da walkiya ya d'aurawa Al'ameen a wuya, Muhammad ka kula da mamanku da kaninka kaji in mamanku ta haifi mace kace asa Mata khadija Inna mijine asa masa Shitu,Yana fad'a Masa hakan police sukazo suka Tisa keyarsa zuwa cikin mota
Bayan an tafi da Yusuf, Alhaji ubangari da danginsa Koran Kare sukama Aisha da yaranta,sosai Aisha tayita kuka tana tattara kayanta zubawa tayi a ak'watin karfe ta d'aurawa Al'ameen da salim,suka Kama hanyar sintali.
Gari gabaki d'aya ya d'auka zancen Yusuf yayi kokarin mawa Yar ubangidansa fyade,bayan isar Aisha gidan ADARA zuwa lokacin labari yazo kunnensu Dayake unguwan da suke da sintali ba nisa
Bayan isar Aisha gida ta sake haduwa da wani tashin hankali shine mahaifinta yace sai ta mayarda yaran Yusuf gun danginsa kafun ta zauna musu a gida Dayake mahaifiyar ta tarasu tun kafun auren ta,yasa ba Wanda yayi yunkurin baiwa baban ta hakuri
Aishan ADARA ta shiga tashin hankali ba kad'an ba na rashin sanin asalin Yusuf abin yayi mugun daga Mata hankali,ta rasa Ina zatasa kanta taji Dadi,don da ta koma gidan ubangari tunda shine waliyin Yusuf ya fad'a Mata inda dangin Yusuf suke Amma rashin mutunci da aka Mata a gidan Koh kyaun gani Babu,karshe dai wani abokin Yusuf ne Wanda sukaye mutunci sosai ya taimaki Aisha bayan Jin labarin abinda ya faru tabbas shima ya shiga tashin hankali Amma Sam Bai yarda Yusuf ne zai aikata wannan abinba, d'auko Aisha yayi ya Basu d'aki a gidansa duk da MATARSA ta tsani zaman su Aisha Amma ba yanda zata iyya Aisha ta koma gidan abokin Yusuf da zama.
Wannan zaman gidan abokin Yusuf shine mafarin haduwar
Al'ameen da kamila
An Kai Yusuf kotu,Amma bashi da hujjan Kare kansa haka yanaji Yana gani,laifinda ba nasaba aka yanke Masa hukunci.
Bayan Shari'a abubuwa sun ma Aisha yawa na rashin mijinta don abinda zataci ma gagaransu yake Dole karatun su Al'ameen a private ya gagara ta ciresu ta maidasu Government school, sukaci gaba da zuwa,itakam wankau take Koh daka take sama musu abinda zasuci sosai Aisha take fama da rayuwa ga bakin cikin_ abinda Yusuf ya aikata,ba karamin bakin jini ya shafawa yaransa ba
Hankalin Aisha Bai Kara tashi ba Saida lokacin komawar Salim asibiti Amma Bata da Koh sisi haka ta d'aukesa sukaje asibitin Amma abin mamaki duk yanda suka Saba da zuwa ganin likita Amma yau kawai da basu da kudin magani haka suka dawo gida kayan sakawarta Aisha ta tattara da kayan dakinta take sayarwa a hakan ta ringa ma Salim jinya da kayyakinta don abokin Yusuf d'aki kawai ya Basu Amma abinci Kam sai dai ta nema musu,
Ta bangaren zainab Kam tayi Dana sani Dana saninda har abada bazata daina yinsu ba sai yanzun take ganin wautarta na biyewa khairat harta aikata wannan mumunan kazafi wa Yusuf gashi abin Bai tsaya iyya Yusuf ba ta raba ma'aurata ta raba uba da yaransa ganin Yusuf da take taji Dadi yanzun Babu shi gashi Koh samarinta ma yanzun duk sun gujeta a dalilin labarin da suka samu
Zainab rayuwa ta Mata zafi Koh baccin kirki Bata iyya wa taso sanar da iyayenta gaskiya Amma kairat ta kwabeta don hakan zai iyya zubar Mata da mutunci fiye Dana yanzun da take ciki.
Al'ameen da kamila yaran makwanta ne gidansu kamila.na kusa da gidan bala abokin Yusuf,
Kamila dalibar makaranta i private school ne Wanda ke kusa da goverments day da Yusuf ke ciki
Farkon haduwar kamila da Yusuf a hanyar makaranta zai tafi itama zata fita.
