kafa dokar ta hana zaman hira agun
Mudi "! Mudi!! Akwai tsoro da kaffa kaffa
Shiko gadanga kusar yaki ai harya mance da anyi hakanma tunda yasan bata isa yaji tsoronta ba shi baiga namijin ma daxai bashi tsoroba ballan tana mace
Aiko dai suna xaunen nn gab da magriba sai kwatsam gata ta futo Allah yabaiwa mudi sa,a ya ankare tuni yamike sadaf sadaf kafin ta karaso gun ya fece
Gadanga bai fahimci mudin guduwa yayib dan baiga nufowar khalisat dinba
tana zuwa gurin ta watsa masa abinda ke hannunta
zob'one me sanyin gaske Ackn d'an kofin glass
Saida yaja numfashinsa Sama yadire dakar jin saukar sanyin ruwan kamar na kankara afuskarsa
Dakayar ya bude idanuwansa ya kalleta yana sharce ruwan zob'on
Kafin ya magantu harta rigashi tana rike da k'ugu cike da tsiwa tace "Kai maloho bakauye ban hana xaman hirar nan ba wato kaine me taurin kai ko to walh duk abinda nayi mk kaika siya don baxan bari aringa gulmar mutanen gidan ina ganiba
Ya taso akufule xaikai mata duka
Taja baya tana nunashi "walh kasake yau jikinka yataba nawa saina maka sharri gun dadyna wanda bazaka taba fidda kankaba don xance masa naji kuna gulmarsa kuma xan fada masa kayimin fyade inkuma ba hakaba nayarda mudafa qur,ani
Lokaci daya jinin gadanga yatsaya da gudana yatsaya cak! Yabita da kallo lallai mace makirace
tace "ko xaka kwatanta kaga aiki da cikawa.
Yanunata da hannu yace "meye ajikinki da za.a yiwa fyaden abinda aka gama baiwa "yan waje mara mutumci kisani cewa ackn mata ke fanko ce mata kk rako duniya ko sadaka kuma aka bani irinki masu mutumci da sanin darajar mutum ma bazan karb'aba balle ke da bakida mutumci da kima aguna.
Duk da taji qunar furucinta aranta amma saita dake tace "oho dai ko me zakace dani baxan fasa yi maka sharrinba inhar kataba fatar jikina ayau.
Gadanga yakoma kan bencin yaxauna zuciyarsa na tausarsa yana kuma tuno kalaman innarsa
Baisake kulataba harta gama masa tsiwarta ta tafi
Yakoma dakinsa yasake kaya dama farar jallabiyace ajikin nasa duk zob'on ya b'ata ta
*******
Tunda khalisat tayiwa Gadanga boren xatayi masa sharri gun dadynta tasami lagonsa akusan kullum saita sami abinda zatai masa na ganin ta k'untata masa duk tsokanar da xatayi masa naganin yaji yaji haushinta bata fasaba yi take amma abinda ke bata mamaki bai tab'a d'aga kai yakalle taba ballantana taga fuskarsa ta canza duk habaicin da zatayi masa baya jin haushi
Batasan cewa tarata yake ba shiru kawai yayi mata ya qudiri aniyar saiyayi mata abinda bazata manta dashiba wanda saitayi dana sanin yi masa hakan
Wata yana karewa Alh yabiya ma,aikatansa
Dubu hamsin yabiya gadanga kamar yadda yatsara zai ringa bashi duk wata
Aifa gadanga na ganin uban kud'aden nn yafara shirin tafiya kauye harda tsaida ranar tafiya
Saidai kash dayajewa Alh da zancen tafiya nan Alh yakansile masa don yace ma.aikaci irinsa baya barin guri yabari da gaggawa har sai inyakama gurin ahannu yabari yakara sabo agun
Baiji dadin hakanba dan yasa rai sosai da ganin zainabu da innarsa akwanakin nan
To haka ya hkr ba yanda ya iya
Wani watan daya zagayo baisa rai da tfy ba kada Alh yahaashi ma yaji ba dadi ammafa xuciyarsa tagama cika da kewar masoyiyarsa da innarsa yasan suma suna can suna xuba idanunsu
Saida yai wata uku da fara aikin kana Alhajin da kansa yatsaida masa ranar tafiya yakuma bashi dubu hamsin na daban yace yayiwa inna siyayya banda salaryn daya bashi
Dubu dari biyu gadanga yahada cas ahannunsa yaringa jujjuyasu yana farin ciki
Ashe zai mallaki tarin kudade masu yawa lallai kaji shawarar manya ma aduniya yayi arayuwa daya biyewa zuciyarsa bai dauki maganar inna yazoba da baisamesuba
Lallai ashe inya kwantar da hankalinsa abirni zaiyi arxiki knn
Ai saiya hau tunanin wai gashi nan yana tuka mota mekyau zainabunsa na ciki a tsohon ciki sun dawo daga asibiti sunshiga tanfatsetsen gidansu
Firgigit yadawo hayyacinsa jin anshigo antabashi
Mudine yashigo dakin nasa yaxauna akusa dashi yana tsokanarsa "lallai mutumina wannan kudi haka nawaye kake rike dasu.?
