Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

biyu kika yi tozali da Yaya Mamman ni fa ɗazu ƙarya na kirfo da na ce ina ganin Fatalwar Mudassiru, saboda yaran nan sai su raina mu ni kuma a duniya babu abin da na ƙi jini irin raini."

Inna Furai ta miƙawa Lantan hannu ta ce, "Lantan taɓa ni na ji." Da sauri Lantan ta kai hannu tana shafa hannunta. Inna Furai ta mirtsika ido ta ce, "Billahilazi idan har wannan taɓawar da kika yi mini mafarki ce to a mafarki na ga Malam. Wallahi da idanuna na ganshi a wurin zaman alwalarsa amma tun da baku yadda ba nan gaba na kuma ganinsa nasa ya fitowa kowa a zahiri." Kamar wacce aka tsamo daga ruwan sanyi haka jikin Lantan ya yi sanyi ta rasa abin faɗa don hantar cikinta ta fara kaɗawa musamman da ta san Inna Furai ba ta yin rantsuwa sai da ƙwaƙƙwaran dalili. Kwanciya suka yi sai dai kowa da abin da yake wassafawa a cikin zuciyarsa.

Duk cikin ƴaƴan Inna Furai babu wanda ya fi farinciki da tafiyarsu irin Auwalu saboda zuciyarsa gabaɗaya hankalinsa yana wurin Yahanasu don ya san a wannan lokacin tuni ta yi fushi sai ya yi aikin rarrashi. Yana tafe yana haska fitila har ya ƙarasa ɗakin, sai dai turus ya yi a ɗan tsorace yana karewa ɗakin da Yahanasu kallo. Fitsarin da ya ƙarasa gangarawa ƙafarsa ne ya dawo da shi daga duniyar tunani, matsawa ya yi gefe yana leƙa fuskar Yahanasu da ke manne da bango ya ce,

"Yahanasu lafiya kuwa?" Yahanasu na jin muryar Auwalu ta rushe da kuka tana cewa, "Auwalu fatalwar Baba na gani wallahi shi ne har cewa ya yi za su tafi da ni." Cikinsa ne ya bada wani sautin ƙulululu! Da sauri ya ja baya yana dafe ƙirji ya ce, "Kina nufin da gaske kema kin ga fatalwar Baba?" Yahanasu ta nuna masa gadon bayanta ta ce, "Duba ka ga shatin carbinsa a bayana har dukana ya yi da shi kuma ya ce daga yau kar sake buɗe idona." Tsoro ne ya mamaye zuciyar Auwalu musamman da idanunsa suka yi tozali da shatin carbin Mahaifinsu ruɗu-ruɗu a jikinta. Hankalinsa bai ƙara tashi ba sai da ya hango wani guntun likkani a gefen ƙafar Yahanasu. Da sauri ya fisgota suka faɗa gado jikinsa na rawa ya ce, "Yahanasu wallahi maganarki haka take kin ga Likkafani can a ƙasa." Yahansu na jin haka ta ƙara rintse ido tana kuka kamar hawayenta za su ƙare. Auwalu ne ya yi ta maza ta miƙe cikin sanɗa ya banko musu ƙofa da ƙarfi ya sa sakata.

Duk abin da yake faruwa a kunnen Baba Sule da Sahura har zancen Likkafani, wannan maganar ba ƙaramin ɗaga musu hankali ta sake yi ba. Don da har bacci ya fara yunƙurin awon gaba da su kukan da Yahanasu ta rushe da shi ne ya wartsakar da su tare da sa su yin carko-carko kamar masu shirin ko ta kwana.

Dubu tun da ta koma ta yi luf sakamakon motsinta ya so tashin Hasiya Matar Rabe, don haka ta yi kasaƙe daga haka ba a jima ba bacci ya yi gaba da ita don hatta sallar Asuba sai da aka yi da gaske sannan Dubulliya ta samu gabatar da ita.

Washegari.

