Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
"ka ga Aliyu ka fita idona bana son kana min hka a gidan nn ita wacece da baxata shiga kitchen ayi girki da ita ba, ta fi wani ne a gidan nn, ko idan ta tafi gidan mijinta ni xan bi ta ina mata girki?" Murmushi Aliyu yyi yace "sae mijin ya yafe mata girkin Mami," wani harara ta balla masa tace "Ka fita harkana fa, kuma ta fito idan ba hka ba in sa Adnaan ya daure min ita yyi mata shegen bugu" Juyawa Aliyu yyi yana hararan Adnaan, Adnaan ya fice daga dakin kmr xae tashi sama, Aliyu ya juya yana kallonsu Jiddah yace "ku bar dakin nn kar in taka ku" ficewa suka yi da sauri, Mami tayi kwafa ita ma ta fice tana cewa ta fito ta samesu kitchen idan ba hka ba sae dae ta ci bbu yau a gidan nn. Suna fita Afeefah ta bude kofar bayin, ta fito tana turo baki, ya Aliyu yyi murmushi ya kama hannunta ya nufi dakinsa da ita, har aka gama girkin rana Afeefah bata fita ba, Mami ta kwashe rabonta ta kara ma mai gadi Jiddah ta kai mashi, sadiya na kai ma ya Aliyu nasa a daki yace "Na Afeefah fa?" Tace "ina jin yana kitchen" yace "to dauko Mata," kai ta gyada masa ta fice duk da tasan bata da rabo, sae da ta isa falo ta fara dariya, ganin sadiya bata dawo ba yasa yace taje ta dauko abincin ta a kitchen da kyar ta yarda ta fita wae Mami xata doketa, tana shiga kitchen taga bbu komae an ma wanke tukunyar, ta koma sama kmr munafuka tace "sun cinye yayanmu" murmushi yyi yace "je dauko spoon ki xo mu ci nawa," kitchen ta koma ta dauko spoon suka ci a tare. Da yamma tana kwance dakin ya Aliyu tana kallo shi kuma yana dakin Mami wayarta ya soma ring mikewa tayi xaune ta dauki wayar gabanta na faduwa, wnn nmbr jiyan nn ne dae, sau uku yana kiranta yau bata dauka ba, mikewa tsaye tayi ta nufi dakinsu da gudu ta mika ma Jiddah wayar tace "Aunty Jiddah ki daga ki tambayi waye don Allah" karban wayar tayi tana kallon nmbr snn ta daga tayi shiru, jin anyi sallama yasa tace "wa ke magana wae," "ba da ke nake son magana ba, mika ma Zainab wayar" kmr munafuka ta mika ma Afeefah wayar. Afeefah tace "wae waye yace maki" Jiddah tace "oho" kara wayar a kunnenta tayi ta hade rae yace "Hello" tace "ina jin ka?" Murmushi yyi jin ynda ta amsa mashi yace "Me yasa kika ba yayarki wayar, kina tsorona ne?" Girgixa kai tayi tace "sbda me xan ji tsoron ka, ae Allah shine abun tsoro?" Yace "yea gskya ne," ta hade rae tace "kar ka kuma kiran layina ni ban san ka ba" yace "amma ni na sanki" a fusace tace "a ina ka san ni?" Cikin sanyin murya yace "nasan ki a bayero da kuma jan bulo" xaro ido tayi da mmki amma ta kasa cewa komae, yace "are yhu there?" Tsaki tayi tace "toh ni ban san ka ba kada ka kuma kiran layi na" katse wayar tayi ta jefar kan gado, Jiddah tace "wllh ki daina irin hka, baki san ko wani irin mutum bne kawae yaje ya cuce ki a bnxa, gwara ki bi sa a hnkli ku rabu lfya" Afeefah kmr xata yi kuka tace "to ni ya xan yi, bace kada ya kuma kirana ya ki ji" Jiddah tace "a hnkli xaki bi sa har ya rabu da ke, amma kar ki masa wlknci ko