gida ba da ita aka zo ba
Sai dai Halwa ta kasa barin kukan, domin ko tayi yunƙurin dena wa, da zaran ta tuna Saleema ce ta rasu sai kukan ta yadawo sabo, an yi rarrashin duniya taƙi yin shiru, dole suka zuba wa sarautar Allah ido, duk idan kukan nata ya dawo yi take yi kawai babu me tsayar da ita, sai idan ta gaji don kanta sai tayi shiru anjima ta sake dasa wa, gaba ɗaya duk ta ya mutse ta saka wa kanta ciwo na ƙarfi da yaji, domin dai sai da tayi wajen sati ɗaya a asibitin kafin a sallame ta, ga hawan jinin ta da yaƙi sauka, likitoci sun yi mata maganar hakan zai iya shafan lafiyan ta da abinda ke cikin ta amma taƙi sauraron su.
Tunda suka koma gida ma babu lafiya, haka rayuwan taci gaba da Gara mata yau ciwo gobe lafiya, Khalil haka yake fama da ita ko kaɗan ba ya gajiya da mata hidima, duk wani farin ciki dake gidan nan nasu yanzu babu, rasa Saleema cikin rayuwan su ba ƙaramin giɓi yay musu ba, idan kashiga gidan sai dai kaji shiru ko motsin kirki ba sa yi
Su Husna sai dai me aikin su ke kula dasu, ita take musu komi.
Daga baya ma Mom zuwa tayi ta tafi da Halwan gidan ta, tunda sosai take jin jiki, kullum cikin ciwo take
Shima Khalil can yake wuni idan ya je aiki ya dawo, aikin ma ba kullum yake zuwa ba, saboda shima har yanzu ya kasa dawo da kuzarin sa, ya kasa manta Saleema a ransa, baya iya taɓuka komi.
Ahaka rayuwan taci gaba da tafiya har sanda cikin Halwa ya shiga watan haihuwa, lokacin ma tuni tana asibiti saboda yanda takoma sai kun tausaya mata, gaba ɗaya ta kumbure tayi suntum kamar ba ita ba, cikin yayi girma sosai har ba ta iya ma tafiya
Lokacin da tasoma naƙuda an ma fid da ran zata iya rayuwa, domin kwanan ta biyu tana a halin ciwon naƙuda, gashi hawan jinin ta yayi mugun hawa
Likitoci sun yi iya yin su amma ta kasa haihuwa da kanta, tunda jinin ta ya kai matakin da baza ta iya haihuwan ba, kuma komi zai iya faruwa da ita
Ganin idan taci gaba da zama ahaka zata iya rasa ranta dole aka shirya yin mata CS, ahaka aka shigar da ita ɗakin Theater bata ma san a inda kanta yake ba.
Khalil yasha kuka sabida tausayin matar sa, daƙyar ma ya iya saka hannu da za'a yi mata CS ɗin, dole Sameer da Brr. Tahir sukai ta tausan sa suna ba sa baki, su ma duk hankalin su a tashe, kowa yayi jugun ana jiran abinda hali zai yi.
Alhmadulillah an samu nasaran ciro wa Halwa yara biyu duk ka maza, kuma duk ka yaran suna a cikin ƙoshin lafiya, sai dai Mahaifiyar su ne da akayi zaton ta mutu ma, sai da likitocin suka yi iya yin su kafin suka gane tana da rai, Oxgyen suka saka mata sannan suka fito da yaran suka yi musu albishir da samun ƙaruwar twins
Sun yi murna sosai duk da suna cikin damuwa da halin da aka sanar musu Halwa na ciki, Khalil kawai aka bari ma yashiga wajen ta
Tunda ya shiga idanun sa na kanta, hawaye ne kawai suke kwaranya a saman kuncin sa, yana saka hannu yana share wa cike da raunin zuciya, ganin yanda Halwan nasa ta koma tamkar ba ita ba, har wani baƙi tayi sabida tsaban rame wa, tamkar ba ita ce wacce ta kumbura tayi himm ba, amma yanzu lokaci ɗaya ta zabge tamkar ba ita ba
A hankali ya taka ya isa gaban gadon, a ƙasa ya ajiye gwiwowin sa yana tura hannun sa cikin tafin hannun ta da aka saka mata Drip, damƙe hannun yayi sosai kafin ya ɗaura kansa saman cikin ta yana ci gaba da hawaye, hawayen tausayin ta, gaba ɗaya zuciyar sa ta gama rauni, bazai iya juran itama ya rasa ta ba, taya zai iya rayuwa idan ta tafi?
Ɗago kansa yayi yana kallon fuskarta, cikin sanyin murya yace, "Ina ƙaunar ki Halwa, don Allah.. kar ki tafi kema ki bar Ni, wlh idan na rasa ku duka zuciyata bugawa zata yi, don Allah kiyi haƙuri ki tashi, ki tashi mu raini ƴaƴan mu da Allah yayi mana kyautan su, kinji ki tashi don ALLAH.."
