An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels https://chat.whatsapp.com/DoFR3n8lLtI1RB5Zd2z2IT 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON🌕 BY NARNAH KANWAR SOJA MARUBUCIYAR MIJIN MAGE FARASHIN SO BIYAYYA GA UWA DUHU CIKIN HASKE RUHI BIYU HANYAR RUWA MAI CIKI CE MADOBIN IDO AHLIN LASHKAR PRINCESSS RAHILAT RAYUWAR UMMAH BAYAN WATA SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star GABATARWA Wanan Labarin zai fara zuwa muku Ranar Litinin da yardar Allah shafin shine asalin gundarin labarin matafiya ne wanda suka bar kasar su zuwa wata ƙasa domin muradun su, a sannan labarin ne cikin labari domin dukkanin su zasu bamu labari mabanbanta daga cikin tafiyar su sanin haƙiƙanin labarin lallai sun mun shiga ciki domin karatu tare.... Masu laɓe a cikin group wanan sabon littafi ku fitoo kafin ayi waje daku fatan zaku na sharhi da share Nagode.. Chapter 1 & 2 Tafiya Mabuɗin ilimi بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على محمد وسلم Ƙara duba email nasa yayi nan John ya dafa kafaɗar sa " Common man muna late fa " ajiyar zuciya ya sauke mai nauyin gaske cikin tunani tsarin ɓarauniyar hanyar da zasu bi daga Kano zuwa Dubai cikin kwana 150 Addu'a suka fara bayan kammala wa motar tasu ta zubin taxi ya tashe da matuƙar gudu Duk wani abun buƙatar su na abinci kuɗi sutura tare da abun bukatar su na yau da gobe yana cikin wannan motar Hannu tasa tana lissafi cikin buguwar zuciya " Kano (Nigeria) Yobe → Chad → Libya → Egypt → Israel → Jordan → Saudi Arabia → United Arab Emirates (Dubai) Yanzu wanan ƙasasshen dukka sai mun tsallake su Innallilahi wai'na illaihin rajiuon " take hawaye ya fara zubuwa a idon ta, harara Maryam ta buga mata " Haba Ihsan meyasa kina da saurin kuka ne tafiya ce kawai duk da munsan akwai wahala a hanyar mu amman ai muna tare ke tuna buri da muke dashi a rayuwar mu idan bamubar Nigeria ba ina zake samu bukatar aikin da muke so " .. Tunda suke magana Yazid na latsa wayar sa wanda yake buga game nasa cikin nishadi sosai Yazid , Yaro ne mai shekaru 25 a rayuwar sa ya gama makarantar secondary school sai dai yana da Babban buri a rayuwar sa ma buɗe katafaren Company gine gine hakan yasa ya yanke shawarar zuwa ƙasar Dubai inda suka samu labarin ana zuwa neman kuɗi sosai kuma ana dace domin kuɗaɗen su mai matukar girgiza ruhin mai neman kuɗi da wanan niyyar ya baro gida Ihsan Yarinya ce wacce take da shekaru ashirin a rayuwar ta sai dai ta tasu daga gidan marayu na nan Kano tabbas Ihsan yarinya ce mai basira sosai ga kuma kyau da ilimi sai dai Ihsan yarinya ce mai neman na kanta duk inda taga zata samu kuɗi tana zuwa neman aiki lungu da sako Ihsan yanzu babban burin ta shine ta samu jari sosai wanda zata fara kasuwanci gari zuwa gari har ma da ƙasasshen waje Amman yanzu dole sai ta tafe Dubai domin samun aiki ko na aikatau ne domin cikkar muradun ta..... John Idan ana neman yaro mai karfe da fikira to John ya samu wanan shaidar babban abokin Yazid kinan wanda suka ye makarantar tare sai dai shi ya samu aikin soja wanda aka Kore sa daga aiki dalilin mugun ƙazafin da abokan sa suka masa shi kuwa ya yanke hukuncin baren ƙasar domin ya tafe nemo kuɗi kodon huci takaice abinda aka masa ..... MARYAM Kuna neman matsoraciyya yarinya ga tsoro ga rashin jin magana ga kuma taurin kai sai Maryam wacce take da shekaru ashirin da ɗaya chifff Maryam ta tasu gaban muguwar kishiyar uwa wacce sai abinda tace baban ta zaiyu hakan yasa take azabtar da Maryam ta kowani yanayi kyakkyawan yarinya ce ga ilimi boko da na arabiyya sanan tayi karatun health care ƙaramar nurse ce dalilin barin ta gida kuwa kishiyar uwarta ne ta yanke mata hukuncin auren wani tsoho a unguwar sa wanda baban ta ya amince hakan yasa ta gudu tabar gidan sai gashi ta haɗu da ƙawa a titti wato Ihsan wanan yasa ta yanke shawarar binsu chan ko ita ma zata tsira da gujje gujje da take ye akan hanya .. ADO Engineer kinan saurayi mai shekaru ashirin da tara mai hazaƙa da basira baiye makarantar ba sabo da tsananin talauci wa da bai san uwar sa ko uban sa ba a kan titti ya gansa yana tafiya bashi da kowa ko komai Amman ko wacce mota ce ya iya gyara ta sanan ya iya duk wani abinda ya shafe igiyar wuta, sanan ya taɓa shiga ƙasar Chad neman kuɗi a takaice dai Ado yana cikin wanan sahun tafiyar domin yana da buri mai yawa a rayuwar sa ... A haka suka kama hanyar Yobe state domin fara tafiya zuwa Chad, muna fatan tafiya yayi kyau a dawo da cikakkiyar nasara... Please don't forget to comment and share Continued........ Narnah ƙanwar soja ✍️✍️ — 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON BY NARNAH KANWAR SOJA 💫Royal Star Association,💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Page 1 & 2 Yawan sharhin ku yawan typing banyi alkawarin posting kullum ba , mujeee zuwa tafiya ta fara tafiya show me some love guy's 🩷 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على محمد وسلم Zaman motar ya fara yi musu nauyi tun kafin su iso Yobe daga nan sai suka shiga ƙasar Chad da yamma, rana ta fara dusashewa cikin baƙin gajimare da iska mai ɗauke da ƙura gaba ɗaya zuciyar su ta fara karaya koda kuwa basu furta ba. John ne ya fara gyara zaman sa yana duba agogon hannunsa. "Wannan hanya wallahi kamar babu wanda ke bi ta yanzu," ya faɗa cikin ƙaramin murya Maryam ta kama hannun Ihsan tana danne tsoro da karfin hali, "Mun riga mun fito, ai sai gaba." Motar ta dinga kutsawa cikin kura da kankara, har aka kusa tsallaka wata ƙaramar kwazazzaba da aka samu a tsakiyar duwatsu. wani ƙara mai firgita ya tashi daga motar. "Grrrrkkk—krrr!" Kafin su fahimta, tayar gaba ta tsinke da wani ƙarfi motar ta faɗi gefe kamar zata tintsire Yazid ya damƙe sitiyari yana ƙoƙarin tsayar da ita amma komai ya gagara Ado ya rike bangon motar yana fadin: "ALLAHU AKBAR!" Sai kawai suka ji "dduuummm!", motar ta buge da wata babbar dutse, ta tsaya cak anan ne shiru ya biyo baya, babu motsi, sai sheshshekar Ihsan da Maryam suna kuka. Yazid ya fito daga motar yana duba tayoyi, idanuwansa sun cika da 'kura. "tayar gaba da gefe duk sun ƙone clutch ɗin ma ya tarwatse. muna cikin matsala mun rasa motar mu." John ya farka daga karyewar da ya sha, ya dubi hanya yana shan iska mai zafi, sannan yace: "Wannan ba hanya ba ce, wannan tabo ne. mu kwashe kayanmu mu shiga cikin dajin nan idan muka tsaya nan dare zai riske mu, barayi ko dabbobi za su iya far wa." Babu wanda ya musa kowa ya ɗauki nashi kaya cikin tsoro da damuwa. Ihsan na riƙe da kwalbar ruwa, Maryam na lulluɓe da veil tana kare jikinta daga cizo.sun fara takawa cikin ƙaton daji, cike da raɗaɗin ƙasa mai kaifi da ciyayi masu yankan ƙafa Ado na gaba yana amfani da torchlight wayarsa yana duba hanyar da zasu bi tsakar dare ne lokacin da suka hango wani tsohon baranda kamar dafa-gari. ba za a iya ce masa gida ba, amma yana da rufi da bango. "Mu tsaya nan mu huta. Allah ya kawo safiya lafiya," Yazid ya faɗa. Maryam ta kifa kanta a kafadar Ihsan, tana kuka cikin salo mai ciwo, "Idan na mutu a hanya ki ba baba sanina... ki ce Maryam ba ta jure tsanani ba." John ya dan murmusa cikin firgici, "Zamu mutu fa kafin mu isa Dubai idan muke tsoron hanya haka tun a Chad."a haka dare ya cigaba da raguwa, zafin rana ya mayar da dare sanyi mai shigowa jiki kowa ya kwanta da kaya a jikinsa yana jiran asuba da fata, da addu’a, da fargaba. Dare ya yi tsayin gaske kamar zai hana wayewar gari ,sanyi ya ratsa kowane sassa na jikinsu, kowane yana neman ɗan nutsuwa da kwanciyar hankali, amma babu shi. sai dai ƙasa mai kaifi da raɗaɗin tunani. Asuba na ƙaratowa, Ado ya farkar da su ɗaya bayan ɗaya. "Ku tashi, lokaci yayi... sai mu yi sallah kafin rana ta fito." Sun fito daga barandar ruwan zufa da ƙura na hade da jikinsu. kowa ya shimfiɗa ɗan zane a ƙasa, suka gabatar da sallah da natsuwa da ƙasƙantar da kai. bayan sun idar, Yazid ya zaro ɗan kwali daga cikin jakarsa. "Ga ruwa nan da snacks ɗin biscuit da gurasa. Amma sai mu kiyaye amfani da su, ba mu san inda zamu isa da kafafu ba." Ihsan ta amsa kwalbar ruwa tana goge fuskarta da tissue, Maryam na gefenta, kukan jiya ya bar wani ɗan kumburi a idonta. "Da gaske zamu ci gaba da tafiya ne?" Ta faɗa da rauni. "Me kike tunani?" John ya juyo yana gyara jakarta. "Za mu jira motar da ba za ta zo ba? Ko barayi su zo su kwashe mu da kaya?" hka suka kammala shiryawa, suka kwashe komai da suka iya dauka akwai leda mai ɗauke da tuwo da miya wanda suka saya kafin shiga Chad, ruwan robobi guda shida, da wasu kuɗaɗen kasar da suka musanya kafin barin Nigeria. Ado ya latsa map ɗin da ya saukar a waya, duk da babu signal sosai, yana ƙoƙarin duba hanya mafi kusa da wata rijiya ko gari “wannan hanyar zata kaisu cikin wata ciyawa mai tsayi—amma akwai wata ma'boyar ruwa da nake tunawa da ita daga lokacin da na taba zuwa Chad.”sai suka kama hanya, dajin yana cike da tsuntsaye masu shewa, ƙasasshiyar ƙasa na sa ƙafafunsu zubar da gajiya. Ciyayi na yanka ƙafafun su, ganyaye na goce su a fuska. Yazid ya riƙe jakar abinci yana gaba, John na gefe yana duba kowane motsi, kamar soja na sahun fama. Maryam na tsakiyar Ihsan da Ado, amma ita ce ta fi fitar da kuka. "Gsky, idan Dubai ne zai kashe mu haka, to wallahi zan koma gida." "To sai a auri tsoho, ko?" Ihsan ta harare ta cikin dariya mai taɓarɓarewa. Maryam ta kyalkyale da dariya cikin hawaye" ke Ihsan wallahi da aure Baba audu gwanda na mutu a hanyar nan" Sun dauki kusan awa biyu suna tafiya cikin daji kafin suka kai ga wani tabo mai ɗan sanyi, kamar ruwan fanfo ya ƙyalƙyala sama, suka zauna a can suka sha ruwa suka ci ɗan abu. Yazid ya duba agogon sa. "Zamu ci gaba da tafiya bayan minti talatin... don kada rana ta fara zafi mu gaji." Cikin wannan rana, sun fara fahimtar cewa tafiyar nan ba zango ba ce, ba yawon shaƙatawa ba ce hanya ce ta ƙalubale da jarumta, da fahimtar juna. Kuma suna cikin ita.... Garin da suka zauna sun ɗan ji sanyi da natsuwa bai kai awa biyu ba, sai ga wani ƙara ya karad'e sararin samaniya. wani irin hadari ne ke tasowa daga gabashin jeji, ganye na yaye sama, ciyayi na karyewa, iska na tashi da kura mai kauri "Na shiga uku! wannan fa kamar guguwar jeji ce!" Ado ya faɗa yana rintse ido "Ku tattara kayan nan! Ku kamo jakunkunan ku!" Yazid ya ɗaga murya. Cikin daƙilewar lokaci suka fara tattare kayan su, Maryam ta faɗi jakar ruwa, sai kuma aka jiyo busa kamar karar motar iska tana fashewa wata bishiya ta karye tana gangarowa da sauri! John ya ɗago Maryam da sauri suka fice daga wajen,kowa ya rikice.