Gadanga ya murmusa tare da turasu ckn jaka yace "wannan duk salary nane da kuma wanda Alh yabani nayiwa inna siyayya.
Mudi yazare idanu "badai tafiyar tazo a?
"Kwarai kuwa nan da kwana uku zantafi ma.
Mudi yakama baki "ah, lallai yakamata gobe lahadi muje kayo musu tsarabar tasu ko. ?
Gadanga yace "insha Allah kuwa dan har waya nakeso nasiya nakuma saiwa Zainabu na.
Mudi yayi dariya yace "ho! Ali gadanga na zainabu kanaji da zainabun nan fiye da kowa aduniya ai dole yaxamo nixan kaika kauyen nan dan inga zainabun Aliyu.
Dariya gadanga yayi yace "ai zainabu tayi ga kyau ga nutsuwa ga biyayya ga asali ga...
"Ka godewa Allah inhar ta hada duk abubuwan nan inka sameta aika gama komi basai ka kara mata kishiyaba
Gadanaga yace "to aini ko bata mallaki wadannan abubuwan ba banida burin inga naxauna da mata biyu.
Nan suka hau hira me tsayi sallah ce ta futo dasu dg dakin
Aranar lahadi kuwa mudi yakaishi store ya lodo wa inna da zainabu tsaraba tayi ta dubu dari harda tsaleliyar waya kirar TECHNO yasaiwa zainabu da layinta MTN da glo aCiki me two sim ce keypard
Aranar tafiya kuwa sassafe suka dau hanya shida mudi
Haj laila ma tabada sako kaiwa inna bakin kifi bushashshe dasu taliya da makaroni katan katan da wake da klin manya
Akarfe sha daya suka dira akauyen marina
Tun ahanya yake ganin yaransa amma baiwa kowa maganaba don suma basu zasi gadangan bane ackn mota don na waje baya ganin naciki saidai naciki yaga nawajen.
Suna dira akofar gidan inna yara suka baibaye motar sun zaci ko Alhajine yazo
Aiko ganin aliyu yasa suka bazama suna fada a ckn unguwa ga gadanga yadawo
Da labarin dawowar gadanga yaxowa zainabu murna taringayi kamar tayi tsintsuwa taje taganshi taringaji taso zuwa babarta tahana tace mata "kibari yahuta tukunna mana kokuma kiyi hkrn dare yayi mana ainasan dole zaixo gidan.
Hk ta hakura badan taso ba
Itako inna murna harda tsalle taga gadanganta tahau masa kirarin data saba masa
Mudi yaringa shigo musu da kayan
Suna zaune dukansu kan tabarma mudi nashan kunun tsamiyar da inna ta dama musu inna nabasu labarirrikan kauyen.
Mudi yacewa gadanga "nifa zantafi sai juma.a xan dawo ko?
