Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT[10/1, 6:18 AM] Zarahh: 🌠🌠🌠🌠🌠🌠 🎇🎇🎇 *S̸͟͞H̸͟͞U̸͟͞H̸͟͞A̸͟͞D̸͟͞A̸͟͞* 🎇🎇🎇 🌠🌠🌠🌠🌠🌠 *StөЯҰ ѠЯЇttЄҋ БҰ* *Z⃡a⃡h⃡r⃡a⃡ A⃡b⃡d⃡u⃡l⃡ (m⃡o⃡m⃡y⃡n⃡ A⃡h⃡l⃡a⃡n⃡* *de̺͆d̺͆i̺͆c̺͆a̺͆t̺͆e̺͆d̺͆ t̺͆o̺͆* A̺͆n̺͆t̺͆y̺͆ f̺͆a̺͆u̺͆z̺͆a̺͆h̺͆ y̺͆a̺͆r̺͆ A̺͆m̺͆a̺͆n̺͆a* *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ *Alhamdulillah dukkan yabo da godiya sun tabbata ga ALLAH mai kowa mai komai salati da ɗaukaka da amince su ƙara tabbata ga Annabi muhammadu S,A,W da iyalan gidansa da sahabbansa dama ma goya baya baki daya har izuwa ranar sakamako ina godiya ga Allah daya bani iko sake fara wannan littafi nawa lpy Allah yabani ikon gamawa lpy Allah yasa mu amfana da abinda yake ciki ameen.* _________________ *P*....1⃣↪2⃣ Kwance take a takure, a wata yagal galalliyar taburma wanda duk ta tattare dan tsufa, ko kyawun gani babu dakin ƙasa ne take kwance a ciki wanda duk ba'rin dakin ƙasar ya zube, a gefe kuwa tumaki ne suke kwance a tare, yanda ta kwanta da ka ganta ka san sanyi ta ke ji domin kuwa lokacin sanyi ne babu abin rufa, dogon rigan jikinta fadin yanda yake b'ata lokaci, tana cikin baccin wahalan da ta ke yi ne ta ji sauƙan bokitin ruwan sanyi a jikinta, a firgice ta tashi tana raba idonuwanta manya dasu farare tass masu kyawun kallo. Duka-duka ba zata wuce 14years ba. Ba ta yi auni ba ta ji sauƙan mari, da sauri ta dafe wajan gami da sakin kukan wahala ta durqusa ƙasa. "Dan Allah *YADIKO* kiyi hakuri me zan miki" Yadiko ta ce. "eh lallai *SHUHADA* kin samu guri har da kwanciya bacci? ai ba ki da sauran wata hutu, maza ki tashi ki ɗauki tulu ki je rafi ki dibo ruwa, kina dawowa ki share gidan nan tas ki ɗaura sanwa kafin mu farka a bacci ni da Shaleleta da kuma ɗana, idan ba haka ba wallahi!! wallahi!! wallahi!! kinji na miki rantsuwa sau uku ko? to na lahira ma sai ya fiki jin dadi shegiya karuwan yarinya kawai!!" Yadiko ta koma dakin'su tabar Shuhada durqushe tana kuka mai cin rai, Yanzu a wannan tsohon dare zata fita diban ruwa rafi? a kalla yanzu karfe uku na dare ga shi ƴan ƙauyen su da lalata yan mata barinma ita da suke kawo mata hari, Yadiko ta leko ta ce. "Wallahi, Shuhada idan ba ki tashi kin fita ba idan kika bari na sake fitowa sai na ci ubanki a gidan nan, na babballaki na ga mai ceton ki duk faɗin kauyen nan" da sauri Shuhada ta tashi ta dauki tulu ta fita ta yi hanyar rafi tana kuka tana adduan neman tsari, ba ka jin komai, kafa duk ya ɗauke, ƙauyen tsit kowa yana cikin gidansa yana bacci domin an ce dare mahutan bawa. Haka Shuhada ta ci gaba da tafiya cikin tsoro tana addua Allah ya kareta, sannan Allah ya kawo mata karshen wannan baƙar azaban da take sha a wajan Yadiko da ƴaƴan Yadiko. Da haka har ta isa rafin ta dibo ruwan, kafin ta dawo an kira sallan assalatu, Tulun ta ajiye ta hau sharan gidan ta nayi tana addua domin kuwa Shuhada hafizan Al'qur'ani ce ta yi sauƙarta