Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

©AMEERA ADAM

FIRST CLASS WRITER'S ASSO...

*Littafin kuɗi ne 200 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin Mtn, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.*


FREE PAGE 7
https://youtube.com/c/DuniyarHausaNovels

Ku dannan👆🏼👆🏼👆🏼👆🏼👆🏼 subscribe tare da alamar kararrawa domin samun shirye-shirye da sauran littafai.

Waɗannan kalamai na Yaya Babba ba ƙaramin sake ɗaga hankalin Hajiya Nafisa suka yi ba, ciki a kaɗe hankali a tashe ta dubi Yaya babba da babu abin da take yi ban da huci ta ce, "Inno ba mu fahimce ki ba. Shi Aseem ɗin za a mayar kamar bayan silba?"

"Ke Nafisa ki fita daga idona, dama ban faɗa don ku fahimce ni ba ehe. Hadiza meye laifina don na nemawa marainiyar jikata maganin tsari?" Hadiza ta girgiza tana faɗin, "Babu laifi Inno!" Yaya babba ta ci gaba da cewa:

"Allah ya jiƙan Idi ɗan wanzam ya gafarta masa shi ya bani laƙani na yi wa yarinyar nan Dubu, akan duk wanda ya farketa to shi da sake zama namiji har abada kenan." Hajiya Nafisa ji ta yi ƙafafuwanta sun yi sanyi har tsayuwar na neman gagararta. Don haka ta jingina ta bango tana bin Aseem da wani irin marayan kallo.

Kafin wani lokaci gabaɗaya iyalan gidan sun hallara a ɗakin Yaya babba dama kuma gidan babu kowa sai iya su ƴan gidan, don haka suka hallara kowa zuciyarsa babu daɗi. Yaya babba ta fara bin su ɗaya bayan ɗaya sannan ta fara cewa, "Na san dai kun san dalilin tattara ku da na yi a wurin nan. A zahirin gaskiya Soja ya keta mini rigar mutumci, saboda Allah wane mugun abin yarinyar nan ta yi wa yaron nan da zai aikata mata wannan mugun halin..." Kuka ya ci ƙarfin Yaya babba saboda zuciyarta ɗaya ta ɗauka Aseem wani abu ya yi wa Dubu da ta tafiyarta ta sauya.

Baba Adamu ya yi sallama sannan ya fara fa cewa, "Inno don Allah ki yi haƙuri. Amma kafin a yanke wani hukunci ya kamata a ji ta bakin yaron nan bana jin Aseem zai aikata abin da ake magana akai..." Yaya Babba ta yi farat ta katse Baba Adamu da cewar, "Ado ƙarya na yi kenan? Ku tashi ku fice daga gabana idan ba so kuke na yaye falsafar albarkar da ke kanku ba." Baba Adamu ya yi ƙasa da murya ya ce, "Inno don Allah ki yi haƙuri ba haka nake nufi amma duk yanda kika ce haka za a yi."

"Ke Dubu me soja ya yi miki bayan ya tafi da ke." Dubu da har lokacin da sauran tsoron Aseem a zuciyarta ta saci kallonsa aikuwa suna haɗa ido ya watsa mata mugun kallon. Sai a kan idon Yaya babba ta ga irin kallon da Aseem ya yi wa Dubu, ai kuwa wani irin gumi ne ya fara yayyafowa Dubu ta fara inda-inda. Yaya babba ta fara salati tana tafa hannuwa ta kalli Aseem ta ce, "Ittaƙillah Soja ka ji tsoron rabbissamawati, idan ka zare mata ido a nan duniya a cikin kabari za ka zare wa Mala'iku ido ne. An ya Soja haka ka koma ban sani ba?" Ta mayar da kallonta wurin Dubu ta ce, "Za ki yi wa mutane bayani ko sai na sa Munkaila ya zane miki jiki ciki da bai." Dubu ta muskuta gefe ta fara cewa, "Da ya kaini mota bindiga ya ciro wai zai harbe ni ya wurgar da gawata a gefen hanya." Da sauri Yaya Babba ta dafe ƙirji ta ce, "Kun ji ko? Na gaya muku tuni ya riga da gama da ita." Hajiya Nafisa saboda ɓacin rai ji ta yi kamar ta shaƙo Dubu da Yaya Babba ta shaƙe su. Dubu ta ci gaba da cewa, "Muna zuwa gidan ya yi mini aski kuma wai da har billen gobirawa zai yi mini. Daga nan ya sani tuƙin babur shi ne muka taho gida." Yaya babba jikinta ne ya fara sanyi ta ce, "Daga haka bai yi miki komai ba?" Dubu ta ce, "Eh"

