Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

d'aga Mata kai saboda irin kukan damuwar da take yi da sauri Husnah ta ri'ko hannunta suna fitowa saida suka shiga mota ta sake kallonta tana cewa "kinga Beelat ki daina kuka tunda baiyi miki komai ba insha Allah bazai kai lafiya ba za'a kamashi zai d'and'ana kud'arsa ta fad'a tana tada mota suka bar wajen Suraj yana tsaye a bakin titi ya parking da mota yana kallon duk abinda yake faruwa domin tun fitowar Husnah daga gida ya biyota yaga inda zataje sai kuma yaga ta shiga hotel gashi ta fito tare da kawarta tana kuka ko hijab babu a jikinta balle takalmi to meya faru dama suna zuwa ko yau suka fara zuwa meyasa Nabilan take kuka tada mota yayi yana bin bayansu yaga inda zasu yi kuma daga nab amma harsun 6ace masa tsaki yaja yana karya kwana ya shiga titin daya tafi asibitin federal ya nufi gida.

Gudun tashin hankalin dazai faru idan suka je gida yasa Husnah ta wuce gidansu da Nabilah ta kaita har d'aki ta had'a mata ruwa tai wanka ta d'auko Mata kaya ta saka sannan ta hado mata tea mai zafi sosai ta bata tare da zama kusa da ita ganin yadda ta ri'ke cup d'in shayin tayi shiru ta zubawa guri d'aya ido dafata Husnah tai wanda yasa da sauri ta d'ago a firgice tana sauke ajiyar zuciya bata ce komai ba Kai Husnah ta girgiza ranta a'bace tace.

"Beelat ki kwantar da hankalinki insha Allahu babu abinda zai faru shi kuma Sïr Ähmäd da Allah ya tsareki daga cikin sharrin sa ki godewa Allah wallahi bazamu yarda ba sai an dauki mataki a kansa ayau zamuje ki fad'awa Daddy komai abinda ya faru zuwa gobe da safe muje school a shigar da report d'in abinda yai Miki tare dasa hannunki da nawa nayi Miki alkawari zan tayaki a yakeshi iya iyawa ta amma please ki cire damuwar nan dan Allah Beelat".

Kai Nabilah ta d'aga cikin jin d'an sassauci tayi murmushin dole batare datai magana ba ta fara shan tea d'in wanda Husnah taji dad'in hakan da taga tad'an sake harta samu kwarin gwiwar tashi ta d'ebo musu abinci suka ci karshe tana d'an janta da hira tun bata magana harta sake suka fara zance da dariya ta manta abinda ya wuce na wani lokaci kafin ciwon ya sake dawo mata.

Bayan fitar Nabilah a d'akin da'kyar Sir Ahmad ya mi'ke yana ri'ke da hannunsa ya jinjina kai sai kuma ya saki murmushi yana d'aukar kayansa yasa kamar kome bai faru ba ya bar d'akin ya fita zuwa inda motarsa take shima ya shiga ya fice daga hotel d'in yana kiran wayar Danual yaji inda suke yaje ya daukesu shida Nazzi suka bar yankin wajen a hanya Danual ya bashi photon da videos d'in ya gani dariya yayi yana kallon fuskar Nazzi a haka sak Nabilah ba wanda zaice ba ita bace cire fuskar tai tana murmushi tace "aiki ya kammala oga saura cash" ta fad'a harda mi'ka masa hannu dariya yai yana jinjina kai yace "ki jira na dawo cikin hayyacina saina gama cika burina idan na kawo daidai inda nake so zan baku kyautar bazata" ok Sir Nazzi tace daidai sun tsaya ta sauka tana gangarawa inda gidan da take haya yake kafin yayi gaba yana sauke Danual sannan ya wuce kai tsaye ya d'auko wata wayar sabuwa wacce already ya cazata tura videos d'in da photon yayi yana fitowa a motar ya fara tafiya da kafa har yaje bakin gate d'in kofar gidan su Nabilah ya tsaya tare da kwankwasawa bud'e kofa mai gadi yayi yana lekowa ganin mutum tsaye yace.

