kukuma Hassan da hussaina kuje driver ya kaiku. Yaran sukace "dady meyasa yau bazaka kaimu da kanka ba? Yace "saboda yayarku bazataba, dama saboda ita nake kaiku.... Yaran suka tafi suna turo baki, duk da suna yara basu son abinda dady yake masu, 'kiri-'kiri yake nuna yafison yayarsu akansu. Cikin takaici Momy ta kalli dady tace "wallahi karage tsananin son da kake nunama ilham, saboda duniyar nan batada tabbas, kaso naka duniya ta 'kishi, ka'ki naka duniya tasoshi,... Cike da jin haushin momy dady yafita yabar gidan, dan bayason jin maganar yarage nuna soyayya ga ilham, kullum fatanshi Allah 'kara ninka mashi son dayake mata a cikin zuciyarshi. Cike da takaici momy ta nufi d'akinta, a zuciyarta tana cewa *Hmm yau naci sa'a ba'a rufeni da fad'a ba* Dan some time duk randa tayima ilham fad'a itama ranar sai ranta ya 6aci... love u all Zee Elkaseem YARINYAR BABA [01:18 PM, 01-Oct-16] by ZAINAB ELKASEEM YARINYAR BABA Written & Edited By Zee Mmn Khady *```Just a short story```* *Page* 11-20 Ilham kuwa tana shiga d'akinta kan gado ta fad'a ta jawo wayarta 'kirar iPhone6 tashiga danne- danne, kusan kullum haka take batada wani ayki daga karatun novel's sai games a waya, kuma a haka dadynta ya d'aure mata gindi yahana Momy ta tsawata mata, acewarshi Momy tabarta ta huta tunda itama Momyn ba wanda yahanata ta huta, tunda gidansu cike yake damasu yimasu hidima kome yaimasu ake hatta da sharar d'akin dasuke kwana akwai meyi. Haka ilham tayita game a waya data gaji ta ajiye ta d'auko wani English novel tacigaba da karantawa, kusan awa biyu tana karatu, saida taji idanunta na zafi sannan ta tashi ta kashe fankar daketa faman juyawa tana ba d'akin iska, Ac ta kunna lokaci guda d'akin yad'au sanyi takoma tabi lafiyar gado, bacci me dad'i yayi awon gaba da ita. Kusan awa ukku tana bacci, ba sallah ba salati, wannnan shine baccin asara, sai bayan sallar la'asar sannan ta tashi mi'ka tayi tare dayin wata uwar hamma, sannan ta fita falo, zama tayi kan dining sannan ta 'kwalama Ameeno kira, "Ameenoo.... Da gudu tazo har tana tuntu6e kad'an yarage yafad'i tace gani, cike da isa da gadara ilham take magana, "maza ki kawomin abincina, da sauri Ameeno ta amsa da "to ,sannan tanufi kitchen jiki na 'kyarma, Ameeno itace yarinyar dakema ilham hidima, wacce da kad'an ilham d'in ta girmemata, dan yanzu lham bata wuce shekara sha tara ba yayinda Ameeno takeda shekaru sha shida zuwa sha bakwai,. Haka Ameeno takawo abincin tajera gaban ilham sannan tanufi pridge ta d'auko mata lemu da ruwa, saida ta tabbatar tagama had'ama ilham duk wani abu dazata bu'kata sannan takoma d'akinsu na 'yan aiki, saratu meyima su Hassan da hussaina hidima ta kalleta tace "hmm 'yar mulkin taki tatashi kenan, naga sai hidima kike tun d'azu, Ameeno tace kedai bari wallahi bacin Albashin da ake bani yanada tsoka da tuni nayi ritaya da aikin waccan 'yar izgilin. Inna jummai dake zaune tana jin duk firarsu wacce itakuma itace me aikin Momy, a gidan dady ne kawai beda me aiki dan momy tahana tace itace zatari'ka yimashi kome, hatta da girki indai name gidanne ita ke Shig kitchen tayi dakanta. Inna jummai tace "Hmm aini narasa halin wannan yarinya, wallahi Albasa batayi halin ruwaba, iyayenta mutanen kirki basuda wula'kanci, amma ita sai ahankali. Haka 'yan aikin suka ri'ka