Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

maimaita kansa a ƙwaƙwalwarta sai sunan Mr Aabdar Dawlah, to ta ya ma zata manta da wannan mugun mutumin?, da ya lalata ma ta Rayuwa bayan hakan ma bai kyale ta ba, har sai da yaso ganin bayan yaran da ta haifa sanadiyar rabata da mutuncinta da ya yi.!

“Mr Aabdar Dawlah nasan sa mugun mutumi zai iya aikata komai muddun zai sama biyan buƙata na daga ƙudirin sa ko wani kala ne, sai dai mene ne dalilin da ya sa ita yarinyar ta yi ma samarin da kake mana abin da ta yi?.”


Aunty ta jero masa tambayoyin da ta fizgo da kyar tana dubansa domin haka kawai zuciyarta ke son sanin ainihin lamarin.


Mahbub ya dubeta sannan ya saki murmushi kaɗan ya ce.

“Koda nayi miki bayani a yanzu ba zaki gane ba, amma dai duba nan kiga.”

Ya yi maganar yana ƙari sawa wurin motarsa sannan ya buɗe gidan baya yana ma ta nuni da ta ƙari so ta duba abin da ke ciki.
Ba iya Aunty kaɗai ba gaba ɗayan su ne suka ƙari sa domin ganin menene a ciki. Sai dai abin da suka gani ya yi matuƙar gigitasu da kuma sake rikita tunanin su ganin wacca ke kwance mai matuƙar kamanni da Lulu kanta ɗaure da bandage jikinta ma kayan marasa lafiya na asibiti ne da alama ma baccin wahala take yi.

“Lulu! Wannnan ai Lulu ce Neina duba mana Lulu ce mene ne ya faru da ita.”


Ramla ta yi maganar da ƙarfi tana nuni da budurwar mai matuƙar kamanni da Lulu dake kwance cikin motar tamkar babu rai a tare da ita.

“Wannan ba Lulu ba ce, to amma wacece kardai a ce ita ce! Ita ce!.”

Maiji ta kasa ƙari sa Maganar bakinta na rawa ta kalla Mahbub ta kasa furta komai ma sai bakinta dake rawa tana kuma nuna budurwar dake kwance.

Jinjina ma ta kai ya yi sannan ya ce.


“Ba Samra Lulu ba ce wannan ‘yar uwanta ce Samara da kuke tunanin ta mutu a shekaru huɗu baya.”

Ya yi maganar yana duban Aunty domin ganin reaction nata. Yayin da Irshad ya yi wani irin zaro ido yana kuma duban budurwar dake kwance tamkar dai babu rai a tare da ita. Tsugunawa ya yi a wurin tare da kai hannu zai taɓa ta, sai gani ya yi wani hannun daban ya rigasa taɓa ta.
Wani irin luguden bugu ƙirjin Aunty yake tun lokacin da taga wannan budurwa bata gama tantance wani hali take ba, ta kuma jin abin da Mahbub yake faɗa da suke sauka a kunnuwanta tamkar saukar aradu.

Bakinta na wani irin rawa kamar mazari ta kuma duban Mahbub lokacin da ta kai hannu ta taɓa Budurwar zuciyarta ta yi wani irin tsinkewa, tabbas jini ba wasa ba ne, wannan budurwar dake kwance jinin ta ce.


Jinjina ma ta kai kurum Mahbub ya yi domin ya fahimci tambayar da takeson ta yi masa.