Tunda kamila.taga Al'ameen take yawan shige Masa har gidansu take zuwa tun Al'ameen baya kulata hardai ya fara kulata Aisha Karan kanta da farko bataso mu'amalar Al'ameen da kamila ba ganin Al'ameen lokacin shikara biyar ya bawa kamila Amma haka ta barsu ganin karatu Yusuf ke koya Mata kullum insun hadu
Bayan wata uku lokacin cikin Aisha ya Shiga wata bakwai,zuwa lokacin Aisha Bata da kome a dakinta sai taburma sai sarkan wuyan muhammad sai tsummo karansu saboda duk kudin sun Kare akan kudin maganin Salim ga rayuwa dai anata gargarawa
Yau ranan juma'a Al'ameen da Salim sun dawo makaranta bayan sun kara kamila gida don yanzun shakuwane Mai tsanani a tsakanin su wanda in kamila bataga Al'ameen ba zatazo gidansu haka shima, suna zaune dumamen safe da ya rage shine Aisha ta Basu itakam haka ta hakura saboda yau sun tashi bako sisi,zainab ce ta shigo gidan da sallama a bakinta
Aisha ta amsa Mata Dan Sam bata Jin haushin family ubangari don Koh itane abinda Yusuf ya aikata saita Masa fiye da haka
Kallon zainab take Wanda duk tabi ta rame kallo d'aya zaka Mata kasan Bata cikin hayyacinta,bayan sun gaisa zainab ta d'aga ido tana kallon Aisha Bata San ta Ina zata fara ba yau tayi Alkawarin zata Fad'i gaskiya Koh zata samu sassauci a rayuwan ta
Hawaye ne ya cika idanun zainab ta bude baki a Hankali tace,maman Muhammad akwai wani magana da zanfada Miki bansan ya Zaki d'auki maganar ba Amma na g'wammaci na karbi Koh wani hukunci akan Wanda nake ciki
Cikin mamaki Aisha kam ke kallon zainab a iyya zamansu da zainab Bata taba ganin ta Mata magana a mutunce ba Kamar yau,toh zainab Allah yasa naji alkhari
Gaskiyan abinda ya faru maman Al'ameen babu ruwan Yusuf aciki,tace tana kallon Aisha
Kamar ya bangane ba zainab?
Eh tabbas Kamar yanda nace , Yusuf Babu ruwansa a ciki nice da khairat Muka had'a kome a tunanin mu Koh in aka Kama Yusuf xai mini fyade babana zai tilastashi ya aure ni Amma ban taba tunanin abinda na aikata ba daidai bane Saida Naga yanda na wargaza muku farin cikin na dasa muku bakin ciki, wallahih maman Al'ameen nayi nadama,Dana biyewa khairat ban tashi nadama ba Saida naji jiya tana Hira da kawarta a waya suna mini dariya, na tsokancin danayi harna yarda da abinda ta gayamin Ashe itama son Yusuf take,ta karasa maganar hawaye ya zuba akan fuskarta
Aishan ADARA Kam daskarewa tayi a zaune itakam wace irin mace ce Mai mantuwa me yasa ta kasa yarda da Yusuf, namijin daya yarda zai rayu da ita Bai damu da tarbiyan gidansu ba Koh halinta ba ya aureta Koda Yusuf Zina yayi hukuncin da ta yanke Masa yayi tsauri,wani irin murdawa mararta yayi na tashin hankali atake jini ya balle Mata durkusawa Aisha tayi tana Kiran sunan Allah.
