Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 10
garkar suga babu rami deeny kuwa ya fara tsurewa dan ya sare ganin ba'a gane karkar ba. a haka suje wannan yace inaga wacan ce su kara gaba yace la na tuna wacan ce wllh. sai da ya musu haka wajan sau 15 sannan suka ce kai zamu ci uban ka fa ya zaka raina muna wayyo kaita sako mu cikin daji. sai daya ya juya baya yaga baya hango titi balle motar su. yace kan uba. ku duba baya. suka waiga suma sunyi mama kin nisan da,sukayo. daya ya falle deeny da mari yace dan uban ka dama karya kake. deeny yana sheshekar kuka yace wllh yallabai ba karya nake ba. can deeny ya daga kai yaga wata garka can makekiya. yace yallabai wllh kaga garkar can.suka ce lalai ka raina mana wayoo wajan sau ashirin fa kenan kana muna haka. amma karka ce mun kware ka da sharadi. kaga daga nan zuwa garkar can da ka nuna yanzu da nisa ko. deeny yace haka ne. police din wanda shine babba a cikin yan sandan yace. to idan muka je mukaga ba haka bane. wllh ka kuka da kanka dan wllh sai mun zanee ka kuma kayi tsallan kwadi tundaga wajan har nan. deeny gaban shi na faduwa yace naji. na yarda. suka kama hanya suka nufi garkar deeny kuwa gaban shi sai faduwa yake yaji irin abunda za'a mishi idan ba garkar bace. ai kuwa tun daga nesa ya hangi wani rami irin an cire rogo a wajan ai kuwa ya fara murna. sukuwa hararan shi kawai suke. suka karasa bakin ramin. daya ya kalli deeny yace dan ubanka wannan rogo aka cira a wajan ba ramin da kace kayi bane. deeny duk da yasan ba shi bane amma haka ya rike gardama wai wllh shine. deeny hada hawaye yana tunanin idan aka koma kotu fa hukuncin kisa za'a yanke mai bayan wahalar da zasu bashi a nan. yana cikin tunani. su kuwa har sun aika a ciro bulala. haba sai ganin wanda aka aika nayi ya dawo a guje yana fadin kura kura. su kuwa cewa suke dalla can a wannan dan dajin ya za'a yi a sama kura. deeny kuwa add'au yake allah yasa kurar ce ma ya samu ya tsere. suna juyawa kuwa sukaga wani katan kare kai saika ce kura. karan baki wul da shi ga gashi kamar buzun kare. suka ce wa wanda ya rugo yana cewa kura.,banza ashema kare ne kake cewa kura. bari mu kashe. wannan dan iskan karan. ai kuwa suka nufi karan da kulakan su da nufi suci uban shi. shi kuwa karan ko matsawa baiyi ba. daya yaje maka ma karan kulki kawai sai gani sukayi ya bace bat. ai kuwa ido ya raina fata. shima deeny da yake gefe yana kallo abun ya bashi tsoro dan saida ya razana. suka duba sama ko kasa basuga karan ba. ashe wannan karan mai gonar ne ya tsafa su sunkai su 20 irin su ashe dayan tafiya yayi ya kirawo sauran. ai kuwa. suna tsaye sai ji sukayi wata irin guguwa ta tashi sama……………https://m.facebook.com/groups/1232550283531628 →BANI NA KASHE TABA← PART 16 N@ BIGBOY isah > suna tsaye suka ga irin karnu kan nan sai zubowa kasa suke yi. ai kuwa da yan sanda da deeny duk suka ari ta kare. sai gudu. su kuwa duk karan da ya fado kasa sai ya nufe su da gudun bala'i haka sukai ta tsere a cikin daji gudu kuwa har sunyi sun fara gajiya daga sun waiga baya sai suga wannan karnuka na biye da su da gudu.sunkai mint 30 suna wannan mugun gudu. daba na wasa ba gudun cetan rai sunsan in har suka bari karnukan nan suka kamo su baza su bar ko da kashin su ba. ai kuwa suka hango wani makeken gida. auka nufe shi kuwa suna zuwa suka tura kofar gidan suka ci sa'a ta bude su duka hudun suka afka ciki suka rufo kofar. su basuyi tunanin ko gidan waye bama a cikin dokar daji haka. su officer anji jiki. duk sun yarda hulonan su a cikin gudun nan nasu. kowa ya zauna sai haki suke sai huci. to da suka huta ne fa suka ce ku