“Nasan a yanzu gaba ɗaya kuna cikin ruɗani kuma kunason sanin ainihin abin da yake faruwa zan faɗa muku amma kafin nan zaku fara sanin ainihin wanene ni.
Sunana Mahbubullah Muhammad Sani haifaffen garin Katsina ne ni anan gaba ɗaya dangin mu suke kuma anan na taso nayi karatu tun daga primary har zuwa matakin secondary daga nan na fita Abroad na ɗauki shekaru ina karatu ɓangaren Shari'a bayan na kammala na dawo Nijeriya kuma a lokacin a ka ɗaura auren mu da Rahama ɗiyar ƙanwar mahaifina tun muna ƙanana a kasan alaƙar dake tsakanin mu shi ya sa koda na kammala karatu ba'a ɗauki dogon lokaci ba a ka ɗaura mana aure, sannan a lokacin ne wani irin rikitaccen case yazo hannuna a kan wasu ɓoyayyun miyagun Laifuka da late commissioner na ƙasar nan yake aikatawa har wani daga cikin jami'an sa ya gane gaskiya, gudun kar ya tona masa asiri ne ya saka commissioner ya kashe sa har lahira, sai dai bai sama hujjojin da suke a tare da wannan jami'in ba, ashe kafin jami'in ya mutu ya bawa Matarsa wannan baya nan, shi ne ita kuma bayan mutuwarsa ta shigar da ƙarar commissioner a kan zargin shi ne ya kashe ma ta miji, lamarin dai duk yadda a ka so kashe sa bai mutu ba har sai da ya kai ga an shiga kotu ni ne nake matsayin lauyan wannan matar kuma ta bani waɗan nan hujjoji da mijinta ya bar ma ta, waɗan da su kaɗai sun isa hujjar da commissioner zai ƙare rayuwarsa a gidan kaso, sai dai ashe shiga wannan lamarin da nayi har na amsa hujjojin nan ba ƙaramin kuskure na aikata ba. Matata Rahama Mai tsohon ciki haihuwa ko yau ko gobe suka kashemin a dalilin shiga lamarin da nayi...”