Gadanga yace "a.a lahadi dai kwana biyar zanyi ai.
Nan sukai sallama yatafi
Har gidan iya kulu yashiga sukasha hira tana tsokanarsa "gadanga kaganka kuwa walh kacanxa kamar ba kaiba ka kara haske da kyau .
Yaringa dariya kawai
Yabata tsarabar daya kawo mata
Da yamma kofar gidansu yacika dam da yaransa sunyi 20 kaf dinsu sunzo ganin uban gidansu
Aiko kowa yasha tsaraba
Zainabunsa sai bayan magriba yadauki nata tsarabar yanufi gidansu....
*Autyn Sayyada da Shahida*💘
*ALI GADANGA...*
🏹🏹🏹🏹🏹🏹
*Short Story*
*Nabilancy Luv*💘
{Auntyn S&S}
*Dis page Dedicated to my sisters*
*Ummi Aisha* (Dan Asali)
&
*Batul mamman*(Gumin halak)
Page 1⃣4⃣
Baifi mintina goma da tsayuwa ba akofar gidan yaron daya aika kiranta ya fito yasanar masa cewar gatanan zuwa
Aiko dai yaron na barin gurin sai gata ta fito a d'okance
Fuskarta dauke da murmushi tanata xuba masa fara.a ahakikatan yaga tsagwaron murna da farin ciki a fuskarta
Lallai zainabunsa na sonsa gashi ta nuna azahiri itanma tayi kewarsa knn
Ta gaidashi tana fadin " mutan burni andawo knn?
Ya gyada mata kai yana kallonta yana xuba murmushi
Tace "amma dai ba saukar knn ba? (Saikace bataji lokacin dawowar saba oh!zainabu kknn ☺
Yace "tun daxun na dawo saida nasamu nutsiwa sannan na nufo masoyiyata da tarin tsarabarta
Ya mika mata ledoji manya guda biyu da tambarin Shop rite jiki
Ta karba da nishinta dakyar ta iya rikesu tana fadin " kai !kai !! Aliyuna wadannan kaya duk ni kad'ai ?
Yace "kedai jeki kaisu gida maza ki fito ki karbi abinda xaifi faranta miki rai ma.
Da sauri tayi ckn gida da kaya niki niki tana murna
Koda ta kai kayan ta fito tasha matukar mamaki dan Aliyunta ya shammaceta na ganin babbar kyauta dayayi mata na waya kirar techno da layin mtn aciki
Taringa tsalle tana k'ank'ame da kwalin wayar akirjinta tamkar za.a kwace mata ita
Gadanga yaita mata dariya yace "amma dai kya nutsu in nunnuna mk ita ko,
Ya karba yafito da wayar dg ckn kwalin tana ta walainiyar sabuntaka
Ya kunna wayar yaita nunnuna mata yadda xatayi control din komi ba wahala atsanake
Dake tanada fahimta kafin yatafi tarike wasu abubuwan ciki harda yanda zata daga waya dakuma kiran waya da danna handsfree dakuma kunna radio
Yace "kin fahimta ?
Ta gyada kai "sosai ma kuwa ashe inka koma burni zamu ringa jin juna ko?
Ya daga kansa "sosai kuwa harma kinga inna bugo saiki ringa kaiwa inna muyi mgn ko??
Ta gyada kanta tana dry wai yau itace da waya ahannunta
Kafin yatafi har cikin gidansu yashiga yagaida gwaggonta
Aiko dai gwaggwon tayita shi masa albarka na ganin abin arxiki da tayi
Dayake shima gadangan yahada waya ahannunsa toching ce ma mekyau kirar geonee
Ya iyata sosai tamkar educated in yana yin amfani da ita duk da dai M.M. Harunan da yake zuwa tana haska masa kwakwalwa da kaifafa masa basira don yafara jin turanci da iya rubutu aharshen hausa da english din
Ckn kwanaki da Ali gadanga yayi da zuwa kauyen nasu wata muguwar shakuwa takara shiga tsakaninsu shida Abun sa
Koda yaushe suna tare ko abokansa da yaransa baya zama dasu sosai
Duk da sun danje yawon farautar da yin gangin amma saiyaji abin ya fara sire masa duk yajishi afagen daga tamkar wani dan koyo
Hatta inna dama bason futarsa farauta takeba sakashi takeyi agaba suyita hirar burni yacikata da hirar hajiya laila da Alh.