tattauna matsalolinsu, da kokawa akan yanda ilham ke wulakantasu, hatta inna jummai wacce a girme ta girmi uwarta amma bata ganinta da gashin arzi'ki... Love u all Zee Elkaseem YARINYAR BABA [01:26 PM, 01-Oct-16] by ZAINAB ELKASEEM YARINYAR BABA written & Edited By Zee Mmn Khady *```Just a short story```* *Page* 21-30 Ilham na kammala abinda take d'akinta tanufa toilet tafd'a kai tsaye ta she'ka uban wanka, tana fitowa taje gaban dressing mirror tafara d'and'asa kwalliya saida tagama sannnan tanufi wadrope d'inta wacce ke sha'ke da kaya ta tsaya tana tunanin wane zata Sanya, zuwa can ta hango wasu riga da wando English wear's shi ta d'auko haka ta sanya wando wanda yayi masifar d'ameta domin irin pencil d'innanne , sannan ta d'auko wata riga wacce zamu iya kiranta akwai ya babu, dan rigar purple colour ce tanada kwalliyar fari agabanta sai akayi ado da purple d'in duwastu aka rubuta *TOUCH ME* haka tasa rigar wacce ko hannuwan kirki batadasu gashinnan na kanta yasha gara ta d'aureshi ya zubu har kan kafad'unta. Ba 'karamin kyau ilham tayiba kamar wata baturiya, dan kusanma tafi turawan kyau dan ilham kya'kkyawace ajin farko, farace me madai- daicin tsayi, tanada shafe me kyau, ga dogon hanci manyan idanuwa sai d'an 'karamin baki. Bayan tagama shiri saida ta kalli kanta a madubi ko ita tasan tayi masifar kyau, sannan tajawo takalminta kalar purple me matsakaicin tudu ta Sanya, wani d'an yalolon gyale ta yafa a kanta wanda zamu iya kira akwai ya babu, dan kusan beda wani qmfani. Haka tafito daga d'akinta tana taku ahnkali kamar wacce ke tausayin 'kasa. Falo ta iske momynta, kallonta kawai tayi sannan tanufi 'Kofa tace Momy zanje Unguwa, Momy bata tanka mataba saida takai bakin 'kofa zata fita taji muryar momy tana magana cikin d'aga murya... "Ilham kada ki kuskura kibar gidannan, cak ta tsaya dan duk abinta tana shakkar momynta, shiyasa tafison idan zatayi abu yakasance dadynta nanan, dan idan yana kusa momy bata Isa ta taka mata burkiba. Muryar momyce ta dawo da ita Daga duniyar tunanin data Lula, "Wallahi bazaki fita a hakaba kamar d'iyar kafirai, wai ilham kinada hankali kuwa?..... Tsaye tayi bakin 'kofar batada niyyar motsawa, ringing d'in wayarta yasa ta motsa ta fiddo wayar Daga side bag d'inta, tana dubawa sunan 'kawarta tagani Leena, saboda haka da sauri ta danna OK dan tasan tare suka tsara tafiyar, sannan ta kara a kunnenta........ Love u all Zee Elkaseem YARINYAR BABA [01:49 PM, 01-Oct-16] by ZAINAB ELKASEEM *YARINYAR* *BABA* Written & Edited By Zee Mmn Khady Just a short story *Page* 31-40 hellow Leena kin isone, a d'ayan 6anagaren Leena tace "kefa nake jira ina a mota bakin get d'in gidanku kinsan su big boy basu san westing time, ilham tace "na dad'e da sanin haka gani nan fitowa yanzu, tafad'a tana niyyar ficewa daga falon. Jitayi an shaqota an d'auketa da wani lafiyayyen mari wanda saida taga wani duhu ya gifta mata, Momy ce ke cika tana batsewa tace "wallahi ilham bazaki fita a hakaba, kodai ki canja shiga kokuma ba inda zaki, ko ubanki daya d'aure maki gindi kina abinda kikaga dama nasan baze barki kifita a hakaba, kamar ba jinin musulmi ba. Ilham kuwa dafe kunci tayi tana zubar da wasu zafafan hawaye, da gudu tanufi d'akinta kan gado tafad'a tana sharar hawaye, hankalinta be 'kara tashiba saida