dakin
Sukaci
Da washe gari
A makaranta shuhada ke bawa hindu labarin abinda ya faru hindu dry take harda hawaye tace amma fa wlh kawata kin burgeni
Shuhada tace humm ai naɗan samu lafiya dan harma na share dakin innata na koma ciki da zama
Hindu tace da kyau wlh hakan da kikayi yayi daidai
Nan dai suka cigaba da hiran su amma yawancin hiran akan karatun su ne
*bayan sati biyu*
Abubuwa dayawa sun faru harda samun yancin shuhada kuwa agidan ubanta dan yanzu yadikko bata shiga hidimarta sale ma yafita tsabgarta nuratu ma haka amma kuma duk da haka dan wani aikin na gidan tanayi harda girki amma wani lkcn tana tilasta nuratu suyi tare amma itama bata shiga hidimarsu kuma hakan yafi mata salama
Yau ta kama asabar
Shuhada tana gida babu makaranta sunata shirin exams
Zaune take akan tabarma gefenta kuma books dinta ne tana dubawa
Masifa taji yana tashi kafin ashigo gidan yadiko tafito daga daki wata mata ce ta shigo sai fizgar yar'ta takeyi tana ruwan bala'i
Miqewa tsaye shuhada tayi dan tasan matar
Yadiko tace lpy kuwa?
Innar lilo tace ina kuwa lpy ina sale?
Yadiko tace baya nan yafita mai yafaru ne kam
Cikin masifa innar lilo tace ina kuwa lpy ɗanki sale yayiwa yarinyata ciki
Zare ido shuhada tayi tana kallon lilo
Yadiko kuwa ƙugu ta riqe ta turo ɗan kwali gaban goshi tace lallai ma innar lilo sharri zakiyiwa ɗana duk tsanar da kuka masa lkcn yana ƙarami da sharrin da kuke kulla masa yana ƙarami bai isheku ba to wlh tun wuri kisan wanda yayiwa yar'ki ciki amma wlh badai ɗana sale ba
Ana cikin wannan hayaniyar ne saiga wata ma tashigo da ashar tana cewa ina dan iskan yaron yake dan akuya wlh bai isaba an isa atabani azauna lpy wlh yau sai gaban mai gari
Yadiko tace ke kuma lpy zuwaiba? Waye kuma kike kira da dan akuya
Zuwaiba tace waye kuwa bayan ɗanki sale yayiwa ya'ta ciki
Nan fa gida ya hargitse da hayaniya
Shuhada tattara books dinta tayi ta fice tabar gidan
Gidan gwaggo mairo taje ta kwanta gwaggo mairo tace lpy kuwa shuhada?.
Guntun tsaki shuhada tayi tace wlh gwaggo mairo yaya sale ya zama abinda ya zama yanzu fa na baro musu gidan suna hayaniya yaya sale yayiwa yar' gidan baba zuwaiba ciki da yar'gidan innar lilo
Salati gwaggo mairo tasa tace wlh ko kadan albasa batayi halin ruwa ba laure kin cucemu domin ko kadan sale da nuratu basuyi halin yaya amadu ba
Nan dai suka dinga jajinta lamarin shuhada kuwa bata koma gidan ba sai dare
Ko da ta koma bata gansu ba
Ashe mai gari yasa an kulle sale ne nuratu kuwa ba aganta ba shine yadiko tafita nemanta
Washe gari
Yadiko abin duniya ya mata yawa
Shuhada ce ta fito tana kiran sunan nuratu yadiko tace nuratu bata gida tun jiya muke nemanta
Hankalin shuhada ne yatashi domin duk abinda yasamu nuratu ya sameta tunda ƙanwarta ce ubansu daya
Fita tayi cikin tashin hankali tana neman nuratu ahanya suka hadu da hindu
Tace ke kuma yana ganki wujiga wujiga haka ?
