Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da laifi ban san samuwar cikin ba, ban san waye da wannan alhakin ba, ban san waye yake da sanya hannu wajan ruguza rayuwata ba, ban san waye ya zama silar rabani da Mahaifina, dangina, haɗi da farin cikina ba, zan tafi Abbu ina roƙan ka yafe mini a duk sanda gaskiya ta bayyana ko da ƙasa ta rufe mini Idanu, zan raini kyautar ALLAH, zan raini Raba Gardama shi ne hujjar da zata iya fiddani daga zargi, Allah ya haɗa fuskokinmu da alheri"
Aaliyyah ta cire hijabin jikinta ta sakawa Majeederh domin rigar barci ce kawai a jikinta, kuka take sosai tana faɗin. "Kiyi haƙuri Anti Jeederh bana da ikon taimakonki na kasa aikata komai kiyi...,"
Kuka ya ci ƙarfinta ta juya da gudu ta shige ɗaki ba zata iya ganin tafiyar yayarta ta ba.
Gently Malama Majeederh ta kalli Mami, ta juya ta kalli Ruma, da kuma Raihana wacce bata ce komai ba har yanzu. Ta jima tana kallon Mahaifinta kafin ta nufi hanyar barin parlourn jiri na ɗaukarta, tana jan ƙafa wacce ko takalmi babu ta buɗe gate tare da ficewa daga cikin gidan, kamar yadda take barin gidansu haka numfashinta ke barin ƙirjinta, ganinta na janye wa, jinta na raguwa, jaririn hannunta na neman ƙwacewa zuwa ƙasa.
Tafiya take jini na bin cinyoyinta, tafin ƙafarta na taka kan titi, tun tana jurewa har ƙafarta ta fara rawa jikinta ya saki ta ƙanƙame jaririn a ƙirjinta, slowly slowly ta fara ganin duhu a Idanunta tayi baya luuu! Zata faɗi a kayi saurin tare ta, ta faɗa jikin mutum ba numfashi a ƙirjinta.