"Lafiya"?.

Kaiya d'aga yana mi'ka masa wayar hannunsa 'kin kar'ba me gadin yayi sai sake jefo masa tambaya dayai "waye Kai daga Ina me za'ai da wannan wayar"? Sake mi'ka masa yayi yana cewa "idan Alhaji Tajuddeen yazo ka bashi kace ya duba cikin wayar akwai sako an bani na bashi" to mai gadi yace yana karba wani irin shu'umin murmushi Sir Ahmad yayi yana juyawa ya shiga mota daga nan gidansu Sultan ya tafi domin tuntuni ya biya Danual da Nazzi sune suka binciko masa gidansu Nabilah da kuma anguwarsu Sultan din parking yana yana fitowa yayi sa'a kuwa Sultan ma ya fito zai tafi masallaci yayi masa magana tsayawa yai yana kallon sa harya karaso wata wayar ya d'auko irin wancan ya mi'kawa Sultan yana cewa.

"Sako ne aka bani na baka" shima Sultan d'in bai kar'ba ba hannunsa na cikin aljuhun jallabiyarsa yace "sakon mene waye ya aikoka"? Kai Sir Ahmad ya girgiza yana cewa "ba bukatar haka yalla6ai kawai nidai ance min ka duba zaka ga komai" ya fad'a yana tura masa shiru Sultan yayi yana kallon sa zuwa wani lokaci yasa hannu ya kar'ba yana cewa ok ya wuce da kallo Sir Ahmad ya bishi yana fashewa da dariya ya jinjina kai batare da yayi magana ba ya juya ya shiga motarsa yabar anguwar yasan ko yanzu yayi nasara indai wadannan 6angarori biyun suka ga komai.

**Bayan an fito daga masallaci Kai tsaye Sultan gida ya koma yana shiga bedroom cikin 'kaguwa ya bud'e wayar yana kunnawa yaga meye a ciki humm wai tashin hankali wanda ba'a sa masa rana abinda ya gani yaso haukatar masa da kwakwalwa a zabure ya tashi zaune idonsa kamar zai fito waje tsabar firgici da tashin hankalin daya tsinci kansa a ciki da sauri ya murje ido domin gani yake kamar ba gaske bane mafarki yakeyi yana bud'e idon nasa yasake ganin zahiri ne dai ba mafarkin yake ba a susuce ya kashe tare da d'auko wayarsa jikinsa na rawa ya danna kiran Nabilah yaji bata d'aga ba harta katse sake kiranta yayi karo na biyu amma dai ba'a d'aga ba wani irin zazzafan huci ya fitar yana d'aukar wayar a fusace ya fita a gidan kansa na matukar sara masa ya sani bazai iya tu'ka mota ba dan haka da qafa ya tafi gidansu Nabilan ko ganin gabansa baya yi.

A can ya samu mahaifinsa Alhaji Tajuddeen ya kirashi sakamakon abinda shima ya gani bayan ya dawo daga office da dare mai gadi ya bashi mamaki ne ya kama Sultan bai iya cewa komai ba duk maganganun da suke shi yanzu babbar damuwarsa ya had'u da Nabilah yaji me ta aikata wannan dama yaudararsa take you dama ita 'yar iska ce? Wannan shine abinda ke cin ransa fahimtar dayai kamar bata gidan yasa bai tsaya ba ya fita yana sake trying numbern ta amma sai yaji a kashe kaiya jinjina ransa na quna kenan tasani tana ganin kiran nasa ta'ki d'agawa saboda tana tare da wani namijin hummm gida ya koma tare da rufe kansa a bedroom cikin rashin nutsuwa ya kasa zaune ya kasa tsaye sai zaga d'aki yake cikin tsananin damuwar abinda Nabilan ta aikata meyasa zatai masa haka saida aka kusa d'aura musu aure ya gama zurfi a cikin sonta ta zama itace komai nasa sannan zata bayyana masa halinta kaiya jinjina tare da kama guri ya zauna ya had'e kai da gwiwa kawai yayi shiru kansa na juyawa yana jin yadda zuciyarsa ke buguwa da sonta har ji yake kamar ya jawo gobe su had'u da Nabilah a yita ta 'kare.

