Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dani dan manzo kai hajiya wlh kin fiya tsoro to dama maganar da kk takalo ce ta Aljanu kin ganni nan to inada su sunkai miliyan daya a kaina innalillahi wa'innailaihir raji'un miliyan daya fa kika ce ?to ni dai ko a mazahabar jama'u ban taba jin kan mutum ya dau Aljani fiye da dari ba daya ba shima cikon na darin danna mutuwa ne shiyasa amma ke kice har miliyan daya sai dai in kece aljanar da kanta to Alhmdllh tunda kin fahimta shikenan na fahimci me ?ba dai da gaske ke din aljanar bace? eh ah'ah rabi mutum rabi aljan nake 😳ke 'yar nan fadamin gaskiya in san abinyi tun wuri ai gaskiyar kenan abinda yasa ma kikaga na tsaya haka sbd naga yadda kika karbeni ni shiyasa ni bana cutarwa da kike ganina ina rayuwata ne cikin bil'adama amma ina azabtar da duk wanda yake kuntatawa jama'a su kuwa masu shiga tsakanin masoya ko ma'aurata kashe su nakeyi gaba daya masu gani ba kyalewa kuwa kamar masu tanka halittata su kam bakin nake murgudewa in tsiyayar da idanunsu ta yadda bazasu moru ba sannan in......... wayooo na shiga uku hajiya ta fada da karfi yusuf da Amina da tun dazu suka zo da niyyar susha hira da dije suna dab da shiga suka tsinkayi hirar hajiya da dije akan sabulu suka tsaya suji yadda zata kaya ai tunda sukaji dije tacewa hajiya ita aljana mutum.ce yusuf ya tuna da yadda naseer ya basu labari dije tayi musu aikuwa nan ya kama dariya Amina ta kalleshi kasa kasa take tambayarsa janta falo yayi ya fara bata labari kafin yace nasan ta fuskanci halin da muke ciki shiyasa ta bullo mata ta wannan hanyar marairaice fuska Amina tayi kamar zatayi kuka tace haba Abban Anwar baka tunanin hakan ya cutar da ita kaga fa tsohuwa ce in jininta ya hau fa? hakanma bazai faru ba nidai kawai fatana Allah yasa wannan yarinyar ta zama silar shiryuwar hajiya ta barmu mu zauna lfy kinga ni tashi mu zaga ta bayan window musha kallo kinji my choice jiki ba kwari ta mike ya kalleta yace haba mana ki saki jikinki pls kin san dai hajiya mahaifiyata ce bazan so abinda zai cutar da ita ba ko nasan halin yarinyar a sai dai ta firgitata kamar yadda ta firgita wadancan kartin tunawa tayi da labarin daya bata aikuwa ta kama dariya suna tsaka da haka suka jiyo ihun hajiya da gudu suka fita suka zaga ta window suka danyi slide dinsa kadan suka kama kallo ni fa ki daina min ihu me nayi miki ? kinga dan Allah yake muminar aljana kiyi haquri daga ganinki hwlh anga me afuwa wlh ban aikata ba duk abinda kika ga inayi ciwon sanyi ne yake tabani badan ma kar ince ki tambayi yusuf ba nasan bai sani ba da nace ki tambayeshi to tun ina budurwa na hadu da matsalar sanyin kwakwalwa inya bugani sai inta abu irin na marasa hankali ni dama tunda na ganki nasanke ba mutum bace amma da naga kuna yanayi da su habibu saina yadda ashe ke mutum aljan ce nasan suma basu sani ba amma ina rokonki da kada ki kasheni inada marayu kinga ni ke kula dasu gashi...... to wai laifin me kikayine da zan kashe ki? nasan nayi kuma kema nasan kin sani kawai kina son kiyimin kisan rashin imani ne bayan kin murgudemin baki kin tsiyayarmin da idanu ki tausayamin ki duba tsufacda furfurata ki duba qananun yarana au har yanzu kina haihuwa dama? ah ah yusufa da farida mana in an hada da irin shekarunki ai kinga su jarirai ne ko? hakane ina zuwa kaya ta ciro tasa dan sanyi takeji kafin ta dawo ta zauna akan bedside drower ta dora data kan daya kafin tace hajiya cike da rawar baki ta amsa ya zuwa yanzu tayi zaman dirshan bisa tiles na'am ranki ya dade me