Mahbub ya ɗan yi shiru yana sauke ajiyar zuciya, sannan ya ci gaba da faɗin.
Jaish Jezim shi ne cikakken sunansa ya taso ne cikin wata kalar Rayuwa da ta banban ta dana sauran ƴaƴa, yana da shekaru goma a duniya Mahaifinsa ya kashe masa mahaifiya a gaban idanunsa, daga nan ba'a ɗauki dogon lokaci ba, shi mahaifin Jaish ɗin ya aura wata baturiya mai suna Clara wacca a dalilin ta ya kashe matar tasa wato mahaifiyar Jaish saboda ta taɓa kamasu a tare suna abin da bai dace ba. Saboda dalilai biyu zuwa uku kwarara mahaifin Jaish ya kashe matar sa maman Jaish, na farko dama can ya aure ta ne saboda dukiyarta bashi da komai ta auresa duk wata daula da suke ciki nata ne, na biyu kuma shi ne ita mahaifiyar Jaish mai suna Falisha bata kasance cikin kyawawan mata ba, tana da wata kalar fata ne mara kyan gani wacca babu likitan fata da basu haɗu da shi ba a kan matsalar amma abu ya cutura domin da hakan a ka haife ta babu wani abu da zai canza kalar fatar nata shi ya sa ma ta rasa mai aurenta, duk da masifar dukiyar da take da, wannan dalilin ya sa lokacin da baban Jaish wato Jezim ya nema ya aure ta bata ƙi ba, anan suka yi Aure kuma ta damƙa masa ragamar dukiyarta gaba ɗaya shekara guda da aure ta haifa ɗan Namiji suka saka masa suna Jaish suke kiran sa da J.
Abin da Falisha bata sa ni ba shi ne Jezim ba don yana son ta ya aure ta ba sai dan dukiyarta kuma sannan shi yana da wacca suka daɗe tare kuma suke da muradin auren juna wato Clara sai dai ita Falisha bata san da hakan ba har zuwa wata rana da dubunsu ta cika ta kamasu a tare, a lokacin ta yi matuƙar ɗaukan zafi da shi, sai dai da yake mugun makiri ne sai da ya san yadda ya lallaɓa ta har suka fita wurin shaƙatawa tare anan ne kuma ya yi amfani da damar sa ta hanyar jefata ƙasa tun daga saman bene, sai dai wani kuskure da ya yi shi ne a gaban idon Yaron sa Jaish ya jefa matarsa Falisha ƙasa da haka ya yi sanadiyar mutuwar ta, dama hakan ya tsara shi da Clara domin ta hakan ne ba za'a zarge sa ba, domin abin ya kasance ne tamkar bisa tsautsayi ya faru.
Ba'a ɗauki lokaci ba ya auri Clara kuma suka ci gaba da zama anan gidan da suke da Falisha.
Jaish a sakamakon abin da ya faru na kashe mahaifiyarsa da Mahaifin sa ya yi a gabansa hakan ya haifar masa da firgici mai cutarwa har hakan yaso ya taɓa ƙwaƙwalwarsa kuma abin ya ci gaba da girmama ne sakamakon abubuwa da basu kamata ba da Babansa da matar baban nasa Clara suke yi a gabansa domin su sumbaci juna a gabansa ba wani abu ne ba a wurin su, har ta kai ta kawo suna iya kusan saduwa da junansu a gabansa, baya da haka Clara tana matuƙar masa horo na azabtar wa sosai ta hanyar tsare sa da wuƙa ta ce sai ya kira da Mama ko kuma ta kashesa, irin waɗan nan abubuwan sune suka ci gaba da faruwa da Jaish tsayin shekaru Biyar zuwa lokacin kuma zuciyarsa ta yi wani irin ƙeƙashewa da lamarin Duniya wani irin mugun tunani ƙwaƙwalwarsa ke basa tana bashi tabbacin komai nene ya yi ba laifi ba ne, a wani lokaci ne kuma wannan tunanin nasa ya kaisa ga aikata wani Babban laifi da ya zama ƙofa na buɗe war miyagun abubuwan da ya ci gaba da aikawa. A wani yammaci Jaish ya yi amfani da bindigar da ya samu wurin wani abokinsa ya yi ma Mahaifinsa da Clara wani irin mummunar kisa wanda ko a tarihin miyagun Laifuka na kisa ya sha banban da saura, bayan faruwar hakan ne Uncle ɗin sa Aashir Aasaal wanda suke uwa ɗaya uba ɗaya da mahaifin Jaish.
Ya ɗauki Jaish ɗin ya ci gaba da rayuwa a tare da shi, sai dai bai saka sa cikin iyalansa ba, ya ci gaba da koya masa miyagun Laifuka kuma sauke yi tare da fari ya fara da koya masa dallanci na miyagun kwayoyi da yadda a ke siyarwa da su, daga baya harkar tasu ta faɗa ɗa suka koma harda safaran makamai, to dama ance makoyi mafiyi, Jaish ya taso wani irin murɗaɗɗen mutum ne shi mai wata kalar baƙar zuciyar da babu ko ɗigon tausayi cikinta kuma sannan ya tsani ma ta wannan dalilin ya sa a lokacin da case ɗin Uncle ɗin nasa commissioner yake a hannuna ganin alamun zasu yi rashin nasara zasu faɗi shi ne dalilin da ya sa shi ya sace matata Rahama Mai tsohon ciki bai duba wannan ba, a lokacin da ya sace ta a garin Katsina yana gudu da motar ne har ya yi sanadiyar da ya kaɗe Samara kuma bai dakata ba daga bisani kuma cikin rashin imani da tausayi ya kashe ta har lahira, ni kuma suka saka yaransu suka sace ni a hanyata na zuwa court suka min shegen duka da tunanin na mutu domin duka da sara suka haɗa min suka watsar dani a daji suka yi gaba, daga nan wasu mazauna nan daji ne suka tsince ni kuma suke kula dani tsawon shekaru biyu da wani abu ina jinya domin har manta gaba ɗaya tunani na nayi sai daga baya na sama sauƙi kuma na taso domin wata kalar muradi na ɗaukar fansa bisa abin da suka yi min, nabi duk wata hanya domin ganin na ɗauki fansa, a nan ne na ƙara sanin cewa Aashir Aasaal Uncle ɗin Jaish da yake matsayin commissioner tantirancin sa ya wuce tunani duk wani ƙaramin mahaluki, kafin na fara wani yunƙuri na ɗaukar fansa sai da na fara bincika Asalin wane ne commissioner nan ne na gano Jaish sanadin binciken da nayi kuma ban tsaya iya nan ba sai da na fara binciken ko akwai wasu masu buri Irin nawa na son ɗaukar fansa a kan su, nan ne na gano tawagar su Lulu duk da cewa sun tabbatar wa kansu domin adalci suke abin da suke bawai na fansa bisa abin da a kayi musu ba, a lokacin ne na bincika Asalin Labarin kowaccensu tun daga kan Ramla da a ka kashewa miji da Lulu wato Samra har Maiji wacca ‘yar uwanta ta taɓa auren Jaish har ya kashe ta saboda ta gano asalin wanene shi kuma ya haɗa hannu da Uncle ɗin ta da yake member na wata hatsabibiyar ƙungiyar da Jaish ya kafa ta shi da Uncle ɗin sa commissioner, Uncle ɗin Maiji wato Alhaji Umair Ubaydullah shi ne suka haɗa hannu da Jaish suka kashe iyayen Maiji gudun kar su gane ainihin abin da ya faru har ya yi silar mutuwar Fanan a lokacin ƙudirar Allah ne kawai ya tseratar da Maiji basu sama nasarar kasheta ba har ta faɗa hannun masu fataucin mutane da hakan ya zama sanadiyar haɗu warta da Lulu...”