ƙasa ta ɗan girgiza, sai ƙara da kuma wata shanya mai ɗauke da ganye da ƙasa ta tashi ta rufe hanya. "Wayyo Allah na! kayi mana sauƙi!" Ihsan ta yi ihu. Kowa da nashi, sai suka gudu sun rarrabu kadan, amma a ƙarshe suka taru bayan sun kusan rasa juna. tafe suke da keɓaɓɓen numfashi, zuciya cike da tsoro da gajiya, bayan tafiya mai nisa da hawan ƙasa da tsallake kwari, sai suka hangi wani ƙauye a can gefe da daji. wurin tamkar ya zauna a gaban dutse ne, akwai ɗan ruwa yana kwarara daga wani ƙanƙanin dutse. Ado ya saki numfashi. "Wannan tamkar lahira muka tsira daga ciki muka dawo duniya ne wallahi."Yazid ya yi dariya. "Kai dai karka fara wahalar da mu da falsafa yanzu shin ka taɓa zuwa lahira ne." Ihsan ta tura masa kafa, "Wai yanzu ni dai idan na nitsu zan rubutta wanan hargitsen cikin wannan littafin domin tarihi sai na rubuta wani Irin Jeji da na shiga."suka tafi da dariya, duk da gajiya ta cika jiki. Sun isa ƙauyen, mutanen gari suka karɓe su da jinkai, suna ba su ruwa da wuri su huta. Sun zauna suka ci abu kaɗan, suka kwanta ƙarƙashin inuwa, Ihsan na kwance a gefe ta ce, "Wallahi idan na isa Dubai, zan fara kasuwancin ganyen magarya na gaji da dogon buri."dariyar su tashi, kowa ya ƙwalla dariya mai sa hawayen idanu. Bayan hutu da shan ruwa, suka sake tashi da niyyar cigaba da tafiya gobe da safe. kamar ba suba, suna dariya, suna kwance da juna kamar ƴan uwa, daga cikin hargitsi da wahala, nishad'i ya fara zame musu masoyi. Kwanaki sun shige suna lissafa wa cikin jeji da ƙasa marar alamar birni, bayan haɗari da suka fuskanta, motar su ta hantsila a ƙasar Jamhuriyar Chad, suka kasa gyara ta, sai suka bar ta can da ƙyallen tarihi suka fara tafe da ƙafa, kamar masu hijira daga duniya zuwa mafarki.tun daga lokacin ne suka soma 'kulla wani ɗaurewa da ba wai jinƙai kaɗai ba, amma kamar ana zuba wani zuma a zukatansu, suka zama kamar ƴan uwa da aka haifa daga ciki guda. Maryam, mai natsuwa da laushin murya, ita ce jinyar jikin su duk sanda ciwon tafiya ya kama daya, za ta tsaya ta fidda ƙananan kayan asibiti daga cikin jakar matafiyar ta—ta fiddo da tawul, ta sha da ruwa, ta gyara bandage. Ita ce ta fi sanin yadda ake shafe jiki da ganyen da suka ci karo da shi a hanya domin rage raɗaɗi. Ihsan kuwa ta fara zama ƙawarta ta gaskiya. su biyu idan suka haɗu sai dariya da tsokana, suna ƙoƙarin mantar da sauran wahala. Ihsan da bakinta mai ɗaukar dariya, ita ce ke ba su nishadi, tare da Yazid wanda kullum da sabuwar waka a bakinsa. Yazid na iya busa leda da furar baki har kowa ya manta da gajiyar tafiya. John, babban mutumin da ke ɗauke da baƙin laya a wuyansa, shi ke gaba da su a koda yaushe ƙarfin jikinsa da jajircewarsa ke kare su daga tsoron jeji da dabbobi. Idan dare ya fado, John ne ke ɗebo itace, yana hura wuta, yana saka su su ji kamar gida suke ciki. Ado, ƙwararren masanin hanya, shi ke tsara hanya. Duk sanda suka tsaya yana fiddo taswira ko yana duba taurari da rana don sanin gabas da yamma,baya cika surutu, amma idan ya buɗe baki, kalmarsa zata zama haske. A daren da abinci ya ƙare, sukayi shiru gaba ɗaya. ba kowa da bakin magana sai ƙarar cikin da ke ɗaukar wululu. Maryam ta rufe idonta da ƙirjinta, tana share hawayen da ba kowa ya gani ba. zai dai Ihsan ta ɗan matsa kusa da Yazid, suka fara raira waka: "A cikin duhu akwai fata, A cikin yunwa akwai madara, Rana ta fito daga bayan wata..." John ya sa dariya, ya ce: "Kun sani, idan muka tsira daga wannan tafiyar, zaku fi daraja fiye da zinariya a gare ni." Ado ya duba sama, yana murmushi da ƙyamshi, sannan ya ce: "Idan muka kai Libya lafiya, zan gaya muku sirrin da ya sa na bar gida." John ya ɗago kansa, ya ce: "To, mu haɗa zuciyarmu." suka kama tare da muryar da ke daɗi ga kunne, duk da gajiya da yunwa, suka rera: Bayan wata akwai dare, Bayan dare akwai haske, Bayan yunwa akwai cika, Bayan hawaye akwai dariya. Idan rana ta ɓuya, Mun san wata zai leƙo, Idan hanya ta dushe, Mun san ƙafafunmu zasu kai. Bamu daina ba, bamu ja baya ba, Zamu cigaba har gobe ta zo. Mu da juna, zuciya ɗaya, Rana ta fito daga bayan wata"… Yayinda suka rufe baitin ƙarshe, wutar da John ya kunna ta ƙara walƙiya, kamar yadda wata ke ɗaukaka cikin dare. Tun daga wannan daren, wannan waƙa ta zama taken tafiyarsu duk sanda sun gaji, ko dare ya musu tsayi, ko cikin su ya fara kuka, sai daya daga cikinsu ya fara: > “Bayan wata…” sauran su kuwa sai su ɗaga murya cikin amsa, kamar ruwa da tsuntsu: “…akwai dare… bayan dare akwai haske…” suna shiga cikin sabuwar rana da sabuwar fata. continued..... narnah ƙanwar soja ✍️ https://chat.whatsapp.com/DoFR3n8lLtI1RB5Zd2z2IT 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON BY NARNAH KANWAR SOJA 💫Royal Star Association,💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Page 3 & 4 28 / 4/ 2025 Yawan sharhin ku yawan typing banyi alkawarin posting kullum ba , mujeee zuwa tafiya ta fara tafiya show me some love guy's 🩷 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على محمد وسلم Wurin da suka iso na kusa da bodar Libya da Niger wata ƙaramar unguwa ce dake shan gajiyar gabar duniya motar da ta biyo hanya daga Agadez zuwa kusa da Libya ta sauke su a unguwar Sakar, inda suka ce daga nan za a wuce da ƙafa har zuwa Sabha a cikin Sahara. Yayinda dare ke neman yin nisa, suka haɗu da wasu 'yan tsirarun matafiya da suka ce akwai hanya ta gefen jeji wacce ake bi don gudun jami'an tsaro. John ya ja su a gaba, yana ɗauke da wata ƙaramin ƙaho na ruwa da bag ɗin burodi guda ɗaya kacal. Yazid da Ihsan na bayansa suna rera wasu baitin Bayan Wata da karfin zuciya, yayinda Maryam ke sanye da hijabi mai kauri, tana riƙe da Ado a hannu, suna tafiya a hankali cikin duhun dare. Amma a kwana na biyar a cikin Sahara, bayan sun wuce wani yashi mai launin toka, a lokacin da rana ke ƙoƙarin ɓullo daga gabas, Maryam ta hantsila ƙasa da karfi, “Aaaaaaah…!” ta fasa ƙara, jikinta na karkarwa kamar daji na girgiza, gaba ɗaya suka tsaya cak. Ihsan ta durƙusa da sauri, tana girgiza ta. “Maryam! me ya faru?” Maryam ta duba ƙafarta—tsohuwar alƙalamin takalmi ya tsinke, kuma dutsen da ta taka ya huda tafin ƙafarta, jini na zuba kamar famfo. Sai hawaye suka cika idon Ihsan Ado kuwa ya durƙusa yana duba ciwon da kwarewa kamar ƙwararren likita “Dole ne mu tsaya nan ba za ta iya cigaba da tafiya ba ” ya faɗa don yagaji da dogon tafiyar da babo matsaya, John ya kalli yamma, inda duhun jeji da yashi ke cike da sauti marar ƙauna. “ba mu da lokaci… idan muka tsaya, mayakan macijin nan zasu iso.” “mayakan macijin?” Ihsan ta tambaya da fargaba, “'Yan fashin daji Idan suka same mu, ba abinci ba ruwa ba 'yanci...” ya dakata yana ɗauke numfashi Yazid ya ɗago kai, idanunsa na cike da yaji ya ce: “To a ɗauketa ba zamu tafi mu bar Maryam ba !” yana kauda fuska don dai har ga Allah cikin wanan yunwar bashi da kuzarir ɗaukar ta ,sai John ya ce da karfi “Ni zan ɗauketa!” Bai jira amsa ba, ya ɗauki Maryam sama kamar jaririya, jikinta yana rawa saboda zafi da ciwon da ke yawo cikin jinin jikinta suka cigaba da tafiya , duhu ya koma, rana ta sake bayyana da ƙyalli, amma zuciyarsu na makare da tsoro da azaba. Lokacin da rana ta ɗora bisa tsakiyar sararin sama, Ado ya sha ruwan ƙarshe da suka rage ya yayyafa kan Maryam. Yazid kuwa ya saka dariya duk da gajiya yana cewa “Yau rana na cin mutum, amma jiki na cin gado…” sai Ihsan ta hau waka a hankali: “Bayan wata… akwai dare…” John ya karɓa cikin murya mai ƙarfi kamar jarumi “Bayan dare… akwai haske…” Suka kama waƙar cikin kuka da dariya a lokaci guda waƙar ta zama mafakar zuciya. Maryam da aka daura a bayan John, tana raɗa wa kanta: “Zan rayu… saboda ku…” Washe gari rana na haskakawa cikin yashi kamar zinariya, suka iso wata ƙaramar sansanin ‘yan gudun hijira da ke bakin Libya, wanda wasu likitoci daga ƙungiyoyin jinkai ke taimaka wa nan ne aka kwantar da Maryam cikin wani tantin asibiti na wucin gadi An gyara ciwonta da tsafta, aka bata allurai da ruwa, har ta fara murmushi. John da Ado suka sauke ajiyar zuciya. Yazid kuwa ya durƙusa ya shafa gashinta yana cewa: a cikin kunnen ta “kin tsira Maryam… ki tabbata za ki rayu har mu ga Dubai!” Ihsan kuwa, da ta zauna a jikin wata tsohuwar matashiya mai suna Mama Simbi—wacce itama gudun hijira ce daga Ghana ta kalli sauran matafiya da kuma wasu daga cikin mutanen sansani, sai ta ce da natsuwa: “Kafin rana ta sauka yau… zan ba ku wani labari. Labari ne wanda ban taɓa fitar da shi ba… kuma shine zuciyata ke ɓoyewa tun ina zan bayyana labarin da Narnah ƙanwar soja ke da burrin fitarwa sai dai bata samu dama ba ne Ihsan zanyi amfani da wannan damar.” Gaba ɗaya suka zauna, wasu suka ɗebo ruwa, wasu kuma suka jera kan buhuna da katifu. cikin nutsuwa da natsuwa, Ihsan ta gyara zama, idonta na kallon nesa kamar tana komawa zamanin da ya wuce. Sauran matafiya suka runtuma cikin nishadi, wasu suna cewa, “Labarin fa kenan!” wasu na gyara zama kamar za su rubuta da likitochin da tawagar Bayan wata duk suna sauraron ta (Yanzu fa lokaci yayi na shigowar sabuwar rayuwa cikin Bayan Wata—wannan labarin Ihsan da za ta fara ba su a sansani, zai kasance labari cikin labari, wanda zai haɗa ƙauna, yaƙi, al’amuran fada da sirrin da ta ɓoye har yau. ) PRINCESS RAHILA EPISODE ONE 2000 Years Back Sunanta Rahila – kyakykyawa ce tamkar hasken wata, bakar fata mai sheƙi, jikinta dirin coca-cola shape gashinta ya sha bamban da na kowa a masarautar Buga African, kuma idanunta sun yi farin haske har cikin duhu. murmushinta na bayyana haƙora masu tsabta da kyau halittarta ta ban mamaki ce, fiye da na kowace mace a wannan ƙarni. Rahila ita ce tilon 'yar da King Numan ke da ita bayan shekara da shekaru ba tare da samun ƙarin 'ya'ya ba, sai ya tara soyayya da dukiyarsa gaba ɗaya ya miƙa mata. Baiwar da bai ba kowa ba, ya ba Princess Rahila – wacce ake kira da wannan suna cikin girmamawa. Masarautar Buga African ta kasu gida biyar: 1. Yankin Burum 2. Yankin Dusrum 3. Yankin Tursum 4. Yankin Kurum 5. Babban yanki – Buga African, karkashin King Numan. Tunda mahaifiyarta ta rasu tana da shekara biyar, Rahila ta tashi tare da mahaifinta