Da gudu matar Bala dake tsaye tun d'azun tanajin bayanin da zainab keye tazo da gudu,tana kwalawa mijinta Kira da gudu ya fitoh su uku suka ciccibi Aisha zuwa asibiti
Al'ameen Kam Kama hannun Salim yayi suka Kama hanyar gidan ADARA,suna Isa kakansu suka samu a kofar gida suka fad'a Masa mamarsu ba lfy an kaita asibiti, hankali baban Aisha ya Tashi matuka don shi Karan kamshi korinda Yama Aisha na haushin yaran Yusuf ne, Amma Yana son yarsa tura su Salim yayi gidan Amina (Goggo) shi Kuma ya wuce gidan Bala agun ya samu wa'inda ke zaune aka fita da Aisha, aka Masa kwatancen asibitin da aka Kai Aisha
Bayan zuwansa ne yaji labarin abinda ya haddasa ma Aisha nakudar Dole abakin Matar Bala,shima sosai ransa ya baci duk da Bai gamu da zainab a asibitin ba Amma ransa ya matukar baci gida ya koma ya sanar da yaransa da yaran Yan uwansa akan suje su fara d'aukar mataki akan zainab kafun hukuma ta shiga
Ayarin gidan ADARA daga Yan Mata har zaurawa da samari sukaye Ayari guda suka fasa unguwa da kafa suka taka har gidan ubangari.
Zainab Kam gabaki d'aya ta rasa nutsuwarta Koh zama takasa waje Daya, tunda ta gudo daga hospital karshe dai Saida mamarta ta tambaye ta Koh meke damunta haka? tunda abinnan ya faru ta fahimci walwalar zainab ya d'auke, zainab Kam kin fad'a Mata gaskiya tayi
Suna zaune dukansu a gida dayake yau Friday ne ubangari ya dawo aiki da wure haka Yan makaranta,ji kawai sukaye an bankado get in gidan an shigo ciki kafun ma su gama tantance suwaye ne har kanwar Aisha ta nufi d'akin zainab jawota sukaye har kofar gidan da gudu su ubangari suka Mara musu baya.
Rufeta da duka ADARA sukaye, saiga khairat tafitob gida makwantan su, Aiko kamota sukayi suka Had'asu suna jibga duk yanda Yan unguwa da ubangari suke kokarin k'wace zainab da khairat abin ya gagara ganin zasuye kisan kai don zainab ta Suma Amma haka Ayarin gidan Adara Basu daina jibgarta ba Saida ta farfado da duka
Police aka Kira lokacin unguwan ya cika makil day'an kallo, abinka da Friday kowa na gida,
bayan zuwan police kafun aka samu aka k'wace su zainab anso Kama Yan ADARA Amma Ina abin ya gagara don fad'ane ya kusa zama na police da Yan gidan Adara,ganin jaraba irin na Yan gidan yasa polisawan tambayar musabbabin fad'an don dai sunyi sunyi su bisu station aye kome agun Amma sunki, D'aya daga cikin samarin gidan ne ya nuna zainab,ke don uwarki fada musu meya faru tsakaninki da yusuf mijin Aisha?
Hakika zainab tayi mugun tsorata hakan yasa Bata boye kome ba ta fad'a duk abinda ya faru,atake Alumman suka fara Allah wadai da zainab da khairat ubangari Kam yanke jiki yayi ya Fadi hawan jininsa ya tashi, police ma tafiyarsu sukaye Basu d'auki kowa ba.
Ta bangaren Aisha Kam ganin tana kokarin rasa Ranta yasa likitoti Mata operation aka cire baby girl bakwaini aka saka a kwalba,Aisha na farfadowa sunan mijinta ta fara Ambata tana sambatu,tunda ta farfado batada magana sai a kaita wajen Yusuf ta nemi gafaransa Amma ba'a barta ta fita a asibitin ba saboda yanayin jikinta Dana baby.
Ta bangaren ubangari ma hakan take jinya ya kwanta har kusan sati baisan inda kansa yake ba abubuwa sun taru sun Masa yawa,Yana Jin sauki kad'an ya Tashi da kafarsa ya koma wajen Alkalin da yayi musu Shari'a,
An nemi ganin Yusuf don a wankesa a kotu Amma abin tashin hankali shine, Yusuf a Randa aka kaisa prison Bai kwanaba ya fita tare da sa hannun kotsosin kasa
Wannan magana ita tafi ko wace magana tashin hankali agun Aisha don anye iyya bincike an had'a hannu da masu kudin da Yusuf yayi mu'amalan kasuwanci dasu don binciko inda Yusuf yake Koh suwa suka fiddasa
Duk Wanda aka tuhuma Mai hannun a cire Yusuf magana D'aya yake fad'a baisan Yusuf ba kawai umurni aka basa daga sama
Wannan magana tayi mugun dagawa Aisha hankali atake ta sake kwantawa ciwo Wanda an rasa kansa kullum gaba gaba yake duk abinda babanta ke dashi ya kare a jinyar Aisha da Salim don shima zuwa lokacin zuciyarsa ta fara tashi.