Mahbub ya kai ƙarshen maganar yana harɗe hannu a ƙirji tare da jingina da motarsa.
Yayin da gaba ɗaya jikinsu ya yi wani irin sanyi tare da cika da tsanani mamaki da jin wannan labari da ya bada wai dan ma a hakan ma a gurguje ya basu domin Jaish da commissioner sun wuce duk wani tunanin mai wani ƙaramin mai tunani.

“Turƙashi! Wato ke nan idan na fahimta kai ne! Kai ne!!.”

Ramla ta kasa ƙari sa zancen tana ƙara girman idanunta a kan sa.
Ya saki murmushi tare da ƙari sa ma ta da faɗin.
“E ni ne na kashe commissioner! Ko dai bai cancanci mutuwa ba ne?.”

Bata kai ga basa amsa ba suka tsinkayi Muryar Aunty tana faɗin.

”Tabbas Samra wato Lulu ita da ‘yar uwarta Samara ƴaƴana ne kuma ba kowa ba ne mahaifin su fa ce Mr Aabdar Dawlah!.”

Gaba ɗaya da wani firgici da tsananin tsoro game da tashin hankali suka dubeta especially ma Irshad, yayin da shi kuwa Mahbub ya kuma sakin lafiyayyen murmushi domin dama ya riga da yasan komai.

“Mr Aabdar Dawlah shi ne mutumin da ya ƙeta alfarmata sanadin hakan kuma na haifa yarana ƴan biyu na saka musu suna Samra da Samara sai dai duk da hakan bai kyaleni ba sai da ya bini har Kaduna da na gudu nake zaune a can saboda nasan koda na koma gida ba za'a karɓe ni da yaran dana samu a sanadin fyaɗe da a kayi min ba, a lokacin nayi matuƙar jin tsoro domin Mr Aabdar so yake ya kashe yaran nawa shi ya sa ni kuma domin tseratar da Rayuwar su nayi sadaukarwar da nake ganin shi ne daidai a wancan lokacin ta hanyar kaisu gidan marayu dake can Katsina, kuma tun daga wancan lokacin ban sake bibiyar su ba, domin a ganina idan na manta da su na kuma haƙura dasu ne kawai Rayuwarsu zasu tsira daga son kashesu da Mr Aabdar keyi.”

Babar Magana! Gaba ɗayansu jinjina girman al'amarin kawai suke. Nan shima Irshad ya basu labarin farkon haɗuwarsa da su Samra har zuwa yau.

“Am ina da tambaya! Shin Barrister Mahbub zamu iya sanin a'ina ka samo Samara?.”

Cewar Maiji. Mahbub ya ɗan juya tare da kallon Samara da har lokacin sharar baccin ta take hankali kwance sannan ya sake juyowa ya dube su kana ya ce.