duk wata buƙatarta ana cikawa, kuma soyayya ce ke ratsa tsakaninsu tana da shekaru goma sha biyar amma ta riga ta kware wajen amfani da makamai kamar takobi, kwari da baka, guggar zana da salon yaki – duk sabili da Slave Kodo, babban gwarzon bawa kuma mai ba King Numan kariya. Fadar King Numan cike take da dukiyar duniya da bayi duk da cewa bai ƙara aure ba bayan rasuwar matar sa, yana amfani da wannan damar wajen tilasta wa matan bayi duk matar bawa da ta rasa mijinta, ko baiwar da take kyakkyawa, za ta faɗa hannun sa. Rahila ta kai shekaru ashirin kyaunta ta kai kololuwa duk sarakuna da attajirai sun so mallake ta amma ta ƙi. a cewarta, ba za ta bar fadar mahaifinta ba kuma ba za ta zauna ƙarƙashin kowane namiji ba. Wannan ra’ayi nata yasa wasu sarakuna suka rasa idanuwansu saboda kallonta da soyayya. Ta yi imani cewa mahaifinta zai rayu har abada ta ɗauka rayuwarta zata kasance cikakkiya har abada a haka ne ta fara koyon mugunta, ta nuna ƙarfin hali da alfahari. Ta san ta fi kowa kyau da ƙarfi. Ta ƙi yarda wani namiji ya kwanta da ita. Tana ganin ƙarfinta da na mahaifinta da na mayaƙa – musamman Slave Kodo – zai iya kareta har abada amma sai wani abin mamaki ya faru… Lokacin da ta dawo daga kogin da ta saba wanka, tana kwance a gadonta, bayi biyu na tausa ƙafarta, wasu na shiryata, sai wani bawa ya shigo cikin gaggawa tayi mamakin ganin shi ya shigo ɗakin ta ba tare da izini ba. Cikin fushi ta watsa masa mari har sai da ya firgita. Yana kokarin cewa “The king sees…” amma ta katse shi da bacin rai, “So what? He's my father, I can go to him anytime I want!” Da ƙyar ya fice, amma cikin mintuna sai ga King Numan da kansa ya shigo ɗakin wani abu ya dame shi, hakan yasa Rahila ta shiga fargaba – abu da ba ta taɓa ji ba. Bai taɓa shigowa ɗakin ta ba da kansa. "My baby, we must leave Buga African immediately!" ya faɗa cikin damuwa. "What? Leave our kingdom? What is happening?” Rahila ta tambaya, cikin tsoro da rashin yarda. "Zuma people (Dursum) have invaded our palace! We've been betrayed. Even our soldiers have been sold out!" in ji King Numan. "NO, Father!" ta ce cikin jin kai. “nu shugabanni ne! Dole mu yaƙi mu mallaki su mu mayar da su bayi!” Ta ɗauko takobinta mai haske, wanda ta keɓe, tana shirin yaƙi. Amma fa, yaƙin da ya zo ba kamar sauran bane. Cikin hanzari, Slave Kodo ya shigo. “Your majesty! Prince Tarhim na Dursum ya shiga tsakiyar fadar da mayaƙansa!” King Numan ya kama hannun Princess Rahila. "My jewel, please, follow Kodo. He will take you to safety." “No! I won’t run like a coward!” Ta ce cikin kuka da bacin rai. Amma King Numan yasan lokaci ya kure kuma burinsa shine ya ceci tilon 'yarsa King Numan ya dube ta da ido mai cike da ƙauna da alhini. Hannunsa yana rawa yana riƙe hannun 'yarsa Rahila, kamar yana ƙoƙarin ƙara ji da ƙarfi a jikinsa da ya fara rauni. "My jewel... I know my time has come," ya furta cikin rauni. "But I will not let them take you. You must live, even if I die." Princess Rahila ta dafa ƙirjinsa da duka hannayenta biyu, idonta na cike da hawaye masu ƙyalli, tana girgiza kai. "No Baba, don’t say that! You will live! we will fight together!" Amma Sarki Numan ya girgiza kansa cikin sanyi."I’ve seen this in my dream... Kodo knows what to do. He’s been waiting for this day." Yayi kallon ƙarshe ga Slave Kodo, wanda yanzu ya yi shiri da kayan yaƙi, gashi yana kama da jarumin da ba a taɓa ganin irinsa ba. "Kodo," in ji Sarki Numan cikin murya mai ƙarfi, "take her... and make sure she survives. That’s an order." Kodo ya durƙusa, ya ce da kwarjini:By the gods of Buga Afirican, I will protect her with my life." Princess Rahila ta sake fashewa da kuka. Tana janye hannunta daga na mahaifinta tana cewa:"Baba... don’t let them take our land..." Sarki Numan ya matsa kusa da ita, ya sa hannu a bayanta ya rungume ta na ƙarshe. Ya furta a kunne ta da ƙasa sosai: "You are the land now. You are Buga Afirican. Go... before it’s too late." Sai ga wata ƙara ta fashe daga wajen fadar. Wuta ta fara tashi daga ɓangarorin fada, ƙamshin hayaki da jini na ratsa iska. Wakilan Zuma da Prince Tarhim sun karya ƙofa, sun shigo da mayaƙa cikin izza da azama. Slave Kodo ya ɗauki Rahila kamar jaririya, ya fice ta wata ɓoyayyar ƙofa dake bayan gadonta—ƙofar da aka gina shekaru dari da suka gabata domin irin wannan lokaci. Sarki Numan ya tsaya da kafarsa, ya zare takobinsa mai daraja, wanda aka gada tun zamanin kakanninsa Ya fuskanci mayaƙan Zuma da ƙarfi, yana ba da na ƙarshe na jinin sarauta domin kare masarautarsa. An bar fadar cikin hayaki. An bar sarki cikin yaƙi. an fita da Rahila cikin duhu. Wannan rana ce ta zame wa Buga Afirican tarihi Ranar da wata sarauniya mai ƙarfi ta rasa gida, ta rasa uba, amma ta samu sabuwar rayuwa—rayuwar da zata yi nasara ko ta mutu tana ƙoƙari...... Continued by narnah ƙanwar soja ✍️ https://chat.whatsapp.com/DoFR3n8lLtI1RB5Zd2z2IT 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON BY NARNAH KANWAR SOJA ( Sayeddan Addah ) 💫Royal Star Association,💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Page 5 & 6 Yawan sharhin ku yawan typing banyi alkawarin posting kullum ba , mujeee zuwa tafiya ta fara tafiya show me some love guy's 🩷 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على محمد وسلم Haka abin ya faru da Sarki Numan haba ɗaya mutanensa sun gaji da mulkinsa, wasu daga cikin mayaƙansa sun juya masa baya, suka sayar da kansu ga mutanen Dursum, wanda suka sayi rabin mayaƙan domin samun nasara a kansa. "Kado, ka kula da ‘yata. Ita kaɗai ce abin da na mallaka," inji Sarki Numan, ya faɗa wannan karo fiye da goma. "Eh, mai martaba, zan kareta da raina," Kado ya sake amsawa cikin nutsuwa. " Baba ka bar ni na tafi tare da kai!" Princess Rahila ta faɗa cikin kuka, tana faɗawa jikin mahaifinta. Ba ta son wani abu ya same shi ita fa ba komai ba ce idan ba tare da mahaifinta ba. “Je Kaɗo , tafi yanzu da ‘yar gadona. Ka kiyaye ta kamar zinariya.” Sarki Numan ya faɗa da murya mai ƙarfi, irin ta jarumai, sannan ya juyawa wajen baya yana barin gurin. Princess Rahila ta sake gudowa ta rungume mahaifinta daga baya da jin ɗumin hawayenta a bayansa, zuciyarsa ta raunana sai dai ya ƙi juyawa saboda kar ta hango hawaye a idanunsa — alamar rauni ga jarumi kamar shi. Duk da haka, yana son Rahila ta ci gaba da tunawa da shi a matsayin jarumin sarki, gwarzon da yaƙi bai faye shi ba, ba mai zubar da hawaye saboda galaba ba. Bayan wani lokaci, Rahila ta saki mahaifinta, sannan ya tafi ba tare da ya waiwayo ba. Baba Baba Ka kalleni ko sau ɗaya,” Rahila ta faɗa tana fāɗowa kan gwiwowinta, amma Sarki Numan bai waiwaya ba yana ƙoƙarin ɓoye hawayensa.“My princess, dole mu tafi yanzu,” Kado ya faɗa yana ƙoƙarin tashi da ita, amma ta ture shi.“Kar ka kuskura ka saka kazamin yatsunka a kaina!” ta faɗa cikin ƙiyayya. (Duk da girman haɗari, girman kai na sarauta ya mamaye ta.) Kado bai ce uffan ba. ya saba da halayenta, tun da shi ya horar da ita duk da haka, shi kansa bai tsira ba suka fice ta wata sirriyar hanya da ba kowa ke san da ita ba, sai dai shi da Sarki Numan. Yayinda Sarki Numan ya dawo fadar sa, sai ya tarar da rabin masarautar an lalata ta. Mayaƙan Dursum sun riga sun mamaye wajen. Sarki Numan ya shiga ɗakin sirrin da ke ajiyar makamai, ya sa tufafin yaƙi, ya ɗauki manyan takubba guda biyu zuciyarsa cike da fushin jarumi, ya kuduri niyyar mutuwa a matsayin gwarzon sarki maimakon guduwa kamar gwanin fargaba. A lokacin yaƙi... Yaƙin ya riga ya barke, sara suka hannu da ƙafa. Sarki Numan ya fafata kamar zaki, yana yanke mayaƙa tamkar bishiyoyi lokacin da ya hango Prince Dursum, tun da farko ya ɗauka Prince Tarhim ne, sai dai da ya kalli fuskar, ya gane cewa uban ne — Sarki Mujus. Da haka ya soki kansa ƙasa, alamar ƙarshen nasarar da yaƙin zai iya kawo masa. Sarki Numan ya ci gaba da gwabzawa har sai da zuciyarsa ta fara kasa dukan da kyau. Bugun zuciya ya rikice, zuciyarsa ta mutu da ganin 'yarsa cikin halin ƙaskanci ya sulale ya fāɗi ƙasa, ya zubar da makamai, hawaye na zuba daga idanunsa. “Ba zai yiwu ba! wannan ba gaskiya ba ce!” ya ƙwala ihu cikin azaba. “… ku bar ta ku kyaleta, ku bar ta haka kawai,” Sarki Numan ya roƙa yayin da aka jawo Princess Rahila cikin sarka, tana kuka. Jikinsa ya kasa tsayawa, ya durƙusa, yana kallon Prince Tarhim yana ja da sarkar Rahila, har ta durƙusa ƙasa yana kai ta gaban mahaifinta, yayin da wasu zaratan mayaƙa suka kewaye su yanda yake ganin ‘yarsa tamkar bayi, ya girgiza zuciyarsa sosai. Princess Rahila ba komai ce a wannan lokaci ba face bawa, jikinta da datti da ƙura, gashinta ya bazu. “Ga ‘yarka, Sarki Numan babu sauran princess, yanzu bayi ce a ƙarƙashin masarautar Zuma,” inji Prince Tarhim, ɗan Sarki Mujus — jarumin da ya kashe dabbobi da suka kai hari garinsu, Zuma shekaru 27 ya fafata yaƙe-yaƙe masu yawa. Dogo ne, baƙi fari, da kyakkyawar fuska. Fuskarsa da sunansa suna tayar da hankali, musamman ga mata.