Jama'ar gidan gabaɗaya kowa ya tashi an ci gaba da harkoki kamar ba taron mutuwa ba. Sai dai gabaɗaya labari ya watsu a ko'ina Inna Furai ta yi ido huɗu da fatalwar Maigaidansu, labarin da wasu suka riƙa ganin kamar tsufa da rikici ne yayin da wasu suke ganin tsabar dukan da mutuwar ta yi mata ne. Sai dai babban abin da ya ja hankulan mutane ganin ɗakin Baba Sule da Auwalu ya rufe. Ko motsinsu babu wanda ya ji bare a sa ran za a ga fitowarsu.

Ɗakin Baba Sule aka fara zuwa ana bugawa, Sahura ta zabura za ta miƙe saboda ta ji muryar mutane don ta yanda ta ayyanawa zuciyarta muddin ta samu ta fice daga ɗakin to ba za ta ƙara kwana a gidan ba sai gidan Mahaifinta. Sai dai tana miƙewa caraf Baba Sule ya damƙi hanunta yana cewa, "Ina za ki tafi ki bar ni?" Sahura ta ƙirƙiro murmushin yaƙe ta ce, "Ai mutanen gida sun tashi ka ga muma sai mu fita zaman ɗaki ba zai kai mu ba." Baba Sule ya yi fakare yana nazari sannan ya ce mata, "Sahura yau ko bayan gida za ki shiga wallahi sai dai mu tafi tare, don ba zan bari matattu su tafi da ni da kwana na a gaba ba." Bugun ƙofar ne ya tsananta don haka suka taso riƙe da hannun juna suka zare sakata, sai dai suna buɗe ƙofa kyallen likafanin da Dubu ta soka musu ya faɗo. Daga waɗanda suke tsaye a ƙofar ɗakin har su na cikin ɗakin bazama suka yi a guje, suka yi cikin gida. A cen ɗakin Yaya Babba suka yada zango sai dai har lokacin Baba Sule yana riƙe da hannun Sahura. Yaya babba sakin baki ta yi tana kallon Baba Sule da ya yi tsamo-tsamo a cikin mata ta ce, "Sule me kake yi a kan cinyar Uwani?" (Uwani ƙanwar Mahaifiyar Sahura ce.) Baba Sule gabaɗaya zuciyarsa a dagule take saboda gani yake rayuwarsa ta zo ƙarshe.

Ba baka sai kunne. Baba sule ban da hawaye babu abin da yake yi. Wannan shirun da Baba Sule ya yi ba ƙaramin ɓata ran Yaya Babba ya yi ba, don haka ta dube shi ta ce, "Bana son iya shege kai Sule idan ba za ka yi magana ba, ka fice mini daga ɗaki ko na kwashe maka albarkar da ta yi saura a kanka." Baba Sule ya sake matsar ƙwalla ya ce, "Inna wallahi Fatalwar Baba ce za ta tafi da ni matukar na saki hannun Sahuwa ƴan sama jannati ne za su tafi da ni." Ku san mutuwar zaune Yaya Babba ta yi saboda labari ya risketa daga wurin kishiyarta ga shi Ɗan cikinta ma ya sanar da ita.

Nan fa gida ya hautsine hantar cikin kowa ta kaɗa saboda fargaba, Sai da Yaya babba ta yi da gaske sannan Baba Sule ya saki hannun sahura. Ai kuwa yana sakin hannunta ta ranta ana kare. Baba Sule na ganin haka ya rufa mata baya. Sai da ƙyar aka samu aka tsayar da su a soron gidan tare da tura Baba sule cikin ɗaki don Yayan Mahaifinsu gani yake kamar gamo ne suka yi. Dubu ban da dariyar mugunta ƙasa-ƙasa babu abin da take yi.

Sai daga baya aka farga da su Auwalu da suke ɗaki don haka da sauri Yayan Mahaifinsu ya je ya sa suka buɗe ƙofar da ƙyar, Auwalu yana maƙale da Yahanasu don gani yake idan ya sake ta kamar Fatalwar Mahaifinsa za ta yi awon gaba da ita.