***
A gidan su Husnah Nabilah ta kwana domin gudun yadda zata koma gida ta fuskanci mahaifin ta gasu suna matsayin manya masu fad'a aji abun kunya ne ace anga 'yarsu a hotel ko hijab babu balle takalmi wannan dalilin yasa ta kasa komawa ta fuskance su sai da safe bayan sunyi wanka Husnah ta dau'ki mota bayan sunyiwa Hajiya Sadiya sallama ta tafi rakata babu abinda gaban Nabilah yake Banda fad'uwa tana fatan Allah yasa labarin zuwanta hotel baikai ga mahaifan nata ba duk da tasan yadda suke sanannu abune mai matukar wahala ace basu ji a bakin wani ba sauke numfashi tai lokacin da suka karaso bakin gate d'in ta kalli Husnah dake shirin horn jiki a sanyaye tace.

"Husnah tsaya daga nan na fita" da mamaki Husnah ta kalleta tana cewa "haba Beelat ya za'ai na ajeki daga nan Kuma idan an tambaye ki inda kika kwana da abinda ya faru waye zaiyi miki sheda"? Runtse ido Nabilah tai jin abinda Husnan tace bata da wani za'bi amma tace "karki damu Husnah hakan ma nagode ba kowane zaiyi min abinda kikai min ba" ta fad'a tana fita a motar domin bata so ta sanya Husnah cikin matsalar da batasan iyakarta ba da kallo Husnah ta bita harta bud'e karamar kofar gate d'in gidan nasu ta shiga kafin ta girgiza kai cikin tausaya mata ta tada mota tana juyawa zuwa gida cike da tsananin damuwa da tunanin halin da Nabilan zata kasance yanzu idan ta shiga ciki tasota bari sun shiga tare ayi komai a gabanta amma tunda Nabilan bata amince ba yasa ta ha'kura saidai ta nai Mata fatan alkhairi.

Jikin Nabilah a sake ta shiga gidan da'kyar take d'aga kafa tsabar yadda jikinta ya matukar mutuwa bata sake tsinkewa ba Saida taga motoci guda biyu a harabar gidansu d'aya ta sheda ta Sultan ce amma d'ayan batasan ta waye ba saidai bazai wuce da mahaifinsa ce Alhaji Mukhtar ba tsayawa tai ta kasa gaba ta kasa baya kusan minti talatiin jin qarar bud'e kofar da akai ne yasa ta d'ago da sauri taga waye ganin a yadda Sultan ya fito a fusace da irin kallon da yake watso Mata yasa jikinta yadau rawa tasan ko ba'a fad'a mata ba wannan abun ya iso musu ko inda take bai sake kallo ba yaje yadau motarsa yana ficewa a gidan wasu kalar baka'ken zafafan hawaye ne suka zubo mata to yanzu ita zatai waye zai fahimta bayan ga wanda take tunanin bazai zargeta ba shine ya fara nuna mata a zahiri wucewa tai tana shiga cikin gidan su uku ta tarar a parlor Alhaji Tajuddeen Hajiya Fatima da kuma mahaifin Sultan Alhaji Mukhtar suna magana sak ta tsaya wanda su Kuma da mamaki suke kallon ta tsakanin jiya da yau harta rame sosai mi'kewa Alhaji Tajuddeen yayi ya nufo inda take yana karasowa ba zato taji saukar mari a fuskarta kafin tayi wani yun'kuri ya sake d'auketa da wani sabon marin da sauri Alhaji Mukhtar ya taso yana janye shi yace.