Hospital
A hankali aka buɗe Ƙofar room ɗin tare da mayarda ita aka rufe slowly. Tsaye ya yi a kanta ya zuba mata narkakkun idanunsa ya ɗauki almost 5 minutes yana kallonta kafin ya ɗaga ƙafarsa a hankali zuwa gaban bed ɗin, ya ja kujera tare da zama akai, cikin nutsuwa ya sanya hannu ya ɗauki jaririn dake kwance yana motsi cikin tattausan showel ɗin da aka saka shi. Soyayyar Jaririn ya samu gurbi a zuciyarsa musamman da bai taɓa samun ɗan kansa ba, bai taɓa ganin gudan jininsa ba. "Ohh baby, your Dad is here" ya furta can ƙasa gudun kada ya tashe ta.
"His Dad?" Ta furta cikin magagin barcin dake ɗaukarta domin allurar bai gama sarkinta ba.
Ya ɗago kai da sauri ya kalleta ba ƙaramin harbawa zuciyarsa tayi ba, this is the first time da yaga fuskarta babu liƙab iya tsayin shekarun daya santa.
Kasa magana ya yi domin duk yadda zuciyarsa ke fasalta masa kyanta abin ya shige haka, musamman da tayi maganar kamar wacce bata hayyacinta idanunta rufe gashin idanunta sun kwanta luf luf gwanin sha'awa fuskarta ta ƙara haske.
"Kin farka? Ya jikin"
Muryarsa ta daki dodon kunnenta yanzu kam allurar ta gama sakinta ta buɗe manyan Idanunta da suka kumbura tare da sauke ganinta akan Aliyu Sufyan Alhassan. Ta runtse idanu yau ƙarya ta ƙare fuskarta available, Allah ya rufa mata asiri jikinta a rufe yake.
"Sorry, In sha Allah komai ya zo ƙarshe zan wankeki wajan Abbu be patient" bata kalle shi ba, domin ƙirjinta ya yi mata nauyi babu wanda ya sake magana har Aliyu ya ce "I love my son, i love both"
"Ka barni" ta furta a kame cikin sanyin harshe. Aliyu ya gyara zama idanunsa akan fuskarta duk da bashi take kallo ba. "You're dreaming, ba zan sake kuskuren baya Jidderh,ba zan sake ba, ina son rayuwa da yarona tare da mother's of the son"
"Ni guba ce, zan iya zama illa ga kowa" ya tari numfashinta ya ce
"Ban dani Aliyu Sufyan Alhassan, ban dani Jeederh" ta juya ta kalle shi kallon daya kusa zautar da shi hannunta ɗaya a ƙirjinta ta riƙe sosai cikin nutsuwarta da kamilalliyyar muryarta ta kame kanta sosai ta ce. "Baka da haɗi da ɗana, kada ka yaudari kan ka ka duba kusancinmu da Latifa ka barni" "Jeederh idan na barki ki ɗauka na bar duniya, Latifa kuma ta bani full opportunity na aurenki" cikin gajiya wa ta ce "ba zaka saman ba"
"Koda na halattawa kai na zama Uba ga danƙi? Wallahi Majeederh na shirya ɗaukan ko wanne ƙalubale akan ki, kuma idan wannan yaron zai sanya ki aureni zan je court ta mallaka mini shi,wanne Irin mallakawa ma? Bayan blood grp ɗina da na shi ɗaya ne, ko DNA text za a yi zai tabbatar da ni ne uban shi" Wayarsa ce ta fara ringing sunan Wife ya fito ya ɗan ja tsaki har kiran ya tsinke aka sake kira lokacin Jaririn ya fara kuka, picking call ɗin ya yi tare da saka wayar a hands free.
Muryar Latifa na rawa ta ce "Sweetheart kana ina? 3days without you ina ka je ina ta kiran number ka a kashe" ba yabo ba fallasa ya ce.
"Ya akai Latifa?"
"Wani abu mai kama da almara ya faru, na kasa sanin babin da zan iya sanya Malama Majeederh"
Aliyu ya ce "Just go to the point Wife" cikin damuwa Latifa ta ce "Majeederh ta haihu,na goya mata baya amma ta bani kunya ta sanya ina yawo da ita har ina kare cikin shege?" Ya tare ta faɗin
"Who told you that?"
"Ruma, ta kirani tun a daren da abin ya faru lokacin na tashi naga babu kai babu motarka, kwana uku kenan yanzu haka Majeederh ta gudu da ɗan gudun surutun jama'a kuma ta shaida ɗan shege ne, Ruma ta ce Majeederh ta bayyana musu cewa daga gidan Abbu ba inda zata sai gidan uban ɗan taci gaba da zaman karuwanci da shi"
Duk maganar da suke Majeederh na ji, tuni ta amshe ɗanta daga hannun Aliyu ta rungume shi,tana jin kawo yanzu shi ne kaɗai ya rage mata, shi zata kalla matsayin wani nata kuma zata kula da shi da dukkan iyawarta har kawo lokacin da gaskiya zata kure ƙarya.
"Ke yanzu kin Yarda Malama Majeederh Abdul'aziz Khan zata iya aikata ZINA?"
"Me zai hana Sweetheart? Tunda ga gaskiya ta bayyana kuma Allah ya isa tsakanina da ita, na gode Allah da ya sanya baka aureta ba, balle mu haɗa iri da shege" "Ba shege bane"
Da ƙarfi ta ce "Wallahi shege ne" cikin tsawa mai firgitarwa ya ce
"Latifa Omar idan ki ka sake sheganta mini yaro zaki sha mamakina, zan miki hauka zan nuna miki true color na" Majeederh ta dafe kanta a hankali ta miƙe bayan ta zare ƙarin ruwan da ake mata, ganin Aliyu ya juya baya yana masifa jijiyoyin kansa na motsawa ta sulale a hankali ta bar room ɗin rungume da jaririn nata.
Kamar mahaukaciya haka ta zama, Latifa ta hargitse tamkar zata cinnawa kanta wuta ta ce "Aliyu Sufyan Alhassan kasan me ka ke cewa? Mene haɗinka da yaron?" Cikin rashin damuwa kuma daman ya shirya amsar ko wanne ƙalubale ya ce.
"Yes that's my name Aliyu, kuma baki taɓa jin nayi hauka ba sai dai ina dab da shirin manna bikin haukan ke, tunda ba soyayyar gaskiya ki ke nunawa Majeederh ba"
Latifa ta zari key ɗin motar ta ce "Don't Tell me kana tare da Majeederh tsayin kwanaki ukun nan?" Ya ware hannu irin he don't care ɗin nan ya ce.
"Yhh, Ina tare da Ɗana da matata, Majeederh is my wife....



