Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
WANNAN PAGE NAKU NE YAN ALBARKA KU BIYU RAK NA BAWA SHI MOM JANNA NIGER DA FANCY HONEY INA YAN AMANATA? MUM SUHAIL MAMAN NUSAIBAT JAMEELA ASMAU B YUSUF MAMAN ABBA MRS ABDULWAHAB MOMYN ZAHRA. JINJINA DA GODIYA GAREKU ME TARIN YAWA. QUEEN MERMU DA REAL MAMAN WALEEDA NA CILLO MUKU GAISUWATA. Cikin garin Kd suka shugo Sardauna ya ja numfashi tare da cewa uhmmm City kinji wani kamshin dadi?Har weather ya canja wow what a nice weather ai komai daban ne ba irin kasar Koko ba uhmmmmm... Dariya Ramlat tayi tare da cewa Son kai ina wani kamshi anan sai dai wari,ni murna nakeyi zanga Mamita,yau tare zamu kwana da Mami, Mamita dai ba wani Maminki,kije wajen Late Gwaggo mirgayyya itace Maminki yarinya,wai Babar Idrisa da ta Dade da rasuwa yake tsokanarta, Fushi tayi tare da yin banza dashi,ba zato Mami taji sallamar gudan jininta Sardauna Ramlat na binsa a baya, Baba me aiki tana kitchen suka shigo,Ramlat sai kalle kalle takeyi yanda komai na gidan an canja sabo latest shi kanshi gidan kamar ba shi ba haka Sardauna ya maida gidan abin kallo da birgewa. Jikin Mami ta fada tana murna harda cire dankwali da mayafi ta jefar dasu a wajen,Sardauna yace a'a dauke abinki malama nan ba gidan Kazami bane ya zaki tara mana kaya a nan?kuma ki daga mata cinya, Baza ta dauke ba cewar Mami sarkin iyayi kai kake shara da mopping? Mami nine fa?ae kai din,to daga mata cinya Malama,Ramlat taki tashi,ya janyeta shi ma ya kwanta,Mami kin ganshi ko,Mami tace zo kema ki kwanta a nan,haka Ramlat itama tasa kanta daya cinyar Sardauna kansa na dayar,kansu ya jone da juna ta tsakiya Ramlat ta tura kansa da nata wannan katon kan naki ki daina buga min shi,Ai kanka yafi nawa girma,karfa Ku balla min kafa wannan shure shuren da kukeyi Ku tashi gaskiya, Mikewa Sardauna yayi tare da shigewa Bedroom abinsa,Ramlat ma dakinta ta shiga bayan sun danyi hira da Mami ta gaishe da Baba, Mami tace Ina Hafsatu da Baban naki? Ramlat tace suna lfy Amma sai da ta kwashe komai ta fadawa Mami,Mami harda kuka tace na rasa me yake damun wannan yarinya,itama Ramlat Kuka takeyi,Mami tace ina jin Maganin Hausa zan mata wlh na gaji,Bari ko bata gida nan da yan kwanaki zan je duk inda take zuwa sai ta daina da yardar Allah Yaran nan so suke ciwon zucuya ya kamani su huta,kin san shekaran jiya Baban Sardauna yazo nan?ban san ya akayi ba sai ganinsa nayi da mutane jimgin,ya bani hakuri sosai har kwana yayi a gidan nan,ni dama na dade da yafe musu yaushe zaka wani rike yaronka a rai, Wai ashe Baban Naufal abokinsa ne da suka hadu a airport shine ya fada masa inda nake,yanzu Sardauna yake son gani daga nan wai ya kaishi cikin yan uwansa suga juna, Ramlat tace kinsan kuma Ya Sardauna da kyar zai yarda yaje domin yayi fushi da yawa sai dai ki lallabashi ko zai yarda Mami. Nasan bazai je ba shi yasa da ya tafi wajenki muna waya ban fada masa ba sam. Wanka sukayi da Sallah tare da fitowa cin abinci,Mami ta kalli Ramlat tace Ramlat wannan girma da kikayi na lafiya ne kuwa kin ciko kalli fatarki ko cikine zanga yayan jika? Dariya Ramlat tayi tace Mami babu komai fa,idan ya fito ai zamu gani,Baba da ke fitowa daga kitchen tace nima kamar haka naso na hango a jikinta, Sardauna yana jinsu kunya ta lullubeshi yanzu shi har ya isa yin ciki,shuru yayi sai ma jawo waya da yayi yana