yi ya amsa yana masu adawo lafiya da ameen abdallah ya amsa yayin da suke fita daga gidan,
abdallah ne yace" dama ana duka school ɗin ku wallahi dasai nasa yau anmaku dukan tsiya. "
"dan Allah ya abdallah kayi hakuri bazamu ƙara ba"
"kundai ci sa'a kawai ba'a duka da kungane kuranku yau da daga yau bazaku sake baccin safe ba, ace wai kuna bacci har school bus tatafi kuga yan hutu koh"
Kayi hakuri dan Allah wallahi baza mu ƙara ba"
, "ni da'allah kuyi man shiru sai bada hakuri sai kace masu tuban gagaskiya bayan nasan ƙarawa zakuyi" ya faɗa yayin da yake hawa kan titin ring road in da nan ne school ɗin su take bakin gate ɗin school ɗin yayi parking tare da cewa "kufito kuwuce ciki, fita sukayi suna yi mashi adawo lafiya Allah yasa yace motar yayi ma key yabar wajen tare da Kama hanyar hospital ɗin da ya
Episode 3_4
.
LITTLE ANGELS PRIMARY AND SECONDARY SCHOOL. shine sunan school ɗin
Kamar yanda school uniform ɗin suka kasance pink and white color haka paint ɗin school ɗin shima pink and white color ne.
Cikin school ɗin suka shiga Masha Allah school ce mekyan gaske ta yayan masu arziki Upstairs ce makarantar wanda ya kasan ce down na yara up kuma na manya ne, up stairs suka nufa domin an daɗe da gama ASSEMBLY shiyyasa suka nufa class, S. S. 3 shine class ɗin su , shiga sukayi ciki for master ɗin su suka samu yana ma shirin fita domin ya gama abunda ya kaishi.
"Aairah And Aaimah Muhammad hashim , why are you coming late" for mastern ya faɗa, Sorry sir we have wake up too late that the reason why we came to school late and it will never Happen again Aaimah ta faɗa yayin da Aairah ke ta bata fuska irin tafi ƙarfin ta bashi amma sa.
this should be the last, get sitet for mastern ya faɗa hadi da fita daga class ɗin .
Kallan juna sukayi haɗi da kwashewa da dariya, Aairah tace Why are you coming late tana kwai kwa yona maganar for master ɗin , dariya suka sake kwashe wa da Ita,
Aaimah tace this should be the last. wannan karan duka yan class ɗin ke dariya.
Sit ɗin su suka zauna suna cigaba da dariya,
Allah ya shirya ku twins domin yanzu abun naku sai adu'a mu samma make Aairah da uncle Hamza na magana sai wani harar sa kike," bazaki gane bane "Aeesha" Aairah ta faɗa wacce akakira da Aeesha tace to ganar dani.
"Ke wallahi haushi uncle hamza ke bani dafa Ina masa kallon mutumin arziki ashe dan banza ne, baki ji munce ya dai na zuwa gida yi mana lesson ba, Ai korar sa ya abdallah yay, saboda abun da ke kai shi bashi yake yiba, Ko kunya baijiba yace wai yana son Aaimah sai kuma yana lesson kiga yana kokarin taɓa ma mutun hannun ai kuwa rannan ashe duk abun da yake faɗa a kunnan ya abdallah, shine fa ya kore shi yace karya Kara ganin sa, to Wallahi inta kaice maki komu dukan da mukasha wurin ya abdallah sai kin tausaya mana dan Wallahi buguwa mukayi kamar gangar church kuma mom tace ba ruwan ta gashi abie baya gari, shiyyasa innagan shi Nake jin kamar na shaƙe sa"Aairah ta faɗa tana hura hanci, Allah ya shirya sa to Aeesha ta faɗa , Ameen dai.
be silent biology teachern su ne yace haka wanda shigowar sa kenan yasame su sunata surutu, natsuwa suka yi suna sauraron lesson ɗin dayake masu.
_F. M. C MEDICAL CENTER_
zaune a office ɗin shi da ke Amenity, waya ce a kunnan sa da alama waya yake.