shekara uku da suka wuce tun tana da 11years kenan, Bayan ta gama sharan ne ta fita neman icce da ƙirare ta zo ta ajiye kafin nan har lokacin sallar asuba ta yi dan an shiga masallaci, alwala ta yi ta koma ba'rin dakin'su ita da awaki ta share tukunna ta tada sallah ta yi nafilolinta da farillah sannan ta ɗaura da addu'o'inta dan kullum bata rabuwa dasu a bakinta da kuma zuciyarta. Hura hutan tayi ta ɗaura ɗumamen tuwon dawan da ta yi jiya wanda ko rabin loma ba a bata taci ba dan kwanonta daya ne a gidan kullum. Ita za ta yi girki amma baza a bata taci ba Sai wanda ya bushe sai a haɗa mata da ƙanzo a ce taci idan kuma taci to ba ita ba sake cin wani abun sai washe gari, wani lokacin ma haka zata wuni ta kwana bata ci ba, Sai dai idan Allah ya taimake ta taje makaranta sai aminiyarta yar gidan mai gari ta kawo mata abinci taci haka zata zauna taci uban aiki sannan ta wuni da yunwa, ko kuma ta kwana da yunwa. Bayan ta gama ɗumamen ta juye musu a langa su na can su na baccin asara babu wanda ya fito balle ya yi sallah. Basu tashi ba kuwa sai da rana ta fito gal asaman kwano tukunna suka fito suna wangale baki suna hamma babu ko rufe baki. Shuhada shirin zuwa makaranta ta yi, uniform dinta duk sun koɗe sun sha ruwa ga uban pachi a jiki. Dama jiran su ta ke yi su tashi za ta je makaranta, domin kuwa bata isa taje ba tare da sun tashi ba, idan ta dawo jikinta ne zai yi tsami, durqusawa Shuhada ta yi ta ce. "Yadiko ina kwana?" "Mtsww!! munafukar banza lafiya!!" Shuhada ta juya ta kalli *Sale* wanda ya fito yanzu shi ma yana wangale baki. "Yaya Sale ina kwana?" Harara ya aika mata da shi ya ce. "Da ban kwana ba za ki ganni? shegiya mai kama da aljana" Ya ɗauki buta ya shiga kewaye, Yadiko ta ce. "Dan ubanki ba ki ga Shalele bane da ba zabki gaisheta ba?" Shuhada ta kalleta ta ce. " *NURATU* ina kwana?" Nuratu ta ce. "Iyah ki gani fa a tsaye take gaisheni, kuma ko ta ce min Anty saboda raini, ta raina ni" Shuhada ta girme Nuratu da shekara daya da rabi. Shuhada ba ta yi auni ba taji sauƙan rankwashi a kanta da sauri ta duqa, Sale ya ce. "Idan ba za ki gyaru ba, ki din ga gaisheta a tsugune sannan ki kirata da Anty ba, wallahi kin din ga shan rankwashe a wajena" ya faɗa yana shigewa dakinsa. Yadiko ta ce . "dallah ɗauko mana abin karin kumallon'mu" Shuhada ta tashi da sauri ta ɗauko ta kawo musu ta ce. "Yadiko, dan Allah ki taimaka min da ko loma daya ne naje makaranta wlh yunwa na ke ji" a hasale Yadiko ta miqe tayi kan Shuhada, da gudu shuhada ta fita tabar gidan tana kuka, Yadiko ta ce. "Dama kin tsaya ki ga loma daya, yau ki je wajan koyan iskancin naku da kumburaren fuska shegiya karuwa kawai!" A hanya Shuhada tana tafiya tana hawaye ga yunwa ta na ji sosai har wani zazzabi ta ke ji na shirin kamata. ###### *zan dakata anan sai na ga yadda ku ka karbi littafin daga nan muci gaba da gashi* *ta hanyar comments dinku