tashi mu tafi suka tashi ai Wannan dan iskan yaran duk shi yaja wo mana wannan bala'i ai tashi sukayi daya ya kama get din da niyar ya bude ai kuwa ina gamgam take ko motsi bata yi ogan cikin su yace me ke faruwa akace kofa taki buduwa yace baku da hankali gyara nan ya kama get din da kansa yaja yaja kuwa kofa taki buduwa abun ya basu mamaki sukayi sukayi kofar taki buduwa. ido kuwa ya raina fata duk sukayi zuro zuro su basu karasa cikin gidan ba kuma kofa taki budewa. haka suka ce ta fanjama fanjam suka nufi cikin gidan duk su hudun yanzu kowa ta kanshi yake ba maganar sa deeny tsakiya.shi kuwa deeny ba haka ya so ba so yayi ya tsere tun kafin su shigo gidan. to sai dai daga ya juya sai yaga kare ya kusan kama mai kafa. da yaga dai ba wajan tsira shi isa ya biye musu har suka shiga gidan< > acan lagos kuwa aliyu ne ya nema Transfer da yake shima police ne. a cewar shi gwara ya koma gida kano zai fijin dadi. ai kuwa aka bashi Transfer hada hutu ya samu na 1month. ya taho gida kano da murnar shi. su maman deeny ne a tsakar gida da ita da amina matar kawu kenan duk su biyun sunyi jagwam jagwam suna ta tunani gobe idan aka sama matsala za'a yanke wa deeny hukuncin kisa fa. Idan ba'a gaskata zancan saba. sai sukaji sallama da sauri amina ta daga kai da yake tasan mai wannan muryar aliyu suka ga ya shigo ai kuwa murna duk suka amsa slm suka tarye shi sai farin ciki suke sun ma manta da damuwar da suke ciki.. Ni wllh alhj duk jikina yayi sanyi da jin zancan yaran nan wllh gani nake kamar ba zai iya kashe halima ba. maman halima ce ta fadi haka. wai ke wace iri ce toh kin san manufar sa ne kika san ko dama can ba santa yake ba so yake ya sace zuciyar ta daga nan sai ya kaita yayi kudi da ita ko ai mazan yanzu basu da gaskiya duk yan yau darane. ni kuwa nace har kai ko. yaci gaba da cewa ai ba'a gane mugu daga fuska ko daga dabi'arsa. ita dai maman halima bata yarda deeny ya kashe halima ba. Domin tasan irin shakuwar dake tsakanin su har zata kara magana sai ya daga mata hannun yace dakata dan allah. kawai ya tashi ya shige dakin sa. wayar hajiya ta dau kara. tana dubawa taga maman Yazeed ne. ta dauka suka yi gaishe gaishan su. nan maman yazeed take cewa maman halima. gasu nan zuwa.…………… https://m.facebook.com/groups/1232550283531628 mu hadu a whatsapp→ 08096831009 Group bigboy on-line 23.04 13:57 →BANI NA KASHE TABA ← PART 17 @N BIGBOY isah tace gamu nan zamu zo dama shima yazeed din yana da dan aiki da,zai yi a kano din. wannan karan har da abban shi zamu zo. ko dan jin maganar .maman halima tayi murna sosai da jin wannan maganar. tatashi cikin farin ciki ta nufi dakin alhj ta fada mai shima yaji dadi sosai. sbd ya dade bai gana da yayan nashi ba. haka ranar akai ta girke girke da soye soye. da yake shida dan nasa kudi har sunyi musu yawa zance amma duk kudin yazeed alhj bai san inda yake samo su ba yasan dai albashin yazeed bai ko kama kafar kudin da yazeed din ke facaka da su ba. alhj ya tambaye shi ya tambaya har ya gaji amma saidai ya cemai wai kudin salary sa ne da kuma busines da yake dan juyawa da ita.amma alhj bai yarda ba sbd kudin ba na wasa bane kuma lokaci daya kudin akaga sun shigo masa. suna abuja amma a sati sau biyu yake kwana a gida. idan suka ce ina yaje sai yace wai harkar Businesses dinsu ne duka ya koma kano. Misalin karfe hudun yanma anata jiran su maman yazeed amma shiru su alhj sanusi ne da matar sa zaune a parllo suna jiran zuwan su alhj bashir. Ko lfy har ynz basu karaso ba ai yaci ace sun karasa ynz kafin ta rufe baki wayan alhj yayi ring ya dauka alhj bashir ne yace mai suyi hkr baza su sama zuwaba sbd wani aiki da ya taso mai..