“Tun bayan lokacin da Jaish ya kaɗe ta sannan Lulu ta kai ta asibiti a ka ƙi karɓar ta har ta dena numfashi wanda ita kuma Lulu ta ɗauka ta mutu ne, har hakan ya yi sanadiyar da ta suma batasan inda kanta yake ba sai farkawar da ta yi ta tsince ta hannun masu fataucin mutane har ta haɗu dake, a lokacin mutane daban daban ne suka ɗauke su wasu suka ɗauki Samara yayin da suka siyarwa da masu fataucin mutane Lulu, suka tafi da Samara wurin iyayen gidan su wato Alhaji Haashir da Alhaji Umair sai kuma Mr Aabdar suka ce musu ɗayar ta mutu shi ya sa suka ƴar da ita, a hannun waɗan nan mutanen uku Samara ta yi doguwar jinyar da har ta manta gaba ɗaya tunanin ta bayan ɗaukar dogon lokaci tana jinya sannan ta farfaɗo su kuma suka sakata cikin ƙungiyar su ta Zwandun Monster's kasancewar idan mutum ya rasa tunanin sa kuma ya kasance yana da wata baiwa tofa wannan baiwar baya rabuwa da ita, to hakan ce ta kasance ga Samara ta fara aiki da ƙungiyar Zwandun Monster's tana taimaka musu ta fannoni da dama sai dai tafi bada gudunmawa ta hanyar ɗauke tunanin mutane ko kuma jami'ai a kan wannan ƙungiyar da hakan ya bada gudunmawa babba ta hanyar tuna ma ta wasu abubuwa na memory nata da ta manta suka fara dawo ma ta, ta shiga cikin firgici sosai sai dai bata faɗa wa kowa ba, har zuwa lokacin da ta tuna Asalin wacece ita, ni kuma da nake bibiyar ta a lokacin ne na haɗu da ita har na samu na shawo kanta ta yarda dani na bata labarina sannan muka fara tsara yadda zamu rusa gaba ɗaya ƙungiyar ta Zwandun Monster's tabbas Samara tasan ‘yar uwanta Samra tana raye kuma har gidan da suke zaune na kaita ta hangeta kuma tana yawan zuwa unguwar kawai don taga Lulu ɗin sai dai taƙi bari su haɗu domin tafi so har sai mun gama da ƙungiyar sannan ta bayyana ga ‘yar uwan nata haka lokaci ya ci gaba da tafiya har muka tsara kuma kuma gabatar da abin da muka shirya ta hanyar kawar da commissioner da hakan ya zama matakin farko da muka bi wurin tarwatsa Jaish da tsarin sa domin mutuwar commissioner ɗin ta yi matuƙar taɓa sa har hakan ya sa shi fara yin abin da ba ɗabi'arsa ba cikin hakan har ya naɗa Samara da take amsa sunan Sanam matsayin shugaba ta biyu a ƙungiyar Zwandun Monster's wanda hakan ya janyo hatsaniya cikin ƙungiyar kuma ta gefe guda har waɗan nan mugaye uku shirya su kashe Sanam wato Samara to dama da shirin mu muke ni da ita, sun shirya haɗuwa da ita a wani gidan gona na Mr Aabdar dake nan a Abuja a yau domin su kasheta har suka yi nasarar buga masa kwalba a kai domin ta yi musu gardama lokacin da suka buƙaci ta sha Juice dake ɗauke da poison mai matuƙar hatsari ita kuma taƙi shi ne abin da ya fusata su har Mr Aabdar ya buga ma ta kwalba a lokacin ne kuma na fito daga maɓoyata ganin zasu kashe ta dama tare da ita mukaje nayi musu barazana da bindiga har na samu na fito da ita, sanadiyar buga ma ta kwalbar da a ka yi ne ta suma kuma har yanzu bata farfaɗo ba sai dai zata farfaɗo ɗin.”

Mahbub ya yi shiru lokacin da kai ƙarshen maganar.

Cikin jinjina kai tare da ta'ajjabi na wannan lamarin Maiji ta ce.