*********
Ana Gobe zai tafi ne yataho shida yaransa guda biyu zasu je farauta da yamma
Wani yaro dan tsegumi a ckn tsukun kauyen yatari gadanga da sauri ya tsurkunta masa cewar wai ga Amadi can gun zainabu wanda suke takara tare suna xance da Abun...
Ran gadanga yai matuqar baci jin ckn yaran nasama wani yace dama yataba ganin Amadin yaje zance gun zainabun kuma tafito gunsa
Ran gadanga yagama baci inzuciya taciyoshi har huci yake yi ajere masu matumar dumi don nishi kawai yakeyi yana fudda hucin ta baka tamkar yakunna karan sigari haka farin hayaki ke futowa abakinsa gadanga knn infa ransa yabaci abin tsoro yake komawa
Azuciye suka rankaya kofar gidansu zainabu yayinda suka taradda Amadi atsaye yaharde hannayensa yajingina da
Bango
Aifa suna xuwa inda yake babu wani bayani suka haushi da duka da sandunan hannunsa
Gadanga ruwan cikinsa yahau yaita naushin fuskarsa
Kankace kwabo yaraunatashi fuska tayi sintin
Ihun Amadi ne yajanyo hankalin jama.a xuwa ckn lungunsu zainabu
Ita "yar tahalikar ma batasan yana kofar gidanba tazaci yariga da yatafi tun mintina goma dasuka wuce daya aiko taxo ita kuma taki futa ashe kaddara ce tatsaidashi
Murna tayi da hakanma tasan ayanxune zata sami salama na takura matan dayake na xuwa kofar gidansu
Tasha gaya masa bata sonsa gadanga ne mijin da zata aura saiyace mata bata isaba soyayya dolene ayita
To yau dai karshen tika tiki tik! Ankawo mata karshen abin
Tsoronta dayama kada dai kuma yakasheshi
Bata yarda ta leko wajenba tana dai jiyo hargowar mutane
Ita godiya ma tayiwa Allah da gadanga baixo gun yatararta agunba da tabbas da ita zai had'a
Sosai Amadi ya doku gunsu gadanga har saida aka yayyafa masa ruwa ashe suma yayi daya farfado aka sami wasu zaratan samari suka sakashi abaro suka turashi aka kaishi can dan kauyensu dake da makwabtaka danasu gadanga
Shima dayake yanada yara da "yan tawaga sun tsorata sosai ganin yanda akaiwa ubangidansu tamkar matacce haka suka kwasheshi said'an karamin asibitin garin
Saida yakwana biyu yasami kansa yafara gane mutane abincima abaki ake bashi me ruwa ruwa dan bakinsa akumbure yk andai canxa masa halitta
Kafatanin yaran sa dasuke futa harkar dabanci da fashi sun kufula sunkuma dauri damarar xuwa daukarwa ubangidansu fansa agun duk wanda yayi ms hakan koda za.ayi yakin daxai kifar da kauyen.