“Wannan ba zai faru ba!” Sarki Numan ya ƙara faɗa. “, ku bar mahaifina shi ne Sarki na Buga Afirka,” Rahila ta faɗa cikin kuka. Sarki Mujus ya fusata, ya jawo gashin kanta. Rahila ta yi ihu cikin ciwo da azaba. “Great king kike kira? kin san abin da mahaifinki ya aikata wa mutanen masarautata?” inji Mujus. Sarki Numan ya ce, “Kaɗo ne ya yi alkawarin kare ki.” “Baba Kaɗo ne ya ci amanar mu,” Rahila ta faɗa cikin murya mai cike da raɗaɗi. Mahaifinta ya firgita. “Kado? Amintaccena?” “Eh, Baba ya ƙaddamar da komai.” Kado ya bayyana yana faɗi, “Na tuna kuka na iyayena da ‘yar’uwata lokacin da suka mutu a hannunka. kayi musu hukunci da wuta saboda haraji na jure, na koya darasin rayuwa har na zama bawan da kake amincewa da shi amma yau sai na ɗauki fansa ta, in ga yadda ‘yarka ke zama bayi, kamar yadda ka mayar da ‘yan’uwanmu bayi.”Sarki Numan ya ƙara fashewa da kuka, “Kado, me nayi maka har ka yi haka?” “Zan bar ka da rai, Sarki Numan amma zan tabbatar ka gani da idonka lokacin da ‘yarka ta fuskanci cin mutunci kamar yadda wasu suka fuskanta.” “Don Ubangiji… a kyale ta ku daina wannan,” Sarki Numan ya ce yana ihu, yana ƙoƙarin miƙewa a lokacin ya sharɓi wuka daga hannun wani mayaƙi. ...ya sharɓi wuka daga hannun wani mayaƙi, ya sharɓa a cikinsa da ƙarfi, jini ya fara malala daga bakinsa, yana kallon ‘yarsa da ƙyalli na ƙarshe a idanunsa. “Rahila…” ya furta cikin muryar da ta dushe. “Babaaaa” ta ƙwala ihu da karfi, tana ƙoƙarin tashi daga kan guiwowinta, amma ankai mata dukan da ta sume nan take. Kafin idon Sarki Numan ya faɗi ƙasa shikake, ya rasa numfashi daga nan, aka ɗaukaka tutar Zuma a saman fadar Buga Afirka aka kama bayi da mata da yara, aka raba su. Masarautar Buga Afirka ta faɗi ƙasa, ta koma cikin tarihin da ake karantawa da ba’a taɓa tsammani ba. "Father please don't dîe. Please don't... don't, I beg you! Somebody please help me. Please save my father." Princess Rahila tana roƙon mayaƙansu "Save your... breath.. my jewel, take...take...care of yourself. I love you my baby rahila ke tuna ke sarauniya ce juye duk abinda kekeso da zaran kin samu dama " King Numan aya faɗa wanan shine sautin sa na ƙarshe , "Father please, please stay with me please don't leave me." p rincess Rahila ta faɗa cikin ƙunar zuciya tana daman jan tokobin daga cikin sa sai da tasha wuya kasancewar hannunta da Chain "Father please don't leave me. "Father no...you can't do this to me, you can't leave me here all alone!" Princess Rahila ta f ad'a da ƙarfi wanda gabaɗaya ta razana gun da ihun ta ta ɗaga tokobin sama tana kallon yanda jinin mahaifin ta yaki wanzu akai , ta saita dai dai cikin ta da wuƙar , "let me go you ....Let me go right now, ka bani tokobi na zan kashe kaina na huta Princess Rahila ta faɗa tana ihu lokacin da Prince Tarhim ya ƙwace makamin hannun ta , "Tarhim ka barta ta mutu duk da haka uban ta baya nan da zaiga kalan hukunci da zan mata let her kill her safe and go , Shashasan ya kashe kansa already don haka ita ma barta ta kashi kankara kowa ya huta useless girl I do not care anymore" ."Father, do you think it will be okay for us da zamuga tana kashe kanta " ya tambaya ciki da sonjin amsa daga mahaifin nasa" ƙwarai da gaske wannan shine tabbatar da cewa mun gama samun nasara a wannan yaƙin.... "Keep quiet, shut up you son of bitch , don't talk to my father like that!" Prince Tarhim ya faɗa yana tunkuɗe ta daga kusa dashi Wanan yayi dai dai da zartar War tokobin king Mujse saitin kanta sanadin bangaja da ta sama tayi ƙasa tokobin ta kwace wa kanta cikin haushe da takaice rashin samun ta raised up his sword again after yayi rashi nasara daga farko da zumar filli kanta charraf Prince Tarhim ya kama hanun sa kafin tokobi sa yakai head of princess Rahila " father u don't have to do this akaiw hanyoyi da dama da zamuyi amfani akanta "What is wrong with you son? shin kaman ta yanda Uban ta ya kashe ɗan uwan ka ?" king Mujse ya faɗa cikin kaɗuwa da mararrin jiki . The king Mujse Taki yaji komai ya zama sabo burin sa kawai kashe ta ko zai rufe wanan chapter daya jima yana mafarkin samun nasara akan sa. Prince Bella firstboy na king Mujse wanda ya bashi matsayi prince yana da mata Princess Afrah wanda suki zauna lafiya sun haifi yarinya ɗaya Aflim tana da wata biyar Prince Bella ya haɗu da mummunar ƙaddarar sa da ta janyo baƙin cikin da tsananin ɗaukar fansa na king Mujse.. King Mujse ya aika Prince Bella zuwa meeting to wanda za'ayi a birnin Kursum inda manya manyan sarakai zasu haɗu su tattauna to solve a issues affecting their kingdom prince Bella Jauro got dressed and said goodbye to his family. inda suka rabo d kyar ta hanyar kukan baby Aflim king Mujse ya amsheta da rarrashin ta yana cewa shi bazai samu zuwa ba duk da cewa yaron sa yana. tareda da sabon baby babu but ya hallarchi taron kasancewar shine next of the king . Shin a hakane zaka jagoranci kujerar mulki idan bana nan ? zaka ajiye duty saboda akan kukan baby ?! a lokacin da ya hangi tsantsan tausayi baby Aflim da mutuwar jikin Prince Bella , "Her mother is here and your mother is here too. We are all here to take care of her so please, you must leave at once son." King Mujse ya maimaita maganar cikin ƙwarin guiwa da yaki bawa Prince Bella ,They didn't know that it was the last hug and last goodbye. Duk sarakuna sun kammala haɗuwa a inda Aki jiran king Numan wanda ya ƙaraso da dukkan tawagarsa cikin isa da mulki da kaddara dukkan su suka miƙi tsaye wasunsu har ɓoya bayan wasunsu suki , kasancewar sa Jarumin jarumai da babo mai ƙarfin ikon sa a wannan nahiyar , Duk abinda yake faruwa Prince Billa ya chigaba da zama ba tareda ko kallon sa yayi ba In one-time ba zato ba tsammani ya zaro tokobin sa ya sara kansa taki y rabi gida biyu sai jini da ya wantsala umarni ya bawa Slave's nasa da susa kansa cikin akushi su ƙona ganganr jikin sa da wuta a idon duniya su " ku ɗauki tokan ganganr jikin sa kukai ga uban sa ku sanar masa dukkan abinda yafaru ya sanarwa ɗaya daga cikin dakarun da suka sa prince Bella rakiya inda yayi arrest na sauran suka zama Slave's nasa . A lokacin da King Mujse yaji wanan Labarin sosai ya razana inda queen Afra ta. kamu da heart Attack a wanan time Prince Tarhim ya chigaba dajan ragamar shugabancin Dursum After sometime soon king Mujse ya warke yafara plan tareda mutanen sa plan to their revenge hakan ya faru sukayi nasara ganin ga king Numan kwance a cikin jini a masaurautar sa king Mujse yana shirrin Kashi Princess Rahila prince Tarhim ya dakatar dashi ..... BACK TO STORY "Father, wanan shegiyar yarinyar can't dîe just like that. I have a better plan for her ." Prince Tarhim ciki da tsananin fushi da fusata King Mujse baxai iya jira ba yaji wanan plan nin ba King Numan already dead but still bazai iya yafe mishi akan kashe ɗan sa ba dole sai ya kashe ta zai samu sallama He would do anything to complete his revenge mîssion "Father, you will be helping her if you kîll her now. a rashin sani uban ta ya tsira daga punishment za muka shirya masa taya zamu barta itama jikinta ya tafe a banza Rahila dole ta biya bashin da ubanta yaci akanmu mu barta har sai ta roqe mutuwa da kanta da muguwar azabar dazamu ɗanɗana mata let's kill her slowly Kanta ta ɗaga sama tana kallon sa da idannunta da suki wanzuwar da jini a kowani tsako daki da jijjiya a. ƙwayar idon "son of bithch kill me now you have only one change kar kabari wanan damar ta wucce ka Tarhim because jaine mutum na farko da zan fara kashewa idan ka barni a raye da Rayuwa ta "I shall kîll you all one by one. gabaɗaya ku sai kun ɗanɗane zumar kaɗai na mutuwar ku a tafkin hannuna i sweer with my beloved father ." "I, the princess of Buga Afirican promise you all today. sai na kawo ƙarshen ƙasar Dursum ta durgusa a kan guiwarta sai na sa kun tsani kanku ta faɗa with her fire eye's bata damu da zaratan mazajen da suki kewaye da ita ba burinta kawai suyi zuciya su kashe ta ko zata huta da wanan bak'ar rana da ko. mafarki batayi tunanin kasancewar sa ba .. "Son, did you hear that? jinin Numan yana kewaye da ita she is devil too kill her rayuwarta tamkar na uban ta ne" , dogon tsaki yaja Prince Tarhim ya kasa fahimtar meyasa ta kasance very hot stubborn duk da cewa tana ganin tana daga da mutuwa even in the face of dànger. "Father, I know how to handle people like her." "One day, you will beg for my mercy." Prince Tarhim ya faɗa yana matso da hannun sa akan fuskar ta matsar da fuskar ta tayi da tofa masayawun da ya haɗa jini in his face dariya ya kicce dashi yawa hannu ya gogge yana dungule hannu yakai mata wani mugun nashi da saida ya fasa mata kefin bakin ta King Mujes daya amince da yaron sa ya yanke hukuncin ya barta ta kasance matsayin baiwar su ,it felt like a dream to Rahila batasan da cewa watarana wanda yaki chan sama duk matsayin da mulkin sa ko ƙaddara sa da dukiyarsa watarana zai faɗo ƙasa warwas ba kaman ƙitfawar ido King Mujse later cût off king's Numan head from his body. ya ƙona ganganr jikin sanan ya umurce dukan bayin sa suyi wasan harbil harbil da kansa a sansanin masarautar buga Afirican the most powerful king of Buga Afirican bazai iya aikata komai ba kasancewar yau da kansa ki wasa a sansanin masarautar da idon dubanne mutane da bai ɗauki su a bakin komai ba yaki wulakanta su sa kiran su baye marasa amfani sai gashi shine yau a wannan matakin All that happened front of Princess rahila wacce taki kuka ta tana rogon sa da yadaina azabtar da kan mahaifin ta sai dai kash hakan ƙarawa king Mujse ƙarfin guiwa yakiye da azama Har abada zaki yafi ƙarfin ayi wasa a gaban shi har akai masa raini ko suka sai dai idan ya kasance mattace har yaro zai iya matsowa don yayi wasa dashi hakan ta kasance kansa ya zama abin nunawa da dariya ga muradun buga Afirican . Cikin Chain a maƙale da wuya ta da hannun ta da ƙafarta Prince Tarhim yana kan dokin sa yana janta cikin ƙunchi suka kama hanyar Dursum ana ball da kan mahaifin ta wanan abin yafi mata muni akan yanda mutanen buga Afirican suki kallon ta a wulaƙanchi even when she asked water sai dai tasha ruwan hawaye ta wanda suki zuba layi layi tsananin tsana da ɓaci rai da mugunta daban daban taki saƙawa prince Tarhim tabbas indai ta ƙungiya shine mutum na farko da zata kai lahira kasancewar bata da wani babban maƙiyi sama dashi ...... Princess Rahila batayi tsammanin isowar Dursum zai kasance sillar tsayawar hawayen ta sakamakon ganin cincirindon al'ummar garin sun fito kansu da ƙwarƙwartansu suna watsa mata duwatsu wasu kuma tumatur da takalma lallai ta sami tarbar na musamman haushi mulkin ubanta da nata taki amsar hukuncin daga gari su Numfashi ta ne ya tsaya chakk lokacin da aka harba wani talkami ya sauka akan fuskar ta tunawa da cewa idan ace yau yana raye babo wanda ya isa ya ɗaga mata ɗan yatsa a gaban ta Taki ta yanke jiki sunammaya inda yayi dai dai da isowar su wani bakin ɗaki su dark and hurt prince Tarhim ya tsuma ta da umarnin kawo ruwan mai ɗumi aka watsa mata taki ta dawo daga suma ta cikin. azaba ta ƙwala ƙara tunda taki for the first time taga irrin wannan duhu duk da cewa takan iya azabtar dawasu a irrin sa batayi tunanin kasancewar haka a garita ba . NARNAH ƘANWAR SOJA 🖋️💞💝💝 https://chat.whatsapp.com/DoFR3n8lLtI1RB5Zd2z2IT 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON BY NARNAH KANWAR SOJA ( Sayeddan Addah ) 💫Royal Star Association,💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Page 7 @ 8 Yawan sharhin ku yawan typing banyi alkawarin posting kullum ba , mujeee zuwa tafiya ta fara tafiya show me some love guy's 🩷 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على محمد وسلم Cikin shigar dogon