08119237616*🌈MIJIN MALAMA🌈*


Nimcyluv Sarauta
*_Arewabooks@Nimcylub_*

*3.....*
Maganganun Aliyu suka kusan tarwatsa mata zuciya, idanunta ya rufe kafin tayi magana ya ce "Ko a lokacin da nake yaro, ban taɓa kuka saboda wahala ba, ba kuma zan yi kuka saboda abin da zaki aikata ba, ki sawa ranki ba a haifi Aliyu domin sadaukarwa ba, amma an haifi ni domin bautawa Ubangiji da kuma cimma burukana, bana da burin daya shige zama da Malama Majeederh Abdul'aziz Khan!" Ya fesar da numfashi ya ce
"Ban taɓa neman abu na rasa ba, kin san yadda nake zama mahaukaci akan abin da nake so....," Da ƙarfi Latifa ta ce "And so what Aliyu? Ni kuma zan tabbatar a wannan karan na zama sanadin da zaka rasa abin da ka ke nema, ka yi ta farauta wacce bata da amfani har zaki ya yi gaba da abin farautar taka, zaka san kuma kaci amanar matarka ni Latifa Omar zaka sani" tayi hanging off na kiran.
Tsakanin ita da Aliyu ba a san wanda ya fi wani shiga damuwa da baƙin ciki ba, shi yana jin baƙin ciki idan ta shegenta ɗan gidan Jeederh, yana jin tamkar gudan jininsa ta shegenta. Latifa Omar tana ganin Majeederh ta munafurceta tayi mata kyakkyawan zato ta ci amanarta, Allah kaɗai ya san lokacin data ɗauka tana bin baza, ko komai nata zai ƙare ba zata taɓa barin Bar Aliyu Sufyan Alhassan ya kasan inuwa guda da Jeederh ba.
Ta dunƙule hannu tare da kaiwa iska naushi cikin zafi ya juya yana faɗin.
"I can't take it any longer Majeederh, dole kiyi haƙuri mu zama abu guda" shiru not respond.
Ya riƙe ƙugu cikin sauke numfashi yana son ya saisaita kan shi ya kasa ya ce. "Ina son na je wajan Dr Jamal, i have something to discuss with him" nan ma shiru sai a lokacin ya juya zai sake kiran sunanta yaga wayam! sai gado da drip yana ɗiga a ƙasa.
Baki buɗe ya tsaya cak yana ƙarewa room ɗin kallo kamar ƙungi.
"What?" Cikin sauri ya buɗe ƙofa ya fita suka ci karo da wata nurse ya ce
"Heee Nurse" "Yes, Sir how can i help you?"
Ya juya idanunsa ya yi ta kallon wajan yana son yaga ta ina zai gano Jeederh. "Sir!" Kiran ya dawo da shi hankalinsa ya ce "Kinga wata yanzu da baby a hannu ta fita?" Ta shiru alamar tunani sai kuma ta ce.
"Yanayinta?" Ya ce "She's beautiful, fara tas yar yellow take tana da jiki zata kai 35 yrs going to 36" Ta kalli hanya ta ce
"Oh Malama Majeederh Abdul'aziz Khan?" Ya ɗaga ya ce "Exlty, where she's?" Ta ce "She Left, alright"
Ya yi baya a fili ya ce "Innalillahi wa'inna ilahir raji'un, why? why Jeederh mun shiga uku daga ni har ke" da gudu kuma yabar world ɗin ya nufi reception har zuwa parking lot na hospital ɗin amma babu ko mai kama da ita.
Motarshi ya shiga tare da yi mata key kamar zai tashi sama haka yabar cikin asibitin bakiɗaya wanda ya yi kwana Uku ciff a cikinsa.
Dr Jamal na zaune a office ɗinsa yana operating system sai gumi yake duk da sanyin A.cn dake office ɗin. Bell aka danna ya ce "Come in" buɗe Ƙofar akai tare da shigowa.
"Dr Jamal wai meke faruwa da kai ne, kwana uku baka cikin hayyacinka" ya share zufa ya ce "Tajju ina cikin damuwa"
"Problem?" Tajju ya maimaita. Dr Jamal ya gyara zama ya ce "Ka san Malama Majeederh Abdul'aziz Khan?" Gaban Tajju ya faɗi hakan ya tuna masa da wasu memories ya ce "Uhm, ina jinka" kai tsaye Dr Jamal ya ce "Ta haihuwa, kuma yanzu an nemeta an rasa, kwana kenan bana barci kullum sai na duba all scanning da na taɓa yi mata, wallahi tsayin shekara biyu result bai taɓa nuna mini Majeederh nada ciki ba ko da wasa, infact results ɗin na nuna she's Good, sai a satin nan dana sake mata wani ya nuna mini ƙari ne a cikinta shi ne ya haddasa kumburin Cikin, sai gashi kuma wai ta haihu harta gudu" cikin wata kalar hausa Tajju ya ce
"Innalillahi, subuhana"
Ya yi ta maimaita wa kafin ya ce "Amma tayi aure?" Dr Jamal ya ce
"Ko engagement ba tayi ba balle aure, bata taɓa aure a zahiri ma babu wani ɗa namiji daya taɓa cewa yana son ta"
Tajju ya miƙe ya shiga kai kawo cikin office ɗin da sauri kuma ya fice yana cewa "ina zuwa"
Yana fita mota ya shiga ya nufi gidan shi dake cikin Nassarawa. Tun da ya shiga bedroom yake tunani,akwai muhimmin abu da yake son tunawa amma ya rasa mene? Dr Jamal abokin Tajju ne gabaɗayansu likitoci ne.
A hankali ya ce "Malama Majeederh Abdul'aziz Khan? Ya Allah!"
Kwanciya ya yi nan take barci kuma ya ɗauke shi.
Can cikin barcinsa ya ci wasu maganganu na tashi a kunnenshi a firgice ya farka yana haɗa zufa jikinsa na rawa ya ce.
"Gang" ya miƙe ya ce "Gang team!" a haukace Tajju ya dinga fito da kayan wardrobe nasa cikin sa a wata envelope ta faɗo ya ɗauka da sauri yana dubawa, har yanzu wani sassan yan ƙamshi ke tashi jikin envelope ɗin, ya duba da kyau idan har ba zai manta ba shekaru biyu kenan da bashi saƙon ya bawa Majeederh, shi kansa ba zai iya tuna abin da ya mantar da shi ba. A hankali ya duba jikin envelope da aka rubuta.