“Dama na sa ni Jaish shi ne shugaba na ɗaya kuma creator na ƙungiyar Zwandun Monster's wanda sanadin sanin wannan gaskiyar da Yayata wato matarsa ta farko, ta yi shi ya sa ya kashe ta ya kuma kashe iyayen ta wato Uncle ɗina da matarsa bayan haɗa hannu da ɗayan Uncle ɗin nawa Alhaji Umair da suka yi.”

“Wai kina nufin ba mahaifin ku ɗaya da Fanan tsohuwar matar Jaish ba?.”

Mahbub ya ma ta tambayar.

Girgiza kai ta yi ta ce.

“A'a amma dai shi ne ya riƙe ni tun ina ƙaramata, kafin mahaifiyata da ta kasance balarabiya ce ya haife ni mahaifina ya rasu sanadiyar hatsarin mota ita kuma mahaifiyata koda ta haifeni ko yaye ni batayi ba ta gudu ƙasar su a cewar ta bazata iya jure zama ba tare da mahaifina shi ya sa ta tafi ta bar ma danginsa ni, a hannun matar Uncle Sahir wato mahaifin Fanan na taso kuma na ɗaukesu matsayin iyaye har zuwa lokacin da wannan mummunan ƙaddarar ta afka mana na auren Jaish da Fanan ta yi dama ita ke son sa shi bai damu da ita ba, kuma bata damu ba a cewarta tausayin sa takeji domin ce ma ta ya yi shi maraya ne shi ya sa zata auresa gashi sanadin hakan ga abin da ya haifar ya saka ma ta da kasheta da kuma kashe iyayen ta nima Allah ne kawai ya tseratar dani daga sharrin sa.”


Shiru suka yi gaba ɗaya su na kuma jinjina girman wannan al'amarin lallai in baka mutu ba ka sha kallo.

Wucewar wasu sakanni....

“Rayuwar Lulu ta na a tsari zaman ta a hannun D.S.S ba zai zama kariya daga gare ta ba, domin cikin jami'an nasu ma akwai ɓata gari ya kamata Lulu ta fito.”

Cewar Mahbub, gaba ɗaya jinjina kai suka yi lokaci guda kowannen su ya shiga motar da ya zo suka bar asibitin domin zuwa DSS headquarter.



*Wato dai ta tabbata Jaish shi ne jezim inkiyar sa Shaytaan 🌚 Babbar magana.!*

Wato ana ta labari baku ce ina Hamraz yake ba ko?.

To mu haɗu a next page domin jin wani hali Hamraz yake ciki tare da sanin mene ne zai faru gaba!!🤦🔥🔥

*Labari fa yazo gangara saura ƙirisss 👌*


*RANAR BIYAN BUƘATA*
_Rai Ba'a Bakin Komai Yake Ba.!_
BY Nainarh KD Nkd's.✍️

_
E. 32 Final Episode.👏



A hankali yatsun ta na hannu suka fara motsi kaɗan kaɗan, yayin da jikinta ya fara kakkarwa kamar wacce a ka jona da wutar lantarki ba ma iya jikinta ba hatta gadon da take kwance shima Shaking yake.

Tana a tsaka da wannan hali Hamraz ya turo ƙofar ya shigo bakinsa ɗauke da sallama hannunsa kamar ko yaushe riƙe da wani ɗan littafi idanunsa sanye da farin Glass.
Da sauri kuma a hanzarce ya ƙari sa gare ta, bayan ya yi wurgi da littafin dake hannunsa.
Rasa mai ma zai ma ta ya yi domin kuwa jijjigan da take yi a yanzu ya mafi na ɗazu a lokacin da ya shigo ya sameta, sai can dabara ta faɗo masa, da sauri ya tallafo ta a ƙirjinsa yana faman bubbuga bayanta, tsawon mintoci zuwa yanzu ta dena jijjigar sai faman ajiyar zuciya da ta ke saukewa a kai a kai, sai can kuma kamar wacca a ka tsikara ta fara ƙoƙarin kwace jikinta daga garesa tana faman sumbatu faɗi take.