Malam Idi shi ne yayan Mai Carbi, tara mutane gidan ya yi gabaɗaya yana yi musu nasiha da nusar da su illar yarda da amincewa abin da suka yi tozali da shi. Sai da ya gama wa'azin sannan ya bawa Inna Furai damar ta yi magana.

Inna Fuarai ta karkace ta ce, "Yaya Idi yadda na ga Fatalwar Malam na ga Annabi. Ganin idona na ganshi kuma har umarnin shayar da su Auwalu ya yi." Sai da suka gama jin jawabinta tsaf sannan aka ce Yahanasu ta yi faɗi abin da ta sani, Yahanasu da ta buɗe ido da kyar tana sunne kai ƙasa don duk yanda hankalinta ya ɗan kwanta har Yaya Idi ya sa ta buɗe ido bata gama sakewa ba. Ta fara yi musu bayani dalla-dalla sanna ta ɗora da cewa, "Kuma da bakinsa ya sanar da ni duk wanda ya wayi gari da likkafani a ɗakinsa to gaba shi za su ɗauka. Shi ya sa na ce tawa ta ƙare." Auwalu ya rumgumota yana cewa, "Ba za ki mutu ba Yahanasuna" Yaya Idi ya yi jim sannan ya ce, "Idan na fahimta wani ne kawai yake son razanar da mutanen gidan amma babu damuwa ku bar mini komai a hannuna zan san yanda zan ɓullowa lamarin.

Dubu tana gefe tana jin duk wainar da ake toyawa don haka ta saci jiki babu wanda ya lura da ita, kuma babu wanda ya taɓa kawo ita za ta aikata wannan abin. Dubu na tafiya ta wuce ɗakin Marigayi ta zaro wasu kayansa da yake zuwa sallar juma'a da su. A wanke suke a goge fari ƙal da su, sai da ta bubbuɗa su ta je bakin katangar banɗaki wacce mutum zai iya haurawa ta wurin ta ajiye, hularsa ta saƙale a jikin wata itaciyar tunfafiya sai kuwa ta kwaso a guje ta shiga wurin taron da suke gabda kammalawa. Ihu take kwarawa kamar wacce ake ɗanawa wuta tana cewa, "Wayyo Allah na ga Fatalwar Baffa na gani zai tafi da ni. Kafin ka ce wani abu tuni wurin ya watse sai takalma da ɗankwalaye da aka barsu suna cin karen su babu babbaka. Yaya Idi sai da ya yi kusan adungure biyu sannan ya samu ya shige ɗakin Inna Furaira. Hularsa kuwa ta yi tsalle ya fi sau biyar kafin ta samu sukuni faɗuwa can bakin ƙofa.
[7/23, 2:48 PM] Ameera Adam🌚: *DUBU JIKAR MAI CARBI*


©AMEERA ADAM

FIRST CLASS WRITER'S ASSO...

*Littafin kuɗi ne 200 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin Mtn, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.*


FREE PAGE 4


Wannan karon gabaɗaya turus suka yi da jin abin da aka faɗa, kallon-kallo aka fara yi a tsakanin juna kowa da abin da yake nazari a zuciyarsa. Suna cikin haka suka sake jin an ce, "Bismillahir rahmanirrahim bari mu fara ɗauka daga kan ta bakin ƙofa." Ai Dubu bata rufe baki ba sai ji ta yi alamar guje-guje, Yahanasun Auwalu tun bayan sallar asuba da ta shiga ɗakin Inna Furai ba ta sake fitowa ba kuma ta ci alwashin ko da fitsari za ta ji sai dai ta matse abin ta, idan ta kama ma sai ta saki abin ta a wurin. To ashe tsugunne bata ƙare mata ba tun da har fatalwar za ta iya kawo musu farmakin dare har cikin ɗakuna, tun da ta ji an ce za a fara ɗauka daga na bakin ƙofa.