Dole yayi shiru sabida kukan da yataho masa, sai ya sake ɗaura kansa saman jikin ta yana ci gaba da tsiyayar da hawaye, sosai yake ji a jikin sa itama zata tafi ne
Yanda hawayen sa ke zuba ajikin ta hakan yasa take jin sanyin har cikin fatar ta, wannan dalilin ne yasa tafarka a time ɗin, idanuwan ta kaɗai ta buɗe tana bin ɗakin da kallo, tsawon sokonni kafin tagane akwai mutum kusa da ita, sai kuma daga baya ta fahimci Khalil ne, hakan yasa taɗago ɗayan hannun ta ahankali ta aza a kansa
Cakk ya tsai da kukan nasa yana ɗago kai dasaurin sa, nan idanun sa suka faɗa cikin nata da suka ƙanƙance suke a lumshe, daƙyar ma take iya buɗe su sabida halin ciwo
Be san sanda ya washe baki ba yana ta faɗin Alhamadulillah...
𝗧𝗢 𝗯𝗲 𝗰𝗼𝗻𝘁𝗶𝗻𝘂𝗲..✍️
_Nima ALHMADULILLAH anan na kawo karshen book ɗin 𝐁𝐑𝐑. 𝐈𝐁𝐑𝐀𝐇𝐈𝐌 𝐊𝐇𝐀𝐋𝐈𝐋, abun da na rubuta daidai Allah ya amfanar damu, kuskuren da nayi kuma Allah ya yafe min._ 𝑎𝑚𝑖𝑛
𝐼𝑛𝑎 𝑚𝑎 𝑚𝑎𝑠𝑜𝑦𝑎𝑛𝑎 𝑓𝑎𝑡𝑎𝑛 𝑎𝑙𝑘ℎ𝑎𝑖𝑟𝑖, 𝑠𝑎𝑘𝑜𝑛 𝑘𝑢 𝑚𝑎𝑠𝑜𝑦𝑎 𝑦𝑎 𝑖𝑠𝑜 𝑔𝑎𝑟𝑒 𝑛𝑖 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎 𝑏𝑎𝑟 𝑧𝑢𝑚𝑢𝑛𝑐𝑖 𝑛𝑎 𝑔𝑜𝑑𝑒 𝑘𝑤𝑎𝑟𝑎𝑖
𝐽𝑖𝑛𝑗𝑖𝑛𝑎 𝑎𝑔𝑎𝑟𝑒 𝑘𝑖 𝐒𝐇𝐔𝐆𝐀𝐁𝐀 𝐒𝐀𝐅𝐍𝐀 𝐀𝐋𝐈𝐘𝐔 𝐉𝐀𝐖𝐀𝐁𝐈, 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎 𝑘𝑎𝑟𝑎 𝑑𝑎𝑢𝑘𝑎𝑘𝑎 𝑘𝑖, 𝑦𝑎 𝑘𝑎𝑟𝑒 𝑘𝑖 𝑎 𝑑𝑢𝑘 𝑖𝑛𝑑𝑎 𝑘𝑖𝑘𝑒, 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎𝑠𝑎 𝑘𝑖 𝑓𝑖 ℎ𝑎𝑘𝑎, 𝑓𝑎𝑡𝑎𝑛 𝑎𝑙𝑘ℎ𝑎𝑖𝑟𝑖 𝑘𝑎𝑤𝑎𝑖 𝑧𝑎𝑚𝑢 𝑟𝑖𝑘𝑎 𝑚𝑖𝑘𝑖 ℎ𝑎𝑟 𝑚𝑢 𝑘𝑜𝑚𝑎 𝑔𝑎 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ, 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎 𝑏𝑎 𝑘𝑢𝐧𝑔𝑖𝑦𝑎𝑟 𝑘𝑖 𝑛𝑎 𝐏𝐞𝐫𝐟𝐞𝐜𝐭 𝐖𝐫𝐢𝐭𝐞𝐫'𝐬 𝑛𝑎𝑠𝑎𝑟𝑎, 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎 𝑠𝑎𝑘𝑒 𝑑𝑎𝑢𝑘𝑎𝑘𝑎 𝑠𝑎 𝑓𝑖𝑦𝑒 𝑑𝑎 𝑛𝑎 𝑦𝑎𝑛𝑧𝑢 𝑎𝑚𝑖𝑛.
𝑩𝒊𝒔𝒔𝒂𝒍𝒂𝒎 𝒎𝒂𝒔𝒐𝒚𝒂🤝, 𝒌𝒖 𝒕𝒔𝒖𝒎𝒂𝒚𝒆 𝒏𝒊 𝒂 𝒔𝒂𝒃𝒐𝒏 𝒃𝒐𝒐𝒌 𝒅𝒊𝒏𝒂 𝐑𝐀𝐔𝐃𝐇𝐀 𝒏𝒂𝒏 𝒃𝒂 𝒅𝒂 𝒋𝒊𝒎𝒂 𝒘𝒂 𝒃𝒂. 🥰😍👌
𝐉𝐢𝐤𝐚𝐫 𝐋𝐚𝐰𝐚𝐥𝐢 𝐜𝐞 𝐭𝐚𝐤𝐮 𝐦𝐞 𝐤𝐚𝐮𝐧𝐚𝐫 𝐤𝐮...❤️ 𝕃𝕠𝕧𝕖 𝕪𝕠𝕦 𝕗𝕒𝕟𝕤.
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 34 Chapter of 34