"haba dude ai dole nace haka tsawan shekarar mu nawa muna tare ace baka taba ziyarta taba su mom ma a suna ka ɗai suka sanka sai waya, ai tare bata ce haka ba amma nasan maganin ka zan haɗa ka kawai da ammy ne nasan ita zata saka kazo ba dan kashirya ba konasa mom takiraka may be kazo ya abdallah ne ya faɗi haka,, On the other hand nacikin wayar yace,, sorry my man ba haka bane nima ina san zuwa to ayyuka ne suka min yawa shiyyasa amma insha Allah ina nan zuwa very soon,, ai nima ina da tarin ayyuka amma Nake ajiye su na ziyarceka,, inkuma Sai zanyi aure zaka zo inji to, duk da in zanyi sai tare da kai don ina samun mata zan haɗa ka da ammy kaima ka fito da taka ko aba da kai sadaka" abdallah ya faɗa yana dariya.
"haba kaima kasan wa za'a ba da sadaka Indai aure zakayi bisimillah ban hanaka ba amma ni ba yanzu ba.
"shikenan tun da kai bazaka chanza ba kullum ace mutum amsar sa ɗaya, ina gaishe da su ammy "ya abdallah ya faɗa .
"zasuji insha Allah nima ka gaishe man dasu mom kace mata ina nan zuwa very soon "
"Allah yasa domin kuwa na san halinka,"
Karka damu dude zan zo insha Allah, to shikenan sai anjima , abdallah ya faɗa , ok nagode sai anjima kashe wayar yayi shiri yayi haɗi da fita daga office ɗin dakin tiyatar yanu fa.
10:00 am
LAGOS.
_EKO HOSPITAL._
Patient ne zazaune wanda da alama sun zo ganin likita ne.
wata Nurse ce tafito daga Office aƙalla zatayi kimanin shekara 25 jikin ta sanye da fararen kaya riga da wando hulace kawai akan ta saɓanin wasu nurses ɗin da ke sanye da baby hijab, baka ce amma ba baki sosai ba wurin patient din tanufo, hadi dacewa DR. Is on the way, yayin da take amsar Katin patient ɗin wani dattijo ne zaune bai bada card ɗin shi ba da alama ma baiji mi nurse ɗin tace ba,"hey bring your card"
nurse ɗin ta faɗa ganin bai ba da nashi Katin ba," ƴata ni bana da Kati yau nafara zuwa".dattijon ya faɗa dakyar alamar ba karamin kamu ciwan yayi masa ba ,cikin harshen hausa tafara mgn duk da batayi Kama da hausawa ba kuma bawani iya hausar tayiba sosai " to ya kake so ayi Katin ka keso nabaka ne komi"
"a'a naji ance ana bada magani kyauta shiyyasa nazo" dattijon yafada, wani kallon rainin wayau take ma dattijon har ya gama magana, cikin karaji tace "hey hausa people nabani mamaki, to bari kiji nan ba charity hospital bane dan hk kitashi kiba mutane wurin, in ban da abunki ta ina wannan hospital ɗin tayi Kama da charity hospital koh ance maki irin hospital ɗiin kune na arewa" nurse din ta faɗa hadi da nuna masa hanyar fita. " haba Victoria kin man ta me doctor yace duk time ɗin da marasa ƙarfi suka zo ne " wata kyakyawar nurse ke faɗin haka chocolate color ce a ƙalla zatayi kima nin shekara 23 itama sanye take da fararen kaya rigada wando sai farar baby hijab, zuwan ta ke nan tasamu victoria nayima dattijo masifa Ita bahaushiya ce sabanin victoria, "ina ruwana ai yan zu ba ya nan sai dai inkece zaki faɗa masa
Kasa tashi dattijon yayi jikinsa sai rawa yake, tsawa ta dakama dattijo, haɗi dacewa "I said get out from this hospppppp, kasa karasawa tayi adalilin saukar wani mahaukacin mari dataji a kuncinta batai aune ba tasake jin wani marin a dayan kunchinta bashiri ta kife ƙasa, gaba ɗaya hankalin patient dana nurses ya dawo kan wanda yayi marin.
Tsaye yake jikinsa sanye da blue uniform ɗin sa na aiki, kafarsa na sanye da black din takalmi sai hannunsa dake riƙe da briefcase da lab coat ɗin sa, dogone yana da tsayi, farine sosai kyakyawan gaske ya nada dogon hanci sai eyes masu black ɗin eyeball, small mouth me ɗauke da red lips, sumar kan sa wacce tasha gyara koma take kan shan gyara black color ta sauko saman neak ɗin shi ya sha rawani irin na larabawa, dama da ka ganshi kai tsaye zaka ce balarabe ne kukuma half cast , akallah zai yi kima nin shekara 29 zuwa 30.