Cikin tashin hankali shuhada tabawa hindu labarin abinda ya faru sannan tace nuratu kuma ba aganta ba tun jiya
Tsaki hindu tayi tace shine kuma duk kika bi kika tayar da hankalin ki haka? Wlh na tabbata yau ace kece aka nema aka rasa wlh yadiko ko nuratu ko sale bazasu nemeki ba
Shuhada tayi murmushin yake wanda yafi kuka ciwo ta girgiza kai kafin tace duk lalacewar naka nakane
Hindu wlh ko kadan banajin haushin hakan
Nidae kawai zo muje ki tayani neman kanwata hindu ta tabe baki tace muje
Babu kalar neman da shuhada da hindu basu yiwa nuratu ba amma basu ganta ba
Har karfe uku hindu tace nikam shuhada gsky nagaji wlh kizo muje gida ko tadawo
Gida sukaje suka tadda yadiko zaune ta rafka tagumi shuhada tace yadiko nuratun bata dawo ba ?
Yadiko tace eh bata dawo ba nima ban jima da shigowa gidan ba
Har akayi sallar la'asar ba nuratu balle labarinta
Sosae hankalinsu yatashi duk kawayenta an tmbye su sunce basu ganta ba
Saida nuratu tayi kwana2 kafin tadawo gida babu kalar tmbyar duniyan nan da yadiko bata yiwa nuratu ba akan inataje kwana2 amma nuratu taqi magana akarshe ma cewa tayi itakam akyaleta gidan saurayinta taje
Har duka shuhada tayiwa nuratu amma abanza
Bayan sati daya
Yadiko taje gidan kawarta talatu take bata labarin halin da take ciki
Talatu tace ai muddin shuhada tana gidan nan tofa kema kinsan al'qadarin ki zata karye dan haka ya zama dole ki ƙaɗa shuhada tabar ƙauyen tanko gabaki daya
Nazari yadiko tashiga yi kafin tace tabbas mgnrki gsky ne amma tayaya zan kori shuhada ?
Talatu tace ai gun boka zamu koma
(Wa iya zubillah)
Yadiko tace to yanzu mubari sai gobe kenn
Talatu tace wani gobe tashi zakiyi yanzun nan muje ai yau kar shuhada ta qara kwana a kauyen tanko haka suka shirya suka wuce kauyen kuka domin nan ne inda bokan nasu yake
Shuhada sun tashi a makaranta sun jima suna hira da hindu kamar yau ne suka hadu da kyar suka rabu domin da sunzo rabuwa zasu sake ɗago wata hiran
Harta koma gida
Shuru taji alamun ba kowa agidan
Dan haka ta canza kaya tayi sallah tayi wanke wanke da shara ta ɗauki tulu taje ta dibo ruwa ta ɗaura sanwa
Da kyar takeyi sbd wata ciwon kai daya zo mata lkc daya
Su yadiko kuwa boka ya musu alqawari kafin suje gida shuhada tabar kauyen tanko
Haka kuwa akayi domin bayan tagama girki taji kanta da kafafunta suna mata ƙaiƙayi da gudu tabar gidan
Tayi tasha ta fada mota batare da sanin inda zataje ba
_________________
*rashin sharhin Ku ne zai sani dakatar da littafin nan so plss agyara bcox nima inada abunyi wlh*
________________
*kambala'i wlh duk wanda ya siyarmin da littafi ko kuma ya canza min wata kalma ALLAH YA ISA ban yafe ba wlh duk wanda ya cire sunana ko yamin editing haka kawai ai bawai anfini son kudin bane kowa ya qirqiri basiransa bawai ya saci na wani ba*
Comments
And
Share
By Maman ahlan Mmn twins✍🏻✍🏻
[10/1, 6:18 AM] Zarahh: 🌠🌠🌠🌠🌠
🎇🎇🎇
*S̸͟͞H̸͟͞U̸͟͞H̸͟͞A̸͟͞D̸͟͞A̸͟͞*
🎇🎇🎇
🌠🌠🌠🌠🌠🌠
*ᔕTOᖇY ᗯᖇITTEᑎ ᗷY*
*z̸a̸h̸r̸a̸ a̸b̸d̸u̸l̸* ( *m̸o̸m̸y̸n̸ a̸h̸l̸a̸n̸*)
( *y̾a̾r̾ s̾a̾r̾a̾r̾i̾n̾ k̾a̾i̾n̾u̾w̾a̾*)
👸🏻 *sᎪhᎥbᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Short story..
