Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
10 / 10
Allah kar ka kalli girma na ko alfarma ta ka tursasa yarka akan auren Anwar don in har Bata son shi to zai hakura ne ko da kuwa zai mutu don haka kar kace zaka bawa Anwar yarka don Ni ba zanso hakan ba idan ta na sonshi zanyi murna idan kuwa Bata sonshi zanyi musu fatan ALHERI ne kawai don muna da Matan da muka zaba mishi Ni da uwar shi ya Kuma yi Mana biyayya to yanzu ne yaga wadda hankalin shi ya kwanta da ita itace yarka shiyasa zanyi mishi Alfarmar aurenta idan har Allah yayi wannan shine makasudin zuwana. AK yayi shiru kanshi akasa Yana nuna girmama wa ga Mr President inda yaji yayi na am da Anwar ya zamo mijin ummita don tarbiyar shi tana burgeshi tamkar ba Dan wani ba Kuma atsari ma yasan ummita zata so shi don yafi badamasi nesa ba kusa ba .har ga Allah ba don abin duniya yaji Anwar ya kwanta mishi fiye da badamasi ba sai don ya zabawa Yar shi miji na gari Amma ko shi din ummita zatace Bata so zai bawa Mr President din hakuri yaro ya nema agaba Ya dago kanshi Yana duban Mr President "Sir Babu matsala Anwar Nima Dana ne zanso ummita ta karbi auren shi duk da nasan Bata da matsala da nace ta karba zata karba Amma a turo Mata Anwar su gana su Kuma daidaita idan da Rabo Amma daga gareni ma Zan iya cewa na bawa Anwar auren ummita sai fa idan Allah ne Bai kaddaro hakan ba. Mr President yayi murmushi "Nagode sosai abdulkarim da goyon bayan da kabani Zan Kuma turo Anwar yazo su gaisa fatan Ubangiji yasa ALHERI zamu hada Da haka sukayi sallama yayi mishi rakiya har wurin motar shi sai ga kyauta ta girma anyi mishi Amma yace ba zai karba ba inda aka aje mishi motar ta fice ta barshi Baki sake Dole ya karba ya shigo cikin gida Yana fadawa lubabatu yadda sukayi da Mr President Akan son auren ummita Ta dubeshi azabure Cikin wani kallo me bayyana takaici "Shine suka Fara siye imaninka da dukiyar su? Ta fada Yana nuna kudin da hannunta abinda ya kona mishi Rai ba kadan ba ya dubeta cikin mamaki "Nayi Zaton ko wani ya fada Miki haka Zaki karyata lubabatu in siyar da yancin ya ta Akan kudi kike nufi ? "Ba Zan ma karyata ba abdulkarim don nasan talauci Babu abinda baya sawa ba zai zamo abin mamaki ba don ka siyar da mutuncin yarka akan kudi da abin duniya ba..... 'sai dai kasani Nima inada hakki akan ummita don haka ban yarda ba ba Kuma Zan yarda ba. Idan har kaci kudin su saboda aurenta to ka kwana da Shirin biyansu. Yaji wani yaji yaji Yana lullube kwayar idon shi Wai don ya talauce ne lubabatu ke son kece rigar mutuncin shi ne kokuwa akwai abinda yayi Mata Wanda ya fusata ta har take mishi wannan dibar albarkar? Ganin idan yace zai biye Mata Kan batun to rayuka ne kawai zasu baci sai ya fito daga dakin nata hakki dai da take magana nata ya Bata tunda ya sanar da ita Yana Duke Yana faman wankin kayan su Mubarak ummita ta shigo da sauri ta aje takardun ta "Abba da Ranar Nan kake wanki? To kawo na karasa maka Ta fada tana kwabe hijabinta Yayi murmushi "Jeki huta kici abinci ummita ai na kusa karasa wa Bayan ta nutsune ya ke sanar da ita "Ummita an sake zuwa da kokon barar neman AUREN ki Ni Kuma nayi alkawarin ba Zan taba matsa Miki Akan aure ba sai Wanda yayi Miki don haka Yaya kike gani? Ta dukar da kanta kasa "Abba na baka zabi duk Wanda ka bincika kaga tarbiyar shi da dabi un shi sunyi maka Wallahi zanyi biyayya duk mijin da ka zaba min Zan karbe shi don nasan ba zaka taba cutar Dani ba . Yayi murmushi "Allah yayi Miki albarka ummita idan har hakane abinda Kika fada to na yarda da tarbiyar Anwar Kuma zai zamo Miki miji abin alfahari don haka na yaba dashi da tarbiyar shi Amma shima zaizo kuga juna shima idan Kinga bai kwanta Miki ba ki sanar Dani kinji ko? Ta amsa da to Abba ..... Lubabatu dake tsaye kansu ta maganta "Kar fa kayi kokarin tabbatar da wanna maganar abdulkarim don na rantse maka da Allah ba Zan taba Bari ka kafa jari hujja da diyata ba don ba Zan Bari ta Rayu cikin Rashin yanci ba................... An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 10 of 10