A ɗan ƙufule Yaya babba ta ce, "To da kika ce ɗan iska ne?"

Dubu ta ɓata fuska ta ce, "Eh mana ba ke kika ce mini duk mace mai bin namiji, ita da shi duka ƴan iska bane?" Wata gwauruwar ajiyar zuciya Hajiya Nafisa ta sauke, Yaya babba cikin jin haushi ta ce, "Amma Allah wadaran halinki Dubu da za ki iskanta mini jika, ina ji ina gani a gaban iyayensa. Kedai an yi makira yanzu ba sai ki sa Garba ya ce ba na son Ɗansa ba. Ni dai kin cuceni za ki haddasa gaba a tsakanina da ƴaƴana. Tashi ki bani wuri makira in Allah ya yarda ba zan ga ɗan iska a kan jikana ba. Don Allah ku gaya mini abin da Soja ya tsare wa Dubu da za ta yi masa mugun fata haka?" Kowa ya yi shiru a ɗakin bai tanka mata ba. Yaya babba ta dubi Aseem da fuskarsa ta yi murtuk saboda ɓacin ra ta ce, "Soja ka gafarce ni wallahi wannan makirar ce ta ingiza ni, ni dama sai da zuciyata ta raya mini babu abin da za ka yi wa Dubu." Ci kanki Aseem bai ce mata ba, sai kuma ta fara matsar ƙwalla ta ce,

"Garba kana gani Soja ya ƙullace ni har ya ɗau fushi da ni. A gidan duniya idan ban yi wa jikana magana ba wa zan yi wa? Kana gani hakkin Soja zai bar ni kwanciyar kabari?" Baba Abubakar ya ce, "Inno bai ƙullace ki ba ina jin bai jiki ba ne." Ya faɗi haka ne don kar wutar rikicin Yaya babba ta ƙara tashi. Yaya babba ta saki murmushi tana goge hawaye ta ce, "Soja!" Ya ɗago ya dube ta har lokacin fuska babu walwala ya ce, "Na'am" ta ci gaba da cewa, " Allah dai ya yi maka albarka. Wallahi ka biyani da ka askewa yarinyar nan kai." Da sauri duk suka ɗago suna kallonta don ba su taɓa zaton haka daga bakinta ba.