"Haba Yaya dan Allah kada kadau hukunci a hannunka ka bari ayi bincike bana jin hakan gaskiya ne" ran Alhaji Tajuddeen a 6ace yace "wanne irin binciken zan bari ayi bayan aikin gama ya gama ta 6ata min suna a gari da duniya baki daya bansan cewa Nabilah zata iya watsi da tarbiyyar dana bata ba saida na gani da idona" kai Alhaji Mukhtar ya girgiza yana cewa "dan Allah yaya ka tsaya ka zauna mubi abun a huce a haka babu wanda zai fahimci wani" ya fad'a yana kokarin zaunar dashi da'kyar ya samu ya zauna yana huci itakam Hajiya Fatima kallon Nabilah take da idanunta da yayi jawur tsabar kukan datai daga jiya zuwa yau da al'amarin ya samesu kallon Nabilah wacce ke kuka cikin tashin hankali Alhaji Mukhtar yayi yana cewa.

"Nabilah karaso ki zauna muyi magana shigo kada kiji tsoro babu abunda zai sake miki ina nan" da'kyar Nabilah ta karasa shigowa parlon jikinta na rawa ta samu ta zauna a qasan carpet amma can nesa dasu kallon Alhaji Tajuddeen yayi yana cewa "Yaya gata nan ayi magana muji gaskiya kafin a dau mataki" kai Alhaji Tajuddeen ya girgiza a fusace yace "ba wata magana dazan sake maimaitawa Mukhtar mataki d'aya zan d'auka a kanta shine ta tashi tabar min gida saita tafi cikin duniyar da niyya tunda ta nuna muba iyaye bane tayi watsi da tarbiyyar da muka bata dan haka zama damu baida amfani saidai ta jawo mana cece kuce a gurin mutane" kuka Nabilah ta sake fashewa dashi tana dur'kusawa cikin tashin hankali zatai magana Alhaji Tajuddeen ya daka Mata tsawa yana cewa "ki 6ace min da gani nace ko"? Kai Nabilah ta girgiza tafashshen ruwan hawaye na zuba a idonta tace.

"Dan girman Allah Daddy kayi hakuri ka bani dama na fad'a maka gaskiyar abinda ya faru jiya ne da..........................


D'aga mata hunnu yayi alamar baison ji tare da d'aukar remote yana cewa "ba wata gaskiya da zaki fad'a min iya wacce na gani ma da idona ta isheni hujja" ya karasa maganar yana kunna mata TV yace "ko zaki ce min ba haka bane wannan abinda ya faru baki san komai ba" da'kyar ta d'aga idonta da sukai nauyi cikin fargabar me zata gani ta d'ago tana kallon TV duk zaton ta ko kokawar da Sir Ahmad ya farayi da ita zata gani sai taga abu dabam sa6anin hankalinta innalillahi wa Inna ilaihi raji'un wata muguwar zabura tai sakamakon ganin fuskarta tar ake nunawa a TV gasu nan a d'akin kamar wanda Sir Ahmad ya kaita amma ba gurin bane batasan nan ba bata ta'ba zuwa ba gatanan a kwance jikinta babu ko d'an kunne tsirara ga wani namiji tsaye ya rufe fuskarsa dan kada a ganeshi Kuma ba Sir Ahmad bane yana ta d'aukarta photo da video bayan ya gama ya fita da sai gashi ya dawo tare da wani namijin sun zo suka taru a kanta duk su biyu kowa da gurin daya nufa suna making sex da ita wani irin ihu ta fasa na tsantsan razana tana d'ora hannu aka ta fashe da wani mayataccen kuka tana girgiza kai muryarta kamar zai fashe ta had'e hannuwanta tana cewa.

"Wallahi tallahi Daddy bani bace wallahii bansan komai ba na shiga uku na lalace waye yayi nufin qulla min sharri ya Allah kana gani idan har nasan wani abu game da wannan al'amarin kar Allah ya kaini sallar azhar innalillahi wa Inna ilaihi raji'un 😭".