taduba madubi taga sawun yatsun Momy guda biyar kwance a kumatunta. Gashi tariga ta 'kwallafa rai ga zuwa birthday d'in class mate d'insu akeyi kuma itace best friend d'insa tare ma zasu yanka cake, to idan batayi wannan shigar ba wace shiga momy keso tayi, sotake tasaka atamfa ko less idan taje a d'auketa bush girl, wasu zafafan hawaye suka 'kara zubowa a fuskarta tasa hannu ta goge. Wayarta tashiga 'kara alamar 'kira na shigowa, kobata dubaba tasan Leena ce dan tasan tana Bakin get tana jiran fitowarta su wuce. Bata ko kalli inda wayar takeba har tayi ringing ta tsinke, kira ya 'kara shigowa karo na biyu, sannan tasa hannu ta d'auka ta danna 'ok' sannan takara a kunne cikin muryar kuka take Sanar da Leena abinda Momy tayimata, wani irin haushin momy yakama Leena, shiyasama koda tazo bata shiga gidanba dan tasan data ganta da ahigar dake jikinta yanzu tafara yimata wata nasiha marar kai, wacce idan zata shekara tanayi bazatayi amfani da itaba. Leena tace "kiyi ha'kuri kitashi ki saka wasu kayan saiki sako wannan a jaka idan mukaje can saiki canja, Haka kuwa akayi wata jallabiya me adon duwatsu ilham ta saka sannan tayi rolling da gyalen jallabiyar wancan kayan kuma ta zubasu a site bag d'inta, sannan ta d'an gyara face d'inta tafito, bata ko kalli inda Momy takeba tasa kai tafice, cike da takaici Momy tace "Allah dai ya shirya. Dan duk abinda ilham keyi dadyntane yake bata go a head, yanzuma wannan abin datayima ilham d'in dayana gidan da sai rayuka sun 6aci, dan Momy tarasa wane irin so yakema ilham, momy ta girgiza kai tace addu'a kawai zan dage dan Al'amarin ilham da dadynta sai du'a'i...... Love u all Zee Elkaseem Yarinyar Baba [04:38 PM, 01-Oct-16] by ZAINAB ELKASEEM *YARINYAR* *BABA* _*Written & Edited*_ _*By Zee Mmn Khady*_ *```Just a short story```* *Page*41-50 suna Isa gidan da za'ayi birthday d'in sukayi parking motor d'insu sannan suka fito, shigar da Leena tayi bazaka ta6a cewa tanajin yaren Hausa ba. tun 'kofar gida sukejiyo sautin kid'a na tashi jikin ilham har tsuma yake dajin tashin kid'an, A cikin gidan kuwa duk wanda yakamata ya halacci birthday din ya halarta mutum biyu kawai ake jira ilham da leena, in ran Hakeem yayi dubu ya 6aci sai cika yake yana batsewa gashi sai kiran wayarta yakeyi taki d'agawa, Hakeem ya kalli big boy yace "gskiya ilham bata kyautamin ba, ace duk taron nan ita kawai ake jira...... Big boy yace "nima inata try no Leena ya'ki Shiga...... Kafin yarufe baki yaga shigowarsu da sauri yataso ranshi 6ace yace haba ilham tun d'azu ake jiranki amma sai yanzu kikazo, kuma ji.....ji dan Allah wata shiga da kikayi miye wannan? Yafad'a yana nuna kayan jikinta. Tace sorry my wlh Momy ce tayi west time d'inmu ka duba kaga face dina, yakai dubanshi ga fuskarta yaga sawun yatsu biyar kwance akumatunta take yaji tausayinta yakamashi yace sorry my dear, Yakama hannunta suka nufi wani d'aki a can ta canja kayan jikinta zuwa Wanda ta taho dasu a jaka, Hakeem yashiga rarrashinta har yasamu ta saki ranta, yayi murmushi yace yauwa my dear ga wannan ki saka a bakinki sweet ya mi'ka mata ba musu ta kar6a ta 6are ta jefa a bakinta, shima wani ya 6are yasa a baki. Ilham kuwa tunda tasha wannan sweet d'in da hakeem yabata sai taji duk wani 'kunci da damuwa da 6acin ran da Momy tasata duk sun gushe. Sun