Ta janyo Dubu tana sulle hijabin da ta ɗaura ta rufe kan da shi ta ce, "Wari dai akanta yanda ka san an buɗe shadda, idan Dubu ta buɗe kai a kusa da kai alƙur'an ko yawu ba za ka iya haɗiya ba. Kwanaki haka na saka mata fiya-fiya saboda kwarkwata amma yarinyar nan duk ta watsar a banza. Don Allah ka gaya mini wane saurayi ne zai ɗauki Dubu tana fama da tsamin kai dana hammata?" Hajiya Rahama ta yi murmushi ta ce, "Inno ai har yanzu Dubu yarinya ce tana ƙara zama budurwa duk za a nemi wannan ƙazantar a rasa." Yaya babba ta taɓe baki ta ce, "Ke Rahama rabani da cewa Dubu yarinya. Yarinyar da tun bara ta fara jini, ki gaya mini ta zama budurwa ko bata zama ba? Ga Ma'awiyya ƙawarta nan tun kwanaki aka yi mata aure wai sai ga ciki, nace kai waɗannan ƴaƴa an yi jarababbu yanda kika san a bakin ƙofa suke cin karo da shi. Yarinyar nan haka ta riƙa kuka da zan kaita ɗakin miji da yake ƙud-da-ƙud muke da kakarta, ina ta zuba ido na ji an ce yarinya tana gudun miji tana dawowa gida, kamar yanda muka riƙa yi muna amare ba sai muka ji shiru ba. Hali ne dai a ƙoƙon rai Dubu ba za ta daina wannan halin ba, ban ƙi ba idan ta haɗu da miji ɗan gayu kamar Soja." Ai kuwa Aseem na jin haka ya ɓata fuska bai gama tsinkewa da lamarin Yaya Babba ba sai ji ya yi ta ce, "Ai shi ma wannan shirun da yake yi ba banza ba wallahi, aure yake so don dai bai gaya muku bane. Ya yi gadon Kakansa Malam, don haka ya bani labari shi ma yana matashi Allah ya jiƙan Malam babba shi ya fahimci aure yake so, ba a ɗau lokaci ba aka ɗaura mana aure. Shi ma Soja ana haɗa shi da ƴar budurwa kamar Dubu shiru za ku ji sai dai ku ji ciki." Aseem a daƙile ya miƙe zai fita saboda takaici. Yaya babba ta bushe da dariya ta ce, "Kun ga abin da na gaya muku wai ya ji kunya na tona asirin zuciyarsa." Baba Adamu ya yi murmushi ya ce, "Yanzu Inno magana ta wuce kenan kowa zai iya tafiya?"

Take ta murtuke fuska ta ce, "Sam ban sallame ku ba wallahi akwai muhimmiyar maganar da nake son yi da ku ko Dubu?" Ta faɗa tana kallon Dubu da ke cika tana batsewa.

Dubu ta gyaɗa kai don fushi take da Yaya babba saboda irin bankaɗar da Yaya babba ta yi mata a gaban mutane, Yaya babba ta gyara zama sannan ta fara cewa.

"Garba wata shawara na yanke don Allah ya sani an daɗe ana shiga haƙƙina." Gabaɗaya suka kalleta suna mamakin jin kalamanta sai dai ba wanda ya tanka suna jiran jin ci gaban sauran maganar.

"Tun Malam yana raye nake son ganin kan iyalaina a haɗe ba wannan ya yi gabas, waccen kudu wani arewa ba."

Hadiza ta jinjina kai sannan ta ce, "Maganarki hake ne Inno amma ai kanmu a haɗe yake don gabaɗayanmu babu mai bijirewa maganar na gaba da shi." Yaya Babba ta washe baki ta ce, "Ai shi ya sa nake son na ƙara haɗa kanku idan na waiga na ga wannan inna juya na ga wannan ko ba haka ba Dubu?" Dubu ta yi murmushi don ta san muddin Yaya babba ta zartar da hukunci to ba fa ba shakka suma sun zama ƴan gayu irin yanda ƴaƴan Baba Adamu da Baba Abubakar suke rayuwa.

"To na zauna mun yi shawara ni da Dubu kuma ta bani shawara mai kyau akan haka." Wannan kalamai na Yaya babba ya yi daidai da shigowar Aseem zai ɗauki mukullin motarsa. Yaya babba ta yi farat ta dakatar da shi da cewar, "Kai Soja tsaya ayi da kai ka ji alherin da zai same ku don wallahi ba ƙaramin gata zan yi muku ba. To ina dalili in kwanta inmutu zuri'a a tarwatse, a'a sam haka ba za ta faru ba dama abin da na riƙa nusar da kakanka kenan ya ƙi gane wa." Aseem bai so zama ba don ya san ban da rikici babu abin da za ta yi musu a wurin. Amma gudun tashin hargitsinta ya sa ya koma ya zauna ba tare da ya tofa uffan ba.