< >acan kuwa su anne ne suka fito sukaje wajan maman anne. maryam ta gaida ta.ina ta amsa tana zolayar maryam.wai yau ta kwana a bukka. maryam tayi murmushi. anne tace mama ina abun karin su gwaggon mu tafi maryam ta raka ni mu kai musu. maman anne tace toh gashi ku kai musu kuyi sauri ku dawo kuma kuzo ku karya. koko da kosai ne sai tuwo. wai sune wayayu a garin shine kokon aka zuba shi a cikin wani tshohn jog ne ja. cike da koko. sai kosai a wata kula. towo da miya a langa babba da karama. anne ce ta riko kwanan tuwan da miya maryam kuwa ta dau koko da kusa. suka fito suka kama hanyar gidan gwaggo suna tafiya suna hira kamar dama can kawaye ne. fulani kuwa sai kallan su ake ga anne da bakuwa yar bunni. anne kuwa sai bude baki take. tana kallan mutane tana dariya.ita kuwa maryam gaban ta sai faduwa yake ta rasa dalili har sai da ta fadawa anne. anne tace kodai gamuwa da yayan nawa ne ya jawo haka kin san fa yayana kyakyawa ne. maryam murmushi kawai tayi. a zuciyar ta tace haba wa a kauyan nan har akwai wani saurayi da zan so. suka dai ci gaba da tafiya anne sai zuba surutu take. gwaggo ce ta zauna kusa da halima tana cewa ya jikin halima tace wllh da sauki sosai wai ni kuwa har yanzu fa banga jikan naki ba gwaggo. gwaggo tace ai yanzu zaki ganshi kin san yana wajan farauta ne.assalamu alaikum. sukaji ance. suka amsa. halima kuwa dayar muryar taji kamar ta maryam amma da tayi tunanin me zai kawo maryam nan sai kawai ta basar tace ba ita bace. sai ji sukayi ance tsohuwa fito ga kokon ki. kina ina ko dai kin mutu ne. anne ce tace haka. gwaggo daga daki tace ai bazan mutu ba sai kin mutu ynz yara suke fara mutuwa. sannan ne anne ta isa kofar dakin tayi salm ta shiga ita kuwa maryam a waje ta tsaya da kofin koko a hannun ta. yanda taji gaban ta sai kara faduwa yake da ta matsa kusa da dakin. anne ta kalli halima da itama kallan ta take tace. gwaggo bakuwar yar burni mukayi halan. gwaggo tace ke sai kin nuna kauyan cin naki a ko ina ko. anne tace hb tsohuwa ai nima ga kawata yar birni. ta mika hannu daya baya wai ta kamo maryam sai taji bata nan.da sauri ta juya maryam maryma. sai ta sama maryam a kofar daki tsaye.anne tace haba maryam kamar dai ke ma yar fulani ce. zomu shiga mana. kawo kokon.……… https://m.facebook.com/groups/1232550283531628 08096831009 →BANI NA KASHE TABA← PART 18 @N BIGBOY isah tana shiga dakin tayi tsaye tana kallan halima. itama halimar kasa yin motsi tayi ta kurawa maryan ido itama. anne da gwaggo su kuwa duk sun saki baki ganin kallo kallo da ake tsakanin maryam da halima. gwaggo ce tace lafiya ko kun san juna ne. sannan ne maryam ta gane ashe suma su anne suna ganim halima da ta dauka ita kadai ke ganin ta. maryma tace halima wai kece anan me ya kawo.ki nan. halimar ma cewa tayi maryam me kika zo yi nan. maryam ta karasa kusada halima ta zauna a kan gadan da halimar take sannan tace.aunty nayi mamakin ganin ki anan. halima tace hmm kedai bari allah ne yayi da sauran rayuwata ai. nidai tun lokacin da muna tare da dina ya tafi sallah ya barni a mota. ni kuma ina nan a mota nayi zuru zuru sai raba ido nake gani a bakin titi mutane kuma duk an shiga sallah shima deeny tuni yayi alwala ya kabara sallah. basai ganin mota nayi an parka ta a kusa da ni ba wasu karti na gani sun fito da sauri daya ya bude lid din motar dayan kuma ya dauko wani pillow ga duk kan alamo dai cikin wannan pillown akwai guba. cikin hanzari tayi shirin fita ta dayan kofar kawai sai mutum ta gani a tsaye da pillow a hannun sa kafin tayi yin.kurin iho tune ya hada mata baki da