shiga gun birthday d'in mutane na zazzaune, suma sun samu guri zun zauna sannan aka fara gabatar da shagalin, ga kida sai tashi yake, ilham da Hakeem suka yanka cake mutanen gurin suka d'auki tafi, Hakeem ya yanko yasmata a baki, itama haka tayimashi, Bayan wannan aka shiga shagali anata ciye-ciye da lashe-lashe, bayan angama kowa yakama harkar gabanshi wasu sun shiga fagen rawa wasu kuma sun kama friend d'insu sunata fira, A da duk inda ilham taje magrib nayi idan hankalinta yayi dubu tashi yake, kuma kome take saita koma gida, amma yau sai taji duk wannan tsoron yafita daga zuciyarta, soyayya sosai sukasha a ranar itada Hakeem, Leena kuma itada big boy, kada kuyi mamaki idan nacemaku duka gurin birthday d'in ba wanda ya haurama shekara ishirin, dan duk class mate d'insu ilham d'inne. Haka sukayita bad'ala tsakanin mata da mazan gurin, sune basu tashi birthday d'inba sai karfe sha biyu da Minti ashirin da biyar na dare. Hankalin ilham yayi matu'kar tashi lokacin data lura da daren datayi bata koma gidaba, cikin rud'ewa tafara magana "dan Allah Hakeem ka maidani gida wallahi nasan yau sai Momy ta 6atamun rai, Hakeem yayi murmushi yace kada ki damu babyna nina gayamaki yau Momy bazata maki fad'aba, dama nasan bakida matsala da dady, itadai hankalinta tashe yake tace nidai mutafi, yace "to muje, ilham ta kalli Leena wacce ke kwance kan cinyar big boy, yanata latsata bako kunya, tace "Leena nizan wuce kedai nasan ba yanzuba, Leena ta d'ago da rikitattun idanunta wad'anda suka canja launi saboda tsabar jaraba tace "ni gaskiya ba yanzuba sai naga abinda yaturema buzu nad'i. Cikin minti sha biyar Hakeem ya sauke ilham 'kofar gida, kwankwasawa tayi megadi ya bud'e mata ta wuce, zaune ta taradda Momy da dady a falo da Alama dawowarta suke jira, Ganinsu zaune yasa gabanta yayi mummunar fad'uwa sai yanzu ta tuna da kayan jikinta Wanda Momy tahanata fita dasune...... Love u all Zee Elkaseem YARINYAR BABA [04:42 PM, 01-Oct-16] by ZAINAB ELKASEEM *YARINYAR* *BABA* _*Written & Edited*_ _*By Zee Mmn Khady*_ *```Just a short story```* *Page* 51-60 ilham tayi matu'kar mamaki yanda momynta ta tarbeta da fara'a ta taso tana cewa "ilham sai yanzu kika dawo kinsa munata jiranki dadynkima yakasa runtsawa saboda rashin ganinki, jiki na 'kyarma ilham tace "wallahi Momy abubuwane sukayi yawa a gun birthday kuma kinsan nice best friend d'in Hakeem dole kome dani za'ayishi yanzuma tahowa nayi badan angamaba kawai saboda ina tunanin kada kiyimin fad'a. Sai lokacin dady yasa baki yace "ba damuwa ilham _*YARINYAR BABA*_ sunanda yake kiranta dashikenan "jeki ki kwanta ki huta, cike da mamaki ilham tanufi d'akinta a zuciyarta tana cewa _{yau meya faru da Momy hartakemun magana me taushi haka, Wanda nasan duk lokacin danayi ba dai-daiba ba wanda ya Isa yahana tayimin fad'a idanma duka yakama ta dokeni}_ Momy kuwa binta tayi da kallo tanason yimata fad'a amma data kalleta sai taji wani Abu ya dakar mata zuciya bakinta yayi nauyi takasa furta mata wata kalma me zafi. Tana shiga d'akinta ta cire kayan jikinta ta d'aura wani d'an 'karamin towel tafad'a toilet ta ahe'ka wanka sannan tafito tashafe jikinta da wani lafiyayyen lotion me dad'in 'kamshi, sannan tasaka kayan bacci tabi lafiyar gado ba sallah ba salati, barantana tayi addu'a yayin