latsawa kamar Bai San me suke cewa ba, Mami ce ta make hannunsa kaga yaro ana masa magana ya share mutane kunyar uban me zaka ji sanda kayi auren da wa kayi shawara?wata kunyace gareka. Ramlat ta tuntsure da dariya tare da cewa Sardauna dan Allah ai ba komai ko murmushi ya saki kawai ya kara share zancen,Mami da fada tace lallai ka rainani ko? Sardauna cike da shagwaba yace to Mami ni me zan mik?ku tsofaffi komai sai kunyi surutunsa bakwa jin kunya idan ya fito zaku gani ai.yaushe wannan yarinyar ta Isa haihuwa, Ramlat da Sauri tace Yara dai,tana fada tayi sauri ta durkusa kasan dining ta buya ciki tana Dukan kafar Sardauna da hannu, Mami tace yanzu na gane kan magana ashe dai akwai cikin gashi Ramlat har buya takeyi tana kunya,fara kula zanyi dake shi yasa kika ji na tambaya,da sauri Ramlat ta fito tace wlh Mami ba komai jin dadine ya ratsani kawai dan baki san yanda jikanki yake bani kudi ba ina schl kullum dadi nake ci,dariya su Mami suka yi gaba daya banda Sardauna wanda yayi shuru yana fushi ko magana baya yi ya wani rumtse ido yana jin dacin yanda Ramlat tace masa yaro yanzu,gashi kofar a kulle take bare ya nuna mata ya girma. Kallonsa tayi ta kama kunnensa tare da masa Rada a kunne nice nace ma yaro?kansa ya daga kamar yaron kuwa yana narkewa, Lallai nayi laifi,tsokanar ka nakeyi ni na Isa ai kai Babban mutum ne,indai kaji nace ma yaro daga yau kawai tsokanarka nakeyi kaji? Kai kawai ya daga mata yana ayyana irin mugunta da zai mata Amma a fuska bai nuna ba sai ma kara shagwabewa da yayi, Tashi yayi tare da nufar dakinsa,kayan dinning ta kwashe ta maida kitchen sannan ta wuce dakinta tare da yin wanka tayi shirin bacci dakin Sardauna ta nufa da flask na ruwan zafi guda biyu daya tea din Sardauna yasha kayan kamshi,daya kuma ruwan zafinta na gayyen magariya da take tsarki dashi, Sardauna ana jikin Mirror yana fesa turaruka cikin shirinsa na bacci, Tea ta zuba masa ya amsa tare da cewa thank u yana kare mata kallo yanda tayi matukar kyau cikin rigar baccin fara yar guntuwa tare da kurbar tea dinsa, Juya baya na gani kamar wani abu a bayan rigar ki,da Sauri ta juya masa shi kuwa dama Hips zai gani sai da ya dade yana kalla ya girgiza kai yace uhmmm Naga wannan juyo gaban mu gani rigar nan kamar ma bata da kyau,Ramlat tace kai tana da kyau dinta fa kamar yarinya, ae ina tunanin haka mene a waccan flask din tace ruwan tsarki ne, Miko min shi nan na gani,Ramlat ta mika masa tana dan Allah karka zubar,aiko ko Saurarar ta baiyi ba ya shiga toilet ya zubar gaba daya ya kawo mata flask tare da cewa maida shi kitchen idan zakiyi tsarkinki kiyi da empty ruwan zafi sai kofar taki budewa sai kace ban hanaki wannan shirmen ba. Kin daukewa tayi ta maida kitchen dauka ki maida kitchen kar ki bari na tashi,tana Kukan shagwaba ta dauka ta kai tana dawowa tace yau ba Kaza?,babu sai ta jikinki,Baza ki kara ci ba sai naci tawa wacce kika dinga cin tun aurenmu. Ya Sardauna Zo na ma kitso Allah gashinka zaiyi kitso,Sardauna yace yi min to Amma gobe zaki wareshi idan na tsokani Mami,kin san na girma fa kar yarana su rainani nan gaba. Kasa ya koma ya zauna Ramlat ta dauko kayan kitsonta ta fara Yiwa Sardauna kitso gashin nasa da santsi ma da kyar take iya rikewa,tana farawa Sardauna bacci ya kwasheshi kansa Saman cinyarta Tana yi tana gyangyandi ko kamuwa gashin bayayi