Shiko gadanga hankalinsa kwance yama mance da zancen yayi duka balle yazauna yatari abin don shirin komawa burni yahauyi ma
Inna sam batada labarin dukan da gadanga yaiwa amadi
Ana gobe zai tafi ya dade da zainabu a kofar gidansu suna tadin soyayya
Yana dad'a jaddada mata irin son da yk mata kuma yana kara jan kunnenta akan tarike ms amana
Zainabu harda kukanta wai bataso yatafi
Yaita kwantar mata da hankali tunda ga waya kamar suna tarene kullum ai zasuyi waya
Da sassafe kuwa saiga mudi dreba yaxo daukarsa
Gadanga yace baxasu bar kauyen da wuriba sai sunyi axahar
Haka kuwa akayi bayan sunyi sallar axahar suka dauki hanyar komawa birni amma saida yasada mudi ga zainabu suka gaisa
Mudi ya jinjina kyan Abu tabbas yaga kyawu tsagoransa wanda ya hasko da ace abirni take rayuwa da anyi kallo tunda ta ninka khalisat biyar a kyawu☺
Ya cika inna da kudi wanda zai isheta amfani kafin yadawo wata uku
Tayita shi masa albarka dan taga canji tattare dashi takuma fara jiyo kamshin alkairin dazai samu anan gaba addu.a dai bazata daina yi masaba nasamun ci gabansa.
Zainabu ma yashaka mata kudi wanda taita juyasu ahannu dubu goma ne amma tagansu kamar dubu dari lallai gadanganta yaxama me kudi😄 akauye waxai baka dubu biyar ma tab to goman ma sadakin wata ne
Aiko dai tun ahanya suketa waya da zainabu har suka shiga kano shiya ringa kiranta suna shan hira
Saida yashiga ckn gida kana suka rabu awaya
Gadanga kenan Allah sarki da kasan me zai faru akauyenku da baka taho ba😭
Wayyo......
_Muje zuwa_
*fans ina godiya da nuna kulawarku akan gadanga kuyi hakuri najinsa shiru munyi biki ne amma yanzu mungama zaku ringa ganin post kullum*
*Auntyn Sayyada da Shahida ce*👌🏼
*ALI GADANGA...*
🏹🏹🏹🏹🏹🏹
*Short Story*
_ina kuke dimbin masoyan_ *ALI GADANGA*_ina matukar yinku ina kuma jin dadin yanda kuke nuna doki akan ganin ganin posting dinsa dajin dadin yanda labarin ke tafiya_
_masu yawan tambayar Novels dina to ga sunansu saisu nema a grps nasan zasu samu_
*"yar makafi*
*"yar mace*
*Tauraruwa me wutsiya*
*Tagwaye*
*zaman marina*
*Ranar wanka*
*Gajimare*
*idan kunne yaji*
*Ali gadanga*...
_Jinjina gareku masu loving din novel din Ali gadanga musamman_*Snaanerh*Ummu Aleesha grp*
*maman gausiya MUSHA KARATU NA YBK* grp
*Nancy MMN USSEEY GRP*
*Nabilancy Luv*💘
(Auntyn S&S)
*Dis Page Dedicated to my Sisters*
*Batul mamman*(Gumin Halak)
&
*Ummi Aisha*(Dan Asali)
*TASHIN HANKALI WANDA BA,A SA MASA RANA....*
page 1⃣5⃣
Tabbas gaskiyar '"yan magana da suke cewa RANA DUBU TA BARAWO...rana d'aya jal kuma ta me kaya
Domin kuwa yau khalisat idonta ya raina fata don dawowarta knn daga asibitin kudi wanda bata yarda taje asibitin da suke da file ba dan kada agano abinda take xargi iyayenta suji
Hankalinta ya matuqar tashi najin wai tana da shigar ciki na wata d'aya
Tayita zarya adakinta hannunta aka kirjinta na bugawa
Yanxu da wane idon zata kalli mahaifanta?
Abinda ma yafi daga mata hankali shine na yanda ta kikkira wayar SAFRAZ amma tajita akashe
Ta zauna bakin gado ta zabga uban tagumi
Da sauri ta dau wayar takira nambar kawarta aminiya wato khairat
Khairat na dagawa khalisat tafashe mata da kuka
Nan da nan hankalin khairat ya tashi tahau tambayarta meke faruwa ?
"kawata nashiga uku kinji wai ashe cikine dani...wani uban tsaki khairat taja tace " to saime dan kina da ciki shine xaki damu harda wani yin kuka haba kawata saikace wata yarinya karama me kk tsoro?