kwanciya bacci. Kullum idan ilham zata kwanta sai momynta tashigo d'akinta ta tambayeta tayi sallah idan batayiba nan zata tasata gaba tayi sannan tasata tayi addu'oi ta kwanta, amma yau Momy tana tunkaro d'akin ilham sai taji kamar ana ri'ke mata 'kafa ana maida ita baya, sai taji bata son zuwa d'akin ilham d'in komawa tayi d'akinta ta kwanta wani irin bacci me nauyin gaske yayi awon gaba da ita. Ilham kuwa koda ta kwanta sai taji kanta yayimata wani irin nauyi, sai juyi take kan gado zuwa can sai taga d'akin na juyamata, lokaci guda wani irin haya'ki ya turnu'ke d'akin wanda idan da mutum ze shiga ciki baze iya ganin abinda ke gabanshiba, ganin haka yasa ilham rud'ewa wani matsanancin tsoro yashiga cikin zuciyarta duk illahirin jikinta 'kyarma yake, Kusan mintuna sha biyar d'akin na juyamata sannan kome ya lafa yakoma yanda yake jitayi anyi sama da ita, tafiya akacigaba dayi da ita cikin sararin samaniya batare dataga Wanda ke tafiya da itaba....... Love u all Zee Elkaseem [04:48 PM, 01-Oct-16] by ZAINAB ELKASEEM *YARINYAR* *BABA* _*Written & Edited*_ _*By Zee Mmn Khady*_ *```Just a short story```* *Page* 61-70 Wani 'katon fili aka jiyeta tskiyar wasu mutane wanda ganinsuma abin tsoro ne, su duka sanye suke da jajjayen kaya sunyi d'amara da wani ba'kin kyalle sannan sun d'aura wani a kawunansu, fuskokinsu anyi wani zane a goshinsu da farin Abu, sannan bakunansu ba'kikkirin kamar sun shafa ba'kin tukunya. Wata mace ce zaune kan wata katafariyar kujera wacce akayima kwalliya da zanen kwarangwal d'in kan mutum, matar tana ri'ke da wata farar yazga a hannunta, koda ganin matar basai ka tambayaba kasan itace shugabar wannan mutane. Ilham na durkushe tsakiyarsu takasa d'ago da fuskarta barantana ta kalli mutanen dake gurin, saida wannan matar ta taso tazo gaban ilham ta nunata da wata sanda take wani haske yafito daga jikin sandar yashiga jikin ilham, lokacin ilham taji duk wani tsoro ya kawar daga cikin zuciyarta ta d'ago da manyan idanuwanta tari'ka bin mutanen dake gurin da kallo, abinda yabata mamaki shine mutum na farko data fara tozali dashi shine Hakeem best friend d'inta sannan big boy sai kuma Leena sai sauran class mate d'insu sunkai su goma sai sauran mutanen dabata saniba. Wannan matar wacce itace shugaba ta kalli ilaham tace barka da shigowa wannan 'kungiya tajin dad'in rayuwa, my name is Abigael, nice shugabar wannan 'kunhiya tajin dad'in rayuwa yawanci duk wanda kikagani a nan suna cikin wannan 'kungiyar ne kuma sun shigetane dan sunason jin dad'in rayuwarsu batare da sun samu takurawa daga gurin iyayensu ko waniba. Nasan jiya zakiyi mamakin yanda Momy takasa aiwatar da kome a kanki lokacin dakikayo dare gurin birthday d'in Hakeem to wannan 'kad'an kenan daga cikin aikin wannan 'kungiya tajin dad'in rayuwa idan zaki lura cikin wannan 'kungiya duk yarane yan kimanin shekaru sha takwas sha bakwai zuwa ishirin, zakiga a zahiri suna aikata abinda sukaga dama ba tare da iyayensu sun takurasuba duk da wasu daga cikinsu basuda iyayen kuma hakan besa sun shiga cikin gararin rayuwaba, to daga yau kema kinzama member ta wannan 'kungiya. Sannan Abigael takoma kan kujerarta ta zauna bayan tagama ma ilham wannan bayani, ilham kuwa zuciyarta tagama dakewa da 'kungiyar lokacin tagama amicewa da zama yar 'kungiyar. Abigael