da dogon sharhin ku zan fahimce book din yasamu karbuwa ngd mah ppls*🥰 C̸͟͞o̸͟͞m̸͟͞m̸͟͞e̸͟͞n̸͟͞t̸͟͞s̸͟͞ A̸͟͞n̸͟͞d̸͟͞ S̸͟͞h̸͟͞a̸͟͞r̸͟͞e̸͟͞ B̸͟͞y̸͟͞ A̸͟͞l̸͟͞q̸͟͞a̸͟͞l̸͟͞a̸͟͞m̸͟͞i̸͟͞n̸͟͞ m̸͟͞m̸͟͞n̸͟͞ a̸͟͞h̸͟͞l̸͟͞a̸͟͞n̸͟͞✍🏻 [10/1, 6:18 AM] Zarahh: 🌠🌠🌠🌠🌠🌠 🎇🎇🎇 *S̸͟͞H̸͟͞U̸͟͞H̸͟͞A̸͟͞D̸͟͞A̸͟͞* 🎇🎇🎇 🌠🌠🌠🌠🌠🌠 *StөЯҰ ѠЯЇttЄҋ БҰ* *Z⃡a⃡h⃡r⃡a⃡ A⃡b⃡d⃡u⃡l⃡ (m⃡o⃡m⃡y⃡n⃡ A⃡h⃡l⃡a⃡n⃡* ( *y̾a̾r̾* *s̾a̾r̾a̾r̾i̾n̾* *k̾a̾i̾n̾u̾w̾a̾*) 👸🏻 *sᎪhᎥbᎪᏒ ᏦᎪᎥᏁuᎳᎪ* 👸🏻 *dedicated to* *Hassan 80k* *Husain 80k* *Mu'az* Short story *بسم الله الرحمن الرحيم* ____________________________________ *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation ____________________________________ *Masha Allah a gsky fans babu abinda zan ce saidai kawai Allah yabar qauna* *muahh*💞💞 _______ Murna murna murna💃🏻💃🏻💞💞 Na tayaki murnan kammala book dinki my luv khadija Jounalist Allah yasa muyi amfani da darasin dake ciki kuskuren ki kuma Allah ya yafe miki ameen _________ *P*......3⃣↪4⃣ Da haka har taje makarantan tana kuka wani malamin su ne yaganta tana kuka ya kira ta shuhada zo nan Tana zuwa yace bana ce kice wa baban ki ya canza miki uniform ba ? Sun kuyar da kai ƙasa tayi domin shuhada akwai kunya da biyayya tace malam bani da mahaifi Allah ya masa rasuwa Mamar ki fa ? Malam mahaifiyata itama Allah ya mata rasuwa bani da mama bani da baba To baki da yaya ne ? Malam ina dashi amma ko nace ya siyamin bazai siyamin ba Malam rabiu ya girgiza kai yace Allah ya kyauta duk makarantan nan kinfisu ilmi duk da a ƙananun shekarun ki kina ss3 amma kuma uniform dinki Tunna primary skull ga uniform din da rashin kyan gani gashi kullum sai kinyi latti abinda yasa ma ba a dukan ki latti sbd kokarin ki da ilmin ki da biyayyar ki Nan malam rabiu ya dinga mita dan shi bai jima da zuwa makarantan ba dan haka bai san halin da shuhada take ciki ba nan dae ya gama faɗar sa shuhada ta duqa kasa tace malam kayi hakuri ba laifi na bane nake yin latti Malam rabiu yace tashi kije Bayan tashiga class jitayi anya yau din nan zata gane karatu kuwa sbd yunwa kalle kalle tafara ko zata hango hindu yar mai gari kawarta amma da alama yau hindu batazo makaranta ba Haka dae aka fara musu karatu tun bata fahimta da ta tuno karatun nan fa jigon rayuwarta ne hasken rayuwarta ne domin kuwa ilmi haske ce kuma burin mahaifiyarta ne tana so tayi karatu domin ta taimaki jama'ar kauyen su tana son zama likiti Nan tadinga tunanin innarta ta manta ma a makaranta take jitayi ana taba ta firgigit tadawo daga duniyar tunanin da ta lula Taga ba kowa a class din alamun anfita break ne tace hindu yau ina kika tsaya? tace hummm kedai bari shuhada yau nazo da wuri malam rabiu ya tare ni wai ilmi na bai kai na yan ss3 ba shine fa wai na koma primary ni kuwa nasa kuka nace wlh ina yar mai gari bazan koma primary ba da kyar aka mai dani js1 dan kawai yaba assignment ba kasa yamin tmbya nakasa amsawa shikenn fa nikam ba