"Yauwa magana muka yi ni da Dubu kuma wannan shawara da ta bani na yi na'am da ita. Na yanke hukunci kai Garba da ɗan uwanka Ado za ku dawo gidan nan da zaman. Kowa ya kwaso iyalansa ya kawo su ɓangarensa. Yo ina dalili ace da mahallinku a gidan gado kowa da ɓangarensa sai dai ace wai idan an kawo mana ziyara a sauka a ciki. A'a sam ba da ni za a yi haka ba Dubu ta ce sai mum fi cin daɗi kuma waye baya san daɗi a rayuwarsa Garba." Ta ƙarasa maganar tana tambayar Baba Abubakar da ya yi suman zaune. Kasancewar ya tafi wani tunani can bai ma san irin tambayar da Mahaifiyar ta shi take yi masa ba.

Hajiya Nafisa da ta cika fam har wani ɗaci take ji a zuciyarta ta ce, "Inno yanzu shawarar Dubu za a ɗauka? Dubu har wata mutum ce da za a saurari shawara daga bakinta. Maganar gaskiya wannan ci baya ne ace shekara sama da ashirin da bakwai muna zaune a cikin birni rana tsaka a ce mu dawo ƙau..." A hanzarce Baba Abubakar ya ce: "Nafisa! Bana son jin bakinki!"

"A'a ka barta Garba idan bata tsefe ni ba ai ba za ta nuna mini ta isa ba. Don Allah ka gaya mini lokacin da ka auro Nafisa a ina ka aurota da ya wuce ƙauye. Ka tuna lokacin da kuka je ƙauyensu ɗaurin aure Labaran ƙanina cewa ya yi ruwan garinsu kamar turɓaya haka yake. Nan dai gidan gado ne ko ana so ko ba'a so dole mutum ya dawo." Rai a matuƙar ɓace Aseem ya ɗago yana kallon Yaya babba, da Dubu da ke gefe. Furzar da iska ya yi ya sunkuyar da kai yana danne-danne da waya, sai dai ba zai ce ga takamaimai abin da yake latsawa ba. Baba Adamu ya russuna ya ce, "Inno a duba lamarin dai saboda yanayin aikinmu ga makarantar yara. Idan sha'awar zama kike kusa da mu ni ko Yaya Abubakar wani sai ya ɗauke ki, koma can da zama."

"Haram giya a gidan liman! Ba da ni ba. Ba zan taɓa bijirewa umarnin Mahaifinku ba, na gama magana idan za ku dawo nan kowa ya gyara wurinsa ya dawo, idan ba za ku dawo ba shi kenan" Tana gama maganar ta rushe da matsanancin kuka.

Zuciyar Baba Munkaila fes don ya san ko ba komai ya san idan suka dawo cikin gidan za su iya ɗauke masa cefanen gidansa. Baba Abubakar yanayinsa sam babu walwala ya dubi Mahaifiyarsa ya ce:

"Inno wannan kawai kike buƙata?" Da sauri Hajiya Nafisa ta hangame baki. Hajiya Fauziya ma ta cika fam tana watsawa Yaya babba harara ƙasa-ƙasa.

Yaya babba ta share hawaye ta ce, "Garba idan kuka yi mini wannan duniya da lahira kun biya ni haƙƙin mahaifiya. Ni dai Allah ne gatana kuma da shi na dogara, ko na dogara da ɗaya daga cikinku?" Baba Munkaila ya ce, "Inno mu kuma fa?"

"Munkaila a gidan duniya ka gaya mini wane abu ka taɓa yi mini." Baba Munkaila zai yi magana, Baba Abubakar ya katse shi da cewar, "Shi kenan zamu dawo Inno amma ki ɗan bamu lokaci tun da kin ga tashin namu babu shiri dole akwai abubuwan da za mu gudanar."