Nabila ƴar wurin Hajiya Nafisa, budurwa ce don ta yi sha tara a shekaru. Turo baki ta yi tana cewa, "Maganar gaskiya Mommy ni fa na gaji da wannan abubuwan kullin abu ɗaya wacce irin fatalwa ana zaune ƙalau bayan kowa ya san babu wata fatalwa a musulunci." Cike da ƙosawa Hajiya Nafisa ta ce, "Nabila ya za mu yi kin san dai ba mu da ta cewa tun da zuwan nan na dole ne ya kama mu haka Allah ya ƙaddara mana." Yaya Babba da ke gefe fuskarta ban da gumi da maiƙo babu abin da take yi, ta dubi Hajiya Nafisa da kallon sheƙeƙe ta ce, "Ke Nafi! Zuman ku a gidan na shi ne ƙaddara? Wallahi za ki ga ƙaddara kuwa ganin idonki. Wannan gidan da kike gani kin zo kenan zuwa sojan badaskare." Tana gama faɗa ta yi ƙwafa a zafafe. Dubu daga wurin da take ta jiyo hayaniya na tashi kaɗan-kaɗan ta sake shaƙe murya ta ce, "Ƴan sama jannati basa lamintar kuskure don haka za mu fara bi ta kan dabbobin gidan kafin mu fara taɓa mutanen ciki, ina tawagar Fatale ku fara dirowaaaa." A hankali ta lallaɓa da sauri ta buɗe ɗakin zabbin Baba Munkaila. Hannunta riƙe da muciya ta fara buga ƙyauren langa-langar da ke jikin ƙofar. Nan da nan zabi suka fitowa a tsorace suka fara tsalle da kuka "Ƙurƙet! Ƙurƙet!" Da yake da hasken wutar lantarki tuni zabbi suka fara bazama suna kuka, Dubu ta sa muciya ta riƙa make kawunansu ɗaya bayan ɗaya. Da ta bugawa zabo ɗaya sai ka ji ya yi ƙara ya faɗi ƙasa. Wannan kukan Zabbin ba ƙaramin ɗaga hankulan mutanen da ke cikin ɗakunan ya yi ba. Shiru suka yi suka zurawa sarautar Allah ido. Kowa da abin da yake ayyanawa zuciyarsa. Sai dai a wannan ƙadamin Lantan ta ci alwashin matuƙar tana da rabon ganin wayewar gari, babu wanda zai hanata tafiya don tun da ta zo duniya bata taɓa ganin masifa da tashin hankali irin wannan ba.

Zabbin nan gabaɗaya haka suka warwatsu suka shiga sauran sashen da ke cikin gidan. Muhsana ita ce ƴar autar Lantan, ta taho daga can sashen Baba Sule ba ta san abin da yake faruwa ba ta hangi Zabbin Baba Munkaila suna guje-guje wanda ya tabbatar mata da alama akwai abin da yake faruwa. Gabanta ne ya faɗi sakamakon ganin gawarwakin Zabbi kusan bakwai a ƙasa jini duk ya ɓata wurin. Sai dai har lokacin bata ga wanda yake aikata wannan abin ba, ɗaya zuciyarta ce take raya mata ko dai da gaske Fatalwar da ake faɗa ce ta fara aikinta, yayin da ta ƙara riƙe hannu Ɗanta Salihu don dama yaron ne ya fito da ita zai yi kashi. Ta bayan ɗakin Marigayi mai carbi ta je wucewa ba ta yi aune ba sai ji ta yi an fisgi hannun Salihu, aikuwa kusan tare suka ƙwalla ƙara daga ita har Salihun da ake ja, jan Salihu ta riƙa yi tana yi tana ihun neman agaji amma ba a daina jansa ba. Dubu na ganin Muhsana ta kusa fin ƙarfinta ta raɗa mata muciyar a baya tana cewa, "Ki taho mu yi rayuwar barzahu da ke. Ko ki bani Ɗanki Salihu na tafi da shi, ko kuma na ɗauke ku gabaɗaga." Muhsana bata gama jin ƙarashen maganar ba ta saki hannun Salihu ta yi cikin gida da gudu tana tafe tana sosa wurin da Dubu ta maka mata muciya. Shi kansa Salihu da ba a yi masa komai ba ya gama tsorata, dama jikinsa babu riga babu wando haka ya zuba a guje da tiƙeƙen cikinsa a daidai lokacin aka ɗauke wuta Salihu ya rasa wurin da zai bi haka ya riƙa gware da bango yana make sauran zabbin da suma ta kansu suke yi.