“Ni kakyaleni wayyo Neina ki taimake ni karya kasheni!!.”

Tana sumbatun ya ɗa gota daga ƙirjinta tare da girgiza ƙafaɗun ta yana karanto ma ta addu'o'i dan a yadda take sumbatun jikinta na rawa ya yi zaton aljanu ne duk da dama Dr Hadiza ta faɗa masa zata iya tashi ba'a hayyacinta ba.
Tunawa da hakan da ya yi ne ya sa ya fara ƙoƙarin ɗaukar ta kacokan domin kaita asibitin da Dr Hadiza ɗin take aiki don ta duba ta dan kuwa baya tunanin zai iya jira har sai ya kira ta a waya sannan tazo gwara ya je ya sameta.





*DSS Headquarter Mai Tama Avenue Abuja*



*OFFICER UMNIA POV.*


Ta ƙari sa shiga Interrogation ɗin tare da jan kujera kamar zata zauna, sai kuma ta fasa ta ɗaura ƙafa ɗaya saman kujerar, ta ɗan rangwafa tana duban Lulu dake zaune saman kujera cikin Interrogation cikin tsimewa da kuma nazari kamar ba zata yi magana ba, sai kuma ta fara.

“Mu ba. Jami'ai mu kan iya kauda ido daga kan mai laifi, mu kan iya bawa mai laifi dama, muyi masa ɗaurin talala kamar bamu san me yake ba.! Now tell me ya sa kika kashe commissioner sannan kuma kika kashe Prof Bakori?, Bana so firan namu yaja lokaci ki bani amsoshi kawai.”

Ta ƙari sa faɗa tana zuba ma ta rikitattun idanunta.

Ɗan taɓe baki Lulu ta yi ganin da irin salon da Officer ta zo da shi, ta ɗan yi baya tare da harɗe hannu a ƙirji tana duban ta da nata kausasan idanun ta ce.

“Yanzu me kike da buƙatar na faɗa miki ne Officer? irin kisar da nayi ma commissioner ko kuwa irin wanda nayi ma Prof Bakori ko kuwa dai na faɗa miki ainihin true color na kowannen su wanda Asalin kwarewar ki a bincike bai saka kin gano ba?.”

A fusace Officer Umnia ta miƙe daga rankwafawar da ta yi tana daka ma ta tsawa dan ranta ya fara ɓaci ta tsani rainin hankali ƙiri ƙiri hujjoji sun bayyana amma wannan ficiciyar yarinyar zata tsaya tana ɓata ma ta lokaci.

“Oh common Officer just relax mana, to mene ne na ɓacin rai? Ai bake ya kamata ran ki ya ɓaci ba, let me tell something da ke baki sani ba, commissioner da kuma Prof Bakori ba mutanen kirki ba ne al'ummar ƙasa gaba ɗaya farin ciki suke da mutuwarsu na sani sanadin mutuwarsu mutane da dama musamman ma ‘yan mata zasu tsira daga fyaɗe da a ke musu duk kwanan Duniya, wai kuwa kin san a kullum ana tashi ne da report na ɓatan yara ƙanana da kuma ‘yan mata kuma ba'a taɓa ganin su?, Kin san su waye ainihin commissioner da kuma Prof Bakori? Duka baki sa ni ba, hummp ina tunanin baki cancanci zama Officer ba Madam, tun da baki san meke faruwa a ƙasar ki da kikayi alƙawari zaki bada Rayuwarki wurin kula da al'ummar ta musamman talakawa da koda yaushe Rayuwarsu take mara ‘yanci, Officer ki sani bana taɓa dana sani a kan abin da na aikata ko kuma wanda zan aikata nan gaba dan kuwa yanzu wasan ya fara ba'ayi komai ba ma, don ba zan dakata ba har Ranar da adalci ya wanzu ga kowa koda hakan zai yi sanadiyar rayuwata naji na aminta. Saboda haka bazakiji komai ba daga bakina kije

Please Login or Register in order to submit comment