"Allah dai ya yi muku albarka Garba, ku yi komai a nutse wallahi. Me ake da gaggawa aikin shaiɗan. Me ye haɗinmu da shaiɗan muna masoya Mazon Allah (S.A.W). Allah ya yi mana tsari da shaiɗan, ku bi komai a sannu ko nan da sati biyu ne." Cikin haɗin baki suka ce, "Sati biyu Inno?"

"Ko ya yi yawa?"

Baba Adamu ya ce, "Inno Sati biyu ai ya yi kaɗan ina laifin nan da wata guda kinsan ko a gun aiki sai mun ɗauki uzuri." Ya gaya mata haka ne don ya san yanda take bawa aikinsu muhimmanci. Sai da ta yi jim sannan ta ce.

"Eh ka fi ni gaskiya Ado maza ku je ku yi komai a nutse kar wurin aikin su ji haushi su sallame ku ko?" Hajiya Nafisa kamar za ta yi kuka ta ce, "Yanzu Alhaji shi kenan ka amince nan ɗin za mu dawo?" Aseem ya sa hannunsa ya damƙi hannun mahaifiyarsa don ba ya son ace ita ta fara ɓullo da wata maganar. Fisgewa ta yi ta ci gaba da cewa, "Maganar gaskiya ba a yi mana adalci ba, sai da aka ga ƴaƴanmu sun zama ƴanmata za a ce mu dawo ƙauye wallahi da sake..." Cikin tsawa Baba Abubakar ya ce:

"Nafisa ya isa haka! Tashi ku fice an sallame ku." Rai a ɓace gabaɗaya matan nasu suka fice daga ɗakin. Baba Abubakar ya russuna ya ce, "Na barki lafiya Inno." Yana fita Baba Adamu da tsirarun ƴan uwansu suka bi bayansa. Ɗakin ya rage daga Baba Munkaila, Aseem, Dubu, Yaya babba sai Hadiza.

Jiki a sanyaye Yaya babba ta kalli Baba Munkaila ta ce, "Munkaila an ya yaran nan ba haushina suka ji ba kuwa? Na ga kamar a fusace suka fita. Don Allah meye laifina don na nemi haɗa kan zuri'ata?" Baba Munkaila ya washe baki ya ce, "Babu Inno kawai dai haka kika gani amma babu abin da suka ji, ya za a yi su ji haushinki." Yaya babba ta yi murmushi cikin jin daɗi.

Hadiza da ke gefe ta ce, "Gaskiya Inna bai kamata ace kowacce shawara Dubu ta gaya miki ki ɗauka ki yi amfani da ita ba. Mu fa mune ƴaƴanki mu ya kamata ki kira mu ji shirinki amma nawa Dubu take da za ta baki shawara." Yaya babba ta yi shiru kamar mai nazari sannan ta ce, "Kuma maganarki fa haka take don kin manta shawarar da Dubu ta bani akan sayar da ƙaton ragona ta ce na siyo ƴan tsaki, me ake yi da kiwon kaji idan ba asara ba? A rana ɗaya sai a fitar mini da mushen biyar suka lalace a banza bai fi ƙwara goma muka mora ba cikin Sittin. Kai amma Dubu an yi shakiyyiyar yarinyar, da ta ga kaza ta fara rufa sai dai na ji ta wasa wuƙa ta yanka, ni an ya ba da biyu ma Dubu ta riƙa yanka kajin nan ana soyawa ba?" Hadiza ta taɓe baki ta ce, "Ai koma meye Inno kun fi kusa. Amma kiwon kaji ana samu da shi wacce kika ɗora akai ce dai sai a hankali. Yanzu mu koma maganar su Yaya Adamu maganar gaskiya Inno ba za su ji daɗin zaman gidan nan ba, tun da sun saba da zaman cikin gari kina gani tun a gabanki me Nafisa take faɗa. Kina ganin zamansu a kusa da ke babu wata matsala?" Yaya Babba ta saci kallon Aseem sannan ta ce, "Ni fa Nafisa ta birgeni, sabo fa aka ce miki Hadiza. Sabo turken wawa, kuma ko ke ce haka za ki faɗa. Gaskiya ki daina cin naman mutane a ɗakina karki haramta mini mala'ikun rahama shigowa ɗakina ina zaune ƙalau. Yanzu ga Soja a zaune idan ya ji kina aibata mahaifiyarsa ba sai ya ɗauki gaba da ke."