Khalisat taja ajiyar xcy tace "ke! Dady na da momy mana walh zasuyi fada nasani duk da sunaji dani amma kinsan zasu iya juyamin baya suji sun tsaneni kuma zasuce nabasu kunya
Khairat tace "aikin banxa ke yanxu saiki bari suji ma? To bari kiji maxa kishirya kifito da sassafe muje mu xubdashi tunda baiyi kwari ba nifa wancen satin na zubda na uku gaya mk ne banyiba kuma duk Auwal ne yayi min amma yace zai aureni akwaima wanda yaki xubuwa akasar nan saida nafita waje kana aka samu yazubu amma naci wahala momy nace ma ta rakani
Kima cire tsoro aranki walh ai indai iyaye nasonka to baxasuso suganka ackn damuwa su kara maka damuwar ba kin gayawa SAFRAZ din?
Khalisat tace "nakikkira wayarsa akashe amma na tab'a yi masa hasashen hakan saiya nuna min rashin damuwarsa
Khairat tace "tura masa sako kisanar masa yayinda duk yakunna wayar zai gani.
Da shawarar kawartata tayi amfani
Ta tura masa bayanin da likita yasanar mata n tanada shigar ciki na wata guda
Takuma sanar masa agobe xata xubarshi yakamata yaxo agoben.
Shiru shiru bataji kiransaba bakuma taga sakon saba sai dare bayan magriba ta gwada kiransa saitaji ta shiga amma har 2 missed call bai daga ba
To me SAFRAZ yake nufi ta tabbata yaga sakonta Allah yasa dai lfy
Yinin ranar ko sallolin azahar da la,asar bata samu damar yiba saboda damuwar da take ciki ko magribar ma batasan anyiba duk da akwai masallaci ajikin gidan nasu wanda awani lokacin ma tana jiyo muryar gadanga yana kwada kiran sallah amma dayake tasan yayi tafiya bata tsaya sauraraba ayau
Shiko gadanga alokacin daya dawo ma gajiya ce ajikinsa bai shiga masallaci yai kiran sallaba saida aka shiga yayo alwala yatafi agaggauce don bada farali na sallar magribar
Tana zaune ta xuba uban tagumi taji kara alamar shigowar sako wayarta
Tayi sauri ta daua ta bude ashe kuwa SAFRAZ dinne yaturo mata reply
_Khalisat ina mai baki hkr najin ban d'aga kiran kiba ina cikin wani hali walh dadyna yamatsamin saina bar k'asar nan agobe gobe kuma ya d'aura min Aure da "yar k'aninsa ajiya da ita ma zamu tafi egipt kiyafeni ina sonki..._
tashin hankali wanda ba.a sa masa rana yau khalisat tashigeshi domin kuwa hannu tasaka aka tarafka uban ihu
Aifa jin shigowar wani sakon yasa tayi shiru da sauri ta rarimi wayar ta bude again SAFRAZ dinne
_ciki kuma inkinga zaki zubar to ki zubar din kawai inkuma kinga zaki barshi to kya sanar dani dan insan jinina na duniya dan ina sonshi ki huta lfy sai wataran_
wani uban ashar ta kurma tareda cilli da wayar gefe ta dafe kanta tana kuka da idonta wanda ta mance rabon taxubda hawaye tabbas tashiga rudani ya zatayi da son da take masa?