*_No words to explain, no words to describe, no words to as your forgiveness, Wait for me, I'll be back sooner or later, Please Jee_*

Tajju na gama karantawa ko gyara bedroom ɗin bai ba ya zari key ɗin mota tare ficewa daga cikin gidan, tana ina zai fara? Ina zai ga Malama Majeederh har ya bata wannan saƙon? A fili ya ce "Allah na tuba, ban san me ya mantar dani ba" haka yaci gaba da driving.
Tun safe Majeederh take tafiya fuska rufe babyn ya yi shiru a jikinta, kamar mahaukaciya haka ta zama bata gane komai bata bambance komai, kiran sallar Magriba ya yi daidai da tsayuwarta a gefen wani shago a lokacin kuma babyn ya kama kukan yunwa, ta samu waje ta zauna ta shiga kallon fuskar jaririn ko Allah zai sanya ta gane dawa yake kama, amma abin mamaki komai nata ne, kamarsa ɗaya sak da ita idanunsa ne kawai da bai fiya buɗewa ba yasa bata gama gane ƙwayar tawa ba, ganin kukansa zai sanya hankalin jama'a ya dawo kanta ya sa ta zura shi cikin hijabi bata san me zatai masa ya daina kuka ba can ta tuna abincinsa yana jikinta ta ɗaga rigar asibitin dake jikinta tare da sanya masa nono a baki, babu ruwa ko kaɗan zai azabar zafi, haka ya dinga jan fata jin baya shan komai ya cika ya dinga tsala ihu. Sai a lokacin ta fashe da kuka take rungume shi ta ce.
"Asstagafirullah Ya Allah, ba san komai, na yarda da ƙaddara, Allah ka kawo mini ɗauki albarkacin Annabin rahama" a hankali ta dinga tattaro yawun bakinta tana bawa jaririn yana sha, tun tana bashi har yawun ya ƙafe bai kuma daina kuka ba. Ta miƙe riƙe da shi tare da ƙara sawa wajan shagon tayi sallama can ƙasa kafin tayi magana ta ji saukar muryar Abbu a kunnenta ta juya da sauri ta kalli T.v dake shagon, fuskar mahaifinta tar a t.v yana yi wa ƴan jarida bayani ya ce.
"Me kuke son sani?" Ɗan jaridar ya ce "Shin da gaske ne ƴarka Malama Majeederh Abdul'aziz Khan kan ta haihu? bayan duniya ta san bata da aure? Ko dai tayi aure a ɓoye ne, ko kuma zargin da ake a kanta ya tabbata?" Abbu ya yi dariya sosai yana kallon Ɗan jaridan ya ce.
"Ina da ƴa Majeederh, amma tawa yarinyar ta zama gawa tun tuni bata raye, ban kuma san yarinyar dake amfani da sunana da kuma sunan familyna ba, zan yi amfani da wannan damar wajan yi mata Allah ya isa har abada, zan kuma shaidawa duniya duk inda suka samu yarinyar nan mai amfani da sunana su jefe ta ko kuma suyi mata bulala akan laifin aikata zina, su kuma ɗauki mataki akan amfani da rigar Muslunci tana aikata alfasha"
Ɗan jaridar ya kalli Abbu sosai, da alama ya firgita da maganganun shi ya ce. "Kenan Malama Majeederh ba ƴarka ba ce wacce muke tunani?"
Cikin tsawa Abbu ya ce
"Yara biyar ne kaf duniya, tawa Majeederh ta zama gawa tun da jimawa bana son wata tambaya bayan wannan" a firgice Majeederh ta dafe ƙirjinta da yake wani bugawa jajirin ya nemi suɓucewa ta shiga kokawa da numfashinta, wani abu mai nauyi ya tsaya mata a ƙirji Idanunta suka tsaya ƙam akan fuskar mahaifinta tunani take ko dai da gaske bashi ya haifeta ba? Mai shagon ya girgiza kai ya ce.