ta d'aga sandar tsafinta sama take wani haske ya mamaye gurin duka yan 'kungiyar suka had'a baki sukace *AJI DA'DIN RAYUWA* Abigael ta kalli ilham tace gobe munason jinin momynki koya yake kiyi kokari yazuba 'kasa. Ba'a jira jin abinda zata fad'aba Abigael ta sallami taro Kowa Yakama gabansa. Love u all Zee Elkaseem YARINYAR BABA [04:52 PM, 01-Oct-16] by ZAINAB ELKASEEM *YARINYAR* *BABA* _*Written & Edited*_ _*By Zee Mmn Khady*_ *```Just a short story```* *Page* 71-80 Washe gari ilham ta tashi jikinta ba kwari ko kad'an, ba abinda take tunawa sai abinda yafaru da ita daren jiya, a zuciyaryta tace _(Ashe dama shiyasa su Hakeem da Leena da big boy basuda wata matsala a rayuwa kullum zaka gansu cikin farin ciki, basuda wata damuwa a rayuwa abinda sukeso shi sukeyi,)_ Ta numfasa tace _"to ay nima banida matsala kan kome tunda duk abunda nakeso dady yanayimin kuma bayason 6acin raina, matsalata dai Momy, kuma itama yanzu tazama labari tunda Abigael ta tabbatar min bazata 'kara yimin fad'aba zanyi duk abinda nakeso_. Cike da 'karfin gwiwa ta tashi tafad'a toilet tayi wanka sannan takira Ameeno ta kawomata break fast, bayan ta gama shirin tsaf cikin kayan makarantarta, sannan tayi kalaci tagama ta tsallake ta wuce, bayan fitarta Ameeno tazo ta d'auke kayan ta maida kitchen... d'akin su hassan da husaina ta wuce ta iske me aikinsu tagama shiryasu takamo hannunsu suka fito, falo suka iske Momy da daddy sun kammala nasu kalacin, dady cikin shigar manyan kaya yana shirin fita gurin aiki, ganin fitowar su ilham yasashi washe baki yana dariya yace "Ilham *_YARINYAR BABA_* yau zakije school d'in, cikin sanyin jiki tace "eh dady zanje, cikin fara'a yace to kuzo muje in saukeku, ilham tace "to amma dan Allah dady inaso kabani 10k zanba wata friend d'ina gudummuwa zatayi birthday, dady yace "ba damuwa kije d'akina ki bud'e loka ki d'auko 20thausand ay dubu goma me zasuyimaku a gun birthday, wani irin farin ciki yakamata tace 'thanks my dear dad, tanufi d'akin cikin rawar jiki a zuciyarta tanata godema dadynta da yanda yake biya mata duk wata bukata data kawomashi. Harta kai bakin 'kofar d'akin, Momy ta daka mata tsawa Ke Ilham dakata..... Jiki na 'kyarma ilham ta tsaya cak inda take bata ko 'kara taku d'ayaba. Momy tace kada ki kuskura ki d'auki kud'innan...... Love u all Zee Elkaseem YARINYAR BABA [04:59 PM, 01-Oct-16] by ZAINAB ELKASEEM *YARINYAR* *BABA* _*Written & Edited*_ _*By Zee Mmn Khady*_ *```Just a short story```* *Page* 81-90 Ke Ilham kada ki kuskura ki d'auki kudinnan..... Ke yanzu dan kina hauka zaki d'auki dubu ishirin ki kaima wata dan zatayi birthday dan bakisan ciwon kankiba, ke shikenan kullum aikinki kenan daga biki sai birthday fatty, haba ilham kiyima kanki fad'a mana, Sannan Momy ta juya gurin daddy tace "haba dadyn ilham bekamata ace ka d'auki kud'i kamar hakaba kaba ilhan takaima wata 'kawarta dan zatayi birthday fatty, ga mutane nan masu Neman taimako da yawa kaje ka basu mana Allah zebaka lada. Daddy ya fusata da maganar Momy yace "banison abinda kikemun kibarni inyima 'yata duk abinda takeso idan banyimataba waye zanyimawa, ilham itace farin cikina kuma itace nafara sawa a idanuna amatsayin 'yarda na haifa, saboda haka kada ki kuma yimin haka. Momy ta 6ata rai tace "to wallahi Alhj yau duk abinda ze