ki gaya masa bakar magana baki san wani irin mutum bne shi, baki kuma san meye a xuciyarsa ba, Afeefah ta bata fuska tace "wayyo na shiga uku to ina ya samu nmbrna Anty Jiddah?" Jiddah tace "oho ta ya xan sani nima" Afeefah tace "to in gaya ma yayanmu?" Da sauri Jiddah tace "ke! Gaya masa to tunda baki sa hnkli, so kike ya kirasa kawae ya xaxxagesa ki ja ma kanki" Afeefah tace "to to baxan gaya masa ba ba ruwana" fice wa Jiddah tayi daga dakin da sauri jin Mami na kiranta Afeefah ta xauna kan gado a sanyaye gabanta na faduwa, to waye wnn mutumin kuma, da daddare tana dan dube dubenta a wtspp Msge ya shigo da wani sabon nmbr, kura ma nmbr ido tayi lkci daya ta gane na me kiranta ne, gabanta na faduwa ta bude Msge din tana kallon sallamar da yyi mata, dakewa tayi ta amsa ko Allah xae taimaketa ya gaya mata inda ya Santa, bude Dp dinsa tayi da sauri tayi don ganin meye a kai, taga wata kyakkyawar yarinya rike da cake me kyau alamar birthday tayi, kallon yarinyar kawae take don gani take kmr ta taba ganinta amma ta rasa a ina, can ta fita taga bae mata reply ba still, kin sauka tayi tana jiran reply din, har bayan kusan minti takwas snn reply ya shigo, "ba ki yi bacci ba? Yhu re suppose to b readin ur book fa, who are yhu chattin with this late?" turo baki tayi ta mayar masa da cewa "Don Allah where did yhu get my contact frm, don Allah na ce" sae bayan kusan minti biyar reply ya shigo, "Go offline now!" Tsaki ta dan yi tana mmkin irin command din kmr ta san shi, reply ta mayar masa tace "ba ka ma Allah knn?" Lkci daya ya mata reply da cewa "to wa ke xan ma idan ban ma Allah ba, common go offline my frnd, idan baxa kiyi karatu ba ki kwanta kiyi bacci nd stop wasting ur tym here" ji tayi kmr ta saka kuka don takaici, gashi tana tsoron masa musu da ta tuno maganganun Jiddah, "OK" kadae ta mayar masa snn ta sauka ta kashe data ta jefar da wayar gefenta tayi kwanciyarta. Washegari kmr jiya vibration din wayar ta ne ya tasheta, ta jawo wayar da kyar tana kallon screen, din ta wara ido da sauri ganin lambar, samun kanta tayi da dagawa daga daya bangaren taji yace "almost tym for sallat baccin ya isa hka Madam" takaici ne ya isheta cikin bacin rae tace "to Ca nayi maka bbu masu tashi na ne a gidan mu" a nutse yace "ban ji ba, me kika ce" tsoro ne ya kamata tace "Ca nayi nagode, ynxu xan tashi" yace "OK" snn ya katse wayar. Da safe suna xaune dinnin suna breakfast, da ke ranan Saturday ne har da Adnaan da ya Aliyu Mami ce kadae bata dinnin din, Sumayya tace "ya Aliyu wnn hutun ka dde sosae" Afeefah ta galla mata harara tace "just two wk shine xa ki ce ya dde...." Wayarta da ke vibrate ne yasa tayi shiru tana kallon screen din wayar, ta dago kai tana kallon Jiddah da ta tabe baki ta ci gaba da shan tean ta, mikewa tayi ta nufi stairs da sauri, ya Aliyu ya bi ta da kallo, dakinsu ta shiga ta daga kiran kan ya katse ta kara a kunne, "Ae nayi xaton baxa ki daga ba" murguda baki tayi kmr yana ganinta ta ki cewa komae, "Zainab!" Ta amsa da "Na'am," yace "Gud