Ihun da Salihu yake yi ne ya tabbatar musu da lallai Fatalwa ta fara zuwa kan bil'adam, tun da; da farko sun ji kukan zabbi. A wannan lokacin Yaya Babba da ƙaramin tsorata ta yi ba don ko kaɗan Dubu bata faɗo mata a rai ba bare ta ambace ta. Lantan da ke ɗakin Inna Furai ta fara hawaye bibbiyu don saboda firgici ta tuɓe kayan jikinta ta sake saka su ya fi sau bakwai. Lokacin da ta riski muryar Muhsana na ihu, kuka ta riƙa yi wiwi don Mushana ita ce autarta. Da ta daina jin kukan Muhsana sai na Salihu wannan ne ya bata tabbacin tuni Tawagar Fatalen sun gama da Muhsana sun koma kan Salihu. Da ƙyar Salihu ya samu ya isa wurin ɗakuna ya fara lalubawa yana kuka, hannunsa ya ɗora akan ƙofar su Inna Furai yana bugawa yana faɗin, "Innaaaaa! Iyaaaa" Lantan na jin haka ta ɗare saman gadon Inna Furai hannunta riƙe da ɗan kanfen Badariyya tana ta tura kai duk a tunaninta rigarta ce za ta saka. Inna Furai wani farfari ta riƙa yi kamar wacce take kan hanyar suma, sai motsa baki take tana addu'a.

Zabbin da suka tarwatse wasu daga cikin su hanyar waje suka yi, suna kuka a firgice. Dubu tun da ta ga an ɗauke wuta ta haye katanga ta dira ta bayan gidan. Sai ga ta kamar mumina ta wuce shagon Lamarana ta siyo maganin sauro, da sauran wata hamsin ɗinta. Zuwanta ƙofar gidansu ya yi daidai tashin Baba Munkail kenan yana kaɗa Zabbin da ya ga suna tsalle suna fitowa ɗaya bayan ɗaya. Mutanen wurin ne suka fara taya shi, Dubu na zuwa ta zabga uwar sallama, ta yi haka ne saboda Baba Munkaila ya ganta don ta sake cire zarginta da yake daga kanta.

Cikin masifa ya fara yi mata magana, "Dallah sakarai matsa kina gani zabbina na fitowa sai wani ya ɓace a cikin duhu." Da sauri ta matsa gefe ta ce, "Baba Munkaila don Allah ara min fitila na kaiwa Inna Maganin sauronta tsoron soro nake." Ci kanki bai ce mata ba har suka samu suka kame zabbin, ban da masifa babu abin da Baba Munkaila yake yi, don a duniya idan kana son ganin ɓacin ransa cikin gaggauwa ka taɓa masa zabbinsa ko kuma wani laulawar keken hawansa. Yana gaba Dubu na biye da shi sai mutum uku da suke riƙe da zabbin nasa. Faɗa yake ta saki yana cin alwashi ga duk wanda ya buɗe masa Zabbi sai ya yi masa rashin mutumci. Suna shiga tsakar gida Baba Munkaila ya hasko gawar wasu zabbi biyu daga bakin ƙofa. Nan take cikinsa ya bada sautin ƙululululu! Jikinsa ne ya ɗau tsuma wani gumi na keto masa ta ko'ina, watsar da na hannunsa ya yi; ya kwasa a guje.

Yadda jaruman Indiya suke kwasar gudu idan sun yi tozali da masoyansu haka Baba Munkaila ya watsar da zabbin hannunsa ya kwasa da gudu har da wata uwar ƙara yana zuwa ya zube a wurin ya suri Gawarwakin zabbin ya rungume yana sauke ajiyar zuciya mai zafi, haɗe da haɗiyar wani irin yawu mai ɗacin gaske.