Tsawon wata biyar ana binciken case in Yusuf Amma shuru ba wani cigaba,yau dai jikin Aisha da sauki,bayan Salim da Yusuf sunzo duba mamar tasu ,don yanzun suna zaune a gidan Adara ne
A hankali ta Kama hannun Al'ameen ta rike cikin nata ta fara magana hawaye nabin Gefen idanunta,Al'ameen ga kaninka nan da Yar uwarka khadija Muhammad ka kula dasu ka zama uba a garesu Koda kowa zai gaji dasu Kai ka zaman musu gata, jagora,Garkuwa,inaji a jikina wata Rana zaka Hadu da mahaifinka,kace Masa ni Aisha Ina neman afuwarsa ya yafe mini Koh Zan samu salama,ka zamo Mai hakuri kamar mahaifinka duk abinda zakaye a rayuwa ka ringa bincike karka yanke hukunci a cikin fushi don karshin sa Dana sanine.
Al'ameen duk da yarone Amma hankalinsa in yayi dubu toh ya tashe in Bai manta ba haka abbajonsa yayi Masa, shikenan ya gudu ya barsu don shi har yanzun baisan takammamen abinda yake faruwa ba,
Mami kema gudu zakiye kamar abbajo ki barmu?yace Yana kuka shida Salim dake kusa dashi
Ah ah Yusuf ba gudu zanye na barku ba inda zanje kowa ma zaije in lokacin sa yayi sanan abbajonka Bai gudu ba wata Rana zai dawo kaji,ga kaninka na kuka ka rarrashesa karka barsa ya zubda hawaye kasan ciwonsa bayason damuwa Koh?ta tambaye sa muryanta na shakewa
Kai muhammad ya gyad'a Mata hade da Kama hannun Salim Yana rarrashensa,
Ji kawai yayi mamin su na wani irin shakuwa hade da Kiran sunan Allah,da sauri ya fita a d'akin yaje Kiran Doctor
Suna shigowa dakin da sauri Muhammad ya matso gareta cikin matukar razana ganin maminsu Bata m...................
πππππππ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* π
ππππ *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa*
ππππ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara*
πππ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace*
πππ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE*
π *Na tsunguno(habil)*
π *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )
π *Turaren turara jiki after birth* ,
π *Na d'aki(halud Al'oud)*
*UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* ππΌππΌ
πππ *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa*
πππ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria*
Contact them vie
πͺ08028827241 or 09033791049
IG @umsadincense
πππππππππππ
π§βπ¦― *MATAR MAKAHO* π¨βπ¦―
~ Na ~
π *Rukayya* *Ibrahim* π
β¨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπ
free book π€§
Page 3οΈβ£8οΈβ£&3οΈβ£9οΈβ£
"Ni Kaya na saya" ta basa amsa
Wani irin Kaya kenan?
sannan Ina Kayana?
"Nina yarda kayayyakin ka duka sabo na sai maka Naga nakan sun kode,Amma kayi hakuri bazan sake ba" tace tana Kama hannunsa dake kokarin zare jallabiyan jikinsa
Sumayya akan me Zaki sayamin Kaya bazaki fad'a mini ba saboda bani da ido saiki zo ki musanya mini,kamar wani yaro.
"Kayi hakuri kaga yanda jallabiyar nan ta karbe ka kuwa yayan khadija" tace ta ja maza zip in gaban jallabiyar,hade da d'aukar Turare ta fisa Masa,vayan ya shafa Mai
Nagode Allah ya miki albarka ya hanani Miki butulci a rayuwa Sumayya
"Ameen" tace tana jera abincin karyawan, Bismillah ta Masa suka fara ci cikin kwanciyar hankali
Bayan sun Gama cin abinci tattara Kwanukan yayi yakai waje,bayan ya ajeye, d'akin yadawo
"Toh yayan khadija wacece kamila"Sumayya ta tambaye sa
Nifa nayi Miki Alkawari ,ai basai kin Kara tambaya taba nida kaina Zan fad'a Miki kome Daya shafe kamila.
"Uhmm ba Dole na tambaya ba tunda sai jamin Rai kake yaufa da wure na Gama aiki Amma sai wani sham kamshi kake"
Nasha kamshin, kema saiki Rama.