riga irrin nasu aka gyara mata gashin kanta tari da sa mata ado akan gashin ta a hankali taki taka ƙasa cikin ƙasaitacciyar takunta na sarauta Princess Afrah kinan tsohuwar matar Prince Bella tsaya tayi da miƙa hannu a gun amintacciyar baiwarta Adila amsar akushin tayi wanda ta haɗa girke na musamman sai ƙamshi takiye a hankali ta tura ƙofar d'akin nasa wanda aka hada masa komai da komai na kayan al'adu na sarauta hango sa tayi ya fito wanka ya ɗaura wane yafi a kungumin da cikkar halittar jikinsa ya bayyana taki tsikar jikinta ya tashi tabbas tasan Prince Tarhim yafi tsohon mijinta ɗan uwa sa komai da komai a jikin sa taki wane sha'awar ta ya motsa na son kasancewa dashi a gado ɗaya tun baya chan tanason Prince Tarhim just pretending takiye domin manya sun shiga tsakiyar auren ta da Prince Bella, chunkusa fuskar sa yayi ganin yanda ta shigo masa ɗaki kai tsaye ba sanarwar ko Slave Harun baigayamasa yana da tabbacin ta masa abu ne ko tahanasa gayyamai tana zuwa ganin haka . Princess Afrah ta ajiye abin hanun ta jikin ta har yakiye burinta kawai ta rungume sa ko zata samu sassauci a hankali ta matso kusa da jikin sa tana harhaɗa ƙafa sakamakon baƙon yanayi da taki riskinta kanta ciki da sauri ya katse ta da nuna mata hannu " Please don't do it what do you want from me? me yasa zakishiaga ɗakina with no exuceses " " You know I love him yes I love him but know he is no more he gone what can I do Prince Tarhim kai kawai nakigani na tuna da ɗan uwa ka kasani yanzu inason ka fiyyeda rayuwar ta i love you now and forever please am begging you please love me nasan ".. Numfashi sa ne ya tsaya chakk ya daina sauraren kowane maganar da taki furstawa daga ƙaramin bakin ta ya za'ayi "It was no secret that his brother loved Afrah so much when he was alive sanan yanzu kuma ta ina zata ce tana sonshi how can she can sleep with the former wife of his blood brother like how ya za'ayi nayi making love da matar yaya na no respect for the dèad at all." "Afrah , can you please excuse me? I need to rest, I just got back." He said, trying to send her away in his room ,"I can help you rest my love, you can place your head on my laps and I shall stroke your hair while you sleep " Afrah I want to be left alone,. Thank you. so much" "I can't leave you alone my love, not when we are going to be one very soon." Afrah tana faɗa ta turesa unexpected suka zube a ƙasaitacciyar shimfiɗ'a gadon sa tana kallon ƙwayar. ido. sa da ta kwanta akan budaɗiyar ƙirjin sa yana ƙoƙari tureta gaba-daya ta saukar mai da wane azazzababbin kasala da yaki dakon sa tsawon shekaru masu yawa domin shi bai kasance mai kwanciya da mata na masarauta ba Da sauri Slave Harun ya faɗo cikin ɗakin cikin tashin hankali da rashin ganin hanya da galibi ganin abinda yayi karo dashi Princess Afrah akan Prince Tarhim cikin good moment da sauri ta miƙi ko kallon sa batayiba ta wucce domin yanayin ta ya canza fiye da tsammanin burinta kawai taki ta kwanta ka zasamu realife.. juyuwa taye ko mai tatuna Slave Harun ta ka'la cikin sauyin fuska tace "Where is your manners? How could you just run into the prince's chamber like that? I will dèal with you later, now just leave this place at once, as you can see, the prince is busy with his woman!" Afrah tafaɗa cikin burin kunya da fushi "I am sorry my princess, I am sorry my prince, but this can't wait. The princess of Buga Afirican Princess Rahila has escaped from captivity!" Slave Harun ya sanar musu yana ƙoƙari juyawa da sauri Prince Tarhim ya sauko cikin hanzarin tunowa da kalmar ta na karshe "You will be the first person I will kîll if I get the chance. "What? How... how did ...how did that happen?" Prince Tarhim ya faɗa yana zaro tokobin sa yasha ɗamara "Ehm...ehm... My prince, muma kanmu bamu lura ba kuma muna wanan gun a a a a a "You were what? Can't you talk? You even called her a princess. How could you! How could you call a prîsoner a princess, ehn? are you màd?" Princess Afrah shouted at the Slave A dàngerous girl like Rahila escaped and all princess Afra ta damu da har yanzu suna kirar ta da sunan ta maimakon ta tuna cewar Rayuwar su tana cikin hatsari da rashin tsaro ."I said it! I said it! We should have just kîlled that daughter of a mónster back there but Tarhim didn't listen to me, now see, she has escaped! "ya akaye haka ya faru ? ya zaku gayyamin kuna busy celebrating and you forgot your duty. murnar gidan ubanwa zakuyi ohhhhh shittt " King Mujse ya fad'a a harzuƙe ya miki tamkar Tsohon Zaki aiki ya Kuma close all the way's find her now isaod now "Th.at girl is going to be more dàngerous than her father. How could she have escaped with her hands and feet tied with a chain, how?" Sorry my king Prince Tarhim yace mu cire mata chain a dark room tell us to yana nagana sai ga Prince Tarhim ya shigo da ƙanƙancewar idon sa da suka sauya ya danne fusatar sa domin bada haƙuri ga king yasan tabbas yanzu baida wanda yakinin haushe sama dashi mussaman a wanan lokachin "I am very sorry father, please forgive me. Let me go and look for her, I am sure she hasn't gone too far." Prince Tarhim ya faɗa yana ƙara ladabtar da kansa ƙasa ga idon mahaifinsa daya zama tamkar garwashi wuta , "How can you even think of going out there to look for her? Have you forgotten Kaine na farko da zata fara kashewa a cikin Zafaffan kalaman ta sanan a wane dalili dazaka ce wa bayi su kumceta daga Chain don kaga ta shiga dark room mafi hatsarin d'akin horo am already lost my first son I won't take any chances with my second son." "Baba kana tantama akan jarumta ta ? na kashe sadaukai dewa a baya nayi yaƙi sosai neme gwarzon mayaƙi dabbobi nine sarkin mafarauta daji ka amince dani i will go and find her I promise you I will back with her " "No son, you don't understand, She can be more dàngerous than any a animals." bai kamalla maganar sa ba sukafara sar'kewa numfashi da tari wane gurd ne yashigo my king hayaki ne ya turnike daga bayan mu idan ka bamu izzine zamu iya zuwa dubawa Prince Tarhim ya xabura yaga direction daga inda wutan ke tashi saman dokin sa . Sarki yabi ɗansa tare da wasu Slave's da suki gaba da bayan su Prince Tarhim yayi mamakin ganin fillin ajiye dabbobi su ya kama da wuta wasu na mutuwa wasu kuma sai gudu sukiye gaba-daya kukan su yana karaɗe fillin a taki a ka fara watsa musu ruwa da ƙasa ta ko'ina Tana maƙale a saman ittace tana kallon yanda suke ƙoƙarin kashe wutar dabbobin su na mutuwa ɗaya bayan ɗaya hakan yasa ta fara ajiyar zuciya da cewa " kafin ku fara mutuwa yana da kyau kuga mutuwar dabbobi ku , baxan taɓa yafe muku ba never". Kune sillar mutuwar mahaifin na kune sillar wargaza masarautar ta kune sillar azabtar da ne and you will see what happened to you all a sannu a hankali Bayan wani lokaci kadan ta farara kuka duk da cewa abataso hakan ba tanason kasancewa vrave and strong women Nan tafara tunanin ta hanyar da zatayi escaping ta Kuma buga Afirka tunuwa da babo wane abu mai amfani a wanan masarautar a gunta yasa ta tuni da fansar ta kafin tayi tunanin barin Dursum place Princess Rahila a hankali ta sauka a saman Bishiya ganin duk hankalin su bakan arzikin dabbobi su ta chigaba tafiya chan ta shiga daji nan ta hango wane bush da sauri ta shiga ba tare da tunanin ko a kwai wane abuba tunanin ta ya tsaya na matafiya ne shiga tayi burinta ta samu relief tayi bachi ga dan banzan yunwa da kishin ruwa da tsinci kanta a cikin muguwar wanan yanayin ganyen bishiya tagani a dai dai tun da yasa ce babban bishiya hawa tayi ta tsinki ganyen ta zauna taci sa tsaff tana zubar da hawaye Zafaffa shiga cikin bush nin taye numfashi sama sama , taki dutse biyu ta dauka da idea ya zumata sakamako duhu da ya ƙauraye dajin a taki wuta ya kama tsa a kan chiyawa da tara gaban ta ta kwanta cikin minti kaɗan wahalalen bachi yayi gaba da ruhin ta Princess Rahila tana cikin bachinta mai tsananin bakin ciki da wahala a hankali tafara jin wane sanyin abu yana ratsa ƙafarta na haqqu mai laushi lumshe idon ta tayi tunuwa da yanayin masarautar ta idan ana mata tausa cin wane azazzababbin ciwon ne yasa ta razana ta farka a harzuƙe tana ƙwala ihu da sauri ta Toshi bakin ta domin kar Dursum people suji wanan sautin na ta a dukkan dajin ........... Muna haɗa turanci da Hausa a labarin Princeces Rahila kuyi haƙuri laifin Ihsan ne amman zata gayamanna dalilin ta nayin hakan ku chigaba da kasance wa a littafin bayan wata labarin matafiya guda biyar wanda zasu bamu labarai mabanbanta...... To be continued… https://chat.whatsapp.com/DoFR3n8lLtI1RB5Zd2z2IT 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON BY NARNAH KANWAR SOJA ( Sayeddan Addah ) 💫Royal Star Association,💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Page 9 / 10 Yawan sharhin ku yawan typing banyi alkawarin posting kullum ba , mujeee zuwa tafiya ta fara tafiya show me some love guy's 🩷 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على محمد وسلم Ta yi saurin janye ƙafarta daga macijin da ya naɗe a jikinta, amma abin ya riga ya faru macijin ya cije ta nan take lokacin da ta motsa, sannan ya ɓace cikin daji kamar bai taɓa zuwa ba , Rahila ta yanke gefen rigarta ta kuma ɗaure ƙafarta don hana venom ɗin macijin yaɗuwa daga wurin da ya shafa ta buƙaci taimako cikin gaggawa, amma su waye za su taimaka mata? A lokacin da mutanen Zuma suka kashe wutar da ke ƙasar gonar sarki, wasu daga cikin dabbobin sun riga sun ƙone har lahira, wasu kuma sun ƙone sosai amma sun tsira. Sarkin Mujsee ya ji zafi sosai saboda gonar dabbobin na ɗaya daga cikin manyan hanyoyin samun kuɗi na sarki. mutanen da ke daga sauran masarautu suna zuwa masarautar Zuma don siyan madara saboda yawan shanun da sarki ke da su a gonar, amma yanzu, mafi yawan shanun sun ƙone a wutar. Tashin dakararru da ƙashin dabbobi daga cikin gonar yana zama taki ga gonakin noma a masarautar Zuma, kuma sarkin yana tunanin me zai faru da amfanin gonar su wannan shekarar. Akwai sauran gonaki a masarautar Zuma, amma wutar ta shafa mafi girman gona a masarautar. Sarkin ya kalli cikin zuciya, yana ɗaukar dabbobin da aka ƙona suna fita daga gonar "King , ina ganin kana buƙatar hutu na tabbata komai zai tafi daidai za mu samu wasu dabbobi nan ba da jimawa ba." Yaron sarki, Mujse yayii ƙoƙarin kwantar da hankalin mahaifinsa. "Yaro