"Kai duniya, kai duniya wai yanzu aikata zina ya zama ruwan dare? Matan aure su aikata zina, ƴan mata su aikata zina, zawarawa su aikata zina, mijin aure ya nemi matar wani, matar aure ta nemi mijin wani? ga Fyaɗe daya ya waita, ga matsalar tsadar abin duniya, ga rashin nefa ga rashin ruwan sha, albashi wannan sai a shige wata ba a biya, wani lokacin ma a rage albashin, ga yawan aibata Musulunci yanzu Fisabilillahi a kaf garin nan waye bai san Malama Majeederh Abdul'aziz Khan babbar malamar musulunci ba ce? waye bai san irin tallafin da take bawa Muslunci ba, waye bai san wa'azin da ta kewa masu aikata alfasha ba, sai gashi ana zaton wuta maƙera sai gata a masaƙa, shi ya sa ake cewa kayi amfani da faɗar Malam kada kayi amfani da abin da yake aikatawa, wallahi ko ki aka bani dama sai na jefe wannan shaiɗaniyyar" Lawan ya girgiza kai ya ce "A'a Bala, amma dai Allah ya kyauta!" Bala ya ce "Amin, shi ya sa taƙi aure tana ta zuba alfasha, kasan daman duk wani mai aikata zina aure bai dame shi ba, kuma ko ya yi aure ba zai daina yin abinda ya saba ba"
Malama Majeederh bata tsaya neman ruwan ba, ta juya da sauri tare da barin wajan a lokacin ji take kamar ta shiga duniya, kamar ta zama ƙaruwar da suke danganta ta da ita, ji take kamar ta zama sanadin lalata sunan mahaifinta dana familyn da yake nesa ta da shi gudun kada ya ɓaci, zuciyarta ta ƙe ƙashe duk damuwarta ta tsaya, lokaci zuwa lokaci take jan numfashi ta sauke sbd abinda ya tsaya mata a saitin zuciya da maƙo shinta. Tayi tafiya mai nisa sosai kafin ta samu wani waje kusa da wata bola ta zauna ta rungume yaron wanda ya yi shiru, jikinsa ya ɗauki zafi. Ji take kamar ta rataye kanta, ga jinin haihuwa daya gaba ɓata mata jiki a haka barci ya ɗauketa.
Tsaye suke gabaɗaya a parlour Hajia ta girgiza kai ta ce "Me kayi haka Zaki? Me ka aikatawa kan ka haka Aliyu?"
Almustapha ya kalli news paper ɗin ya ƙara ware idanunsa akan photon Bar Aliyu Sufyan Alhassan da kuma photon Malama Majeederh Abdul'aziz Khan dake zaune fuskarta rufe da liƙab. Almustapha ya shiga karanta headline ɗin jaridar. "Bar Aliyu Sufyan Alhassan shi ne ya aikata zina da Malama Majeederh Abdul'aziz Khan, tare da saninta domin su wulaƙanta matar Aliyu wato Latifa Omar kasancewarta aminiyar Jeederh" ya karanta a fili cikin zafin nama da faɗa Almustapha ya ce "Wanne shirme da hauka ne haka Aliyu? Zina? Ɗan shege?" Aliyu ya kalli yayan nasa ya ce..
"Ba shege bane" "To uban mene? Aurenta kayi?" Aliyu ya ce "Ko ɗaya, ina son ta am ready to marry her, ɗa kuma ba shege ba ne" Almustapha ya ɗauke Aliyu da mari ya ce
"Mahaukaci, to kayi gaggawar zuwa gidan jaridar nan ka ƙaryata rubutun su, ina da tabbacin kuma matarka Latifa Omar ce tayi wannan aikin ai a gidan jaridar take aiki"
"Tayi dubun su, ba zai sauya mini ra'ayi ba"
Cewar Aliyu. Almustapha ya ƙara ɗaga hannu zai mari Aliyu,cikin sauri Aliyu ya riƙe hannu ya ce
"Kasan Allah ka ƙara marina zan karya hannunka,ka bar ganin kai yaya na ne, idan kun shirya korata kamar yadda Mahaifin Majeederh ya koreta fine I'll leave the house" abu kamar wasa dambe ya sarƙe tsakanin wa da ƙani cikin ɓacin rai Hajia ta zabgawa Aliyu mari ta ƙara zabga masa mari ta ce "Ka nutsu Zaki, ka nutsu" Aliyu ya fashe da kuka ya rungume Mahaifiyarshi ya ce
"What should I do Hajia? Dame zan ji ne? Wallahi idan kuka matsa mini zan iya aikata komai, Hajia I love Majeederh don Allah ki nemo mini ita, hajia hajia....,"
Da Hajia da Almustapha su kayi kan Bar Aliyu Sufyan Alhassan wanda ya faɗi a ƙasa sumamme...