"Wallahih ka Gama iyya jarabanka bazan biye maka ba sai naji lbrn nan ehen"
Toh zoki zauna a kusa Dani samun lbrn yafi Dadi,yace Yana zama akan kujera
Saboda tsabar sonjin lbr yasa Sumayya mikewa da sauri tazo Kan kujeran ta xauna kusa dashi
Hannu yasa ya matsota jikinsa a hankali ya rungume ta a jikinsa cikin sanyin hallintarsa murya a sanyaye yace Sumayya!
"Na'am yayan khadija"
Yau Zan baki labarin kamila Amma saikin ji labarina Nima kafun ki gane lbrn kamila dakyau.
"Yauwa Aiko Ina sonjin lbrn ka da dangan takarka da gidan ADARA duk da Ina tunanin dangin mahaifinkane Amma halayenku sun banbanta,hakan matsayinka da khadija a gidan nan na fahimci a kaskance kuke ba Kamar sauran Yan gidan ba"
Duk xakiji insha Allah Koh Nima Zan samu amsar dalilin auren mu Wanda har yau bansan dalili ba.
"Wai kana nufin ba Kaine kace kana Sona ba,aka aura maka ni "?ta tambaye sa cikin zare ido.
Nima ban sani ba Sumayya bansan dalilin auren muba Amma koma menene inaji a jikina insha Allah haduwar mu dake alkhari ce
"Insha Allah insha Allah yayan khadija" tace tana share hawaye Daya gangaro mata
Gyara zama Al'ameen Yayi a hankali ya fara magana................
*Shikaru Talatin da biyar da suka wuce baya* π’
Malam Yusuf sumul, shine cikekken sunansa da aka Sansa dashi matashine Dan shikara 35,Yusuf mutum ne Mai Hakuri addini ga kawaici baid'auki duniya da zafi ba,Yana da tsananin zurfin ciki duk yanda zaka zauna dashi bazaka taba fahimtar wani abu a tattare dashi ba shiyasa ba Wanda yasan shid'an inane Koh daga Ina yake, duk da kowa ya gansa Kuma yaji yanayin hausar sa da maganar sa Dole yasan cewa ba D'an kasa bane .
Alhaji Rabi'u ubangari. Wanda akafi sani da ubangari,maikacin gonnati ne Kuma Mai rufin asiri sosai,Yana da Mata biyu.
shine Mai gidan Yusuf, saboda tsananin hankali da nitsuwar yusuf yasa ya d'aukesa Kamar D'an gida ya basa d'aki a cikin gidansa,Yusuf na Masa aikace aikace kamar zuwa kasuwa wanki da gugan kayan yaransa da NASA na kansa Yana Kai kananun yaransa makaranta ya dawo dasu,
Yaran ubangari guda biyar ne sai yaran Yan uwansa maza biyu Mata hudu,kenan yara goma Sha D'aya ne a gidan ubangari
Zainab Fatima Auwalu lukman Nasir,sune yaran ubangari na cikinsa
Haidar Umar khairat munira safara'u murja sune yaran Yan uwansa Dayake rikewa
Yusuf da ubangari akwai kyakkyawar fahimta a tsakaninsu duk da baisan Yusuf ba Amma da zuciya d'aya yake zaune dashi ganin tsawon shikaru Bai taba nuna wani mugun halinsa Wanda mutane zasuye Allah wadai dashi ba.
Yaran gidan na basa girmansa kasancewar duk yaran gidan ya fisu a shikaru,yanajin dadin zaman gidan sosai don tun kafun Alhaji yayi aure suke tare har Allah yasa yayi aure
Yaran suna ganin girman Yusuf saboda yanda mahaifin su ke tare tashi hakan yasa suke kiransa da bappa yusufa
Zaman Yusuf a gidan ya fara gunduran sane bayan girman Yar Alhaji Rabi'u ubangari zainab,wance Allah ya diga Mata son yusuf Mai tsanani duk da a lokacin tana da shikaru 14 yayin da Yusuf keda shikara 35
Tun tana boyewa har abin ya gagara ta tinkare Yusuf da maganar.