mrnin" da kyar ta iya mayar masa da gaisuwar, yace "kinyi breakfast," girgixa masa kai tayi tace "shi nake yi" yace "okk srry, sae anjima" ji tayi an bude kofar dakin ta katse wayar da sauri ta juya tana kallon ya Aliyu, yace "wa ya kira ki?" Kame kame ta soma yi tace "yayanmu, kaga dama yayanmu Maryam kawata ce ta kirani," a nutse yace "karya kike, tell me the truth wa ya kira ki" muryarta na rawa tace "Ita ce yayanmu" ya fi minti biyar yana tsaye yana kallonta snn ya fice daga dakin, ta sulale kan gado ta xauna tare da sauke ajiyar xuciya, hka ta karashi mid break a gida a kullum xa a kirata sau hudu sau biyar kuma bata kin dagawa sbda abinda Jiddah ta gaya mata sae dae har lkcn ya ki gaya mata waye shi, kiri kiri ta daina hawa wtspp sbda shi don da ta hau xae ce ta sauka barin da nyt, gashi bata iya masa musu. Ran Monday da yamma ya Aliyu ya kare hutunsa ya kama hanyar lagos, Washegari Tuesday kusan a tare suka shigo sch da Dr Sharif, Afeefah ta sunkuyar da kai bayan su Jiddah sun nufi department dinsu, har sae da ya karaso inda take snn ta gaishesa, ya amsa va tare da ya kalleta ba ya nufi office dinsa. Har ya dan yi nisa ya juya yana kallonta yace "come, xo ki gyara min office" kmr munafuka ta bi bayansa ya bude office din suka shiga, yace "Just 10 mins ki gama gyara min office kafin in dawo" yana kai wa nn ya fita ta fara abinda ya sa, har ta gama bae dawo ba, ta gyara masa kan table dinsa ta jera masa duka buks dinsa gu daya, snn ta nemi guri ta xauna, har kusan takwas da rabi bata gan shi ba gashi suna sa lecture, taji kmr tayi kuka, sae kusan Karfe tara da rabi ya shigo yana kallonta yace "srry na je clinic ne, you've missed ur lecture koh?" Hade rae tayi bata ce komae ba ya karaso ya xauna yace "Wani lecture ku ke da shi" kanta a kasa ta gaya masa yace "to fiddo littafin kiyi karatu" mikewa tayi yace "ina xa ki?" Tace "xan fita in je inyi" yace "sit, kiyi a nn wajen" komawa tayi ta xauna kmr xata yi kuka snn ta fiddo littafin, shi dae sae kallonta yake ta farin glass din idonsa, can bayan minti kusan bakwae ta saci kallonsa taga idonsa na kan wani littafi, ta sunkuyar da kanta, bude kofar aka yi aka shigo da sallama Afeefah ta kafa ma yarinyar ido, yarinyar ta karasa kan table din tana cewa "yaya don Allah ka xo kayi ma baba sanusi magana, ka ji wae baxae kai ni ba yawo nake son xuwa" kallonta kawae yake ta ajiye basket din hannunta ta marairaice, Ya ajiye pen din hannunsa yace "Ummi ta sa ni ne" tace "ta sani mana, kawae shi sae ya dinga min abinda ya ga dama," mikewa Dr Shariff yyi yace "mu je" yarinyar tayi gaba yana biye da ita a baya, Afeefah ta bi su da kallo snn ta fiddo wayarta da sauri ta duba Dp din mutumi me kiranta taga hoton yarinyar ce a kai, duk sae tayi confuse tana tunanin to ko Dr Sharif ne ke kiranta, amma ae bae da nmbr ta, dubara ce ta xo mata tayi dailin nmbr dake kiranta, cikin second biyar wayar Dr Sharif da ke kan table ya soma ring, still tayi tana kallon table din, jiki ba kwari xata karasa table din ya