hanci ya danne da pillow dayan kuma ya ririke hannun ta kuma ya danne mata kafafu saboda shure shuren da take can sukaji ta yi lakwai bata iya motsi baban naku mugu sai cewa yayi kai kumurci saketa mana bakaga ta mutu ba ko gawar ma kashe ta zakayi.dai dai nan suka kula anyi zaman tahiya a masallaci za'a salam ce ne da sauri suka kukule kofofin motar suka ruga da gudu tasu shi kuma ogan nasu yana ciki yana jiran su aikuwa suna shiga yaja mota . nidai tun daga lokacin ban farka ba sai a nan gidan. gwaggo da anne duk sun tausaya mata. suna tunanin to waye yazo binne ki tace nima dai ban sani ba itama maryam tayi jum kadan sannan itama ta kwashe lbr ta duk ta gaya musu sukayi mamaki sosai. sallam sukaji anyi duk suka amsa. halima kallan saurayin take azuciyar ta tace wannan da alamo shine wanda ya cetoni. ita kuwa maryam kanta a kasa ta kasa dagowa ta kalle shi ma. sakamakwan gaban ta da taji yana faduwa. cewa yayi gwaggo ina kwana ya jikin bakuwar gwaggo ta amsa. tace bakuwa gatanan har ma ta warware har hira muke. anne ce ta durkusa tace yaya isah ina kwana.yace lafiya lau ya mamana. maryam jin anne tace yaya da sauri ta daga kai tana kallan sa taga ita yake kallo shima. ai kuwa a tare suka kauda kai.sakamakon wani mumunan faduwar gaba da sukaji su biyu. wai me hakan ke nufi daga kallan yarinya gabana ya fadi. nida naga yan mata kala kala. iri iri. duk ina kura musu ido amma ban taba jin irin haka ba sai yau isah ne ke fadar hk a zuciyar shi. maryam kanta a kasa tace ina kwana yaya isah ya dan kalle ta sannan yace lafiya kalau yace sis wannan fa ya tambaya annee. annee tace wannan sunan ta maryam jiya muka hadu da ita yan daba sun biyo ta allah ya kawo ta garin mu a dandali muka hadu kuma a gidan mu ta kwana. bayan anyi shiru daga can halima tace yaya ina kwana ya amsa lfy ya karfin jikin tace jiki da sauki. yace to allah ya bada sauki amma baki bani lbr abunda ya faru da ke ba. halima ta kwashe lbr kaff ta fada mai. ya girgiza kai alamon mamaki. sannan kuma anne ta ci gaba da bawa yayanta lbr maryam sai da ta fada mai duk tun daga fitowar maryam daga gida har zuwa sace ta da tserowar da tayi da haduwar su duk ta fada mai komai yayi jum kadan can sai yayi wupp! yace mutum nawa kika ce ya kalli halima tace uku.ya juya kan maryam yace kema uku ko. maryam da kanta ke a kasa ta dago ta kalle shi da kwala kwalan idanon ta masu daukar hankali tacje eh su uku ne. .......... Washhh har naji dadi halima bata mutu ba kufa ???? ." →BANI NA KASHE TABA← Part 19 N@ bigboy isa Yace tabbas mutum daya ne yasa ayi muku wannan aiki domin kuwa la'akari da labarin ko wacce daga cikin ku amma ba wani wanda kukawa laifi kuwa ko wulakan ci ko maka mancin hk duk suka girgiza kai alamun babu yace to alhmdulilah ynz dai tunda allah ya tsalllakar daku ku biyun yanzu abunda yafi shine zamu jira kudan huta kafin mu tatara mu tafi birni can wajan iyayan ku domin kuwa bamu san wane hali suke ciki ba a halin yanzu. Duk wannan zancan da yake yanayi yana satar kallan maryam lokacin nema ya dan gaskata zcyar sa a bisa zargin da yake akan maryam. Gwaggo tace gaskiya ne allah ya maka albarka sannan yace gwaggo ni zan fita ya mike hade da kallan wajan da Maryam ke zaune ai kuwa kamar hadin baki suka hada ido wani zazafan faduwar gaba sukaji a tare cikin su kowane ya rasa daliln haka.nan dai ya fita ya barsu sai hira suke shi kuma ya nufi gidan su wato gidan su anne domin haka yake duk safiya sai yaje ya gaishe da iyayan sa ( hmm iyaye ba abun wasa bane ya kamata mu lura mu kyautata musu wani zaka same shi shi gani yake gaida iyayan sa ma kamar wani