kasancewar na maza ne kuma nasa me santsi ne sosai, Sakin gashin tayi ta kwanta ta baya tana kallon sama,Sardauna yana zaune kansa a cinyarta yana bacci itama bacci ya kwashe ta,sai can dare ta farka ta ganta saman Bed jikin Mijinta sai dai shine ya farka ya gyara musu kwanciya,Alwala tayi tare da sallar Nafeela ta koma ta kwanta. Washe gari basu fito ba sai 12pm Ramlat ce ta fito ta cakare cikin wata shadda pupple tayi kyau sosai tasha Daurin yan gayu na gogaggun mata, Mami dariya tayi tare da cewa Ramlat wannan dauri haka kamar rainon cikin tasha,Dariya Ramlat tayi tare da cewa mijinki nayiwa ya gani yau sai ba da ladan daurin nan. Lallai naga Alama ai yanzu ya fita kina daki kina ta kwalliya,yace na fada miki zai dawo yanzun ki masa farfesun kifi,to cewar Ramlat,Mami ina Baba na gaisheta?taje Makwafta ta'aziyya anyi rasuwa. Mikewa tayi tare da shiga kitchen din ba bata lokaci ta shirya Farfesun kifinta,ta fito tare da gyara dakin Sardauna fes yana kyalli ko ina da kamshi,kayan sa ta tattaro ta bawa me wanki,Inner wears kuma tasa a washing machine din ta wanke masa ta busar dasu sannan ta gogesu tare da shirya masa su a inda ya dace, Mami na Palo sai ga Baban Sardauna Alhaji Kabiru Fakas ya zo cikin shiga ta Alfarma tare da guards sun cika palon sai gaisuwa suke kwasa wajen Mami,umarni ya basu da su basu waje, Sosai ya duka har kasa ya gai da Mami,Cikin fara'a ta amsa masa tana sa masa Albarka, Mami kan maganar mu ce dai na dawo pls Mami kiyi hakuri mu koma Abuja gaba daya abinda ya faru ya wuce Dan Allah Mami,yan Uwansa su sanshi suma ya sansu. Mami tace indai Sardauna ne bazai bi ka ba wlh ba karamin sa'a za ayi ba yaron da Bai sanku ba sai da ya girma har yayi aure zaku zo kuce mu koma,da ai mantawa kukayi damu Ku ga masu kudi duniya ta samu, Allah Mami ba irin neman da bamuyi miki ba bamu sameku ba,har muka koma Ghana da Zama wani business ya kaini har 3yrs daga nan na koma Canada a can Allah ya kara bamu wasu yaran su Uku maza biyu mace daya,wanda yake bin Sardaunan naki Namiji ne shima ya girma sosai, Da Mace sai auta namiji ne shima sunyi girma.daga nan bamu kara haihuwa ba har yau,nayi niyyar kara aure ko dan na haihu da yawa amma yarinyar bamu dai daita ba,sai jiya ma na ganta da wani a mota hanyar Zaria. Mami tace wannan matsalarku ce Ba tamu ba Sardauna ba inda zaije baya neman komai a wajenku Allah ya rufa mana asiri kuyi rayuwarku a Abuja mu muna nan,ko Ku koma inda yafi Canada ma Ku zauna,Kabiru sabo da baka da kirki Ashe Hafsatu ma fada kayi da ita kace karta kara zuwa gidanka sabo da rashin zumunci irin naka,to Allah bai hanata rayuwa ba,dan ta daina zuwa gidanka sai me, gashi har yau tana rayuwa,ashe da ace bani da rai da baza ka iya rike min Hafsatu ba,baza ka iya tallafa mata ba,kana gani tana garari wato matarka tafi kowa a wajenka wlh ka kiyayeni,yanzu Danka ya girma kaga Allah bai baka da yawa ba ka dawo zaka maida mu, wa zaka yiwa wayo,Sardauna ne Babba idan sun matsu suzo su ganshi ban hanasu ba amma bazai je ba, Fakas sai lallashin Mami yakeyi yana bata hakuri amma taki yarda,sai hakura yayi sannan yace Mami,ko ruwa baza ki bani ba to? Ramlat ta kwalawa kira tare da cewa kawo Ruwa wa bako,Ramlat dake labe tana Jin hirar su Mami ta gane mutumin dama kuwa Ashe shi dinne Baban Sardauna, Lemo kala biyu tasa da ruwa Eva,sai ta hado masa