shigo office din, juyowa tayi da sauri, yana kallonta yace "kina neman abu ne" girgixa masa kai tayi a daburce tayi saurin katse kiran da take masa, ya karasa table din yana kallon wayarsa murmusi dauke fuskarsa yace "lfya kike kirana" sunkuyar da kai tayi a hnkli tace "Sirr," Karasowa gabanta yyi yana kallon fuskarta yace "ya aka yi" kin bari su hada ido tayi murya can kasa tace "kayi hkuri ban san kai bne ba" murmushi yyi yace "to ynxu kin sani koh?" Juya masa baya tayi da sauri ta rufe fuskarta, ya nufi kujera ya xauna ya jawo basket din da Kanwarsa ta kawo masa ya shiga hada coffee, Ita dae har lkcn bata juyo ba, can ta nufi kofa tace "Na tafi Sir" a nutse yace "Zainab!" Juyowa tayi tana kallonsa snn ta karasa table din tace "gani sir" kujera ya nuna mata ta xauna snn ya mika mata mug din coffee. Girgixa masa kai tayi kanta a kasa tace "Ngd sir" jin bae ce komae ba yasa ta dago kanta a hnkli ta ga kallonta yake, sauke idonsa yyi daga kallon nata ya ajiye mata gabanta yace "je ki xubar a waje to" murmushi tayi ta dauki mug din a hnkli ta kai bakinta, rabi ta sha ta ajiye ba tare da ta kallesa ba tace "na koshi Sir" bae ce mata komae ba ta mike kanta a kasa tace "Sir I want to go nd read for test" yace "OK" snn ta fice daga office din. Ana gama sllhn Azahar Afeefah ta nufi lecture hall dinsu da Maryam, Maryam ta xauna kujerar gaba Afeefah tace "ke test fa xa muyi, mu koma baya" Maryam ta xaro ido tace "wani test?" Afeefah tace "na Dr Sharif mana" harara Maryam tayi Mata tace "ke wa ya gaya maki" Afeefah tayi shiru da dan mmki tana kallonta, sae a snn ta tuna ashe fa ita kadae ya gaya ma, "wllh nayi xaton kin sani, kuma bamu hadu yau bne da na gaya maki" Maryam tace "kin kyauta ae, da ni ce da na kira ki" bata jira cewar Afeefah ba ta nufi seat a baya, Afeefah ta bi bayanta sanin bata kyauta mata ba, gefenta ta xauna ta marairaice tana bata hkuri, Dr Sharif ya shigo hall din, tsit kke jin hall din bayan minti daya kowa yyi settle down, Dr Sharif yace "I will b conducting my last test today, hope yhu all are ready" kallonsa students suke da mamaki, bae damu da hka ba ya bukaci duk su fito da jakansu da any material da suka san is nt proper to b with dem while writtin his test, mikewa Afeefah tayi ta karbi jakar maryam da nata bayan sun dauki pen da takardar sa za suyi test din ta nufi front din hall din ta ajiye, hada ido suka yi ta dauke kai da sauri ta bar wajen ya bi ta da kallo, dictating questions din yyi masu snn ya basu time yace "this my last test, any one dat misbehaves I will cancel all the test he has done so far, I strictly warn yhu once more to respect ur selves" tsayuwarsa yyi bakin kofa yana danna wayarsa, bayan minti goma Afeefah ta juya tana kallon Maryam ta ga guda biyu kadae tayi ta ajiye pen, kallon Dr Sharif Afeefah tayi taga wayarsa yake danna wa, murya can kasa tace "kawo in rubuta maki 2 nd 4 a bayan paper da pencil sae ki goge da eraser" Ganin maryam bata tanka ta ba yasa ta mika mata papern nata gaba daya tace to