Kashe TV Alhaji Tajuddeen yayi tare da dafe kansa ya runtse ido cikin wani irin mawuyacin yanayi kansa ne gabadaya ya kulle gashi a zahiri cikin TV itace yanzu kuma taga abun itama hankalinta ya tashi tayi rantsuwa bata san komai ba shiru yayi yana yin xurfi cikin nisan hankali da tunani kafin ya d'ago yana kallon Nabilah yace.

"Nabilan zonan".

Tsoro ne ta sake rufe Nabilah lokacin da yace taje tuna marukan daya sharara mata yanzu yasa ta kasa koda motsi harya sake magana a karo na biyu "Nabilah nace kizo nan" mi'kewa tai jikinta na mugun rawa da tsoron abinda zai sake mata da'kyar ta karasa inda yake tana tsayawa a nesa dashi ri'ko hannunta yayi wanda cikin raunin murya tace.

"Wallahi tallahi Daddy bansan komai ba nasan koda ace kowa zai qaryata ni kai zaka gasgata ni sharri akai min don a 6ata min suna dan Allah Daddy ka yafe min" ta karasa maganar cikin kuka me tsanani Allah sarki wani irin mugun tausayin tane ya rufe Alhaji Tajuddeen baisan lokacin daya sata a jikinsa ba yana rungume ta domin koma menene hannunka baya ru6ewa ka yanke ka jefar koda da gaske Nabilan ce babu yadda ya iya dole yad'au ha'kuri shafa bayanta yake a hankali cikin lallahi yace.

"Ok Nabilah na fahimta shikenan kiyi shiru haka babu komai zamu bincika koma waye yake neman 'bata miki suna a gari saiya fuskanci mugun hukunci wanda sai yayi dana sanin zuwansa duniya".

"Nifa Yaya abinda na kasa ganewa waye yayi mana wannan d'anyan aikin meyasa yayi hakan wanne lefi Nabilah tayi masa wanda zai tozarta ta har haka"?.

"Humm Nima ban sani ba mukhtar tunda Nabilah ba mu'amala take da wasu samarin ba balle nace ta samu sa6ani da wani" mayar da hankalinsa kan Nabilah yayi wacce idonta yayi jawur Kuma har lokacin bata daina kukan ba'kin ciki da damuwa ba yace "Nabilah kiyi shiru haka ina so zan tambaye ki ko da akwai wanda kuke soyayya dashi a waje ban sani ba"? Ya fad'a yana 'kureta da kallo da sauri ta girgiza tana cewa "wallahi Allah Daddy ka yarda dani bana kula kowa koda school naje muna tare da Husnah ko friend ban ta'ba yi da namiji ba har nayi graduate".

"Ok na gane amma kwata-kwata babu wani wanda kika ta'ba samun matsala dashi ko kuka samu rashin fahimtar juna ki nutsu ki tuna sosai ba gaggawa muke ba ki fada mana a sannu zamubi komai".

Shiru Nabilah tai tana tunani a ranta to ita dawa take mu'amala wa take kulawa a iya saninta banda Sultan babu namijin da take magana dashi can wata zuciyar tace mata "Nabilah kin manta jiya Sir Ahmad yazo har kofar gida ya yaudare ki sannan ya daukeki da nufin lalata miki rayuwa Allah ya ku6utar dake tabbas ko shakka babu idan ma ba Sir Ahmad ne yayi mata haka ba to akwai had'in bakinsa iya abubuwan daya nuna mata nason ta bashi had'in kai sun isheta hujja,, tuna hakan datai yasa lokaci guda taji zuciyarta ta buga da mugun 'karfi harda zabura tayi kamar wanda aka daka mata tsawa a razane ta d'ago tana girgiza ta kuma fashewa da kuka tana cewa.

"Daddy ina zargin mutum d'aya da aikata min wannan sharrin domin ya soni yaso aurena na'ki amince masa yabi hanyoyi da dama yaga ban biye masa ba kuma shine yazo kofar gidan nan jiya bansan a gurin wa ya samu number ta ya kirana cewa dan Allah na fito zaiyi min Allah ya sanya alkhairi kuma akwai maganar da yake son fad'a min da farko na'ki fita yayita min magiya da hadani da Allah sannan na fita inda yake" shiru tai tana jan wani irin numfashi domin tunanin a yadda zasu d'au maganar gashi da zata fita kuskuren datai bata sanar da Hajiya Fatima ba..........