zubar da class ne alhalin kuma wannan dabi'ar banza ce bata kirki ba allah yasa mu gane ameen) yaje yayi sallama aka amsa ya kuwa iske su a daki suna hira ya tube takalmi ya shiga dakin ya ce ina kwanan ku suka amsa ya gwaggo inji maman anne yace duk suna lafiya wllh baban yace kaga munyi bakuwa ko eh baba nima dama ina so in gaya muku jiya bayan na fita farauta da dadare sai na biya ta garka to kaiwai sai naga mutum yana rami na dauka barayi ne kawai sai na far masa na bisa ina harbi amna allah bai bani saa na same shi ba ya shiga motanshi ya gudu to ina dawowa wajan kuma sai na iske mutun ashe wai mutum yazo binne wa dana taba kawai sai naga macece lokacin kuma anyi sa'a ashe wai dogwan suma tayi kuma lokacin da naje ta farfado kawai sai na dauke ta na kaita gida ynz dai tana can ta farfado ta sama sauki sosai sudai kawai gyada mai kai suke jin abun sukayi kamar al'mara badan mgnr daga bakinsa take fitowa bama da wanine ke fada musu cewa zasuyi karya ne. yaci gaba da cewa umma kuma wani abun mamakin shine da yarinyar da ta zo nan gidan da kuma wacce na tsinta sun san juna wai kawaye ne ma maman anne ta rike baki tace sarautar allah kenan shine yayi ikon sa a kansu. sannan tace to ai yanzu kamata yayi muje can gidan gwaggonka domin asan mafita domin kuwa iyayansu zasu shiga wani hali. baban anne yace to kuyi gaba nima gani nan zuwa ynz ba irin tashi hankali da kuma fargaba da maman deeny ta shiga ganin har an kwana kuma ba labarin su deeny har yanzu basu dawo ba domin sai zarya take police. su ma haka yan gidan su halima ya daya kenan ita kadai gare ta yanzu idan ta mutu ya zatayi gashi yanzu na daima haihuwa hawaye ne zafafa suka kwaranyo a idanonta can kuma sai naga ta tashi ta bude wardrobe ta dauko hijab tasa ta fito ta ko ina zata oho haka ta fita rai a bace ko ta kan driver bata bi ba domin gani take bata lokaci ne ta fito haka mai gadi ma ko kallo bai isheta ba balle ma ta fada mai inda zata napep naga ta tsaida..... .......... big boy kune 😫🔫 BANI NA KASHE TABA 😫🔫 Na 👑 king boy👑 Part 20 Tana tsayawa ta shiga tace muje nan baya zaka kaini ranta a murtuke… bata zame ko ina ba sai kofar gidan su kawun deeny wato dai wajan mamar deeny ta zo. Tafito ta nufi cikin gidan ganin bata da niyar bashi kudin sa ne yace hjy kudin fa. Jirani haka tace mai ba tare da ta juyo bama. Suna zaune Suna zaune suna jimami sai ji sukayi. Murya kamar daga sama ku fiddo min ya'ta tana hawaye dan allah ku taimaka min ku bani yarinya ta ita kadai na mallaka sai hawaye suka fara zarya gaba daya hankalin su ya tashi bama kamar maman deeny tace ga kujerq zauna mana aa ba zama nazo yi ba nidai kawai ku taimaka min ku fiddo min da di'yata mamar deeny kasa cewa komai tayi daga haka kawai kuka take abubuwa sun mata yawa ko abinci kwanan nan biyu bata iya ci duk ta rame. Aliyu naga ya fito daga dakin sa wanda yana jin duk abunda ke faruwa yazo gaban maman halima ya kalli maman deeny yace wannan ita ce mahaifiyar yarinyar? Kai kawai ta iya daga mai alamun eh ya maida hankalin sa ga matar wacce kuka yaci karfin ta sai sharar hawaye take da hijab dinta ya yi kasa da murya sannan yace inaso ki kwantar da hankalin ki ki saurari abunda zan gaya miki pls ki natsu ya dauko wata kujera ta katako wa ajiye sannan yace zauna ba gardama ta zauna ita da farko da niyar masifa taxo amma harga allah yanda ta iske su suma gidan gaba daya ba wani walwala shi yasa taji duk jikinta yayi sanyi. aliyu yace to da farko inaso ki natsu kiyi tunani sannan zan gaya miki wannan maganganun ne bawai dan baki sani ba aa kawai dan tunatarwa yace ki san cewa komai