Kamar mai shirin yin kuka haka Baba Munkaila ya rinƙa shafa matattun zabbin yana cewa, "Don Allah wanene ya yi mini wannan ɗanyen aikin. Wallahi duk wanda na kama yana da hannu a ciki sai na ci ubansa." A daidai lokacin Dubu da sauran mutum ukun da ke riƙe da zabbinsa suka ƙaraso. Dubu ta yi tsaye tana kallon yanda gumi ke ɗiga daga jikin Baba Munkaila. Yana ɗagowa ya maka mata duka yana cewa, "Don Ubanki za ki kamo mini sauran ko su ma sai an kashe mini su." Kamar mai jira haka Dubu ta sheƙa da gudu kamar gaske tana dariya ƙasa-ƙasa. Daga can ɗan nesa Baba Munkaila ya fara hango ƙaramin yaro yana tafe yana jan ƙafar wata ƙatuwar zabuwa, wacce da alama ita ce uwar garken ciki. Salihu yana tafe yana murmushi yana zuwa ganin Baba Munkaila na riƙe da sauran zabbin ya sa ya miƙa masa yana sake yaƙe baki yana cewa, "Baba an ci kaza." Kusan suman zaune Baba Munkaila ya yi, ya ƙurawa Salihu ido ya ganshi tik ko wando babu. Cikinsa ya yi kurcici sai sheƙi yake da maiƙon abinci. Baƙin cikin ne ya kama Baba Munkaila ya dubi Salihu murya a daƙile ya ce, "Kai a ina ka gano wannan?" Salihu ya juya bayansa ya nuna ya sake cewa, "Baba an ci kaza"

A fusace Baba Munkaila ya buga masa tsawa ya ce, "A gidan uwarka za a ci kaza?" Salihu ba ƙaramin tsorata ya yi ba don haka ya saki zabon hannunsa jikinsa na rawa. Baba Munkaila ya sake ɓata fuska ya ce, "Waye ya kashe mini zabbi ko kaine?" Tsoro da ganin yanda Baba Munkaila ya ɓata fuska ya sa Salihu bai yi wata-wata ba, ya ce, "Ni ne a cen"

Baba Munkaila zuru ya yi yana kallon Salihu kamar wanda ya yi tozali da sabuwar halitta, ya sake haɗiyar yawu mai ɗaci murya a daƙile ya ce, "Wato kai ka buɗe daga keji suka fito ko?" Salihu ya gyaɗa kai wannan karon har da murmushinsa na ƙarfin hali ya ce, "Ni a Umma ne..." Haushi ya sake kama Baba Munkaila ya ji kamar ya shaƙe wuyan Salihu. Kawai sai ya miƙe ya damƙi hannun Salihu ya juya ba walawa ya cewa mutanen da suka rako shi ciki, "Malam Hamza ga kejinsu ku zuba su a ciki." Mugun kallo ya watsawa Dubu don Allah ne ya taimake ta ba ta yi wani laifin ba da ragowar fushinsa a kanta zai sauke.

Yadda Baba Munkaila yake fusgar hannun Salihu ba ƙaramin tausayi da dariya zai baka ba, yana zuwa wurin ɗakunan ya fara kwaɗawa Muhsana kina. Sai dai babu motsin wanda ya ji hasalima ƙofar ɗakunan gabaɓaya a rufe suke. Haushi da ya kama shi ya hau buga ƙofofin ɗakuna yana faɗin,

"Wai lafiya kuwa mutanen gidan nan wannan wanne irin abu kuke yi ne." Wannan bugun ƙofar ba ƙaramin razana Salihu ya yi ba, don haka ya fara tsanyara kuka yana murza idanu tare da wurga tsilla-tsillan ƙafafuwansa. Cike da takaici Baba Munkaila ya tallaƙe ƙeyarsa yana cewa, "Rufe mini baki don ubanka. Shegen yaro mai siffar ƴan ruwa."