Tadauki wayar asukwane donta kira khairat tasanar mata amma sai wayar taki kunnuwa
Aguje ta futo daga dakin nata nufinta ta tafi gidansu khairat din donsu samu mafita ayau
Adaidai lokacin da tafito daga sashin nata afirgice shikuma gadanga yadawo daga masallaci
Takusa bangajeshi sauran kiris su gogi juna ya matsa da sauri yabata hanya
Saidai yalura atashin hankali take don kuka ma kawai take tana fadin tashiga uku
Yaja yatsaya yaga tashiga mota ta tasheta ta matsa hon da karfinta ta fizgi motar tafice agidan
Sauran k'iris tabuge baba me gadi aget wajen bude mata get d'in banda yai tsalle gefe guda
gadanga yalura da ita da alama akwai babbar matsala jikinsa yabashi ba qalau ba kawai saiyaji gara yabita yaga ko lfy
Shima motar yashiga wacce akafi kaishi aiki da ita
Yabi bayanta
Yana hangota agabansa duk da tana sharara gudu
Shima gudun ya tsinci kansa dayi
Sunyi nisa akan titin saiya hango wasu motoci guda biyu masu glass da tintek sun shige gabansa aguje suna masa fitila
Sun takewa khalisat baya har yadaina ganota ma
Abin ya daure masa kai tosukuma wadannan suwaye haka dasuka fishi sauri da alama suma suna ckn tashin hankalin
Ganin sun dauke hanya kuma sunbi hanyar da khalisat din tabi yasa shima yarufa musu baya amma sun dan rage gudun
Abin mamaki babu yawaitar abin hawa da mutane a arear din da suka biyo sun sauka atiti
Can yahango sun saka motar khalisat atsakiya sun rikitata da horn
Motar gabanta ta tsaya itama dole taja tatsaya ta waiga taga motar bayanta itama ta tsaya anma jikinta yabata wani abun dan motar bayanta iri dayace data gabanta
Sai gani tayi maxa biyu sunfito amotar gabanta da bakaken kaya harda bindigu ahannunsu
Hantar cknta ta kada take tsoro yashigeta tahau kiran sunan Allah aranta
Suka nuno mata bakin bindiga suna fadin ta bude maxa ta fito
Asanyaye tafito suka tisata agaba tashiga motarsu
Gadanga yayi saurin tada motarsa yabisu dasauri ganin abinda ke faruwa daga nesan daya tsaya kada dai "yan fashine ko masu garkuwa
Aikafin ya isa harsun tashi motarsu sunyi gaba aguje bai cin musuba tunda sun gwanance a iya tuki
k'iri-k'iri yanaji yana gani suka take masa suka b'ace baya hangosu yatsaya da motar tasa ya buga kansa ajikin sitiyarin motar tashin hankali yanxu yazaiyi ?su waye wadannan da suka dauke khalisat? Yaxaice da Alhaji knn?
Duk baida amsoshin tambayar mafita guda kawai yakoma gida baibi takan motar da khalisat tafito ack ba tunda hannu daya baya daukar jinga taura biyu bata taunuwa dole saidai indawowa xaiyi daga baya yadauketa gashi baida nambar ilu awayarsa yakira mudi kuma bai dagaba ballantana yace masa yabiyo bayansa a abin hawa
Yana xuwa gida ya faka motar a farking space yashiga ckn gidan afurgice Anyi sa.a dadyn yadawo suna falon shida momy
Sun furgita suma ganin gadangan yashigo afurgice ckn damuwa yazayyane musu abinda yafaru
Kuka momy tahauyi tana fadin "nashiga uku sun d'auke min "ya d'aya tilo Allah katallafa mana ka karemin "yata ya ubangiji
Dady kuwa innalillahi kawai yake cewa yakira kwamisanan yan sanda yasanar masa yace maza abaxa jami,an tsaro ahanyoyi yabada kwatancen kalar motocin da nambar motocin kamar yadda gadanga yasanar masa
Gadanga ckn sanyin rai yace "momy ba kuka zakiyiba alwala zakije kiyo kisallah ki gayawa ubangiji
Dady yace "maxa Aliyu muje masallaci inmunyi sallar ishsha,i inbada sadaka akwana ana tayani addu,a
Suka rankaya masallaci atare kaf mutan gidan aranar kowa yaji abinda yafaru har yan unguwa anshiga tashin hankali
Haka aka kwana darura na sace khalisat da akayi
Yanda gadanga yaga rana haka yaga dare don bai runtsaba gizo abin yaringa masa take yaringajin tausayin iyayen khalisat din hatta ita kanta khalisat din tausayin tane yamanne masa aransa ko wane hali take ciki?