Sosai Yusuf ya ja Mata kunne akan zancen kuma ya tabbatar Mata shi bazai aureta ba donshi a matsayin diyarsa,ya d'auketa duk yanda tayi kokarin ganin tashawo Kan Yusuf abin ya gagara,taso fad'awa mahaifyarta zancen tanason Yusuf Amma khairat Yar bappanta ta hanata saboda tasan mundin maman zainab tasan zancen daker zainab ta aure Yusuf.
ADARA FAMILY HOUSE haifafun jalingo ne tun iyaye da kakanni anan gidan Adara suka tashi don duk fad'in sintali ba gida Mai dumbin tarihi da shikarun mazauna ciki irin family ADARA tun husul sai chanje chanjen gini da ake in zamani ya shude,
Tun husul ma haka suke mutane ne masu masifan tsiya ga fad'a kamar ahlin dambe shiyasa aka musu lakabi da ADARA
Aishan ADARA d'aya ce daga cikin yaran gidan adara ,macece Mai matsifa na bugawa a jarida duk yanda kaga mala'in yaran gidan ADARA Aisha ta damasu ta shanye saboda tsananin masifarta yasa Koh saurayi Bata dashi don a lokacin abin kunyane mace takai shikara 20 batayi aure ba Amma Aisha shikarunta 20 Koh saurayi Bata dashi saboda tsananin tsoronta da maza keye
Gidan ADARA tun asali haka yake har wa yanzun.
Aishan ADARA na Saida Dan wake a bakin kasuwan main market na jalingo
Sun hadu da Yusuf ne lokacin da yaje kasuwa sayayyan kayan Miyan gidan ubangidansa,ya saye danwaken ta by mistake robanta ya fashe a hannunsa,
Ba karamin bala'i Aishan ADARA ta sauke Masa ma kwando kwando da Kuma uzzurawa saiya biyata robanta
Yusuf Kam ba karamin mamaki yasha ba ganin irin bala'in da Mai danwake ke Masa akan robanda Bai wuce sule biyar ba sai bala'i take Masa Kamar ya Mata Satan jari
Sosai Yusuf yaji haushi kala baice Mata ba ya Kama hanya Yana tafiya itakam sai binsa take sayya Biya robanta
Yusuf kam yasha Alwashin bazai biya ba ganin jarabanda take Masa haka tayita binsa harya Gama cefenen ya Kama hanyar gida bayan ya tare machine.
Duk jaraban Aishan ADARA yau taga iyyakarta don ba zagi ba duka da Mannin hauka Yusuf ya rabu da ita
Bayan dawowar Yusuf gida Sam ya rasa sukuni,tunanin Mai danwake Kam ya hanasa sukuni Sam
Ta bangaren Aishan ADARA ma hakane Sam bayan tafiyar kyakkyawar mutumin da Bata Sansa ba gabaki daya ya hanata sakat a tsawon shikarun ta Bata taba bi takan soyayya ba Amma wannan Karo tayi tuntuben so a bakin titi Wanda Bata San inda zata sake ganinsa ba
Bayan sati biyu Sam Yusuf ya kasa sukuni ya kasa hakuri sosai Y'an kwanakin nan ya gane meke d'awainiya dashi,sai a lokacin yaji tausayin zainab Ashe haka takeji yake wulakanta ta,
Farga bansa d'ayane kar yaje gareta da soyayya ta tsigalesa don Tabbas daga ganinta Yar bala'i ce sosai Abu na biyu Kuma asalinsa kar rashin sanin danginsa yasa a hanasa auren ta.