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*P*...1⃣1⃣↪1⃣2⃣
Anyi tafiya mai nisa tana zaune a motan ba tare da tayi magana ba yawancin yan motan kallonta sukeyi suna yaba kyawunta a zuciyarsu
Karba kudi aka fara kowa ya cire nasa ya bayar har akaxo kan shuhada
Kawo kudin ki cewan conductor din motar zare ido shuhada keyi dan bata da ko kwandala ahannunta balle kudi Inama ta taba riqe wani kudi
Ganin tayi shuru ne yasa shi fara mita yana cewa matsalar kenan mutum ya ɗauki turawa ko larabawa a mota duk su zame maka matsala karasa gane wani yare zaka musu ni ina na iya wani turanci ko larabci gashi wannan daga ganinta balarabiya ce
Da karfi yace kee
Shuhada ta ɗago tana kallonsa yace
Hee lunga sanyara kudinki ki kawo yanayi yana misali da hannu gabaki daya motan akasa dry
Wani saurayi ne yaketa kallon shuhada bisa alama kuma shi kam yadan waye ba kaman sauran ba
Magana yayi mata da harshen turanci
Akan cewa taba da kudin motan ta rau rau da ido shuhada tayi zatayi kuka tace mishi da turanci itama
bani da kudi
Ya sake tambayarta Ina zataje tace masa itama bata sani ba
Kallon conductor din yayi sannan yace tace bata da kudi nan yashiga mita tana cewa wlh bata isaba saita biyasa kudinsa Sam Sam bai san wannan zancan babu ba ko kuma ya wullata ta window
Ganin da gske conductor yakeyi ne yasa wannan saurayin saurin tarosa yace karka tabata zan biya kudin
Ya kalli shuhada ya mata murmushi tace think you
Yace don't mind pretty
Conductor yace wlh dai karku zage mu ehe dan naga alama kuna shirin zaginmu dan kunga bamujin yaren ɗauka irin wa innan amota matsala gsky oga daga yau bazamu ƙara ɗaukan farin fata ba a motan mu
Ita dai shuhada shuru tayi abunta bata kuma cewa komai ba dan takasa gane dalilin dayasa tabaro gida kuma bata jin ko a mafarkine zatayi sha'awar komawa tunani take tayi barkate wanda ita karan kanta takasa ganesu
Sunyi tafiya mai nisa sosae kafin akayi parking mutane sunata sauka amma banda shuhada tana zaune ta zuba ma wa inda suke fita a motar ido har suka gama fita saura ita kadai
Kallonta driver yayi yace malama dan Allah ki sauka Zan sake lodi ne ahankali ta miqe tafita amotar jama'a tagani wanda saida suka bata tsoro dan bata taba shiga mutane haka ba gabaki daya atakure take gashi ba hijabi jikinta sai kallonta ake wasu na yaba kyanta wasu kuma suna yaba kyawun zubin halittan ta dan shuhada akwai diri
Tama rasa wani hanya zata bi magana taji ana yimata a bayan ta ta juya da sauri taga ashe mutumin daya biya mata kudin mota ne murmushi ya mata ta sun kuyar Da kanta kasa ahankali ta bude bakinta tace nan inane wani gari ne dan naga baimin Kama Da kauye ba
Zare ido yayi cike da mamaki yace dama kinajin hausa? Shuru tayi batare da tayi masa mgn ba yace nan *kaduna* ne baki san kowa bane ?ta gyada kai alamun eh yace to zaki bini ? Nan ma shuru tayi masa yayi gaba ta bisa abaya keke nape ya tare musu suka shiga suka kama hanya suna tafiya shuhada sai kalle kalle takeyi dan bata taba tunanin zata fito daga kauyen tanko ba tasa aranta kawai nan ne rayuwarta to amma meyasa ta baro kauyen taji gabaki daya ta tsani kauyen ta bata ma so a tambaye ta tace daga kauyen tanko take meyasa to kuma ai.......bata karasa ba taji saurayin na mata magana kallonsa tayi yace an iso fito mana yan mata fita tayi tana karewa unguwa kallo ginin block ne kam gidajen daidai wadaida dan ba zaka sakasu alayin masu kudi ba kuma bazaka sakasu alayin talakawa ba saidai kasasu alayin masu rufin asiri