"Nabilah".

Taji saukar muryar Alhaji Tajuddeen d'agowa tai hawaye shar yana zuba kallonta yake cike da fargaba shima zuciyarsa tana mugun harbawa tunda yaji ta soma maganar wani namiji ya tabbata tofa akwai abinda ya faru Allah yasa ba wani abu yayi Mata na 6atar da hankali ba yayi amfani da hakan ya dau'ki wancan videos d'in da photon subahanallah shine abinda ya fad'a a fili tare da rufe ido ya kuma bud'ewa kanta ya cigaba.

"Nabilah dama kina kula wani namiji a school waye kumà sir Ahmad a ina yake d'an waye shi"?.

Lokaci guda ya jero mata tambayar sunkuyar dakai tayi muryarta na rawa tace "lecturer mune".

"Dama kin sanshi ya sanki ne kuna mu'amala dashi"?.

Da sauri ta girgiza kai tana cewa "a'a wallahi ko kulashi bana yi idan yayi min magana ko Husnah zatai min sheda wallahi ba ruwana dashi kawai yace yana sona na fad'a masa akwai wanda zan aura ya rabu dashi ya'ki".

"Ok mubar wannan maganar fad'a min da yazo kofar gidan nan d'in bayan kin fita meya faru me yace miki sannan taya kike tunanin zan yarda bayan baki kwana a gida ba jiya a Ina kika kwana"?.

Jikin Nabilah ne ya dau'ki sabuwar rawa da tsuma tsoro yana lullu'be ta da'kyar tace "dana fita cewa yayi na shiga motarsa muje ya sai mun wedding gown nace masa a'a na gode sai yace akwai maganar da zamuyi dashi idan munje can yanzu zan dawo dake nan ma ban amince masa ba...................


Shiru tai tare da d'agowa tana kallon Alhaji Tajuddeen wanda ya d'aga kai yana cewa "Ina jinki fad'a min meya faru" kuka Nabilah ta saki cikin damuwa da takaici ta soma fad'a masa dukkan abinda ya faru tsakanin ta da Sir Ahmad da kuma zuwan da Husnah tai ta d'auketa zuwa gidansu ta d'ora da cewa "dan Allah Daddy ka yafe ni wallahi tsoron irin tashin hankalin da zan zo gida na tarar yasa na kasa dawowa gida jiya ban kwana a gidansu Husnah da wata niyya ba sannan ban amince sir Ahmad ya yaudare ni ya samu nasara a kaina ba kayi hakuri Daddy" ta karasa maganar tana kneeldown a gabansa tare da had'e hannuwanta guri d'aya alamar neman yafiya kai Alhaji Tajuddeen ya jinjina yana cewa.

"Kin tabbata haka ne abinda ya faru tsakanin ku babu son ranki a ciki dole ya d'auke ki"?.

"Eh Daddy wallahi babu yarda ta".

'Ok shikenan a wacce anguwa yake da zama"?.

Kai Nabilah ta girgiza tana cewa "ban sani ba Daddy kawai a iya makaranta nake ganinsa Kuma dama tare damu zai bar school d'in shima zai koma state dinsut".

"Ba d'an nan garin bane"?.

"Eh ba anan haka yake ba yare ne shi sannan bansan ranar dazai tafi ba ko yau ne".

Mi'kewa Alhaji Tajuddeen yayi jin abinda tace ya kalli Mukhtar yana cewa "tashi muje zan shigar da report a baza jami'an tsaro a yau d'in nan sai an nemo shi ba state d'insu ba ko ramin gyare yake wallahi saina fito muje" mi'kewa shima Alhaji Mukhtar d'in yayi suna fita yayim da Nabilah ta tashi daga inda take dur'kushe ta karasa tare da fad'awa jikin Hajiya Fatima ta fashe da sabon kuka shafa bayanta Hajiya Fatima keyi batare datai magana ba domin bata da abun cewa kanta ya gama kullewa da wannan al'amarin fatan ta Allah yasa ayi nasarar kama wannan lecturer d'in gaskiya ta bayyana a fahimci komai.