Government House
Labarai ake ta ko'ina gabaɗaya kuma akan Malama Majeederh Abdul'aziz Khan ne, Human rights sun shiga maganar, ƙungiyar mata ta shiga maganar, shugaban ƴan hisba. Ya sauke ɓoyayyiyan numfashin tare da juyawa kaɗan ya kalli tulin jaridun da aka wallafa, gefe guda kuma yana mamakin gidan Jaridar Hausa lastest News, domin sun fi ko wanne gidan jarida ɗaukan zafi da kuma aibata Malama Majeederh. Sama sama yake kallon photon ta, bai taɓa ganinta ba amma muryarta kullum tana yi masa amsa kuwwa a kunne. "Ham...mad" Hammad ya yi sauri ya rusuna ya ce
"Your excellency" "Waye me wannan Shirman?" Hammad ya ƙara yin ƙasa ya ce "Wata ƴar Jarida ce, Latifa Omar"
Abu-turab ya ce.
"A dakatar da gidan jaridar" with so much respect Hammad ya ce
"With pleasure Your excellency" ya jinjina kai kawai, Hammad ya juya cikin sauri. Kai tsaye akai sanarwar da yawun Gwamna tare da bada umarnin rufe gidan Jaridar. Abu-turab ya kasa komawa gida, tun safiyar yake jiran ya ji ance an samu Malama Majeederh Abdul'aziz Khan amma shiru har biyar na yamma ya yi. Tajju ne ke driving hannunsa riƙe da Envelope yana ta yawo amma bai samu Majeederh ba, gashi har an kwana wani daren na shirin yi kamar ance masa ya juya idanunsa ya sauka akanta tana nan zaune bakin bolar ta ƙanƙame jaririn kamar za a kwace mata shi, ta fita hayyacinta duk jini ya ɓata jikinta, cikin sauri Tajju ya gangara gefen titi tare da yin parking yana Hammadala a ransa ya fito,bai san mene a envelope ɗin ba amma yasan dole yana da alaƙa da wannan jaririn babu ko tabbata musamman yanzu daya tuna wata rana. Yazo daidai tsakiyar titin yana ƙoƙarin tsallakawa wata ƙatuwar tifa tayi awon gaba da shi....