Wata kofa ya bude yashiga yacewa shuhada ta shigo
Shiga tayi amma faduwan gabanta ya tsananta sai.ɗari ɗari takeyi ahankali tashiga tsakar gidan wanda yaji siminti daki biyu ne kacal agidan wani daki ya bude yashiga
Shuhada zama tayi awajen ta takure
Leqowa yayi yace ki shigo mana girgiza misha kai tayi alamun aa tace inaso nayi sallah gashi yanzu har magriba tayi kuma banyi la'asar ba kuma bani da hijibi
Murmushi yayi yace to ina zuwa bari naje na nemo miki ki shiga dakin ki zauna yanzu zan dawo yafice da sauri
Amma shuhada tana na zaune awajan ta rafka tagumi
Zuwa can anjima yadawo da leda ahannunsa yaganta a inda yafita yabarta miqa mata ledan yayi yace mata gashi ga bandaki nan akwai pampo aciki ki shiga kiyi wanka ki shirya sai kiyi sallah ta karba tace to ngd ta shige bandakin
Bude ledan tayi taga dogowar riga da hijabi soso sabulu brush turare makilin da body lotion Ajiyewa tayi agefe tayi wankan sannan ta ɗaura da alwala ta shafa mai ta feshe jikinta da turare tasa rigan
Ita karan kanta saida tabi jikinta da kallo yadda rigan yamata ɗas ajiki hijabin tasa tafito taga baya nan dan lokacin ana sallar isha'i itama tada sallan tayi sannan tayi addua sosae ta koma ta jinginu da bango zuciyarta na harbawa da sauri sauri ta rasa dalili
Sallamarsa ce tadawo da ita natsuwarta kallonta yayi yace baki shiga dakin ba har yanzu duqar da kai kasa tayi batare da tayi magana ba
Lade ya miqa mata ta karba ahankali ta bude baki tace ngd sosae
murmushi yayi yace tashi ki shiga dakin kici abinci ta girgiza kai alamun aa yace meyasa ?
Tace ba kowa agidan ne banga su maman ka ba ko ƙannan ka
Sosa keya yayi yace to ai nan gidan haya ne nidan azare ne amma ina sana'ata cikin garin kaduna yanzu dai kici abinci idan yaso saimu yi magana ko ?
Tace to ta shiga dakin tana ɗari ɗari shi kuma ya fice agidan
Zama tayi taji tanajin zafi tunda rigar dogon hannu ne yasata cire hijab din ta yafa gyalen rigan akanta ta bude takeaway din daya bata jallof din spaghetti tagani yaji kayan lambu Da hanta wani yawun yunwa ta hadiye sannan tafara Cin abincin tana lumshe ido a zuciyarta tace dama zanci wannan abincin Kafin na mutu
Tana cikin ci aka ɗaga labulen kofan dakin da sauri ta miqe dan ta tsorata wani saurayi tagani yace mata yi hakuri nabaki tsoro ko bakijin hausa ne nan ma shuru tayi batayi magana ba
Yace wlh bala akwai ɗan iska bana kuma harda balarabiya ya ɗauko zaisha gara kenan dan wlh wannan yarinya daga ganinta gonanta zaiyi ruwa yana magana yana kallon shuhada yana lashe baki kamar sabon maye
Jin kalaman sa ne yasa shuhada sumar tsaye au dama badan Allah ya taimake taba jikinta ya ɗauki rawa tafara tunanin yanda zata fita agidan
Shi kuma yana tsaye yana kallonta yana sambatu
A karshe yace bari naje na shirya dan wannan shagalin dani za ayi dole nima na ɗiba rabo na dan wannan yarinya za ashana ba kadan ba wannan ruwa zatayi yana lashe baki yafice
Yana fita shuhada ma ta miqe da sauri tasa hijabin ta ɗauki takalmi ahannu abakin kofar fita taji maganar su