📝✍️🌻Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë.


See you tomorrow morning tnks for ur supports 🔥 be with me at always my lover's.


Ya cikar cikakku alhamdu ka dayantu kai kad'ai Allah yake so Annabi 💕 yabo zanyiwa baba gashi Kuma ban iya ba bansan Yaya ake ba dan Wanda kaiwa maraba rannan a fadarka rabba yazam madubin ka rabba yarda inmar nasan kana so ya dad'e.

🌹Baya goya marayu mekai dakai ya rayu dakai kan kowa ya wayu dan Kai ka koyar da gayu abinda bai yuwu ya yuwu madarar kyau sai wanda muke so Annabi SAW 💓💯.

10~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Raki'inah.
***

TYPING📲SUN, JAN5/25 10:20AM YUSRAH MUSA ABUBAKAR🤘💯.


💕MÏÑÏSTËR ÄSHRÄF💕


ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta.


In the name of Allah the must benefits and the must merciful ALLAH THE MOST HIGH DOESN'T SLEEP ALLAH THE MOST HIGH IS PURE HE ACCEPT ONLY WHAT IS PURE we love our NABI MUHAMMAD S.A.W💓 (May the blessings and the peace☮️ of Allah be upon him Amin🙏🙏🙏.


©Yusrah Musa Abubakar
yusrahmusa65@gmail.com
°°° YMA °°°
°°° °°°
°°° °°°
°°°


11~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Sajidinah.


💦Yüsëëñ Sïr Äl-ämëëñ çë💦
PG____11&12
Humm duk nisan turin da akaiwa lilo zaije ya dawo inda yake manya maganin karagar 'kasa tun ba'aje ko'ina ba a ranar komai ya kammala dukiya me yawa Alhaji Tajuddeen ya bayar domin yayi matukar fusata da abinda sukaiwa Nabilah tuni aka baza jami'an tsaro wanda gabadaya gari ya zama an rufe lokaci guda yanayin tafiye tafiye ababen hawa suka canza duk abinda ake yi Sir Ahmad bai sani ba yana gidansa inda ya kama haya yana holewa tare da Nazzi Danual ya shiga a gigice yana sanar dashi abinda ke faruwa tare da bashi shawarar a yau suyi gaggawar bakin garin nan kafin hukuma ta damke su sun ta'bo 'yar manya sun d'auko damin daba saukewa, in hankalin Sir Ahmad yayi dubu ya tashi jiki na rawa ya mi'ke ya soma hada kaya yacewa Danual da Nazzi suma suje yanzun nan su d'ebo kayansu subar garin tsautsayi ne yasa bai tafi ba harya d'auko trolley yakai cikin motarsa ya fitar mayar yana mayar dashi ciki yace sai gobe zai tafi maybe tausayin za'a kamashi ne.

Da yake ita 'karya fure take bata 'ya'ya idan har baka da alhakin mutum ya cutar dakai Allah yana saka maka cikin gaggawa tare da Nazzi da Danual suka d'ebo trolleys d'insu suma kamar zasu tashi sama da yake akwai 'yar tafiya tsakanin su yasa suka taho a 'kafa a hanya suna tafe suke sake maimata abinda ya faru a jiyan caraf a kunnen wani jami'i cikin azama ba zato suka ga yasha gabansu tare da nuna musu bindiga alamar su d'aga hannaye a firgice suke kallonsa tare da tsoron Allah yasa baiji maganar da suke ba zubar da akwatunan sukai suna she'kawa a guje rufa musu baya yayi da yake an sanar ko'ina gari fal yake

Please Login or Register in order to submit comment