#Bar Aliyu Sufyan Alhassan
#Dr Jamal
#Abu-turab


Na'ima Sulaiman Shu'aibu
08119237616
Not editing*🌈 MIJIN MALAMA🌈*


Nimcyluv Sarauta

*_Please kuyi following Acct ɗina a arewabooks🫰🏿_*
https://www.arewabooks.com/u/nimcyluv


*AN SAMU MISTAKE, WANNAN SHI NE FULL PAGE NA 4 KUYI SHARING, A GOGE WANCAN🙏🏿*

*4......*
Mummunan hatsarin ya ja hankalin mutane da yawa, hatsari ne wanda za a iya cewa tsautsayi ne da kuma gangan cin driver da yake driving yana waya. Da gudu babbar mota tayi gaba bayan tayi wurgi da Tajju zuwa gefe guda, nan take kan Tajju ya fashe jini ya fara zuba hannunsa guda ɗaya ya fita fit daga jikinsa ko shurawa bai ba rai ya yi halinsa. Motar dake bin bayan babbar motar data buge Tajju ce ta tsaya, cikin sauri driver da wanda yake gefen mai zaman banza suka fito bakinsu ɗauke da sallati "General kira mana Ambulance" cikin sauri General ya ɗakko wayarsa tare searching asibiti mafi kusa da kuma motar asibitin. Hammad ya ce "Allah sarki, haka rayuwa take Allah ya jiƙansa ya yi masa rahama" General ya amsa da "Amin" da sauran jama'ar wajan suka amsa.
Har Hammad zai juya idanunsa ya sauka akan Envelope dake can gefe guda iska na kaɗata a hankali ya ƙarasa tare da ɗauka, a ransa yana tunanin maybe a samu wani bayanai akan mamacin. Ya ware Envelope ɗin first abin da ya gani shi ne ring irin na al'ƙawarin nan, ya juya ring ɗin sosai sai kuma ya zura acikin aljihu, gently idanunsa ya sauka akan headline na wasiƙar kamar haka.
*_BAD MAN, THE STUBBORN BOY, CRIMINAL, GANG BOY, THE LEADER_*

Daga wannan rubutun idanun Hammad ya sauka ƙasan headline ɗin inda aka rubuta “The memories, was going on my mind, har abad, nasan ni mahaukaci ne da gaske kamar yadda ki ke faɗa Jee” jikin Hammad ya shiga rawa ganin General na ƙara suwa ya tura wasiƙar Aljihu "Lafiya?"
"Actually, good"
Kafin suyi magana Ambulance ta ƙara su aka ɗauki gawar Tajju tare da sanyata ciki, Hammad ya buɗe ya ɗauki wata number da yaga ana ta kira anyi saving da "Bad boy"
"His phone" cewar Hammad bayan kammala komai Ambulance suka tafi asibiti da shi. Suma su Hammad mota suka shiga driving kawai yake amma tuni ya yi losing mind ɗinsa, fatan sa kawai ya isa Gov. Abu-turab Alƙasim, ya san cewa yanzu ya koma gida kasa jurewa ya yi ya ɗauki Wayarsa tare da kiran keɓantacciyar number Abu-turab kusan kira uku kafin ya ɗauka cikin nutsuwa ya ce.
"Uhm" Hammad ya ce
"Your Excellency, akwai damuwa" a taƙaice ya ce
"Kace komai, banda rasa Majee" cikin ladabi ya ce "Am very sorry for that, amma bamu sameta ba, amma mun sami maganin matsalarta, ɗan

Please Login or Register in order to submit comment