Bala yace tana jin hausa fa tanimu yace to badai taji abun da nace ba bala yace idan ma taji kanta tayi mawa dan wlh saina fanshi kudi ajiyeta zanyi yanda nake da karfin sha'awan nan ai nasamu inda zandinga juyen baqin mai na
Suka sa dry tanimu yace mun samu dai zaka ce bala yace kaga mu shiga na fara latsan kudi na
Dan yarinya zata kai inda akeso domin akwai diri iya diri
Shuhada zawo ne kawai batayi ajikinta ba sai adduar neman tsari takeyi suna bude kofar da sauri ta matsa bayan kofar suka shiga gami da banko kofar amma hankalinsu yana ɗakin basu juyo ba
Ai suna wuce wa shuhada ta bude kofar ta fita da mugun gudu karan kofar sukaji da sauri suka rufa mata baya suna binta
Kuka shuhada takeyi kamar ranta zai fita bata ma san inda ta dosa ba gudun kawai take harta fito bakin titi
Da kyar ta samu wani lungu ta boye
Bala da tanimu babu kalar nemanta da basuyi ba amma basu ganta ba nan dambe ta kaure atsakanin su shuhada duk tana kallonsu ta riqe bakinta gam dan ko numfashi bata so ta saki balle sujita su ganta
Nan suka gama dambatuwan su sukayi gaba ahankali ta leqa taga basu nan wani marayan kuka tasaki ta hau rerawa yanzu ina zata je awannan daren
Irin wannan rayuwa haka kuka sosae shuhada takeyi tana godewa ubangiji daga bisa ta fito daga inda ta labe tafiya kawai takeyi akan titi batare da tasan inda zataje ba
Ga motoci sunata wuce wa tsintar kanta tayi awata kasuwa duk da dare ne amma akwai mutane wata mata ta hango ta awata yar bacanta wanda da kagani kasan na saida abinci ne
Ahankali shuhada taje wajen matar tayi mata sallama juyowa tayi tana kallon shuhada amma saita dage ta amsa sallaman gami da cewa lpy baiwar Allah idan abincin ne kike so yakare sai kuma gobe shuhada tace Aa hajiya ba abinci nake so ba dan Allah ki taimaka min da wajan kwana ko aiki ne saina dinga miki
Kallon shuhada matar tayi sosae sannan tayi wani shu'umin murmushi na yan' duniya tace ba damuwa aiki kuwa kisa aranki kin samu shiga ciki akwai yan mata yan uwanki gdy sosae shuhada tayiwa matar sannan ta shige ko ba komai yanzu ai tashiga cikin mata yan uwanta
Sallama tayi tagansu zaune su biyar kowacce taci uban riga da wando damammu wanda kamar zasuyi nishi kayan su yage dukkan suka zubawa shuhada ido suna kallonta
Daya daga cikin yan matan tana tauna cingum tace to bana kuma *hajiya kila* harda larabawa tafara ɗauka ne
Wata ma tace tabb wannan yarinya zata iya kashe mata market wlh
shuhada dai bata ce komai ba ta nemi gefe ta zauna ta rakube
Hummm wacece matar da aka kirata da suna *hajiya kila*
Hajiya kila gogaggiyar yar'duniya ce tana saida abinci abakin kasuwa sannan tana mu'alama da manya masu kudi ta yanda take aika musu yara yan mata idan suna da bukata wani lokaci har inkiya ake mata da mai abinci biyu ko kuma hajiya mai abincin dadi tana da gidan kanta wanda take tara yan mata aciki idan har mutum ya caske mata kudi to saiya zo ya zaba wacce yake so ya ɗauka
Yanzu kuma tanayin tozali da shuhada harta hango irin kalar kudin da zatayi akan shuhada
Leqawa dakin tayi tace ku fito mutafi gashi anzo ɗaukar mu tashi sukayi ko wacce tana tafiya tana kararraya tana jijjiga jiki mamaki ne sosae yakama shuhada tabb lallai ana budiri aduniya saika ce baza amutu ba
Hajiya kila tace yan mata fito mana mutafi ko. Ke anan zaki kwana?