da Farfesun kifin da tayi ta fito cikin nutsuwa, Fakas sai kallonta yakeyi tabbas itace,bata nuna komai ba ta ajiye gabansa tare da durkusawa ta gaisheshi cike da ladabi, Da murmushi ya Amsa yana kalonta yace Mami wannan ai na Santa a Zaria,tace matar danka ce dai,rashin zumuncinka yasa baka Santa ba amma dangin matarka ai ka sansu gaba daya Wannan yar gidan Hafsatu kanwarkace ce,itace kuma matar Sardauna, Nan take ran Alhaji Kabiru Fakas yayi baki sosai Baban Ramlat matsiyaci talaka za a hada dansa aure da ita,salon su Haifa masa jikoki irin Idrisa yan shaye shaye. shi da ya masa tana din yar gidan wani kusa a Ghana shahararren me kudi,wanda shugaban kasa ne zai daura aure wanda duniya kaf zata San dansa Sardauna yayi aure,social media a watsa tare da yin biki a Dubai,ya gama tsarinsa da planning komai amma yaji har an masa aure yana yaro haka an kashe masa rayuwa da wuri,kuma abin haushi ko a sanar musu a matsayinsu na iyaye. Kuma abin takaicinma yar Idrisa karshen Talauci duk da cewa yar gidan yar uwarsa ce amma shi Sam baya kaunar Ubanta, Shi da ya gama buri za a tafka shagali yanzu ma maybe ba Lallai yarinyar abokin nasa taso Zama da kishiya ba,yanzu ya zaiyi a saki Ramlat ne ko ya kara auren Madeenat na kece raini wanda duniya zata kara saninsa yayi suna ya kara shahara dole. (Madeenat Ishaku Yaro baka San Talauci ba)taken Abbansu Yaro baka San Talauci ba,Yan Ghana ne asalinsu ba musulmai bane daga baya suka musulunta,a turai sukayi rayuwarsu kaf, Madeenat yarinyace da ba ruwanta me hankali kuma nutsatsiya sai abinda akace tayi takeyi kuma kyakyawa ce ba laifi,tana da tarin Ilmi da addini bata da makusa ta ko ina, Tuni Dama Baban Sardauna ya Sanarwa ubanta yana nemawa dansa Auren Madeenat,Yaro baka San Talauci ba kuwa mutumin kirki ne da zuciya daya ya aminci ba da wata manufa ba sabanin Kabiru Fakas, Su Madeenat shirye suke ko yaushe ayi zancen auren basu da matsala su. Sardauna ne ya shigo dauke da Sallama a bakinsa,Babansa ya gani a zaune a Palo kusa da Mami Shi dama baiyi Mamaki ba domin yana ganinsa a news da pics, Ko kallon inda Kabiru yake Sardauna baiyi ba sai Mami da yacewa Sannu da gida Mami ina Ramlat?Mami tace dan Albarka ka dawo tana kitchen, Hanyar kitchen yayi,Kabiru yana ta faman kallon dan nasa farin ciki na ratsashi yanda yaga Sardauna kato ya girma harda saje da gemu kamar dan Uwansa na gida, Amma Sardauna duk yafi yaransa na gida kyau,ga iya daukan wanka duk da cewa suma hakan take amma Sardauna daban ne,su da suka taso ma a Turai. Mami kina gani ko kallona baiyi ba fa?Mami tace ah kai ka kawo kanka ni na saku baku raineshi kun shaku dashi ba,ai duk wanda Bai shaku da dansa ba,bashi ya raineshi ba Bai San komai nasa ba ci Sha sutura,ilmi Bai ma sanshi fuska da fuska ba to dama wlh yaron bazai taba sonsa ba bazai shaku dashi ba Umarninka ma ko tsinewa Sardauna zakayi bazai bi ba,n a sanka farin sani Kabiru kana da wata manufa kan Sardauna kuma ko kaffara bazanyi ba wlh Sardauna bazai maka biyayya ba zaka gani kuma. Sabo da a wajensa Ku da mutanen kwararo daya kuke Bai sanka ba baka sanshi ba kaga kuwa kai da wanda suka hadu a tasha daya kuke wannan matar taka ba matar kirki bace har ta kasa shayar da danta ta raineshi ta bashi tarbiya ai naso ace wlh Allah bai kara baku haihuwa ba naga yanda zakuyi ba yara. Mami dan Allah kiyi hakuri