na, ya kamata ka gano gaskiyar abin da ya faru a gare ni ya kamata ka gano wanda ya ƙona gonar nan." "Na tabbata wani ne ya aikata wannan ta yaya gonar zata fara ƙonawa haka ba tare da wani ya yi ba? wannan bai taɓa faruwa ba, ko kuma masarautata tana cikin wani ɓoyayyen hari?" sarki ya tambaya cikin damuwa. "King , masarautar ba ta cikin hari mun yi nasara kan wani sarki mai hatsarin gaske kamar sarkin Numan , na tabbata sarkuna daga sauran masarautu za su ji tsoron tunanin fara yaki tsakanin masarautar mu da nasu, " Yaron Prince Tarhim ya ƙoƙarin kwantar da hankalin mahaifinsa. "Shin ina cikin damuwa fiye da kima? ta yaya wutar ta tashi idan ba wani ba ne da ya ƙone ta?muna cikin daminar ruwa kuma ganyayyaki da ganyen itatuwa suna sabo, ta yaya?" Sarki Mujse ya tambaya sannan ya tsaya na ɗan lokaci. "Tarhim." ya kira bayan ɗan lokaci. "Eh, Uba." yaron sarki ya amsa. "Shin kana da tabbacin cewa wannan 'yar Numan tana ɓoye a wani wuri?" Sarki ya tambaya, yana duba ko ina, sai yaron sarki ya haɗa ido da shi. Yaron sarki, Mujse ya kasance yana tunanin abin da mahaifinsa ya faɗa tun da ya ga gonar tana ƙonawa. ya san yadda hankalin irin waɗannan mutane kamar Rahila ke aiki, kuma yana da tabbacin cewa tana can tana jiran lokaci ta sake kai hari, amma ba zai bar ta ta sake ba. "King , kada ka damu game da wannan zan gano inda take ɓoye, kaɗai ka yi amana da ni." yaron sarki, Mujse ya yi wa mahaifinsa alkawarin. "Ka zama mai hankali, yaro ka rufe kofa da tagogin ɗakinka kafin ka tafi gado a yau da dare wannan yarinyar tana da hatsari. zamu tafi neman ta gobe kuma zamu kashe ta idan muka same ta." Sarki Mujse ya faɗi kafin ya tafi gado cikin damuwa a wannan daren. Yaron sarki Mujse da sauran su ma sun tafi bacci, amma lokacin da yaron sarki ya shiga ɗakin sa, bai samu bacci ba. ya ƙara juyawa yana cikin gajiya. Ta yaya zai iya samun bacci alhali wanda ya yi alƙawarin kawo ƙarshen rayuwarsa yana ta faɗa? Lokacin da ya yi tunani da kyau, ya yanke shawarar fita neman Princess Rahila a wannan daren, bayan duk da haka yana zuwa farauta da dare a wasu lokuta. Yaron sarki Mujse da wasu daga cikin gungun masu tsaron sa sun tafi neman Princess Rahila a cikin dare, suna shirye-shiryen duk abin da zai iya faruwa.sun ɗauki takobinsu, igiyar harba da arc, da sandar mai wuta a ƙarshen sa. Ba su yi nisa ba kafin su sami wani daga cikin dajin yana kwance a cikin rashin lafiya. Lokacin da suka kusanci, sai suka gane cewa wanda ke kwance a ƙasa ba wani ba ne face Warrior Princess Rahila. Princess Rahila ta yi tunanin za ta iya yaƙi da venom ɗin macijin ta hanyar ɗaure wani yadi a ƙafarta, amma ta yi kuskure. Bayan wani lokaci, venom ɗin ya tashi daga ƙafar da aka shafa kuma ya fara yawo a jikin ta gaba ɗaya. Ta yi ƙoƙarin yakar ta, amma nan ba da jimawa ba ta fara jin gajiya, jikinta ya ƙasa aiki kuma ta rasa sanin kanta. haka ta kasance a kan wannan wuri har yaron sarki Mujse da masu tsaron sa suka same ta. Zuciyar Tarhim ta buga da ƙarfi lokacin da ya ga Princess Rahila tana kwance a ƙasa cikin rashin lafiya, ya yi sauri ya karkatar da hannunsa don jin ɗokin sa. Ya gano cewa tana gajarta sosai lokacin da ya ji bugun zuciyarta, amma maimakon jin daɗi, ya kasance cikin ruɗani. "Yaron sarki, mu cẽke ƙashin ƙafarta mu kai wa sarki." ɗaya daga cikin masu tsaron ya ba da shawara lokacin da ya yi kamar ba ya san abin da zai yi. "Mu ƙone ta a cikin wuta." wani mai tsaron ya ba da shawara. dukkanin masu tsaron sun bayar da shawarwarin su, amma yaron sarki ya zaɓi bin shawarar farko bayan tunani mai tsawo. Mahaifinsa zai yi farin ciki idan ya kai kanta ga sarki. ba zai rasa hakan ba, ba a lokacin da Princess Rahila ta ba su komai sai matsala ba. Wataƙila wannan zai zama abu mai kyau. wataƙila zai samu bacci cikin kwanciyar hankali idan princess Rahila ta mutu ya yi tunani yayin da ya ɗaga takobinsa cikin sarari, yana shirye ya aikata! "Prince Tarhim lafiya lau?" Daya daga cikin masu tsaron ya tambaya lokacin da Prince ya dauki dogon lokaci ba tare da sauke takobinsa ba prince Tarhim ya riƙe takobinsa saman don yanke kai Princess Rahila, amma don wasu dalilai da ba a san su ba, bai iya sauke shi ba. Eh, ta ba su wahala sosai ta yi masa faɗa mai tsanani a cikin ramin ƙasa, amma tana faɗa ne kawai don ceton ranta. Ba ya tabbatar da ko ta ƙona gonar su, amma ko ta yi haka, rayuwarta ta cancanci fiye da dubban dabbobi. Prince Tarhim ya ƙirƙiri hujjoji da yawa a zuciyarsa game da Princess Rahila, sannan ya tuna cewa ta yi masa alƙawarin kashe shi idan ta samu damar yin hakan. To, zai tunkari wannan lokacin idan ya iso, amma kawai ba zai iya kashe ta ba. Ya sauke takobinsa a hankali yayin da masu tsaron sa suka kalli shi cikin mamaki. Sun kasance cikin shauƙi na ganin Princess Rahila ta ƙare, amma yaron sarki ba ya nuna yana niyyar kashe princess a kowanne lokaci kuma ba za su iya yin komai ba saboda shi ne shugabansu. "Prince Tarhim, sarki ba zai ji daɗi ba idan ba mu... kashe... ta ba." ɗaya daga cikin masu tsaron ya faɗi cikin ƙyama. Prince Tarhim ya yi watsi da mai tsaron yayin da ya yi ƙasa da kyau don duba Princess Rahila. Ya yi tunani kan abin da ya faru da ita. ya san ta a matsayin mai ƙwazo, don haka duk abin da ya sa ta zama rashin lafiya dole ne ya zama abu mai tsanani. Ba ya buƙatar duba sosai kafin ya ga ƙafarta da ke kumbura wanda aka ɗaure ba ya buƙatar mai fada masa abin da ya faru daga yanayin ƙafarta ta, ya san cewa an cije ta da maciji mai guba kuma tana buƙatar magani cikin gaggawa ko kuma za ta mutu. Prince Tarhim ya ɗauki Princess Rahila a hannayensa kuma ya nufi wajen daji cikin sauri yadda zai iya, masu tsaron sa sun bi shi cikin shiru, suna mamakin wannan juyin halin. Sun yi tunanin inda yaron sarki zai kai Princess Rahila shin yana shirye ya miƙa ta ga mahaifinsa ya yi da ita yadda zai so? masu tsaron suna da tambayoyi da dama a zuciyarsu yayin da suke tafiya a cikin masarauta, suna bi ta wajen daji, suna biin Prince Tarhim wanda ya riƙe Princess Rahila a hannayensa. Yaron sarki ya kai Rahila zuwa ga mai magani mafi ƙarfi a masarautar Zuma. Ba ya san dalilin da ya sa ya yi hakan, duk da haka, bai iya kallon ta ta mutu, bayan haka ba ita ce ta kashe ɗan uwansa ba. uban tane yayi hakan kuma hakan ya isa. continued by narnah ƙanwar soja ✍️✍️ https://chat.whatsapp.com/DoFR3n8lLtI1RB5Zd2z2IT 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON BY NARNAH KANWAR SOJA ( Sayeddan Addah ) 💫Royal Star Association,💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Page 11 / 12 04 / 05 / 2025 Yawan sharhin ku yawan typing banyi alkawarin posting kullum ba , mujeee zuwa tafiya ta fara tafiya show me some love guy's 🩷 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على محمد وسلم Sarkin ya umarci sojojinsa su buga ƙofar mai magani yayin da ya kwantar da sarauniya Rahila a ƙasa da hankali, Sojojin sun yi jinkiri, amma daga bisani sun buga ƙofar, sai mai maganin ta fito bayan ta tambayi wasu tambayoyi. ta saba da mutane da ke kawo marasa lafiya zuwa gonarta a dare, don haka ba sabon abu ba ne a gare ta. "Prince Tarhim shin ka tabbata da wannan? Mahaifinka sarki yana iya rashin jin daɗi da hakan, " mai maganin ta ce yayin da take duban Rahila Ta taba ganinta a lokacin da Prince ya jagoranci ta cikin sarautar su cikin ƙafa, kuma ta fara mamakin dalilin da yasa Prince ke ceton ta yanzu. "Ni ne zan damu da hakan ke ceto rayuwarta kawai." Prince ya ƙi jin damuwarta. "Zai yi Prince guba ta ratsa jikin ta gaba ɗaya." mai maganin ta ce "za ki iya ƙoƙarin, taimaka mata." ya matsa, mai maganin ta fara maganin sarauniya Rahila nan take. "idan Atishawa tayi bayan ta sha warin wannan maganin da zan kawo, to tabbas za ta tsira, amma idan ba ta yi ba, to ina baƙin ciki, babu abin da zan iya yi, ya Prince" mai maganin ta ce. "To, sai ke ci gaba." yace ya amince. Sojojin sun fara magana cikin husɓa suna kallon wannan abin da ke faruwa. Prince ya koya musu cewa ba su da jin kai ga abokan gaba, kuma yanzu yana aikata abin da ya ke gargadi akai mai maganin ta tafi cikin ƙaramin gida na ta sannan ta dawo da wani haɗin ganyayyaki a cikin ƙaramin kwararan kwano. da ta kawo warin kusa da hanci sarauniya Rahila, ta atisaye sau da dama amma idanuwanta sun kasance rufe. "Yarinyar tana da ƙarfin zuciya." mai maganin tsohuwa ta ce, tana girgiza kai kamar tana gano wani sabon abu. Gaskiya ta gano wani abu sabo saboda babu wanda ya taɓa samun damar atisaya bayan sun sha wannan maganin a irin wannan yanayi. Ba kawai mai maganin ba ce, amma tana da baiwar ganin gaba, kuma ta iya gano cewa matar da take gaban ta ba ta cikin kowane irin yanayi na al'ada ba. "Ya Prince za ka iya komawa gida yanzu, zan kula da ita. zai yi kyau." mai maganin ta tabbatar maii Ya yi tunanin dalilin da yasa har yanzu tana cikin wannan yanayi duk da atisayar, amma mai maganin ta tabbatar masa cewa komai zai tafi daidai kuma ya yarda da ita. Matar tsohuwa ta kasance mai taimako sosai ga mutanen Zuma, har ta kasance daya daga cikin masu maganin da suka kula da mahaifinsa, don haka me zai hana? "Ba za ki taɓa faɗa wa kowa ba, har ma mahaifina, abin da ya faru a daren nan. sanan inason ke ɓoye ta zuwa lokacin da zan dawo bayan tafiya tafiya ta ," ya gargadi sojojin sa yayin da suka tafi gida sojojin sun amince da cewa ba za su ce komai ba ga kowa, amma ba abu mai ɗorewa ne ɓoyewa ba. da Prince Tarhim ya dawo gida, wasu tambayoyi sun ci gaba da gudu a cikin zuciyarsa. me yasa ya ceci sarauniya Rahila kuma me zai faɗa wa mahaifinsa? Wane tabbaci yana da cewa sarauniya ba za ta kashe shi ba idan ta warke?...... BAYAN WANI LOKACI Rana na shirin faɗuwa lokacin da Prince Tarhim ya dawo fadar fuskar sa cike da shakku da ɓoyayyen tausayi yana sane da cewa idan aka gano cewa ya ceci Rahila, matsayinsa na ɗa ga sarki Mujse zai shiga haɗari, amma zuciyarsa ta yi shiru a kan komai – ya fi yarda da abin da yake ji fiye da hukunci ko hukuma. A ɓangaren mahaifinsa, Sarki Mujse ana ta cigiyar ɗansa. hana mamakin dalilin da yasa bai dawo da wuri ba, amma yana zargin akwai wani abu da ɗan nasa ke ɓoye masa. A cikin wani ƙaramin ɗaki a ƙasan ƙaton gida mai dakuna ashirin da huɗu, tsohuwar mai magani ta shimfiɗa Rahila akan shimfiɗa mai ƙyalli da ɗan kamshi na turare, tana jin jikin