Good morning sir, nurses ɗin suka shiga gaishe da shi hannu kawai yake ɗaga masu yayin yake kiran security
ƙara sowa security ɗin sukayi suna gaishe da shi cikin girmamawa, amsa masu yayi yana nuna masu dattijon haɗi da cewa kushigar min dashi office yayin da yake ba daya daga cikin securityn key din office ɗin shi, kamashi sukayi suka ɗaurashi akan keken daukar marasa lpy wannan nurse ɗince wacce tayima victoria mgn ta matso kusa da shi hannu ta mika zata anshi briefcase ɗin dake hannun shi dakatar da Ita yayi, magana ya fara cikin harshen turanci nurse "hidaya me nace ne gameda masu zuwa neman tai mako? "
" kace duk wanda yazo neman tai mako ah EKO aturashi ABNOOR, kuma itama nurse Victoria tasani kuma sai da nasake faɗa mata da tana ma datijjon faɗa"
"shikenan koma dai miye Wannan yazama nakarshe ina ba haka ba dukkan ku sai ranku ya ɓaci "ya fada haɗi da nufar office ɗin shi
🌹~ KAINAAT ~ 🌹
Tasowa victoria tayi daga duƙewar datayi domin ta maru, haryanzu bata dawo dai dai ba, masifa tafara yima nurse Hidaya akan Ita ta haɗa ta da dr haryayi mata wannan marin, "to bari kiji Victoria garama tun wuri kifita daga harkata basai da na gar gaɗe kiba amma mikika ce ke kina ganin dr shazim bazai iya yimaki komai ba ke yar gaban goshi, kedai kawai za fin mari ne yasa zaki sauke a kaina mizai hana shi dr bazaki bishi office kiyi mashi masifar ba "hidaya ta faɗa tana dariya sauran nurses ɗin ma dariya suke saboda sun san magana ce hidaya ta faɗa ma victoria saboda ba ƙaramin so take ma DR. SHAZIM ba, mutsww victoria taja tsaki saboda haushin dariyar dasuke mata ta kuma gane miyasa su dariya wuce wa tayi office ɗin dr saboda itace ke tura mashi da patient,
Shiga tayi cikin office ɗin haɗi dacewa, good morning sir zaune yake yana rubutu ajikin file wanda da alama na wannan dattijon ne yayin da shikuma dattijon yake kwance bisa gadon marasa lafiya a office ɗin , ko kallon inda take bai yiba sake gaishe da shi tayi, call nurse hidaya for me abun da kawai ya ce mata kenan, hakuri ta shiga bashi dan bazata iya daina aiki dashi ba domin in har chanzata zaiyi da nurse hidaya to sai dai tabar hospital ɗin saboda bazata juri ganin shi tare da wata ba, tsawa yada kamata domin yaga bata da niyyar fita daga office ɗin yace " get out from my office" haɗi da nuna mata hanya, fita tayi daga office ɗin zuwa office ɗinsu na nurses fashe wa tayi da kuka, tana faɗin bazai yuwu ba wlh dr shazim nawa ne ni ka ɗai babu wacce ta isa ta raɓesa sai ni taƙara fashewa dawani kukan, wata nurse ce tashi go office ɗin wacce itama daga ganin ta ba muslma bace tana cewa , "ai yanzu kika fara kuka victoria, dama ba sai da na faɗa maki ba kitashi tsaye amma kika kiji to wallahi Idan bakiyi wasa ba kina nan sake dabaki hidaya zata kwace shi, sai dai kizama ƴar kallo"
"haba destiny yaza ki man wannan mumu nan maganar, kisan kuwa yanda nake son dr shazim kuwa da kinsan yanda nake son shi da baki ce haka ba"
" victoria kenan inaga bakisan halin hausa peoples bane zaki sha mamaki inkika tsaya wasa domin kuwa Ita hidaya yarensu ɗaya bayan nan religion ɗin suma ɗaya kina ganin zai kula ki ne yana ganin hidaya, kawai kitashi tsaye"
"to ya zanyi ki bani shawara pls"wani munafukin murmushi destiny tayi haɗi da cewa yanzu dai kifara kiramashi hidaya tukkun nan zuwa anjima sai muyi magana "
" haba destiny yazakice nakirata sai dai yaji haushi amma ni bazan kira taba wlh" "kaji sakarya in ban da kina sakarci in baki kira mashi ita ba taya zai gane kintuba kuma itama hidayan ki roketa akan ta tayaki bashi hakuri nasan zatayi," "uhmmm shi kenan ta faɗa haɗi da barin office ɗin domin kiran hidayar, dariya destiny ta kwashe da Ita haɗi da cewa "zaki gane baki da hankali Victoria zakisan cewa ni ba kanwar lasa bace yanda kika ki brother samuel to haka zaki rasa shazim shima sakarya kawai" .