Tun dayayi sallar asuba baifito dg masallacin ba yanata lazimi yana addu,o,i gabansa yanata faduwa yanaji ajikinsa akwai wani abun tabbas da zai faru dashi yaita hailala yana salatin annabi
Wajen karfe goman safe yakoma ckn gida jikinsa asanyaye ganin polisawa sunzo gun Alh sun kawo masa bayani kan cewa bawani bayani naganin yan ta,addan
Amma sunxo da bayani kan cewa kwamishina yabada umarni akan cewa sutaho da gadanga don ya masa tambayoyi domin suna xarginsa ko da sa hannunsa aciki
Gaban Ali gadanga yafadi tabdijan ya Allahu.
Alh bai amince ba yace musu ya yadda da Aliyu baxaici amanarsa ba yace musu sukoma suce da kwamishina yature wannan maganar gadanga dan,uwan sane kada akara dora zargi akansa
Koda suka tafi Alh ne yadafa kafadar gadanga dayake xubda hawaye yace "kada kadamu Aliyu babu wanda zaiyadda da zarginsu na yadda dakai Allah zaibayyana su da karfin addu.a zata dawo itama.
"Allah yasa '" gadanga yace
Koda yakoma dakinsa ma kasa nutsuwa yayi wato shiyasa yaji gabansa keta bugawa abinda zaisameshi knn naqalen sharrin yan sanda lallai Alh na qaunarsa tunda har ya yarda dashi yakamata yayi wani abu akai yataimaka masa don "yarsa ta dawo to wace hanyar?
Wayarsa ta katse masa zuxxurfan tunanin daya shiga kafin yadauka harta katse
Yana duba wayar yaga ashe Zainabun sace har 15 missed call
To ko lfy zainabu da kira haka
Kai tsaye yana kira daya yaji ta d'aga tana kuka tana fad'in " wayyo Allah gadanga munshiga uku kaxo sun kashe mana inna....
Ya mike tsaye da sauri afusace yace da karfi "wacce innar suka kashe?
Tace '"inna kulu mana innarka gadanga....
"Suwaye suka kashe min inna? Mesukai mata ?me tayi musu?
Zainabu ckn kuka tace "yaran Amadi ne wai sukazo d'aukar fansa wayyo gadanga inna ta mutu tabarmu......
_muje zuwa_
*Auntyn Sayyada da Shahidah ce*👌🏼*ALI GADANGA...*
🏹🏹🏹🏹🏹🏹
*Short Story*
*Nabilancy Luv*💘
(Auntyn S&S)
*Dis page Dedicated to my Sisters*
*Batul Mamman*(Gumin halak)
&
*Ummi Aisha*(Dan Asali)
😭😭 *Dolene inkoka da rashinki Aminiyar Arziki Wasila maman* *ummulkhairy mace me halin kwarai da iya zama da miji da iya mu,amula da jama,a mace me tsafta da gyara da* *kwalliya yar gayun da banga ya itaba me iya tattalin miji uwar gidan da banga kamar taba* *wajen boye kishinta mace mebin miji da biyayya ga dangin miji Allah yajikanki yasa kin huta yabayyana wanda yai miki kisan wulakanci*
*Allah ya raya abinda kika bari ke taki tayi kyau wanda yai mk hakan kuwa yasani Alhaki biyu ke kansa harda dan dake cikinki kuma Allah baxai barshiba tun aduniya xai ane kuransa ga duniyar nan sai yazauna gadinta*
_Dole muiy kuka ai ancucemu dai_ _Fans ina godiya da yimin ta,aziyya da kuma addu,arku ga kawata masu yo waya da turo sako nagode Allah yabarmu tare duk naga sakonku_
Page 1⃣6⃣
Wayyo Abu goma da Ashirin gadanga yashiga tashin hankali
Domin baisan yafadi bama ashe suma yayi
Adaidai lokacin daya fad'ine mudi yashigo d'akin da sauri don yakawo masa labarin wad'anda sukai kidnapping din khalisat sunyo waya suna bukatar mak'udan kud'ad'e.
Sai farkawa yayi yaganshi