A hankali Yusuf ya fara zuwa gun Aishan ADARA cin danwake Wasa Wasa harya kasance ba ranan da baya zuwa ci haka ba ranan da basa fad'a a tsakaninsu kafun su rabu ,har shakuwa yazo ya shiga tsakaninsu Mai tsanani Wanda a zahiri kowa son junane ke d'awainiya dashi,Amma ya kasa sanar da D'an uwansa
A hankali Yusuf ya fahimci masifar Aisha a tarbiyan gidansu yake a Hankali ya Soma nutsar da ita sosai yake nuna Mata abin Bai dace ma Abu kamar Wasa Aishan ADARA ta nutsu sosai sai dai fa har lokacin in ka tabota zaka Sha bala'i sai dai in abinda ba ruwantane Bata Shiga haka zalika ta daina dambe da kowa,abin harya fara bawa jama'a mamaki sauyawan ta
Lokaci da Yusuf ya bayyana ma Aisha soyayyarsa gareta Babu wani jinkiri ta amsa sosai suke zuba love
Yusuf ya samu Alhaji akan maganar Aisha ba karamin murna alhajin yayi ba dayaji Yusuf ya samu wance yake so don burinsa kenan,ya tambaye Yusuf danginsa don maganar aure Dole ana bukatan dangi na jini
Hankalin Yusuf ya Tashi matuka don har kwanciya yayi a gadon asibiti Akan zancen danginsa da Alhaji ya matsa Masa akai
Karshe dai fa ubangari yaga abin fa nayine yasa sa hakura da tambayar Yusuf shi yashiga maganar auren Yusuf
Da yake ubangari ya jima tare da Yusuf kowa gani yake kamar Yan uwane hakan yasa ba dogon zance aka basa auren Aisha don Suma sun Matsu tayi aure ganin ta girma a gida
Ta bangaren zainab Yar ubangari Kam in hankalin ta yayi dubu ya Tashi tayi kuka tayi kuka Kamar zatayi hauka Amma khairat ta taka Mata birki tare da Mata alkawarin sai Yusuf ya aureta amma tabare ayi auren taga matakin da zata d'aukar Mata
Bayan auren Yusuf sumul da Aishan ADARA, Alhaji yaki yarda Yusuf ya Kama gidan haya a gidansa sukaci gaba da zama, soyayya suke shimfid'a wa Mai tsafta sosai Aisha ta nutsu suna zaune da yaran ubangari da matansa lfy Sam bata nuna musu Yar Hali sai daifa basa shiri da zainab ganin kallon banza da take mata
Sai Bayan shikara uku da auren Aishan ADARA da Yusuf kafun Allah ya baiwa Aisha ciki sosai sukayi farinciki da wannan cikin da Allah ya azurtasu,sukaci gaba da rainon cikin cikin farin ciki
Bayan Aisha ta haihuwa sun samu d'a namiji Mai matukar Kama da mahaifinsa Kamar an tsaga Kara, mahaifinsa yasa Masa suna muhammad.
Mahaifiyarsa na kiransa Al'ameen.
Da sauri Sumayya ta d'aga ido tana kallon Al'ameen dake Bata lbr"kana nufin kace mini gidan n........"
Bai bare ta karasa ba ya girgiza Mata Kai Yana Kara kwantar ta ita a jikinsa,ki aje tambayoyin ki Inna Gama saiki tambaya
Kai kawai ta gyad'a Masa
Ya cigaba.....har lokacin zainab Bata saduda da soyayyar Yusuf ba don a lokacin ta kammala secondary school nata,Amma Taki aure Dole yasa babanta nema Mata wani makarantan gaba da secondary taci gaba
Bayan haihuwa Al'ameen da shikara uku Aisha ta Kara haihuwar wani da namiji yaci sunan Salim, tun daga lokacin Aisha Bata sake samun ciki ba,sukaci gaba da kula da yaransu don a lokacin Alhaji ya budewa Yusuf shago yabar aikace aikacen gida basuda wata matsala sai na d'ansu Salim Wanda ke fama da mummunan ciwon zuciya,duk bayan wata D'aya sai sunga likita Kuma sai anci kudi.
A hakan rayuwa tayita tafiya yau Dadi gobe akasinsa Al'ameen da Salim suna matukar samun kula daga iyayen su suna Isa shiga makaranta aka sakasu yarane da suka shagu da junansu matika Kamar wasu tagwaye Dayake Salim nada gaban girma tuni ya tsara da yayansa har lokacin Aisha Bata San cewa Yusuf ba Dan uwan Alhaji bane duk da tana yawan tambayan sa labarin Yan uwansa Amma Yusuf daga tayi tambar saiya hau hada Mata fuska
Bayan wasu shikaru lokacin Al'ameen nada shikara 11 Salim nada shikara 8 a duniya. Aisha na d'auke da karamin ciki.
wata ranan juma'a da zuriyan yusuf bazasu taba mantawa da ranan b a tsawon rayuwansu ba har Abada ciwon bazaibar zukatan su ba
Da misalin karfe bakwai na dare yusuf ya dawo gida,Yana
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 13 Chapter of 35