ki daina fadan haka dan Allah ki yafe mana itama zata zo ta nemi gafara,kar tazo Bana nemanta munafuka ko tazo baza taga Sardauna ba. Farfesunsa yaci da lemo ya koshi sannan yaci gaba da lallashin Mami,Mami tace bari kaji ni bazan taba lallashin Sardauna ba idan sun Matsu suzo su ganshi yaro Allah ya ya hore masa yanda kake gani shi yake mana komai wanda yafi irunku masu kudi da ka kasa yi. To Mami a bar zancen kiyi hakuri ni dai zan ci gaba da lallashinsa,wannan matsalarka cewar Mami. Murmushi Kabiru Fakas ya saki ya tuno cewar kudi na Canja komai kudin Mohd nawa suke sai na rufin asiri dan haka zai bashi manyan companies nasa sai ya Zaba ko kala nawa ne,ba kasar da bazai kaishi ba,zai masa kyauta na Alfarma wanda dare daya zai koma me kudi na gaske. Sardauna ne ne ya fito rike da kugun Ramlat,Ramlat kunya ta kamata ta fisge kanta ya jawota yana murmushinsa wanda yasa Kabiru Jin dadi Yana ta kallon dan nasa me matukar kyau samun irinsa sai an tona Magana Fakas yayi baka iya gaisuwa ba Mohd, Sannu An yini lfy?ya aiki Allah ya taimaka a jere ya furta ba tare da ya kalli inda Daddynsa yake ba,Ramlat dake Shan kankana yake ta faman kallo yana cire mata abu fuska,muje ki bani abinci haka ake kula da mijin?ke indai a gidan nan ne kina ganin Mami bakya komai, Dariya tayi a hankali tare da sa masa cup din da ta jajjaga kankana da Madara a ciki ya shanye tare da cewa dole kiyi kiba ai. Je ki shirya anjima zamu fita unguwa,dadi taji tace Allah kaimu,Sardauna sabo da ya nunawa mahaifinsa shima fa ya girma da kudinsa wajen Mami ya karasa tare da Zaro bundle na 1k Dubu Dari ya mika mata gashi Mami ki a ajiye cikin wancen sabo da lalurar gida ko matsala zata taso,komai an kawo na abinci,Mami ta karba tare da cewa Allah maka Albarka dan nan, Baba me aiki ce ta fito tana ta faman yiwa Sardauna kirari kamar wani sarki,Kabiru yana jin Kirarin yana dariya Sardaunan Mami ikon Allah fari me farar aniya,Allah yaja zaminka,Ramlat ta kara da kyakyawa na Mami Ranka ya dade me Hadarin Naira a bamu kaji yau gobe muci naman rago,me mace daya daga ni ba kari sai dai a Lahira ko a lahira nice Uwar gida, Shi dai Baban Sardauna dake zaune murmushi yakeyi kawai na wannan kirari kala kala,ga Sardauna yana wani basarwa yana iyayi kamar Sarkin ne da gaske, Ita kanta Ramlat yar Hafsatu kanwarsa ta bashi dariya ga kuma tun farko Allah yasa masa kaunarta haka kawai yaji yana son yarinyar Ashe ma yarsa ce ma shi yasa maybe yake Jin ta a ransa har yace yana sonta gashi tayi kama da yaransa gaba daya. Amma duk da haka baiyi tunanin fasa yiwa Sardauna auren kece raini ba, Kallon Ramlat yayi tare da cewa Ina Hafsatu tana lfy?lfy take kowa,great cewar Fakas. Kudi masu yawa ya ebo tare da mikawa Mami,Mami fafur tace wlh baza ta karba ba yaje da kudinsa basa so Mohd yana musu komai,Sardauna tuni baya palon ma,Haka Fakas ya fita jiki a sanyaye. Ramlat ta matsa gefen Mami tace Mami me yasa kika masa haka?kiyi hakuri ai komai ya wuce,rufe min baki Sha Sha Sha kinsan me ya mana fa zaki min shirme tashi ki tafi inda zaki Bana son Surutu. Yi hakuri Mami ta furta tare da kwanciya a gefenta saman Sofa. Lantan ta gama shiri tsab na tafiya birni neman Sardauna Saurayin ta da take matukar Kauna, Kafin ayi kiran sallah Babarta ta tasheta ta kaimata Markaden wake suna kosan siyarwa,Da asuba tana yin Salla ta