dabadin ke ba aradou bani ba wata karatu na allon ma tunda nayi rabi Allah ya isheni haka Allah ya amfana Shuhada duk da batajin ddi sosae amma mgnr hindu yayi matukar bata dry dan haka ta hau dry hindu kuwa tacika tayi fam dan ita ta tsani dry zata fita da sauri shuhada ta riqota haba kawata yi hkr mana nabari bazan sake ba Dawowa tayi ta zauna tace to wlh kibari idan ba haka ba kuwa mu bata dake na sati daya Shuhada tace haba hindu ina murna kece kawai mai sona idan kika bata dani ai mutuwa zanyi Hindu ta zaro ido waje tace tab lallai kibar mgnr mutuwa ba yanzu ba Murmushi shuhada tayi tace ai dole nayi zancan mutuwa ina innata ina babana ta faɗa tana hawaye ya gangaro a idonta sosae hindu ta tausaya mata tace kiyi hkr shuhada wata rana sai lbr gashi kina da ilmi da natsuwa na tabbata a wannan ƙauyen namu mijin da zaki aura sai angani insha Allah yadikko sai taji kunya domin zakiyi abinda ba ataba yinsa ba a ƙauyen tanko Gashi na taho mana da abinci innata ta dafa shine na juyo mana ita a leda amma kici kawai idan na koma gida zan kara ci tunda kafin nazo ma naci Da sauri shuhada ta karba ta hau ci tana kuka hindu tana tayata Hindu zata girme shuhada da shekara daya domin ita shekaranta 15 ne shuhada kuma 14 Hindu bata jin mgn ko kadan kasan cewarta yar gidan mai gari haɗuwar su da shuhada kuwa abakin rafi ne taga shuhada nan taji tana sonta da kawa duk yan mata ƙauyen suna son yin kawance da hindu sbd hindu tana da kyau daida gwargwado sannan tana haske abunta bai rufe mata ido ba tana da kyauta ga neman tsokana Hindu bata da hkr idan kayi mata abu tofa saita rama haduwarsu da shuhada ne yasata ta koyi hakuri Akan kawancen shuhada da hindu Nuratu bata so ba dan ita tafi dacewa tayi kawance da hindu ba shuhada ba Akan wannan kawance saida shuhada taci dan banzan duka Wannan dukan kuwa har gaban mai gari ********** *wacece shuhada* Shuhada mlm amadu isa shine cikakken sunanta Mahaifinta malami ne haifafen dan AZARE acan cikin wani kauye mai suna kauyen tanko nan iyaye da kakanni suke na mlm amadu Mlm amadu yafara auren laure wato(yadiko) kwata kwata laure bata son kishiya ko da kuwa a maƙota ne balle ace kuma ma ita za akawo mawa Mlm amadu bai san halin laure ba ya aureta ga ƙazanta dan wasu halayyan nata saidai sukayi aure take fitowa dasu da haka harta haifi ɗanta sale Sale harya shekara 7 amma laure bata sake haihuwa ba Sale yaro ne wanda baya jin mgn dan kullum iyayen yara sai sun kawo karansa wajan babansa mlm amadu daya gaji ya bugama sale keji yana kullesa aciki dan yafi masa salama Babu kalan bala'i da laure batayi ba akan an tsani ɗanta sale akauyen amma ko kulata mlm amadu bayayi sbd shi mutum ne baya son hayaniya Mahaifiyar shuhada kuwa ba yar azare bace bafulatanan TILDE ce bikin kawarsu sukazo a ƙauyen tanko dake cikin azaren tunda mlm amadu yaganta yaji ta kwanta masa arai Da haka dae yayi ta tmbya