Aseem bai tanka musu ba Hadiza ta ce, "Inno gaskiya fa na faɗa ko a gaban Nafisa zan faɗa ba wai Aseem ba. Ina guje miki abin da za a zo ana yin babu daɗi Amma tun da haka kike so shi kenan Allah ya dawo da su lafiya." Hadiza na gamaƙ maganar ta tashi ta fice, Baba Munkaila ya rufa mata baya.

Aka bar Yaya babba da riƙe haɓa, Aseem na shirin ta shi ta ce masa, "Soja don Allah ka bar ni na kwashewa yaran nan albarka, kana ganin abin da duk suka yi mini wai haɗe mini kai za su yi su ware ni daga cikinsu. Cikin halin ko'inkula Aseem ya ɗaga kafaɗa ya ce: "Ki kwashe musu mana, idan kin ga dama ki tsine musu ƴaƴana ko naki. Wallahi akwai abubawan da dama da idan muka dawo zan saita muku zama ke da sheɗaniyar jikar taki mutum ya kawo mini wargi na sa bakin bindiga na harbe shi." Yana gama maganar ya fice a fusace. Da sauri Yaya babba ta dafe ƙirji a firgice da jin maganar da Aseem ya faɗa.

Ummou Aslam Bint Adam🌚
*DUBU JIKAR MAI CARBI*


©AMEERA ADAM

FIRST CLASS WRITER'S ASSO...

*Littafin kuɗi ne 200 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin Mtn, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.*


FREE PAGE 8
https://youtube.com/c/DuniyarHausaNovels

Ku dannan👆🏼👆🏼👆🏼👆🏼👆🏼 subscribe tare da alamar kararrawa domin samun shirye-shirye da sauran littafai.

Aseem haka ya tafi ya bar Yaya babba hangame da baki, ta yi ƙasa da murya ta ce, "Dubu kin ji abin da Soja ya ce mini kuwa?" Dubu ta bushe da dariyar ƙeta don duk wanda ya ga yanda Yaya babba ta tsure sai ya fahimcin irin fargabar da ta shiga. Dubu ta ja hijabinta ta rufe kanta ta ce, "Ai wallahi Inno tsaf zai harbe ki don ba imani gare shi ba. Ni fa wallahi ina jin ma da ƙyar idan kafiran nan ba su fara koya masa kafirci ba." Da sauri Yaya Babba ta dafa cinyar Dubu ta ce, "Ke Dubu raba ni da jin wannan maganar, Mai sunan Malam ne zai amshi addinin kafirai?" Dubu ta ɗauke kai gefe ta ce, "Yoo musulmin ƙwarai za a haɗa shi da Allah da manzonsa ya ƙi ji ne?"

"A'a! Amma ki ji tsoron Allah Dubu kar ki sa na tuhumi Garba ya sake ɗaukan gaba da ni." Dubu ta ɓata fuska ta ce, "Ai dama ke ba a magana da ke sai kin kwashe kin gaya musu, haka kika gama ci mini mutumci a gabansu kina kirana da ƙazama." Yaya babba ta janyo Dubu cinyarta ta ce, "Ina sane na gaya musu haka idan ba haka ba wallahi Soja gaba zai ɗauka da ni amma ki bar ni da su idan suka dawo gidan nan duk za mu saita musu zama." Dubu na jin haka ta bushe da dariya don har ta gama tamawa yanda za ta yi wasan kura da Nabila don da alama ta lura ita ce hoton Hajiya Nafisa da duk wasu halayenta.