gashi ki kwafa, nn ma bata ce komae ba, hkn yasa ta daga kai tana kallonsa ta ga kallonta yake, ajiye takardarta tayi da sauri, Dr Sharif yace "stand up" a hnkli kmr me shirin kuka tace "am srry sir" wani kallo ya watsa mata ba shiri ta mike ya nuna mata kofa alamar ta xo ta fita, kmr xata yi kuka ta nufi gaban class din tace "sir plss am srry i...." Tsawa ya daka mata yace "out!" Jakarta ta dauka ta fice daga class din ta nufi main gate, ta rasa dalilin da yasa bata yi kuka ba, cukuikuye takardar test din nata tayi ta jefar snn ta tsaida adai daita sahu ta hau ta tafi gida abunta. Eeshatullah Goni๐Ÿ˜˜๐Ÿ˜˜ [5/22, 07:56] Umar Dalha: Ya mace kyautar Allah A true life love story By Ashmaad 29..... Mami na kitchen Afeefah ta shigo gida, Mami tace "Har kun tashi?" Afeefah tace "ehh," snn ta gaisheta ta nufi sama, kwanciyarta tayi bayan ta jefa jakarta kan gado, nan da nan bacci ya dauketa, vibration din wayarta da ke jakarta ne ya farkar da ita ta mike xaune tana mitsika ido ta jawo jakarta ta bude ta ciro wayar, tana kallon me kiran nata, Nmbr Dr Sharif ne, ta yi tsaki ta ajiye wayar ta koma ta kwanta. Da daddare tana gugan Hijabbanta wayar ta ya fara vibrate ta dauka tana kallon me kiran taga Nmbr Dr Sharif ne still, sae da ya kusa katsewa snn ta daga, ta kara a kunne tayi shiru, "kin ga dama knn" nn ma shiru tayi masa, yace "Zainab!" Kin amsawa tayi se da ya kuma kiranta tace "Na'am" hade da murguda baki, "me yasa na kira ki daxu ba ki daga ba" a takaice tace "bacci nake" yace "koh" shiru tayi masa, ya dan yi murmushi yace "yhu will explain dat tomorrow," katse kiran yyi, ta ja dogon tsaki ta ajiye wayarta ta ci gaba da abinda take. Tun daga ranan Afeefah ta soma wasan yar buya da Dr Sharif da ta gansa xata gudu ta canxa hanya idan ya kira ta ki dagawa, duk inda tasan xae ganta daina xama tayi a gun, in suna da lecture dinsa to ranan da wuri xata wuce gida, masallaci ma Dena xuwa Wanda xa su hadu tayi, sbda shi ta goge wtspp a wayarta, sae dae fa ynxu kukan ta ya ragu ssae har aka dinga Mamakin hka a gida, sau da yawa Maryam kan tambayeta wae me ya hadata da Dr Sharif take gudu idan ta gansa, sae dae tace bbu komae, ana hka suka fara Shirye shiryen exams, ana saura sati daya exams dinsu Afeefah na xaune gaban department dinsu da su Maryam an gama tsula ruwa knn, duk ta sakankance ranan dr Sharif bae xo ba don bata ga motarsa a parkin space ba kawae ta hangosa yana tahowa da wani student da alamar lecture ya fito, mikewa tayi da sauri ba tare da ta lura da wani katon dutse dake gefenta ba xata falla a guje ta buge kafa da dutsen sae ga ta kasa cikin ruwa, lkci daya ta fasa ihu uwa wata jaririya tana cewa wayyo kafarta, su maryam tuni suka mike a rude, Maryam ta fara kkrin dagota amma ta kasa don kin tashi tayi, Dr Sharif ya karaso gun da sauri shi ya dagota ta fashe da wani matsanancin kuka tana cewa wayyo kafarta, office dinsa ya nufa da ita ya sa ta xauna kan kujera har lkcn tana kuka, yana mata mugun kallo yace "ni dodonki ne da xaki dinga