faru saidai yafaru Amma wallahi ilham bata isa ta d'auko 20k takaima wata banzar 'kawaba wacce batada tarbiya, ni wallahi wannan makarantarma ko kad'an yanzu bani 'kaunarta. Dady ya kalli ilham yace "jeki d'auko ninace ki d'auka kuma kud'inane bana momynkiba, ilham ta matsa da niyyar shiga d'akin Momy ta daka mata tsawa "kada ki d'auko.... Dady yace jeki d'auko..... Ilham tawuce tasa kai d'akin Momy na kada tayi amma bata sauretaba ta kutsa kai cikin d'akin aiko a fusace Momy tabita d'akin ta ficikota ta falla mata wani lafiyayyen mari, tace wuce dan ubanki. Ilham ta dafe kunci tafasa 'Kara saboda tsananin zafin marin da momy tayimata, jin haka yasa dady shigowa d'akin yana tambayarta abinda yafaru. Su Hassan da Hussaina kuwa sungaji da jira saboda haka sukaje driver ya kaisu school, dan dama kullum shine ke kaisu idan kaji dady yace ze kaisu to tare da ilham za'ayi tafiyar to itakuma ba kullum take zuwa school d'inba. Ranar dai hatsaniya akayi sosai tsakanin Momy da daddy, Momy kuma ta dage akan baza'a d'auki kud'inba 'karshema kulle d'akin tayi ta tafi d'akinta da key d'in. Cikin 6acin rai daddy Yakama hannun ilham suka nufi mota, suna tafiya yana rarraahinta itakuma sai kuka take, har cikin ransa yakejin kukan nata, Bank suka biya yasaka ATM yaciro kud'i yabata 30thausand sannan ya wuce. Haka ilham tashiga school d'in ranta 6ace. A class ne bayan anyimasu break fast duk Kowa yafita amma ilham batada niyyar fita saboda har yanzu zuciyarta zafi take, tunda tashigo Hakeem ya kula da halin datake ciki saboda haka shima kasa fita yayi ya tsaya yana tambayar ilham dalilin 6acin ranta. Nan ta kwashe kome tagayamshi, cike da damuwa yace "ilham bakiyi abinda Abigael tace kiyiba da kinyi da Momy bata Isa ta 6atamaki raiba, ilham ta share hawayenta tace kada ka damu Hakeem yau Dana koma zan aiwatar da kome, Hakeem yayi murmushi yace yauwa babyna saikin daure bekamata ace babbar yarinya kamarki kullum kina cikin 6acin raiba...... Aranar dai haka Hakeem ya rinka 'karfafama ilham gwiwa tare dayimata kalamai masu dad'i harta saki ranta. Love u all Zee Elkaseem YARINYAR BABA [05:04 PM, 01-Oct-16] by ZAINAB ELKASEEM *YARINYAR* *BABA* _*Written & Edited*_ _*By Zee Mmn Khady*_ *```Just a short story```* *Page* 91-100 Da misalin 'karfe d'aya aka tashi su Hassan da hussaina driver yazo d'aukarsu ilham naganin haka ta tattara yanata-yanata tayima 'kawayenta sallama, duk da ba wannan lolacin bane na tashinsu tunda yanzu ilham tana ss 3 ne sai 'karfe biyu ake tashinsu, yan biyu kuma suna primary 2 ne ana tashinsu 'karfe d'aya, abinda yasa zata bisu shine tanaso tayi amfani da wannan damar taba 'kungiuarsu jinin momynta, dan bakin iya 6acin rai yau momy ta 6atamata, amma daga yau angama. Saboda haka 'yan biyu na isa gurin motar itama tana isowa, sun Shiga itama shiga kawai tayi ta zauna batare datacema kowa 'kala ba, husaina ce ta kalleta tace aunty ba'afa tashekuba kuma naga kin shigo mota,..... Ilham ta daka mata tsawa na shigo d'in dan ubanki kinfini sanin ba'a tashemuba d'in, ainasani yanzu nakeson tafiya. Hassan yace "mudai ki sauka kibari daddy yazo ya d'aukeki tunda dama kullum shine ke kawoki kuma yana d'aukok....... Kafin ya ida fad'a tasa hannu ta dokemar baki, cikin masifa tace tunda bansan da hakaba Kaine zaka

Chapter 1 of 2