haskrn sallah dan naga ke din musulma ce ko a cikin aljanun kinada imani bakya wasa da ibada duk naji yanzu dai ki fadamin dalilinki na hana yaranki sakewa da iyalansa kika zo kika takura musu kika...... kinga duk basai kin fada ba nasan kin sansu wlh sharrin ciwon sanhi ne kamar yadda na fada miki amma ina nan ina neman magani oh kenan shi kesa kike aikata abinda kikeyi ? sosaima kuwa ni tsorona ma kada yasa in aikata kisan kai gara in nemi magani tunda wuri ai indai magani ne kin gama samu dan ni har maganin dayafi nashi ma ina bayarwa cikin hajiya ne yace quuuuuuu cikin sauri ta yamutsa fuska tace ah ah bama sai kin bayar ba dayake na karbi wani ina kan aiki dashi yau ma wa'adin zai cika nasan gobe na warke to shikenan naji amma yanzu dole ki karbi hukuncinki na yin katsalan dan da tanka halittar Allah da kuma shiga shirgin daba naki ba haba yallabiya kiyi haquri sharrin shaidan ne da kuma.... ganin da dije tayi duk hajiya ta hada zufa duk da sanyin A.C dake dakin ga kuma fanka saita bata tausayi dan haka ta rage abinda tayi niyyar yimata sbd gudun kada taje jinin tsohuwa ya hau ta shiga uku garin gyara ayi barna shikenannaji tunda kin bada haquri kuma kin smu maganin cutar dake damunki ba matsala zan kyaleki amma daga yau kullum da dare zan dinga kwana gidan nan sannan da rana zan ding zuwa zagaye batare da kowa yasani ba inga halin da ake ciki idan naga baki warke ba sai in dora da nawa maganin wlh nama sn zan warke sannan kada ki sake inji in fadawa kowa ni ba cikakkiyar mutum bace dan ba wanda yasani wace ni ai ni banida wannan subutar bakin nifa banda yanzu magana ma bata dameni ba ta fada tana me marairaice fuska sai da dije ta dan yi murmushi ganin yadda ta danyin ita ko hajiya da qarfinta ta yunkura tace Allah ya baku haquri ni zan tafi dan wlh bacci nakeji kije ina ai ke tare zamu kwana dake da waya kawoki? wlh dama zuwa nayi in shiga bandaki tsautsayi ya ritsa dani oh dama anan kike shiga toilet din dakinki babu ne ko me? kaddara wlh kaddarar haduwa da ke tkawoni ko kafin dije ta bata amsa har takai bakin kofa dije na shirin yin magana taga tsohuwa ta bude kofa ta sheqa da gudu ba ko waiwaye aikuwa nan ta fada saman gado ta dinga dariya su yusuf ma dariyar suka shiga yi suka zagayo koda suka shigo dakin dije nata dariya saida yusuf yace sannu da gama rikitamin uwa bata daina driyar ba gnin hakan yasa amina tace kaga mu gudu fa kar a ritsa damu ko na gasken sunzo nan suka juta suka fita har sun wuce yusuf ya nufi dakin hajiya yana zuwa ya tura yatji shi bame gam ya kwankwasa amma shiru kk ji dariya yayi a fili yace Allah yasa ki gyara Ameen *Alqalamin khady* ✍ [3/15, 6:32 PM] El~hajj: πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€ TA ME GARI NA khadeeja usman 2⃣7⃣ up up up irin wannan cigiya haka masoya tame gari lallai dije tasha jaje to an nemota da kyar tace a gaisheda masoyanta dan haka ina muku fatan alkhairi tare da jinjina da miqa godiyata gareku masoya ta me gari masu yimin magana ban samun amsa musu da wuri suyimin uzuri ba lallai dan an gani online ya zamana ina kan whatsapp bane ta yiyu wani uzurin nakeyi amma naji wasu masu abar a kusa sun fadamin magana amma banji haushi ba nasan so ne ya kawo hakan amma kuyi haquri jin da hajiya tayi ana buga kofar yasata saurin shigewa toilet ta rufo har saida taji bugun ya lafa ta jima a cikin toilet din jin da tayi an daina bugun yasata dan bude qofar ta ziro kai kasancewar a tsorace take sai taji kamar muryar dije na fadin ku bita bandakin ku kamota ai