Inna Furai tun da suka dawo daga asibiti take ta bacci ba ita ta farka ba sai bayan magriba, tana farkawa ta hangi Larai a gefenta. Da murnarta ta tarbe ta da sannu sai dai ta lura da yanda Mahaifiyar tata take ƙarewa ɗakin kallo, matsawa kusa da ita ta yi ta ce, "Sannu Inna ya jikin?" Inna Furai ta yunƙura za ta tashi, Larai ta taimaika mata tashi sannan ta ce, "Larai ina su Lantan suke?" Larai ta yi murmushi ta ce, "Inna su Lantan ai sun wuce tun safe yanzu dai bari ki yi alwala ki yi sallah sai ki ciki abinci, ko sai kin fara cin abincin?" Inna Furai ta girgiza kai tana faɗin, "Wane mutum sallah ai ita ce gaba da komai, bare yanzu da Fatale suke kawo mana farmaki. Amma ya maganar tawagar fatwar da ƴan sama jannati?" Larai ta ce, "Inna don Allah ki bar maganar nan wannan fa duk ya wuce komai ya daidaita yanzu bari na kawo miki ruwa ki yi alwala." Tun daga lokacin Inna furai ta ɗan saki jikinta ta fara harkokinta.

Kafin wani lokaci tuni maganar dawowar su Baba Abubakar ta karaɗe cikin gidan, wasu daga cikin facalolin ban da murna babu abin da suke yi don dama ba ƙaramin haushi suke ji ba, a duk lokacin da suka ga su Hajiya Rahama sun zo garin fes kowacce ta ƴaƴanta cikin gayu. Wasu daga ciki kuma suna jin haushi don gani suke matuƙar matansu Baba Abubakar suka dawo gidan sun koma bola a wurin Yaya babba, don a haka ma ya suka iya da tsiyar da Dubu take shuka musu amma basu da abin faɗa? Wasu kuma murna ɗaya suke ta dawowar tasu don suma su dangwali abin arziƙi saboda ko banza za su ci gaba da cin mai kyau saɓanin da, da sai dai su ga an direwa Yaya babba kayan alatu na more rayuwa sai dai idan ƴaƴansu sun je ta zaunar da su ta ba su, su ci su yi ƙat su suna daga gefe suna lasar baki.

Kamar haɗin baka duka matan Baba Abubakar da Baba Adamu suka haɗa kai kowacce ta kwashi ƴaƴanta suka yi tafiyarsu. Shi kansa Aseem yana fita ya shiga motarsa ya yi gaba, Hajiya Nafisa ta tasa ƴaƴanta suka wuce bakin titi suka tari abin hawa suka tafi don saboda ɓacin rai ko ta kan Maigidanta bata bi ba. Hajiya Rahama da Hajiya Fauziyya ma tafiya suka yi, a hanya babu mai tankawa kowa saboda takaici har suka ƙarasa gida.

Suna zuwa gida kowacce ta yi sashenta da iyalanta saboda ko da cen ma dama ba wani cikakken zaman lafiya suke yi ba. A ranar ma abin da ya sa wani abu bai haɗo su ba saboda ba daɗi ya sa su tafiyar ba kowacce zuciyarta cunkushe take da baƙin ciki.

Gidan Baba Abubakar.

Hajiya Nafisa na zuwa gida ta ɗau waya ta kira ƙawarta Hajiya Ikilima, bata jima da shiga ba aka ɗauka da sallam. Ko ƙwaƙƙwarar gaisuwa ba su yi ba Hajiya Nafisa ta fara da cewa, "Ƙawata don Allah kina ina? Ina son ganinki cikin gaggawa!" Daga can ɓangaren ta bata amsa, "Lafiya kuwa Ƙawas ko tsohuwar ita ma ta sheƙa ne?"

Hajiya Nafisa ta yi murmushin takaici ta ce, "Wallahi da za ta sheƙa da na fi kowa murna a rayuwar duniyar nan. Kai ni tun da nake na taɓa ganin ƙaddararriyar tsohuwa kamarta kuwa, yanzu kina ina kizo na dawo

Please Login or Register in order to submit comment