har yaje tilde yagana da mahaifin iklima wato mahaifiyar shuhada Ba tare da bata lokaci ba mahaifin iklima ya amince da mlm amadu aka ɗaura aure Laure bata sani ba wata kawarta ce talatu wanda halinsu yazo daya da laure tare suke kashewa su binne ta kawo mata jawabin ai mlm amadu yayi aure tana nan sake da baki acikin gida Ranar babban hauka mlm amadu yagani awajan laure.haka ta dinga fasa tulunan ta da langa tana timasu da ƙasa Mlm amadu bai bi ta kanta ba yasa aka sharewa amarya daki aka kawota Tunda iklima tazo gidan sam batajin dadin zaman gidan bawai da mijinta ba aa saidai laure da ɗanta sale sun hanata sukuni Da haka a daddafe har Allah yabata ciki ba ƙaramin wahala take sha ba haka laure tadinga azabtar da iklima Ko abinci bata ta Ranar haihuwa kuwa iklima tasha wuya kamar bazatayi rai ba. Laure tana kallonta yanda take juyi tana salati tana kiran sunan laure ta taimake ta amma laure tana zaune tana shan rake abunta har iklima ta suma Malam amadu ne yashigo gidan da wata kanwarsa mairo basu shiri ko kadan da laure tsakaninsu saidai kallon banza Da gudu mairo tayi kan iklima tana jijjigata gashi babu asibity a ƙauyen tanko sai sunje kauyen gangare. Hnkln su yatashi matuƙa Suka rasa yanda zasuyi mlm amadu yace bari naje gidan mlm sabitu yabani aron amalanken sa saimu kaita asibityn ƙauyen gangare mairo tace to yafita da sauri Duk wannan bidirin da sukeyi laure ta hakimce a tsakar gidan tana kallonsu ga dan kwalinta gaban goshi tana shan raken ta Haushi ne ya kama mairo tazo gabanta ta fizgi raken ta jefar ta ɗaga hannu da niyyar kai mata mari ta tuno da mgnr babbar yayarsu dan haka mairo ta fasa marin laure ta nuna ta da tsaya tana mgn Laure baki da hali baki da tausayi kisani ita rayuwar duniya makaranta ce duk abinda kikayi to ina gaya miki zaki tarar da sakamakon sa ko bajima ko ba ɗaɗe Laure tace hoohoo hoo naji din wlh dukkanku atafin hannuna kuke kar nake kallon ku gabaki dayanku zanyi maganin ku ita kuma wancan shegiyar Allah ma yasa ta mutu Mairo zatayi magana taji muryan yayanta dan haka bata bi ta kan laure ba suka ciccibi iklima suka sata a akori kura Gudu sosae sukeyi a hanya duk kansu sunji jiki kafin suka iso Aka karbi iklima bayan awanni da wahalhalu ta haifo yar'ta mai kyawun gske wanda kamar ka taba ta jini ya fito mairo murna takeyi tasa hannu ta karbi yarinyar Mlm amadu yace ya ita mahaifiyar yarinya Bayani suka farayiwa mlm amadu cikin fada akan cewa suna da sakaci domin sunyi jinkirin kawo iklima domin kuwa tasamu matsala babba Salati kawai mlm amadu da mairo sukeyi Kafin mlm amadu yace wani irin matsala ne haka Likita yace cutar shanyewar barin jiki ga kuma yoyon fitsari Kuka mairo tace tana salati Mlm amadu saida idonsa tayi ja amma baiyi kuka ba Satin iklima 2 a asibity aka dawo da ita gida Mairo ke kula da ita da yarinyar Iklima da kanta tacewa mlm amadu yayiwa yar'ta huduba da sunan *SHUHADA* domin tana son sunan Har tsawon wata uku mairo tana.kula da iklima da shuhada domin mairo tana son iklima ga shuhada yarinya ce mai shiga rai Watan shuhada 7 Laure ta samu ciki Kafin laure ta haihu Shuhada tana da shekara daya daya da rabi Babu kalar azaba da wulaqanci da mlm amadu da iklima da kuma yar'su shuhada basu gani wajan laure Kuma mlm amadu baya iya tsawatar ma laure saide shima idan abun ya damesa yayita hawaye Shuhada tana da shekara 7 Babu aikin da batayi laure tayi mata duka agaban iklima tayita kuka gashi bazata iya tashi ta kwaci yar'ta ba Idan laure wulaqancin ta yatashi ta dinga zagin iklima kenn wai miskiniya Ranar wata jumma'a shuhada ta gama yiwa mahaifiyarta komai zata tashi Ta kira sunanta a hankali *shuhada* Gabanta ne taji ya fadi dan haka ta dawo da sauri tace naam innata me kikeso Murmushi inna tayi tace duk rintsi duk wuyan rayuwa shuhada ki riqe mutumcin kanki shuhada ke yarinya ce amma kina da hnkln manya Shuhada karki bar zuwa makaranta kiyi karatu kizama likita ki taimaki al'umma shuhada kina da hakuri da juriyar wahala amma inaso ki qara akan wanda kike dashi Shuhada kiyiwa yadikko biyayya tamkar ni duk abinda zasu miki shuhada kibarwa Allah Domin innallaha ma'assabireen Kinji ko shuhadata? Shuhada kuka take ta rungume innarta Inna tace kibar kuka shuhadata Duk wuyan rayuwa karki bar karatu domin ilmi haske ce jahilci kuwa duhu ne Duk da shuhada shekarun ta bakwai amma tasan rayuwa Tace insha Allah innata na miki alkawari zanyi karatu sosae na zama likita Inna tayi murmushi tace Allah ya miki albarka shuhada Allah yasa ki zama abin alfahari Allah ya raya min ke Allah yabaki miji nagari wanda zai jikanki ya so ki sosae Ameen shuhada tace Inna tace shuhada jeki kawo min ruwa nasha Shuhada tana dawowa da ruwan taci karo da babbar tashin hnkl Mgnr take yiwa inna Amma shuru kuka tasa tahau jijjiga inna tana cewa ga ruwan amma shuru Ihu shuhada tasa daidai lkcn da mairo ta shigo gidan da gudu tayi kansu tana tmbyar shuhada mai yafaru Cikin kuka tace gwaggo mairo innata Mairo taba iklima tayi tace innalillahi wainna ilayhirrajiun kullu nafsin za'ikatil maut rufe idon iklima mairo tayi da zafi Taja hannun shuhada Suka fita Mairo tana kuka shuhada ma tana kuka har gona sukaje ta fadawa yayanta mlm amadu Shi karan kansa saida yyi hawaye ga tausayin yar'sa shuhada Haka akazo akayiwa iklima sutura su gwaggo mairo ne suka mata wanka Agaban shuhada aka fita da innarta a makara sumewa tayi jama'a suka taro akanta sosae suka tausaya mata Duk wannan abun yadikko bata gida KO da tadawo taga mutane cike tam agidan tasan akwai abinda ya faru Cikin ranta tace Allah dai yasa shigiyar nan mutuwa tayi da sauri tashige cikin gidan Tasamu mata anata bawa shuhada hakuri tare da lallashinta Tmbya tayi.akan mai yafaru ? Akace mata kanwarki ce Allah ya karbi abunsa Kukan munafurci

Chapter 1 of 13