kuwa da sauri ta fito ta fara qoqarin shiga cikin wardrope din amma kasancewar ba irin wadda mutum zai iya shiga bace abu ya gagara ganin hakan yasa ta tura kanta kasan gado tare da jan ciki harta shige duk wani motsi da zatayi gani takeyi dije na kallonta yayin data dinga karanto duk wata aya data sani kai harda hadisai gashi ba damar tayi juyi haka ta kwana a gurin batare da tayi baccin kirki ba har aka kira sallar asuba a kunnenta kafin ta zamo ta fito ta shiga toilet da kyar tayo alwala aikuwa tunda tahau sallaya taketa jera salloli tare da addu'ar Allah ya kareta daga sharrin jinni🀣 ita ko dije saida tayi me isarta kafin ta miqe ta dauro alwala ta haye gado ta kwanta cikin zuciyarta tace oh ni dije ina karya da aljanu ina cin uban mutane Allah yasa dai basa ganina bakuma sa jina kada su zo daukar fansa tana wannan tunanin ko itama taji kamar motsi a dakin aikuwa da sauri taja bargo ta rufe har kanta ta fara karanta ayatul kursiyu ni ko nace su dije ashe ana....... πŸ™Š ***** washe gari yusuf na dawowa daga masallaci gari ya danyi haske dan dabi'arsa ce inyaje sallar asuba baya dawowa sai gari ya waye tarr yana shigowa ya riski hajiya a falo da gima giman jakunkunanta cike da mamaki ya karasa gabanta ya duka ya shiga gaisheta ga mamakinsa amsawa tayi cike da fara'a kafin tace kun tashi lfy dai ko ? duk lfy kalau am ya naga wadan nan jakunkunan kuma na miye? nawa ne dama na yanke shawarar komawa gidana jira nakeyi ma ka shigo ince kasa a gyara shi yanzu dan nasan yayi kura a zuciyarshi yace lallai khadija kin iya saiti amma a fili saiya marairaice fuska yace haba hajiya me yayi zafi haka laifin me muka miki da har zaki ce zaki bar gidan nan lokaci daya kuma da gaggawa haka idan munyi miki laifi ne ai saiki fada mana mu gyara inma ita Aminan ce tayi miki wani abu ai saiki fadamin in dauki mataki a kanta dan baxan lamunci a bata miki ba kafin ya gama rufe baki sukaji budewar kofa Amina ce ta fito sanye da dogon hijab dinta tare da carbi a hannunta fitowarta yayi dai dai da fitowar dije itama kusan a tare suka qaraso falon suna zuwa Amina ta gaisheda hajiya ta amsa cike da sakin fuska sabanin da dasaita samu rabon zagi koda dije ta karaso gurin kowa ta shiga gaidashi koda ta zo kan hajiya ta gaisheta sam kin amsawa tayi sai dai ta maido mata da gaisuwar itako dije ta ci gaba da gaisheta jin ta kuma maido mata yasa tace hajiya aini ya kamata in gaisheki ranki ya dade dukansu kallonta sukayi ganin yadda ta ke duddukar dakai itako dije tace haba hajiya meye abin ranki ya dade anan dan Allah ki bari kada kisa su yaya su zaneni duka fa kikace wane mutum ai ba wanda ya isa ya tabaki ya kwana lfy inaaaaaa ai kinfi karfin kowa ganin yadda takeyi yasa dije saurin dakatar da ita ta hanya fadin wadannan jakunkunan fa baki akayi a gidan? yusuf ne yace inafa baki a rigimar hajiya ce a motsa wai ita dole saita koma ainihin gidanta data fara zama kiji fa kawai rana tsaka tace zata tafi ai dole mu binciki kanmu ko mu tambayi dalili dan ni bazan taba yarda ta tafi ta barmu ba bayan kowa a gidan nan yasaba da ita aikuwa dole in tafi in barku ko kuna so ko bakwa so dama can lalura tasa na zauna daku ba komai ba dan in kula da yadda zamanku zai gudana insa muku ido kasan ku yara farkon aure sai ana lura daku dan kun fiya rawar kai yanzu kuwa naga kunyi hankali ai gara in tattara in koma inda nafi wayo ko haba hajiya gaskiya ni ban goyi bayan ki tafi ki barni ba in su Anwar suka tafi school ni da wa zan dinga zama yana debemin kewa cewar Amina haba 