nata yana murmurewa, amma zuciyarta ba ta fahimtar inda take ba. “Ki kwanta, ki huta. rayuwa tana juyawa,” in ji mai magani cikin murya mai laushi kamar ta uwa. Prince Tarhim, ɗan sarki Mujse , ya dawo daga tafiyarsa ta tsawon wata uku a ƙasar Habasha inda ya je neman dabarun mulki da ilimin soji. Kyakkyawan saurayi ne, mai hikima da nutsuwa, amma ba ya shiga cikin al'amuran soyayya ko fadace-fadace na fada. Da isowarsa, ya tarar da wata ƙatuwar shiru a fada an ɓoye masa komai, amma ba don haka ba sai da hankalinsa ya kai ga jin cewa akwai wani abu mai ɓoye a gidan sarki. A daren da ya dawo, ya shaida ganin wani bawa yana shiga ɗakin sirri da kwanon abinci. yayi mamaki, domin wannan ɗakin ba a yawan amfani da shi sai da wani sirri mai girma. "Waye a ɗakin?" ya tambayi bawansa. “mai martaba ne ya hana kowa magana akai, ranka ya daɗe,” bawan ya ce da kansa yana rawa Tarhim ya gyara tsayuwarsa, ya ce cikin natsuwa: “Na isa in sani. gobe da asuba, zan je kaina.” Washegari da safe, Prince Tarhim ya leƙa ɗakin sirri. kafin ya buɗe, ya tsaya yana sauraron wani motsi. daga ciki, ya ji murya mai rauni tana karanta addu’a cikin sanyin murya. ya bude ƙofar da hankali... idanuwansa suka sauka a kan Rahila, wacce ta zauna cikin tabarma, tana daure da farin zani, gashinta ya bazu kan kafadarta. Lokaci ya tsaya. Rahila ta dago ido lkacin da ta kalli Tarhim, zuciyarta ta ɗan tsinke – ba domin tsoro ba, amma domin tunanin irrin halarci da ya mata na ceto rayuwar ta duk taye sanyi tasha tambaya kanta cewa me yasa har yanzu bai dawo garita ba har sarki Mujse ya gano inda take ya rufe ta yana azabtar da ita bisa laifin mahaifinnta duk gaba da faɗa da take tunkaho dashi tun da Prince Tarhim ya ceto ranta ta rasa dalilin faɗan da zataye akansa tabbas tana da. burin kashe su dukkan su to amma akan wani dalili tabbas mahaifin ta mugun sarki ne akan bayin sa ya aikata zunubi daban daban amman hakan ba wai ya na nufin a ɗauke fansa akan ta ba ita ma bawai tayi ta faɗa har tsawon rayuwar ta ba Amman rashin ganin Prince Tarhim ya tabbatar mata da tazama losser !.. Bai ce mata komai ba ya juya zuwa fada kai tsaye domin ganawar sa. da mahaifinsa Sarki Mujse ya tsaya gaban sa da ƙarfi da girmamawa " Ya kai baba na nasan rashin ɗa akwai cutarwa musamman idan ya kasance maƙiyanka ne sukaye galaba akanka" yakai Baba na Sarki Numan mutum ne azzalumi da duniyar mu ta sanshi akan mulkin sa baya barin kowa cikin sallama a haka muka samu nasarar shiga har fadar sa mukaye galaba akan sa shin Baba kasan dalili !? Saboda karshen zalunci sa a hannun mu yake kuma karshen mulkin sa ya ƙare a dalilin mu mun raunata sa mun kashe sa har abada bazai dawo ba mun ɗauke fansar kashe mana namu da yayi ,to shine me laifin me yasa muma yanzu muka dawo azzalumai irinsa ka tuna mulkin da kakiye cikin aminci da adalci ya za'a yi mu azabtar da Rahila bisa laifin uban ta ?, shin ta kashe mu ko ta dauke fansa ko ta cutar damu a'a Baba to me yasa ka rufe ta kake azabtar da ita tsawon wanan lokacin "?. Rungumar juna sukaye nan Sarki ya share hawayen sa da cewa " tabbas na aika ta kuskure mai girma na azabtar da wanda bashi da laifi kuma nasan cewa soyayya mai girma ce a zuciya ka daga lokacin da kaganta shiyasa na fara gaba da ita don inason ka kasance da Afra matsayin mijin ta Amman nayi laife ka gafarta min yaro na ka zaɓi muradin ka a rayuwar nan sanan sanyi murabus zaka kuma kan sarauta nan da wata ukku za'a yi wanan bukin ... BAYAN WATA UKKU Jama’a suka ɗaga kai cikin mamaki. Dukka yankunan sun taro an tabbatar da Prince Tarhim a matsayin sarautar sa “Ban tursasa masa ba, ya aikata haka bisa adalci da tausayi kuma yanzu na yarda da zaɓinsa. Idan zuciyarsa ta karɓi Rahila, to hakan na nufin akwai wani ƙuduri na sama.” Sanan Princeces Rahilat ta dawo daga muƙamin ta na asali yankunan mu na ƙarƙashin ta sarauta ɗaya ne kuma itace asalin jinin yankin Buga Afrika Rahila ta ci gaba da zama ginshiƙi a masarauta, yayin da ake yawan kawo mata mata da yara don karɓar yaƙi da shawara ta zama cikakkiyar Princess nata a inda ta rungume jarumin ta Tarhim domin a duniya idan akwai wanda take muradun to mijin ta ne shine asalin jarumin da take buƙatar kasance wa dashi tsawon rayuwar ta...... --- BACK TO STORY BAYAN WATA AJIYAR ZUCIYA Ajiyar zuciya mai nauyi Ihsan ta sauke, yayin da ta buɗe idonta a hankali, idon ta kai ga duk sansanin da suka taru a kusa da wutar da suke zaune, idanun mutane sun cika da kewa, da kuma ƙaunar jin ci gaban labarin da ta kawo musu suna kallonta da nutsuwa, kamar sun manta da gajiyar hanya, yunwa da ɓacin rai tayi shiru na ɗan lokaci, sannan ta sake numfasa. “Wannan shi ne labarin Princess Rahilat,” ta faɗa cikin natsuwa. “Ina fatan ya ɗan ɗauke muku kewa a cikin wannan mawuyacin yanayi.” duk suka jinjina kai sai Maryam ta ɗaga hannu cikin annashuwa. “A gaskiya labarin ya kayatar, Ihsan. Amma ina da tambaya,” ta ce tana kallon ta kai tsaye. “Meyasa kike mana labari da Hausa da Turanci a haɗe?” Ihsan ta murmusa, ta gyara zama kafin ta amsa. “Hakika tambayar ki ta da muhimmanci Maryam domin shekaru fiye da dubu biyu da suka wuce, kafin turawa su shigo nahiyarmu, sukan ɗauki baƙaƙen fata tamkar bayi ne sun raina mu, sun mulke mu , amma akwai wani sarki mai suna Numan, wanda ya ƙwato yanki biyar daga hannun turawa, ya mayar da su 'yan ƙasa masu cikakken 'yanci.” Ta dan yi shiru, tana kallon yadda idanu suka cika da sha'awa. “Shi ya sa ya zama sarki na musamman a zamaninsa duk da kuwa mahaifin Rahilat azzalumi ne, amma saboda bajintarsa da yaki da turawa, aka ba diyarsa Rahilat sarauta – don ta ci gaba da kare mutuncin mutane kamar ku da ni. Wannan ne dalilin da ya sa nake haɗa Turanci da Hausa – domin har yanzu muna da ragowar tasirin turawan, amma da karatun irin wannan ne za mu dawo da mutuncinmu da fahimtar tarihinmu.” Hannu suka sa, suka rungume ta duka daga gefe kuma Yazid ya ce da dariya: “Wallahi, Ihsan, wannan tafiya tazo da darussa labarin Rahilat ya ɗaga min zuciya!” John ya ɗora: “It’s like traveling into history and coming back with strength.” Ado ya jinjina kai yana murmushi, “toh yanzu fa dai na tabbata, Ihsan ke ce jigo a cikin wannan tafiya, bari mu ci gaba da tafiya gobe, amma yau... yau dare ne na tunani.” Suka kalli juna da murmushi, suka miƙe suna shirin kwana. Daga can gefen zuciyar Ihsan, sai ta ɗan lumshe ido tana tunani: "Bayan wata... akwai haske kuma wannan shi ne farkon komai." continued by narnah ƙanwar soja ✍️✍️ https://chat.whatsapp.com/DoFR3n8lLtI1RB5Zd2z2IT 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON🌕 BY NARNAH KANWAR SOJA MARUBUCIYAR MIJIN MAGE FARASHIN SO BIYAYYA GA UWA DUHU CIKIN HASKE RUHI BIYU HANYAR RUWA MAI CIKI CE MADOBIN IDO AHLIN LASHKAR PRINCESSS RAHILAT RAYUWAR UMMAH BAYAN WATA SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Page 13/ 14 04 / 05 / 2025 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على محمد وسلم Maryam ta shafa gumi a goshinta, hannunta na rawa sai yanzu zafin jikin da ya ɗauke ta tun safe ya fara raguwa duk da haka, Idanunta sun ƙi buɗewa sosai, sai ihun zuciya da tafasar hawayen da take riƙe. "Ihsan..." ta kira da rauni, "zan iya tafiya." Ihsan ta rungume ta, hawaye na gangarowa daga idanunta. “kin ƙarfafa zuciyata fiye da yadda na zata,” ta ce cikin sanyi Su Yazid, John da Ado sun zuba ido, zuciyoyinsu cike da yanke shawara basu da ƙarfi sosai, amma lokaci yana guje musu. “Yanzu ko ba yanzu ba ne idan yanzu muka tsaya nan wata rana, za a cafke mu.” Yazid ya ce da ƙarfi, yana gyara jakar sa a bayansa. sukai shiru har sai da aka ji murya kamar ƙarar iska daga can nesa sai suka lumshe ido, suka lumshe zuciya. Su biyar suka tattara kayan su da ƙarancin haske suka ratsa cikin duhu, gaban su cike da fargaba, amma babu wanda ya waigo baya, Gabar boda na ƙasar Libiya ba kasafai ake iya shige ta da sauƙi ba. Rana ba ta faɗuwa sosai a hamada. Gashi da ke fesowa daga ƙasa kamar harshen wuta, yana fitar da zafi da ƙamshi irin na ƙasa mai mutuwa babu bishiya, babu ruwa, sai yashi mai girma kamar kogon wuta. Tsakanin dare da kwana biyu, sun ratsa titin ƙasa da ƙafa, su na bin jagorar wani tsoho wanda suka biya sauka-ka-tafi tsohon yana da hannu biyu kawai, amma gwaninta da sanin hanya sun fi soja da komfuta. “Yanzu nan,” ya ce da ƙasƙantar murya yayin da suka isa ƙaramin rami da aka lulluɓe da dausayi. “Nan ne na ƙarshe kafin ku tsallaka Libiya. bayan nan, ba ruwa, babu tsaro kawai da zuciyar ku kuke tafiya.” “Shikenan,” Yazid ya ce, yana gyara rigarsa. “za mu fuskanta.” Maryam ta kama hannun Ihsan. “In muka tsallaka, to Allah ya bamu mafita.” John ya lumshe ido. “I’ve never seen darkness this wide... but I feel hope.” Suka shiga cikin hamadar da babu ƙyalli, suna tafiya suna shan iska mai zafi kamar wuta tana hura musu cikin hanci, cikin dare, rana tana walƙiya, ba saboda haske ba – sai saboda yashi yana motsi kamar ruwan teku. Ado ya ce da jinjina kai, “wannan garin ba na mutane bane...” “amma mu fa mutane ne da mafarki,” Ihsan ta ce, murya kamar zuma “mu ma muna da hakkin tsira". Zuwa wannan lokaci, tafiyarsu daga bodar Libiya ta ɗauki kwanaki, daga na farko zuwa na biyu, ƙarfinsu yana ragewa. Na uku sun fara kwana da cikinsu babu ruwa, babu abinci rana ta huɗu, numfashinsu ya zama kamar na dabbobi, idanu sun ɗebe, fata ta bushe ta fara fashewa. Hamadar Sahara ba fili bane na yashi kawai wani lokaci dutse ke cikinta, wani lokaci gami da koguna da suka bushe shekaru da suka wuce amma duk inda suka kalli yanzu, sun haɗu da komai: rairayi masu santsi, ƙasa mai zafi, iska mai ƙarfi da tsintsiya da ke ɗagawa daga ƙasa har sama kamar baƙin hayaki. Maryam ta fara jan ƙafarta a jikin yashi. takalminta ya dade da karyewa, yanzu ƙafarta bare – jajaye sun yi, cike da toka, ƙyalli daga rana. “Ihsan... ruwa... just one sip,” ta furta kamar mafarki. Ihsan na bin ta da ido, kanta yana juyawa. Idanunta sun canza launi, sun zama kamar ƙwai, ba su da ƙyalli gashinta ya manne da gumi da ƙura, har ta daina jin sauyin iska. “Ba ruwa, ba komai amma ki tsaya Maryam... ki tsaya.” Yazid yana gaba, yana rarrafe, yana fitar da numfashi kamar wanda aka sakar daga ƙarƙashin ruwa. John yana masa baya, amma yazo ƙasa. “I can’t feel my tongue...” ya ce da harshen da ya fara murɗewa. Ado, wanda