gudu idan kin gan ni Zainab? An ce maki ina da lkcn ki, listen daga yau kika kuma gudu idan ki ka gan ni, I will make yhu spell doom" kuka kawae take tana yarfe hannunta, a dan tsawace yace "pull off dat hijab my frnd" tana kuka ta fara kkrin cire hijab din don duk ruwa ne da datti, yyi tsaki ya mike ya nufi first aid box dinsa ya dauko ya dawo gabanta ya durkusa yana kallon kafarta da ke jini amma ya kasa taba kafan, yace "ina ke maki ciwo?" Ankle dinta da toes ta nuna masa da kneel, ya rasa ynda xae ce ta daga skirt din ma, kawae ya Mike ya nufi table ya dauki wayarsa, wata nurse ya kira tana dagawa yace "kina duty ne pls farida" ta amsa masa da tana gida, yace "OK plss ki xo Buk ynxu, over to my office wata student dina ce taji ciwo xa kiyi mata dressing" tace ga ta nn xuwa, yace "olryt tnxx" snn ya katse wayar, kanwarsa teemah ya kira yace "Fatima plss ki taho sch ynxu da spare hijab din ki" bae amsa tambayoyin da take jefa masa va yace "just come over" snn ya katse kiran ya dawo kusa da Afeefah dake hawaye har lkcn, ya daure fuska yace "srry" kae kawae ta gyada masa a hnkli ba tare da ta kallesa ba, yana tsaye kanta har Nurse Farida ta shigo office dinsa da sallama yyi welcoming dinta, Nurse Farida ta duka tana kallon kafar Afeefah yace "garin ya hka" Dr Shariff yace "she's runnin ne" yar dariya Farida tayi snn ta shiga fiddo kayan da xata gyara mata kafar a first aid box, yace "ki duba mata ankle dinta ma its hurting her" kuka Afeefah ta fara ganin matar ta tsoma cotton wool tace "na shiga uku sir kace ta min a hnkli xae min xafi" harara ya balla mata yace "Naki" da kyar ta bari nurse Farida ta wanke mata kafar tana kuka, ya fita don bata waje ta duba mata knee dinta, nurse Farida ta ga gurjewa kawae tayi shima ta wanke mata snn tace "to sannu an gama yan mata" Afeefah ta share hawayenta ta mike xata sa hijab dinta ta ji ta kasa tsayuwa da toes dinta ta koma ta xauna da sauri tace "xafi" matar ta kuma duba kafar tace "kin yi targade knn" kuka ssae Afeefah ta dinga yi tana yarfe hannu, nurse din ta fita ta kira Dr Sharif tace "Doctor tayi targade ne fa" kallon kafar kawae yake snn ya karasa ya duka kusa da ita yace "Sae an kai ki asibiti knn" Afeefah ta fashe da kuka tace "Sir ni ba sosae fa yake min ciwo ba" nurse Farida tace "Haba Dr ka gyara mata mana ba sae anje asibiti ba" girgixa kai yyi yace "su tafi asibiti dai" Dubu daya ya ba ma nurse din tayi transport bayan yyi mata godiya ta wuce, tana fita Fateema ta shigo, ledan hannunta ya karba ya ciro hijab din ciki ya mika ma Afeefah, ta karba kanta a kasa, Fatima tace "Yaya me ya sameta" yace "gudu take ta fada cikin ruwa" Fatima tace "eyya sannu" kasa dago kai Afeefah tayi, Dr Sharif yace "yhu can go, ko ba tare da driver kike ba," sallama tayi masa ta fita daga office din, ya kalli Afeefah yace "tashi in yi dropping din ki a gida, sae ki fadi kinyi targade a kai ki clinic" mikewa tayi ta dauki hijab dinta ta linke snn ya fita daga office din bayan ya dauki car key dinsa ta bi bayansa