wurin su hidaya Victoria tanufa,ta zuwa ta tsaya hannunta riƙe da ƙugu tace" kizo dr . nakira tana faɗa ta juya kai gefe, "wakenan acikin mu?" watace cikin nurses ɗin dake zaune ta faɗa , "tasan kanta ai acewar Victoria , sarai sungane hidaya take nufi sbd sun San tana yar tsama da Ita amma sai suka nuna basu gane ba "hidaya kinsanfa ke nake nufi amma kinyi kamar baki ganeba zanje na faɗa masa bazaki zoba"
" kejiman Victoria da karfin halin, kin faɗi sunan tane daza kice ta ƙizuwa"
"ah to gane mana hanya sister maryam" acewar wata daga cikin nurses ɗin "haba Victoria nina rasa me hidaya ta tare maki a hospital ɗinnan,ai ko bakomi ƴar uwarki ce tawurin aiki, amma ace kullum baki da abokiyar faɗa sai Ita"
karka faɗa man mgnr banza mana Joseph ina ruwanka"
"sorry shawara ce" barin wurin yayi wanda akakira da Joseph
"mike faruwa ne anan cewar destiny wacce isowarta kenan, a'a hidaya Victoria bata faɗa maki dr nakira ba nagan ki zaune ko har kin dawo daga wurin shi
"A'a destiny yanzu zanje, ok destiny ta faɗa haɗi dacewa kefa Victoria naga kinyi tsaye kutafi mana bin bayan hidaya destiny da Victoria sukayi suna ɗan yin nisa da sauran nurse's ɗin destiny ta ɗan taba Victoria alamar ta roki hidaya akan ta taya ta ba dr haƙuri ganin baza tayi ba yasa destiny dakatar da hidaya haɗi da cewa "kiyi hakuri hidaya akan abun da Victoria tayi maki haushin dariyar da kuka yi matane ɗazu, amma kiyi hakuri" "shikenan bakomi, ni da man bawani riƙe taba" "shikenan amma ki taya ta ba ma dr hakuri pls karya cireta daga cikin nurses ɗin dake tura mashi patient pls, a ranta take faɗan"ok shiyyasa kenan tazo ta ciman mutun ci"amma a zahiri sai tace "bkm yawuce insha Allah zan taya ta" thanks Victoria ta faɗa yayin da suka kawo office ɗin shiga ciki sukayi sallama hidaya tayi yayin da Victoria ke bayan ta, dr gani hidaya ta faɗa, ok a saka patient a layi amma mutum 15 kawai zan duba sauran kiturasu office ɗin DR KABIR, sorry sir ni ina iya tura su a cewar Victoria data ga yayi kamar bai san tana wurin ba, as from today this is the last time dazaki Kara zuwa office ɗin na I hope you understand, a fuwan sir kayi mata haƙuri bazata ƙara ba hidaya ta faɗa gaban ta na faɗuwa tsoron kar itama ya koreta, nagama magana get out
ƙasa Victoria tayi akan gwiwo winta tana ci gaba da bashi haƙuri harda kuka, I said get out from my office ya faɗa da tsawa yana nuna mata hanyar fita, fita tayi tana kuka kamar ranta zai fita ,kema zaki iya tafiya" Ok sir hidaya ta faɗa fita itama tayi " wajen office ɗin ta samu Victoria da destiny suna ganin ta suka nufe ta rokonta suka shigayi a kan ta taya victoria ba ma dr haƙuri " shikenan insha Allah zan taya ta kar ku damu hidaya ta faɗa hadi da sharema Victoria hawayen dake fuskarta ta cigaba da kwantar mata da hankali godiya sukayi mata sannan suka koma office ɗin da suke zama ita kuma ta wuce wurin patient domin tura ma dr su .