mukaddari ne daga allah duk abunda ya faru da mutum to daga gare sane alkhari ko makaman cin sa saidai abunda wasun mu basu gane ba shine a lokacin da allah ya sauko da alkhairi ga mutum sai yay ta jin dadi wani ma baya godewa allah domin gani yake kamar wayansa ne ya kawo mai wannan alherin. gaba daya maman deeny da maman halima da kuma ita kanta amina wato maman sa duk sunyi shiru shi kawai suke sauraro. yace to idan kuma allah ya jarabci mutum da wata masifar kuma sai mutu kaga duk ya rikice a nan ne ma zai tuna da allah hmm shi kuma allah zaima wannan abun ne dan ya gwada iya imanin ka..... nandai yata mata nasiha itadai tayi shiru sauraran sa kawai take.yace to ina so ki dauki wannan abun a matsayin kaddara sannan ki dage da addu'a domin addu'a itace maka min mumuni yace ke naki mai sauki ne ma domin ke kin fara cire rai ga yarki domin ance ta mutu ya nuna maman deeny yace kinga maman sa nan itama da shi din da kuma maryam wato kanwarsa duk ba daya daga ciki domin ita maryam tun ranar da abun ya faru ta tafi islamiya bata dawo ba har yau shi ma dini kuma haka domin suma basu dawo ba daga binciken da suka tafi mamar deeny wasu zafafan hawayan ne suka kubuto mata wanda ita kanta hjy khadija wato mamar halima saida ta tausaya mata sannane ma ta san wai maryam bata dawo ba yace ynz abunda za'ayi shine kiyi hakuri ki koma gida kici gaba da addu'a domin lamarin nan sai addu'a dai. jiki ba kwari ta tashi ta musu salama duk a kunyace domin yanda ta shigo musu da fari tana fita da tarar da dan adaidai tar nan inda ta barsa ya fiddo waya sai chat yake abunsa shi kam yama manta da wata yake jira chat yayi dadi ta hau tace mayar dani inda ka dauko ni. yayi mamaki shima yanda yaga matar da farko cike da damuwa ynz kuma gashi ta fito ba kmr dazu ba ya tuka ya maida ita tana sauka bata tsaya tambyar ko nawa ne kudin ba ta zaro 1000 sabuwa dall ta mika mai domin tasan kudin sa baikai hk ba ta wuce zata shiga gida yace hajiya chanjin fa tace ka rike ba tare da ta waiwayo ba dadi ne ya cika shi shi kuma domin riba biyu ga ya huta kuma ga kudin da ko lokacin aiki yake bai isa ace dubu ta shigo ba yaja adaidaitar sa yayi gaba tana shiga gidan sai wayarta tadau kara tana dubawa taga hjy saratu ce take kira ta dauka suka gaisa nan take tmbyar ya lbrn halima tace abundai gashinan sai addu'a nan hjj saratu take gaya mata suyi hkr da basu sama zuwa ba amma ga yazeed nan zuwa yau yau.... ........... A CAN BANGARAN SU DEENY KUWA......... ISAHN ♥ KUNE 😫🔫 BANI NA KASHE TABA 😫🔫 Na 👑 king boy👑 Part 21 . CIKIN gidan suka nufa suna waige waige yana yin gidan ya fara furgita su domin ko motsin basuji ba wata kofa ce katuwa wacce akayi da zinary a sukazo kofar dakin sukayi curus kowa yaki yarda ya fara taba kofar ogan ya kalli deeny da jikin sa ke rawa yace kai zo ka bude mana kofar nan dan uban ka. Haka ya taho yana makyarkyata kamar ya kama kamar kuma yaki saidai yasan ba yanda ya iya Wata zuciyar tace mai kai koma fa kun kubuta daga gidan nan to ba makawa kashe ka za'a yi domin banda wannan hujar ba wata tunda anzo ba'aga ko ramin ba kaga kuwa ba makawa kashe ka za'ayi sai yaji duk tsoro ma ya fita a ranshi. Ya rufe ido yayi yan addu'o'i sannan ya sa hannu biyu ya tura kofar da yake kofar mai hannu biyu ce kamar get gani sukayi kofar ta bude kai tsaye Suka nufin parllo suka fara salama shiru basuji ko motsi ba hakan yasa suka kutsa kai sukayi cikn. Katan farllo ne tan gameme yasha ado kujeru ne jere birjik a parllan ga kuma can wasu dakuna ba adadi a jere sai kalle kalle sukeyi domin dakin ya hadu sosai durum wuta sukaga

Chapter 3 of 10