'yar albarka ai zaki saba da sannu kinji kada ki damu zan dinga zuwa lokaci zuwa lokaci ina duba ku ai kallonta dije tayi kafin tace au kice ma kin tafi baki tafi ba kenan tunda zaki dinga zuwa ah ah ina nufin su in sun sami dama su dinga zuwa dubani ni me zanzo nayi a gidan yara kuma dukansu saida sukayi dariya kasa kasa a haka suka tsinkayi muryarta tana fadin ke Amina maza tashi ki dora abin kari mana kada abar bakuwa da yunwa a ranta tace duk da nasan ya zuwa yanzu Allah kadai yasan irin abincin data dibga taci na mutane taci nasu na aljanu amma a fili taci gaba da cewa ki debe duk abinda yakamata a girka kinji harda farfesun kajin nan duk ayi kada su lalace toh Amina ta amsa tare da mikewa ta nufi kitcheen a ranta tana hamdala tare da godewa khadija data zama silar ganin wannan ranar a gurinta tana shiga ta shiga hada kayan break masu rai da motsi irin wanda yakamata ace wanda ya taka matsayi irin na yusuf ana ci a gidansa tana tsaka da aikin dije ta shigo da sallamar ta ta qarasa inda take ah ah haba ranki ya dade ke da kanki a kitchen kuma dariya dije tayi kafin tace kai Aunty kema kin zama hajiyar kenan ba dole ba irin wannan aiki da kikayi shekara da shekaru muna zaune da mata yau kinsa zata bar gida rana tsaka au to tunda bakya son ta tafi bari inje in dakatar da ita ai ba matsala ni na isa wlh ta tafi na dinga zuwa gaisheta ai kedai Allah yayi miki albarka wlh kin gamamin komai duk da cewa uwar miji uwa ce amma ita tata matsalar tasa na gundura da zamanta yanzu kuma Allah yakawomin mafita kice wai ta zauna ai sai dai kice in shirya yin rakiya dariya dije tayi kafin tace ai na dauka kin fi son zaman nata ne da sai ince tasha zamanta kawai ta qarasa maganar tana dariya itama Amina dariya tayi nan dije ta kama mata aikin suka gama sunata hirar hajiya akan abinda yafaru jiya yau kam gida ko yara sun san ya canza inda kowa yaci yasha cikin nishadi bayan an gama ne yusuf yasa wani yaronsa yace yaje yasa a gyara gidan hajiya aikuwa cikin qankanin lokaci aka gama komai ya kira ya sanar masa an gama .saida yadan qara sayen wasu abubuwan aka dan kwaskware gidan abinka da masu abin cikin qanqanin lokaci aka gyara ko ina fess tunda dama bawani komai gidan keda ba kawai kura ce koda aka tashi tafiya hajiya kuka ta fara yi a ranta tana ta jama dije Allah ya isa data rabata da kujerar ta ta mulkin mallaka a gidan danta wadda bata tashi yin ritaya yanzu ba amma ko wannan ko'a cikin aljanun ta cika marar imani nan dai ta dinga sharbar majina har gida aka rakata yayin ita da dije ke zaune a bayan mota ko motsin kirki hajiya ta kasa har suka isa sam ba wani farin ciki a fuskar hajiya hakan yasa dije rabawa ta bayanta ta rada mata a kunne naga alamar cutar sanyin nan bata rabu dake har yanzu dan haka zan kawo miki magani anjima kuma wlh kada ki sake inga kafarki kwana kusa kin koma gidan nan duk abinda kike buqata ki kira ki sanar za'a kawo miki in na bukaci kije zanzo cikin dare in sanar mikk kije naga yanzu kina ta kuka nasan kukan da kikeyi ko na miye ki kiyaye gyada kai hajiya ta shiga yi a hankali tace naji ranki ya dade yusuf da duk abinda dije keyi yana lura da ita dan haka ya saki murmushi a ranshi yace khadija hooo duk wanda ya aureki zaisha fama haka suka gama zama a gidan hajiya bayan yusuf ya kira wata qanwar hajiya akan ta zo su zauna tare sannan yasa a nemo musu mai aikin da zata dinga kula da gidan tare da me gadi nan sukayi musu sallama bayan ya vasu kudi tare da sanar dasu gobe zai dawo in Allah ya yarda haka hajiya