haka ya cigaba da ganin patient shikuma wannan dattijon ruwan da aka sa mashi na ƙarewa yasa driver ya mai dashi ABNOOR aka bashi gado , bashi ne ya bar EKO ba sai wurin 12:30 sannan ya wuce ABNOOR nan ma yaga patient dayawa saboda da nan yafi jimawa a nan a kan eko , abnoor hospital ɗin sane halak malak Ita kuma eko aiki yake a chan, sau biyu yake zuwa eko a sati idan yana lagos saboda yana visiting wasu Hospital ɗin , kuma in yaje 2 to 3 hours yake yi yaje abnoor , amma standard in da yafi zama abnoor ne saboda chan har ranar Saturday yana zuwa in yana lagos ,sai wurin 6:00 ya tashi daga aiki dan har an fara kiraye kirayen sallar magrib masallacin hospital ɗin ya nufa domin gabatar da sallah sai bayan angama tukkun nan yanu fi gida,
horn yayi a bakin wani katafaren gida naji da faɗa dake Victorian Ice land , gida ne har gida wanda daga gani ba sai an faɗa maka ba kasan cewa an narkar da kuɗi, me gadine ya bude masa gate, ciki ya shiga ya nufi parking lot da ke chan cikin gidan,ɗakin mai gadine farko daka shigo gidan sai boys quarters daga chan gaba sai kayi ƴar tafiya sannan zaka iso part ɗin masu gidan sai parking lot dake gefe sai wani katon garden dake bayan part ɗin masu gidan hade da Wani katon swimming pool me kyen gaske,ride's ne gasunan kala kala a kallah zasu kai 6 a parking lot ɗin , parking yayi cikin gidan ya nufa tura ƙofar shiga part ɗin yayi bakinsa ɗauke da sallama,parlor ne me kyan gaske komai na cikin sa ya kasan ce golden and white color ne royal sofas ne masu kyan gaske set biyu sai wani ƙaton dining table mai chairs kusan guda 10 , sai wasu bedroom guda 3 dake hannun dama sai kitchen da store atare, wani corridor ya nufa inda yana shiga nan ma wani madaidaicin parlorn me dauke da sofa a set 1 komai na cikin sa golden color ne sai dining mai dauke da chairs guda 5 sai two bedroom, daya daga cikin su ya nufa bakinsa ɗauke da sallama, wata kyakyawar mace ce zaune a kan sallaya itama farace sosai suna Kama da dr banbanchi Ita mace ce shikuma namiji zata yi kimanin shekara 50 , sanye take da hijab hannun ta reke da chasbaha tana ja , da a lama sallah ta gama, sallamar da yayi ta amsa mashi yayin da yake ƙarasa wa inda take zaune wuri ya nema ya zauna "an wuni lafiya ammy, ya gida"ya faɗa , amsa mashi tayi da" lafiya qlu Alhmdllh ya aiki ya fama da patient, alhmdllh ammy, Masha Allah ta faɗa haɗi da cewa katashi ka shiga ciki domin kasamu ka huta zansa fatima ta kawo maka dinner ɗinka , dama shi ba ma'a bocin cin abinci a dinning bane, to shikenan ammy bari na wuce ciki, fito wa yayi daga bedroom ɗin yanu stairs dake parlor wani part ya shiga wanda da alama nasa ne tura ƙofar yayi haɗi dayin sallama, ya kutsa kai ciki parlor ne shima ma dai dai ci me kyan gaske komai nacikin sa ash and black ne bedroom ya nufa wanda shima bedroom ɗin kayan cikin sa ash ne hattada furnitures ɗin ciki ash ne ɗan corridor ya nufa cloth set ne sai gefe laundry basket, kayan jikin sa ya shiga ragewa ya koma daga shi sai boxer bathroom yanu fa domin watsa ruwa after 15 minutes ya fito jikin sa sanye da bathrobe wurin clothes set ɗinsa ya nufa jallabiya ya saka ajikin sa bathroom yakoma domin ɗauro alwallah sbd time ɗin sallah isha yayi masallachin gidan ya nufa dan gabatarda sallah anagama sallah part ɗin sa ya koma a parlor ya zauna kan sofa bai jima da zama ba yaji ana nocking tambaya yayi waye ne " fatima " ce Yaya ok shigo ya faɗa , turo ƙofar tayi tashigo bakinta ɗauke da sallama kyakyawar matashiya ce akalla zatayi kima nin shekara 18_19 fara ce itama tana kamada ammyn su amma ba sosaiba dr dai shine ke kama da Ita sosai " ina wuni Yaya andawo lafiya, lafiya qlu , dama ammy ce tace nakawo maka dinner ɗin ka, ok ajiye kan table, ajiye mashi tayi haɗi dafita jawo table din yayi , serving ɗin kanshi yashiga yi, yana kammala cin abincin bedroom ɗinsa ya koma laptop dinsa ya jawo dake kan bedside aiki yashiga yi.....