Ahankali shuhada ta miqe daya daga cikin yan matan tace dama hajiya tanajin hausa ne
Hajiya kila tayi dry tace nima da tamin hausa nasha mamaki
Nan dai suka shishshiga mota
Aka fara tafia itadai shuhada ido ne nata
Har aka iso wata karamar unguwa mai suna zango awata yar karaman kofar gida amma irin gida mai tsayi din nan ne kofar gidan saika ce ana cin kasuwa
Fitowa sukayi hajiya kila taja hannun shuhada sukayi cikin gida sbd wani kallon da a kebin shuhadan dashi
Sai kallon gidan takeyi wani daki hajiya kila ta budewa shuhada tace mata gashi nan ki shiga dakin ke kadaice akwai toilet sannan idan kin shiga ki kulle kofar saida safe ko kina buqatar wani abu?
Girgiza kai shuhada tayi sannan ta duqa har kasa tace ngd hajiya murmushi hajiya tayi sannan tace ba komai ya sunan ki?
Sunana *shuhada*
Wow nyc name shuhada to ki huta yanzu gobe zamuyi magana shuhada tace to ta shige dakin ta sa masa key kallon ɗakin takeyi ga katifa akasa sai ledar tsakar daki
Zama tayi ta riqe kanta hannun biyu ta hau matsinacin kuka sbd hindu data fado mata kuka tayi sosae tana kiran sunan hindu da taga kukan ba mafita bane yasata tashi tashiga toilet ta ɗauro alwala ta tada sallah ta jima tana addua kafin ta koma karatun al qur'ani da kai daga nan bacci mai nauyi ya ɗauke ta
Da washe gari
Harta dan makara sallar asuba bayan ta idar ta sake kwanciya bacci ya kwasheta
Cikin baccin taji kamar hayaniyar fada kaman ana dambe da sauri ta farka ta bude dakin ta fito ganin wasu yan mata su biyu sai dambe suke ana musu kiɗa da waka ana cewa
..ku casu mata ku casu ku casu ba mai raba ..ku ...ku casu ku fidda rainii....
Riqe baki shuhada tayi ganin yanda suke damben tsakaninsu da Allah
Jitayi an dafata tana juyawa taga hjy kila jan hannunta tayi suka koma daki ta miqa mata leda tace gashi abinci ne kici .
Nan bariki ne duk abinda zaki gani babu ruwanki balle ki tsaya kallo dan yanzu sai fadan ya koma kinji ko ? Shuhada tace to hjy insha Allah hjy kila tayi murmushi tace yau ki huta amma gobe zamu fara zuwa kasuwa karki sake ki fita adakin nan kinji ko shuhada tace to hjy ngd
Hajiya kila ta tashi tafice shuhada ta maidawa kofar key
**************
*a kauyen tanko*
Bayan hindu sun rabu da shuhada jitayi gabanta na faduwa gashi takasa samun natsuwa ko abinci takasa ci innarta tace waini hindu yau lafiya kuwa kike ?
Hindu ta turo baki tace inna bari naje gidansu shuhada inna tace ohh ni ramatu ba dazun nan kuka rabu ba
Hindu ta tashi ta dauki hijab dinta tafice tana cewa bari dai naje na dubota inna tayi dry tace wannan kawance dai Allah yakarata nidai zance irin wannan shakuwa haka
Su yadiko kuwa zuciyarta gal data dawo gida bata samu shuhada ba girkin da shuhadan tayi tasa agaba suna ci itada talatu
Yadiko tasa dry tace ashe dai zakimin bautan karshe kafin ki tafi shegiya
Talatu ta kai loma tace amma fa yarinyan ta iya girki domin yayi dadi yadiko tace ai tsinanniya ba baya ba wajan girki talatu tace ai naso ace haukata ta boka yayi wlh yadikko ta kuma cewa ai yarinyar bata sake da sallah shiyasa boka ya kasa haukata ta amma yanzu kam taje tayita yawon duniyarta suka sa dry harda tafarawa
Sallaman hindu ne ya katse musu hiran
Yadiko tana ganin hindu hantan cikinta ya kaɗa talatu ta harareta
Hindu ta duqa ta gaishesu talatu sai washe baki takeyi da jajayen hakwaranta tace ai sahura tana ban labarinki ke kawarta ce ko
hindu da mamaki take kallon talatu kafin tace aa duk faɗin kauyen tanko banda kawa sama da shuhada yanzu ma ita nazo nema
Yadiko ta qara tsurewa talatu tayi caraf tace yadikonta ta aiketa
Atakaice hindu tace ina? saina bita mu dawo tare
Talatu tace kauyen yar'mai dille
Zare ido hindu tayi tace da kafa ?