tanaji tana gani suka fice zuciyarta kamar ra fashe amma ba halin bayyanawa tana tsoron mutum aljan ***** yau kwanan dije biyu a gidan yusuf kuma yaune zata koma gida yayin da kallo daya zakayi ma masu gidan ya zuwa yanzu ka tabbatar suna cikin nutsuwa tunda akayi sallar la'asar dije ta shirya ta zo ta kame a falo masu gidan ne suka fito suna dariya da alama hirar tayi musu dadi ganin dije da sukayi a zaune yasa su fadin ah ah ranki ya dade dan yanzu sunan da suke fada mata kenan tunda sukaji a bakin hajiya me zamu gani haka kamar an gaji damu? murmushi tayi. kafin tace ba batun gajiya illa dai inason in koma ne dan nayi kewar mutanen gidan hmm kajita sai kace ba ita tacemin nan da can duk daya ne ba cewar Amina bar ma ta wannan su wadanda take cewa tayi kewar tasu tunda tazo ko waya basuyimin ba sabanin da da kullum sai munyi waya da safe kinga alama ta nuna su basuyi kewarki ba kamar yadda kike cewa ke kinyi ta su to ya za'ayi su kira kuce sunyi rashin kunya inaga shiyasa suka ki kira ah ah ko dai ko dai?? ko dai me ? ko dai an gwada musu irin na hajiyata ne shiyasa suka shiga taitatayinsu dariya tayi kafin tace ina ni ina yiwa ysyyena haka kunga ni duk ba wannan ba gida nake so na kuma gama shiryawa a zo a kaini ko in hau taxi rufa mana asiri ai mu bazamu yadda mu batawa mumina rai ba haba wane mu tashi maxa ki kimtsa in maida ke salin alin ni nagama shiryawa ina yarana muyi sallama nofal na bacci Anwar kuma yana gidan hajiya ko kin manta ok hakane to bari mu mike mu saita hanya ta fada tana kokarin miqewa Amina tace ta jirata inda tshiga ciki ba jimawa ta fito dauke da leda a hannunta ta damkawa dije da farko kin karba tayi saida Aminar ta nuna rashin jin dadinta sannan ta karba fayi godiya har bakin mota ta raka su inda dije ta kame kyam a baya ba yadda basu yiba ta hau gaba tace ita tafi jin dadin zaman baya dole suka haqura suka kyaleta a hanya ya tsaya ya qara mata siyayya inda suka nufi gida koda suka iso yamma ta danyi kasancewar yau weekend duk bamai zuwa aiki yasa mutan gidan suka zo garden suka zauna duka suna hira ana nishadi gabansu kayan fruit ne sai lemuka da ruwa inda duka suke hira ana babbaka dariya sam sun ma msnta da wata wai ita dije tunda kowa ya warke🀣 horn din da suka jiyo ne daga bakin gate yasa suka maida hankalinsu gurin inda sukaga motar yusuf ta danno kai kasancewar gilashin gaban a bude yake yasa ba'a suka ga ba kowa ciki sabanin na baya dayake a rufeπŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€ *TAME GARI* NA khadeeja usman 2⃣8⃣ kasancewar bayan motar a rufe yake yasa basu ga dije ba har yusuf yayi parking kafin ya fito ya zagaya ya budewa dije data kame kam kai kace wata hajiya ce innalillahi wa'inna ilaihir raji'un sukaji naseer ya fada habeeb da sajida da hankalinsu bai kai ga dije ba suka ce meya faru kk wannan salati Annoba ta dawo cewar yusra habeeb daya gutsuri apple kenan tsayawa yayi shi bai hadiye ba kuma bai fito da ita ba duk sun kasa motsawa sallamar dije ce ta farkar dasu inda ta shiga fadin Assalamu alaikum my brothers n'd sisters gaskiya nayi missing dinku duk da naga ku kamar bakwa farin ciki da dawowata ma dan naga fuskokinku kamar wadanda aka aikoma da mutuwa waya isa yace baya farin ciki da dawowarki cewar naseer yana yake ko ba haka ba duka gyada kai sukayi amma banda sajida data hade rai sosai ganin hakan da dije tayi yasa itama ko kallonta batayi ba ta nemi guri ta zauna yusuf ne ya miqa musu hannu suka shiga gaisawa bayan ya samu guri ya zauna kafin yace to ga