Dukan da Baba Munkaila ya yi wa Salihu ba ƙaramin ratsa kansa ya yi ba don haka ya kuma fashewa da kuka. Lantan da ke cikin ɗaki ta kuma zabura tana cewa, "Innamal A'amalubinniyati..." Sai kuma ta hau gado ta sauko, sannan ta sake cewa, "Sadaƙallahul azeem. Kuna ji fatalwar nan har rikiɗa take yi za ta yaudare mu, mu buɗe mata ƙofa." Inna Furai da ta yi ɗai-ɗai a ƙasa ta ɗauko wani rawanin Marigayi Mai carbi, ta ƙadandane shi tana numfarfashi ta ce, "Ni dai na san idan da zazzagar amana to babu makawa fatalwar nan koda ta shigo ba za ta illatani ba. Wannan rawanin tun na ranar aurenmu ne wannan kaɗai ya isa shaidata..." Bata ƙarasa sambatun ba suka ji bam Baba Munkaila ya ɓallo ƙofar, ya koma ta ɗakin Yaya Babba ita ma ya ɓalle ta. Nan fa suka yo carko-carko masu ihu na yi masu gudu suma suna yi. Tsawar da Baba Munkaila ya buga ce ta saita nutsuwarsu, yana huci ya nuna Salihu da ke rarraba idanuwa ya ce, "Ina uwar yaron nan?" Tsit suka yi aka rasa mai magana sai Lantan da ke zare idanu ta ce, "Ai Muhsana kam tuni Fatalwa ta daɗe da gamawa da ita..." Da sauri ya katse ta da cewar, "Don Allah Inna Lantana ki rabani da zancen fatalwar nan. Ku duba irin ɓarnar da aka yi mini." Ya ƙarasa maganar yana haska musu gawarwakin zabbinsa.

Yaya Babba da fitowarta kenan ta zuba kabbara tana cewa, "Kazalika mun ga tabbaci wallahi ya tabbata fatalwa na bibbiyarmu a gidan nan. Dama fa kafin su aiwatar sai da suka faɗi cewar za su fara ta kan dabbo. Don Allah ku kira mini Garba don idan na ƙara kwana a gidan nan ba Mai Jama'a ne ya haife ni ba."

Ana cikin haka sauran Mazajen gidan da ke zaune a ƙofar gida suka shigo sakamakon Malam Hamza ya sanar da su abin da suka gani. Ganin su Yaya Babba carko-carko a tsaye ya sa su tambayar ba'asi, nan take aka sanar musu Baba Munkaila ya kora musu jawabin zabbinsa. Cikin Baba Auwalu da na Baba Sule kusan lokaci ɗaya ya kaɗa, tuni gumi ya wanke musu fuskoki. Nan fa aka shiga tausar Baba Munkaila akan ɓarnar da aka yi masa sannan magidantan mazan suka ci alwashin ɗaukan mataki a cikin gidan. Baba Abubakar da kansa ya fita ya sanarwa ƴan bijilanti abin da yake faruwa ya basu umarnin kula da gidan tun daga bayan gidan har zuwa cikinsa.

Lantan duk wannan matakin da aka ce za a ɗauka bai yi mata ba, don ta kasa ta tsare akan dole sai ta tafi a daren sai da Baba Abubakar ya lallaɓata sannan ta amince da sharaɗin gari na waye za ta kama gabanta. Hajiya Nafisa na jin haka ita ma ta yi tsalle ta ce washegarin ranar za ta tafi don ba za ta ƙara kwana ba. Gabaɗaya suka ɗunguma zuwa sashen Auwalu da ƙyar can ma aka samu suka buɗe ƙofofi don Muhsana sai da ta suma ya kai sau Uku, da ta farfaɗo idan ta ce ina Salihu? Suna ce mata baya nan take sake zubewa.

Duk plan ɗin da ake shiryawa Dubu ta yi fakare tana sauraronsu, kuma zuciyarta ƙal da ta ji kowa ya ce zai koma inda ya fito.

Sai dai suna haɗa ido da Nabila sai ta bushe da dariyar mugunta tun Nabila bata lura ba har ta fara fahimta. Faɗa suka yi kace-kace har Nabila ta cewa Dubu, "Ballagaza ƴar ƙauye." Buɗar bakin Dubu kuwa ta ce mata, "Ubanki ma ɗan ƙauyen ne kuma kema

Please Login or Register in order to submit comment