tana dingishi, har kofar gidansu ya ajiyeta, kanta a kasa tace "ngd sir" snn ta bude motar ta fita ta nufi gate da kyar sae kuma ta tsaya tana yarfe hannu, Dr Sharif ya fito yana kallonta yace "ya aka yi?" Durkushewa wajen tayi Cikin kuka tace "ni baxan iya tafiya ba kuma ciwo kafata ke min" xae yi magana aka bude gate dinsu, Mami ta fito da Rahamah, Afeefah ta mike da sauri, Mami da bata ma kula da Dr Sharif ba ta bude baki tace "meye hka Zainab" kuka ta saka tace "Mami faduwa nayi a cikin ruwa a makaranta ynxu gashi bn iya tafiya sosae ba, shine ya dawo dani gida, ina jin kafar ya karye ne" Rahmah ta juya ta fashe da dariya, Mami ta hade rae tace "ke mahaukaciya ce da xa ki fada cikin ruwa Zainab," ta girgixa ma Mami kai tana hawaye, sae a snn Mami ta kalli Dr Sharif, kansa a kasa ya gaisheta ta amsa tare da cewa "mun gode bawan Allah" Afeefah ta karbe da sauri tace "kuma makarantar mu daya fa, shine ya kira aka sa min spirit da magani" tana kai wa nn ta nufi cikin gida da kyar tana dingishi, godiya Mami ta kara masa tace baxa ka shiga daga ciki ba, dan murmushi yyi yace "A'a mama, ngd" tace "To Allah saka da alkhairi" sallama yyi mata ya shiga motarsa ita kuma suka koma cikin gida da Rahmah don dama kasuwa xata rakata ynxu kuma bbu maganar xuwa kasuwan. Da daddare Afeefah na kwance daki bayan Mami tasa Adnaan ya siyo mata mugunguna a pharmacy ta sha kiran Dr Shariff ya shigo wayarta, jawo wayar tayi ta daga a dan kunyace tayi shiru, cikin sanyin murya yace "ya kafar Zainab?" A hnkli tace "da sauki," yace "kun je asibiti?" Tace "um um ni nace bna so," yace "to ae sae an ja maki kafar xae daina," tace "ni bana so ya dan daina" shiru ya dan yi snn yace "in kawo maki fruits xa ki sha," shiru tayi bata ce komae ba, yace "Zainab!" Tace "umm xan sha" yace "mama xata bari ki fito?" Nn ma ta dan yi shiru snn a hnkli tace "kila." Eeshatullah Goni [5/22, 07:56] Umar Dalha: ๐ŸŒธ๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป 'Ya mace kyautar Allah๐Ÿ‘ฉ๐Ÿป๐ŸŒธ A true life love story By Ashmaad 30...... Bayan minti sha biyar Jiddah ta shigo dakin tana kallon Afeefah tace "ke ana neman ki downstairs," Afeefah ta mike xaune tace "ni?" Tsaki Jiddah tayi tace "A'a ni" snn ta fice daga dakin, Afeefah ta mike tana kallon kafarta da ke mata ciwo har lkcn, kasa taka kafar tayi don wani shegen ciwon da taji yana mata, da kyar tana dingisawa ta fita daga dakin ta sauka kasa, xaune ta ga yarinyar a falo Mami ma na xaune falon da Adnaan, Da kyar ta karaso cikin falon tana dingishi Mami tace "wae kafar har ynxu?" Kmr xata yi kuka tace "ciwo yake min sosae Mami" Mami tace "to sae a tafi asibiti gobe" Afeefah ta dan yi Mamakin ganin kanwar Dr Sharif, ta kirkiri murmushi tace "sannu da xuwa' yarinyar ta mayar mata da murmushin tace " ya jikin" Afeefah tace "da sauki" Ledan hannunta ta ajiye tace "Yayana yace in kawo maki" Afeefah ta kalli ledan a dan kunyace tace "ngdd" mikewa yarinyar tayi tace "ni xan koma Mumy ana jirana waje" Afeefah tace

Chapter 7 of 30