KATSINA....
Su Aaimah ne zaune a falon mom suna kallo, sanye suke da pajamas sky blue, mom ce tafito daga bedroom ɗin ta, ita ma sanye take da pajamas purple color, waya ce a kunnan ta da alama waya take wuri tasamu kan sofa ta zauna tana cigaba da wayar " mom abie ne Aaimah ta faɗa yayin da take matsowa kusa da mom, daga mata kai mom tayi alamar eh" mom dan Allah kice muna gaishe shi munkira shi bai ɗauka ba, to kaji Wai twins ɗinka nagaishe da kai wai sunkiraka baka ɗauka ba mom ta faɗa , mika ma Aaimah wayar tayi da a lama cewa yayi a basu wayar, amsa tayi haɗi da cewa" inawuni abie ya Abuja, ya kuma aiki " on the other hand abie yace" lafiya qlu Alhmdllh ya gida ya kuma school " Alhmdllh abie ta bashi amsa, abie ko kace ina nake Aaimah ka ɗai kasani" Aairah ce ke mgn wacce ƙara sowarta kenan "afuwan yanzu zance kina ina sai kuma gaki ya gida ya schll" Alhmdllh abie yaushe zaka dawo, jibi insha Allah zan dawo " to Allah ya kaimu abie , ameen ya faɗa sun jima suna waya sannan suka yi sallam, bedroom ɗinsu suka nufa domin bacci dan mom ta daɗe dashige wa nata bedroom ɗin ....
Episode 5_6
_FRIDAY......._
sauko wa yake daga stairs jikin sa sanye da baƙaƙen coat hannun sa riƙe da briefcase , ammy ce zaune kan sofa ƙaraso wa yayi kusa da ita " Ina kwana Ammy ina fatan kintashi lafiya " ya fada yayin da yake samu wuri kusa da Ammy ya zauna " lafiya lau Shazim har kafito," eh ammy ya bata amsa," ga breakfast din ka nan kan dinning" "to,ammy kinkuwa yi waya da NORAIZ "( kanin sa mai bimasa yayan fatima dayake baya nan yana kasar portland yana masters akan business ) ya fada yayin da yake nufar dinning "eh naji yace yana nan zuwa ranar sunday ( lahadi ) , ammy ta fada " eh ammy haka yake fada man jiya, "to Allah ya kaimu lafiya" Jiya uncle ɗin ku ya kirani, yace kai ka ɗai suke jira" shiru yayi baice komai ba sai da ammy ta sake cewa "da kai fa nake magana, ni ban san mikake nufi ba , da anyi magana sai kayi shiru, tun yaushe ake abu ɗaya sai yawo kake ma mutane da hankali"
"kiyi haƙuri ammy, wlh ban gama abun da nake ba, kuma nifa bani da wata wacce zance ina so, nafi son su barin harsai na samu wacce nake so"
"to bari kaji na faɗa maka ni ba ruwana daga yanzu bazan sake shiga maganar ba duk hukuncin da suka yanke akan ka babu ruwana "shazim yace "dan Allah ammy karkice haka idan kika zare hannunki innah zata iya zuga su su yanke man hukuncin da duk sukaga dama"
"to idan har baka son haka tafaru to dole sai ka nema ma kanka masalaha" "insha Allah ammy"
"to Allah ya yarda, ameen ammy ".
fatima ce ta fito daga bedroom dinta dake kusa da na Ammy jikinta sanye da uniform , dinning ta nufo Ita ma domin breakfast
" Ina kwana Yaya dafatan antashi lafiya " lafiya qlu ya bata Amsa, yana gama breakfast ya mike hadi da daukar briefcase din shi " Ammy ni zan wuce, to a dawo lafiya Allah ya bada sa'a, ameen Ammy fita yayi zuwa parking lot, gaisawa ya tsaya yi da masu aikin gidan tun daga kan maibama flower ruwa Har izuwa kan maigadi sannan ya fuce daga gidan, ABNOOR ya nufa domin yau baya zuwa EKO.
ABDULƘADIR ABUBAKAR NURADDEEN PRIVATE HOSPITAL ( ABNOOR ).
Direct office din sa ya nufa briefcase din sa ya aje akan table zama yayi hadi da bude laptop dinsa Aiki yafara kafin time din daya ke duba patient yayi. sallama a kayi hadi da turo kofar wani matashin saurayi ne wanda zasu yi sa'anni da shazim din.
Amsa mashi sallama
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 33