kulle kayanta cikin Leda Viva ta dauki Markade tana fita ta kai Markade tace zata dawo ta dauka,komawa tayi gida ta manta kudin mota da Sauri ta lallaba ta jawo wani kwano da Babarta take ajiye kudin adashin mutane da sukeyi,ta saci Dubu biyar ta boye ta fito da gudu sai da taci uban tafiya ta isa titi tana ji mota tana Kaduna Kaduna Zaria ta buga tsalle tare da kyalkyalewa da dariya kamar taga Sardaunan tace wlh ta garin ce yee ku tsaya Kaduna Kaduna tana daga Hannu Amma garin murna motar ta riga ta wuce ta,Kuka ta fara tana wayyo masoyina na shiga Uku na,Sai ga wata ai da Sauri jiki na rawa ta tsaida motar Kaduna wanda mutum biyu ne rak a ciki,kawai ta fada ciki,tana shiga suka figa da uban gudu,sunyi Tafiya me dan Nisa sanna wani cikin Samarin nan ya Shaka mata wata Powder tana shaka sai luuuuuu bacci ya kwasheta kamar gawa, Tun a motar dayan ya dakko sabuwar Aska ta askin Maza tana sheki ba tare da bata lokaci ba ya shafa ruwa da sabulu a saman kitson Lantan wacce tana da gashinta ba laifi irin na yan fulani, Daya Saurayin ya kyalkyale da dariya tare da cewa Halina da yan kauye ba dai gashi ba sai rashin gyara kalleta kyakyawa wlh light chocolate gaskiya yawuna ya tsinke hancinta me dan tsayi kadan ya ja tare da cewa uhmm a'a a lafiya dai mutan kauye fulanin Asali, Driver yace haba Jeckob oga fa yace banda lalata Sabo da sihiri zai karye a kama mu,hhhh Jeckob yace na gode da ka tuna min Dan Magyatso. Nan take da kitso da komai Jeckob ya askewa Lantan gashi sal sal ba ko digon gashi. Daya Saurayin yace da Allah rufe mata kan nan ba kyan gani, Tafiya sukayi me matukar tsayi sannan suka je gidan da suke kai mutane,Lantan sai da ta kwana ta yini tana bacci sannan ta farka,ihu ta kwala ganinta tsakiyar mutane rutu rutu kowanne da askakken kai, Tace wayyo ashe anyi tashin alkiyama ban sani ba,tunda naga haka ba kyan gani wallahi ina cikin yan wuta shike nan shedan ya cuceni,nan ta fara ya Allah ka ceceni kayi min Rahma, Duf taji babu me motsi bare magana cikin tarin dan Adam da suke ciki, tace shike nan ina cikin shakiyyai,wayyo Inna da Baffa ko suna Aljanna su? wani mutum ne kato me mummunar sura ya kwadawa Lantan Mari sai da ta daina gani na wani lokaci, Lantan zumbur ta mike tare da cewa gudumar walakirice wayyo Allah ka yafe min. Wani duka mutumin ya kai mata sai ga Lantan ta sume ta farko tace wayyo wayyo wlh nayi Kalmar shadaha ni musluma ce,Astagafrillah,Iza waka'atil waqi'a ma na iya haddarta wlh wailullukulli ma zan kawota.takaici ya kama Katon marar imanin nan ita tunanin Lantan ta mutu a kabari take, mutumin ya kai mata wata wawar masga,Lantan ta fashe da kuka me karfin gaske,sai ta dawo hayyacinta ta tabbatar a duniya take ta tuno ba haka ake suffanta mala'iku ba,a ranta tace ko dai wannan mutanen sune kiyashin Kabari?a'a mutane ne Tace kayi hakuri wlh ban san ku yan yankan kai bane,malam kaji tsoron haduwarka da rabbulsamawati wal ardi, Ni wlh da nasan ku yan yankan kaine ina zanyi magana ai Bazan yi ba,mutumin ba Imani idonsa jajir baki wuluk dashi Kazami ya ware karfinsa ba magana ya fara jibgar Lantan ko ihu ta gagara yi, shi kansa bai taba ganin me taurin kai irin Lantan ba duk tsoron shi da mutane sukeyi Amma ita sam asirinsa bai ci Lantan ta kasa magana ba,idan aka kawo mutum gidan basa iya magana ko da an fitar dakai ba

Chapter 22 of 38