Talatu tace eh ran hindu ya baci ta miqe afusace ta bar gidan
Tana mitan rashin imani na yadiko akan mai zata tura shuhada har kauyen yar'mai dille da kafa kamar zatayi kuka haka take ji
taja ta tsaya tana tunanin kodai tabi shuhadan ne
____________
Dogon sharhi dogon typing
Commments
And..
Share
*by mmn ahlan & twins*✍🏻
[10/1, 6:18 AM] Zarahh: 🌠🌠🌠🌠🌠
🎇🎇🎇
*S̸͟͞H̸͟͞U̸͟͞H̸͟͞A̸͟͞D̸͟͞A̸͟͞*
🎇🎇🎇
🌠🌠🌠🌠🌠🌠
*ᔕTOᖇY ᗯᖇITTEᑎ ᗷY*
*z̸a̸h̸r̸a̸ a̸b̸d̸u̸l̸* ( *m̸o̸m̸y̸n̸ a̸h̸l̸a̸n̸*)
( *y̾a̾r̾ s̾a̾r̾a̾r̾i̾n̾ k̾a̾i̾n̾u̾w̾a̾*)
👸🏻 *sᎪhᎥbᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ*👸🏻
*_sadaukarwa gareki tawan smart feenert_* _inayin ki irin sosae din nan_😘
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
*P*...1⃣5⃣↪1⃣6⃣
Turesa takeyi tana kai masa duka tana ihu amma ina alh tukur duk ya gama fita daga hayyacinsa sbd tunda yake bai taba ganin siffa mai kyawun shuhada ba kafin ta ankara yafara laluben bakinta yana so ya hada danasa wani karfi ne yazo mata lkc daya ta zage ta gantsara masa cizo yasaki ihu kafin yayi wani motsin kirki ta bugesa ta tashi da gudu cikin zafin nama ya sake fizgota
Idonta ne ya sauka akan plate din tangaran bata tsaya wani tunani ba tasa hannu ta ɗauka ta saukewa alh tukur akai ihu yasa sannan ya saketa ba shiri ya zube kasa yana birgima
Da gudu shuhada ta bude kofar ta fice tana kuka mai cin rai gudun kawai takeyi amma sam hankalinta baya jikinta ga titi ne mutane sai kallonta sukeyi ta zama kamar wata mahaukaciya
Ganin kallon da ake mata yayi yawa agefen titin da take ne yasata juyawa da niyyar zata tsalleki ta koma dayan gefen mota ce qirar ranger rover yayi Sama da ita wanda ya bugeta yasa hannu akai yana salati
Wasu yan'matan yara ne abayan motar su biyu dayar tace innalillahi garba kayi kisan kai mun shiga uku
Da sauri garba ya fito suma yan matan suka fito dayar ganin kayar jikin shuhada a yage ga maza duk an cika awajan yasata cire gyalenta da sauri ta lullubeta dashi sannan suka taimaka wa garba ya ɗauke ta yasata a mota
Sai asibity suna shiga aka wuce da ita emagency hankalin yan matan ya tashi matuƙa dayar tace wlh *ra'eesa* ke ce kika yawo mana muna zaman zaman mu agida kika ce mu fito shan ice cream yanzu gashi bamu sha ice cream ba garba ya buge mutun yanzu idan ammi ko abbi yaji wlh kashin mu ya bushe saukin mu daya yaya baya gari da sunan mu sorry
Wacce aka kira da ra'eesa tace dan
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 3 Chapter of 13