kayan aro nan na dawo muku dashi kada ace na riketa waya ce da kadawo da abinda aka ara maka din ? ai da nan da can duk dayane daka barta ma a can din ba matsala da sai a biyota da kayanta khadija ai tafi karfin a bada aronta sai dai kyautarta kawai cewar habeeb daya qarasa hadiye apple din bakinsa dayaji tazamar masa kamar dutse ah ah so kukeyi matanku su yankomin sammaci suce na dauke musu 'yar qanwarsu babu ruwana wallahi indai mune bakada matsala ai munada kakkyawar fahimta da mazajenmu komai suka yanke bama musawa cewar yusra au hakane to tunda hakane bari inyi farin ciki dan na lura bazan sha wuya gun dauketa gaba daya ba cike da rashin fahimtar maganar tashi habeeb yace kamar ya gaba daya kuma ai dole zatayi aure ko? ah to idan kuma ya kasance nine zan aureta din fa dammm kirjin habeeb ya buga domin jin furucin da yusuf din yayi ji yayi zuciyarsa tayi masa zafi cikin dan zafi yace ita kuma Aminan ka kai ta ina ? sajida da sai yanzu tayi magana tace tana nan a gidan nasa ku maza kunya ce daku in kun tashi kara aure ah ah Aunty na ai a aure ba batun kunya kuma kin san Amina batada matsala a wannan fannin ba Aunty ba cewa zakayi mama habeeb ya qara fada a dan hasale kai gwafdede dakai ka kalli sajida kace mata Aunty ko kunya baka jiba dariya yusuf yayi kafin yace to banda abinka yaya ai ko yusra yanzu Aunty zan dinga kiranta bare kuma sajida datake matar babban yaya inka so ka kirani da baba malam karewar yaya kaga bana son iskanci malam kabar wannan shirmen naka ita wannan yarinyar duka nawa take da zaka kama fadar irin wadannan maganganun a gabanta so kk yi ta raina mutane kawai du du du me khadija ta sani cikin week din nan zasu fara zana S.S.C.E fa amma kk wani maganar aure a gabanta haba malam ai sai kaja ta raina mutane duk abin nan da akeyi sai ka rantse da Allah dije bata gurin tana zaune abinta ta dauki lemon bawo tana sha jin sun 'danyi shuru da dramer tasu yasa ta tunawa da wayarta da daddy ya siya mata wadda ita taso ta dauka ranar da zata tafi gidan yusuf bata samu dama ba dan haka tana tunawa ta mike dan shiga ciki ta fara tafiya ta tsinkayi muryar yusuf yace kayanki fa princess? batare data daina tafiyar ba kuma bata juyo ba tace biyoni dasu pls ta shige ciki abinta girmanki ya wuce haka ai ya fada yana me kokarin barin gurin suka hada ido da naseer dake ta masa ruwan harara au to yaya laifin me kuma nayi ake min wannan harara haka ? baka kirana da abinda yafi yaya ka wani tsaya kanata sakin magana gaban yarinya salon kasa ta raina mutane banda abinka meye abin raini a ciki a gara ayi komai a gabanku a matsayinku na manyan yayye nifa inka ce yayan nan ji nakeyi kamar in kurma ihu wlh inba iskanci ba ina ni ina kai banda ma zamani daba ruwan abota da shekaru ai da sai ince kai sai dai kayi abota da qanin daddy ai ba komai koma dai sa'an daddy ne soyayya bata tsufa dan haka bari kuga in tashi nabi ta kada ran 'yammata ya baci yana gama fadar haka ya juya ya nufi motar ya bude ya fito da ledar ya nufi part din habeeb da mugun sauri habeeb yasha gabanshi yace ina zaka malam? kaji ka yaya da wata tambaya gurin princess mana in kai mata kayanta haka kawai zan barka ka shiga ciki ka sameta a matsayinta na wadda ba muharamarka ba kallonsa yusuf ya shiga yi yana murmushi kafin yace haba yaya kamar baka san halina ba wannan wane irin magana kk yi naga fa tun kafin ayi nisa kafara adawa anya kuwa zaka iya min jagora gurin daddy ? habeeb da inda akwai kalmar data ke qona masa rai to bata wuce yace masa

Chapter 12 of 25