shi ke riƙe da jakar kowa, ya durƙusa. “I’m seeing mirages I saw my mother – she was standing in water, calling me.” Yashi ke rawa, rana ke ƙuna. Iska ta taso – iska mai nauyi, ƙamshi kamar zafi duka suka durƙusa, suka lulluɓe kansu da tsintsiya da kaya, amma iska ta kwashe su kamar hayakin gobara sun yi ta birgima kamar jakunkuna, har aka jefar da su zuwa wani ƙaramar rami – wani tsibiri a cikin sahara, tamkar tafkin dutse da ya bayyana daga ƙasa, cikin haka suka faɗi su ka suma. Wani lokaci daga baya... Cikin ɓangararren inuwa da aka samu daga wata harsashen dutse, suka farka jikinsu a sanyi, amma cikin yashi babu ganye, babu ruwa, babu abinci. sai ga jikinsu ya fara nuna alamar rushewa – la'bbansu sun fashe, hancinsu ya bushe, idanunsu ba sa kallon juna, fatar hannu da ƙafa sun fara murɗewa, ta rikiɗe tamkar kaho “Zan mutu,” John ya furta, yana kallon sama, “Ba ruwa na sha fitsari na jiya ba zai isheni yau ba.” Yazid ya kalli jikin sa, ya ji kamar naman jikinsa yana motsi. ya taɓa fatarsa – ta cire. “Wallahi mun gama.” ya fashe da kuka, amma ba kukan da kake ji ba ƙara, sai hawaye masu zafi kamar gawayi. Ihsan ta lumshe ido, ta kai bakinta ga wani ƙaho da ke ƙunshe da ragowar fitsari. ta sha kadan gaban Allah, ya fi komai wannan ba lokacin kunya bane, ko tsoron mutuwa. wannan yanayi ne da rayuwa take ƙi barin jikinsu , Maryam na jingine da dutse, tana kallon jikin ta kamar ba nata bane. “I’ve become sand,” ta ce. “Even my voice sounds like wind.” Daga nesa... Ado, wanda ya fi ƙarfinsu kaɗan saboda tsawon jikinsa da kwazon zuciyarsa, ya fara bin duwatsu da sandar da ya kakkarya bayan lokaci – sai ya hango wani abu wani rami mai zurfi da ke wani rami kamar tukunyar wuta. Yayi tsalle, ya kalla – ƙananan ragowar ruwa! Yayi ihu kamar kura mai murna: “Ruwa! Wallahi, ruwa!” ya dawo da gudu yana faɗuwa, yana hura numfashi kamar za a sa wuta a jikinsa. “gashi chan ! gashi chan!” Suna ta matsowa da karfin halin da ba su san inda ya fito ba. kowa da dabara, suka tsinke leda, suka tattara ƙwanƙwaso daga jikin su, suka kai bakin su... dan kadan, amma ceto. sannu a hankali zuciyarsu ta dawo ba da kyau ba, amma da rayuwa suka kwanta, suka kalli sama, tsibirin da suke kai tsaye ne a tsakiyar Sahara, ba ruwa sosai, amma nan ne Allah ya basu mafaka. Yazid ya ce da karamin dariya, “Idan muka tsira daga nan sai na ce duniya ba baƙi bane. duniya rana ce da yashi, amma ina da mafarki.” Ihsan ta ce, “Na fi son mutuwa da mafarki fiye da rayuwa babu buri.” Maryam ta rufe idanunta " ya Allah mun gode maka da kyautar ruwa lallai ruwa zai rayu inda ba halitta amman mutum bazai rayu ba ruwa ba ".. Ruwan da suka tsinci ya zama tamkar aljanna. kowa ya samu ɗan kaɗan ya ji cikinsa ya huta. bayan kwanaki biyu a cikin wannan tsibirin – inda babu ciyawa, babu dabbobi, amma akwai inuwa da ƙaramin ramin ruwa – sai zuciyarsu ta ɗan dawo. Ihsan ta janye rigarta mai sheƙi, ta taka da ƙafarta mai jini zuwa ga sauran su, ta ce cikin sanyin murya: “Ku ji ni mana...” “Mu ne matafiya, Wanda ba su da gida, amma zuciyarmu da rai, suna cikin mafita...” Maryam ta kama hannunta, suka fara juya da kasala, suna dariya da hawaye. Yazid da Ado suka buga ƙafa a yashi, John ya murɗa murya kamar yana wake, sai suka kama da karfi. “Ruwan nan, ka ceci mu, yashi da rana sun cinye mu, amma muna raye, muna tafe – cikin fata!” Sai suka rungume juna – gaba ɗaya biyar – suna sharar hawaye, suna murza fatar jikinsu da suka rasa. Wannan rana ce da suka yi murmushi cikin azaba. " Bayan wata akwai haske Bayan wuya akwai daɗi "... Bayan sati biyu a wannan wuri, ruwa ya kusa ƙarewa sai suka yanke shawarar ci gaba da tafiya, domin sun san idan sun zauna za su mutu da yunwa da ƙishirwa. sun ɗaura jakarsu da fata, suka fito daga tsibirin suna zamewa a yashi. Kwana biyu sun yi suna tafiya cikin rana da yamma. rana na dafa ƙafarsu, yashi na kai musu zafi daga ƙasa. idanuwansu sun fara ganin abu biyu, zuciyarsu ta fara shakku da juna. Maryam ta fara rikicewa, ta yi ihu tana zagin Yazid tana cewa: “Ka ce zaka kawo mu Dubai! ka ce za mu ci kuɗi! Ashe ba haka bane?!” John ya zube a ƙasa yana dariya da kukan hauka. “We’re already in Dubai – in hell's part!” Ihsan da Ado suka kama su, suka kwantar da su kamar yara. Bayan wata guda cikin tafiya da yunwa, sai suka hango wani gari daga nesa – amma ana shigarsu kusa da shi sai suka ji hayaniya. mutane masu bindiga da dabbobi ke yawo a kusa – mafarauta ne amma ba na noma ba – ‘yan fasa-ƙwauri ne da ke farautar masu tsallaka haddi don su sayar da su ga masu aikatau ko masu fatauci. Sun kamasu a dare sun ɗaure su da igiya, suka ajiye su a cikin wani daki tamkar kurkuku da yashi a ƙasa. Maryam ta fara kuka, John ya yi shiru yana kallon su kamar wanda ya hakura da rayuwa. Yazid ya yi ƙoƙarin fita, aka yi masa dukan tsiya, aka zubar da jininsa. Ihsan da Ado sun tsaya suna kallon juna da hawaye. Ado ya ce: “Na rantse, idan muka tsira daga nan, ko ruwa ne, ko wuta, zan kawo ki gida da hannuna.” Ihsan ta runtse ido. “Zan riƙe ka da zuciya har ƙarshe.” Continued ............. by narnah ƙanwar soja ✍️✍️ https://chat.whatsapp.com/BsQ0CkOCA83FgwnQ177z9y 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON🌕 BY NARNAH KANWAR SOJA MARUBUCIYAR MIJIN MAGE FARASHIN SO BIYAYYA GA UWA DUHU CIKIN HASKE RUHI BIYU HANYAR RUWA MAI CIKI CE MADOBIN IDO AHLIN LASHKAR PRINCESSS RAHILAT RAYUWAR UMMAH BAYAN WATA SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star 15 / 16 08 / 5/ 2025 Kamar yadda aka saba duk shekara, Alhaji Saminu bai taɓa yin ƙasa a guiwa ba wajen nuna ɗimbin darajarsa a idon mutanen ƙauyen Gembò amma wannan karon daban ne. wannan karon ba kawai don shanaye ya zo ba ya zo ɗaukar amana. A gaban Moddibbo da wasu dattawan gari guda biyu, Alhaji Saminu ya fito da sadakin Halima. kudi ne masu yawan da fulani ba su fiye gani ba a lokaci guda baya ga hakan, ya kawo 'yan dabbobi da kayan gyaran amarya, tare da alkawarin dawowa bayan Sallah da sati biyu—kai tsaye daga birnin Tarayya Abuja inda matarsa ke zaune. Moddibbo ya karɓi sadakin cikin nutsuwa da girma ya san me hakan ke nufi: yanzu Halima zata koma karkashin Alhaji Saminu amma ko da yake zuciyarsa na cike da nauyin amana, bai nuna ba, saboda a rayuwa irin tasu, alƙawari tamkar doka ne da ba za a karya ba. Halima kuwa... ta zauna a gefen mahaifinta da cike da kunya, fuska a kasa kamar yadda aka koya mata, duk da cewa an ba ta labarin cewa rayuwar birni ce zata zame mata gaba, kuma Alhaji Saminu mutum ne mai arziki da daraja—amma a zuciyarta babu motsin soyayya ko ɗokin aure. Zuciyarta tamkar fili ne, babu shuka, babu furanni kawai akwai wata siririyar lafazi da take maimaitawa a ranta: "Na yarda da mahaifina na amince da kaddara. kuma zan bi Alhaji Saminu, ko da zuciyata ba ta motsa ba." Irin wannan biyayya ce da ta sa ta karɓi sadakin da lafazi guda biyu: “Na yarda.” Moddibbo kuwa kamar kowa yana ganin yana murna amma shi da zuciyarsa sun san gaskiya , ya san Halima ba ta kai matsayin aure ba tukuna ta girma da sauri, amma zuciyarta har yanzu karama ce, tamkar macen da bata fara sanin al'amuran soyayya ba. Sai dai kuma, Moddibbo mutum ne mai daraja da mutunci ya rike amanar Alhaji Saminu fiye da yadda wasu ke rike 'ya'yansu. Yana fatan Alhaji Saminu zai kare martaba da tsaron Halima kamar yadda ya rike alkawari na shekaru goma sha biyar. Wani iska ya buso daga arewa, ya kada ganyen kuka da ke bakin ruga Halima ta lumshe ido, tana jin iskar kamar wata alama ce daga sama ko soyayya zata zo daga baya? ko kuwa hakan nan ne rayuwa ta rubuce mata? Bayan sati biyu da cikar alkawari, ƙauyen Gembò ya sake fuskantar wata rana da ba za a taɓa mantawa da ita ba rana ce da komai ya sauya—rana da tarihi ya ƙara rubutun zinariya cikin ƙwarya mai ƙyalli. A safiyar ranar asabar, tun ƙarfe tara da mintuna goma, sai ga jere-jeren motoci guda shida masu sheƙi da ƙyalli irin wanda bai saba zuwa ƙauyen ba, motoci ne kirar Lexus LX 570 guda biyu, guda bakar fata, guda kuma fari ɗan haske mai cike da adon zinariya. Sauran kuwa motoci ne kirar Hilux da Toyota Highlander, dukkansu cike da kaya, kujerun zamani, manyan jakunkuna da akwatuna masu lulluɓe da furen ado da yajin rawaya. A wata ƙaramar Prado, wanda aka ɗora babban laifan jajjayen furanni da tutar Kaunar aure, Alhaji Saminu ne ya fito sanye da babban ɗan-baban Shadda mai launin zinariya da ruwan hoda , babbar hula ce ta fulani bisa kansa, mai ɗinki na musamman da adon sarka fitarsa daga mota ta sa yara suka yi tsalle, mata suka fara cewa: “Ga angonmu ya iso! Allah ya sa a dace!” Shi kuwa, yana da murmushin da ba'a san a zuciya akwai tsoro da jin nauyin amanar da ya ɗauka ba bayansa, abokansa biyu da shaidu—Alhaji Babangida da Alhaji Laushi—duk sun fito cikin kayan zamani ƙauyen ya sha ado kamar an shirya masa sallah gari ya ɗau shela da kade-kade na kalangu da waka: “Alhaji Saminu yazo! angon Halima yazo!” Tun daga makon da ya wuce, iyayen Halima sun ɗora shagalin al'ada, mata na unguwa sun taru kullum ana sallake, ana gasa binkami, koskoso, da kilishi. Halima tana zaune cikin ɗakin mahaifiyarta marigayiya, cikin duhun tunani da zumudin rayuwar da ba ta san me take cike da ita ba ,aka yi mata lalle, aka sa mata ƙwarya ta ruwan turaren wuta a gefenta, aka shafa mata manshanu a fata, aka ɗinke mata zani da riga mai alamar Fulani na gargajiya—jar zani mai adon ratsi da santali na tsaf. An saka ta cikin wani ɗaki mai ƙyalli da kilishi, ana yayyafa mata ƙamshi da bakhour, ana duba fatarta da gashinta, yarinyar ce kyakkyawa da kyau na halitta, ba ado ke ƙawata ta ba—rashin yawan maganganu da nutsuwar ta ce abin kallo. A gaban limamin ƙauye da shaidu, aka daura auren Halima da Alhaji Saminu da sadaki naira dubu ɗari biyar, da sarkar zinari da kayan gida., adaidai lokacin da aka furta "na ɗaura", Halima ta fashe da kuka mai ƙarfi. Sai dai ba kuka na soyayya ko jin daɗin aure ba ne—kuka ne na rabuwa da matar mahaifinta, wacce ta raineta tun rasuwar mahaifiyarta, wani kuzarin tunani ya cika ta, kamar tana jin kamar yanzu rayuwarta ta sauya daga yarinya zuwa amarya, daga ƙauye zuwa birni. Moddibbo ya share hawayen sa da alwala, yana murmushi mai cike da damuwa, yana fatan Halima zata dace da sabon rayuwar da zata tafi ciki, a zuciyarsa yana fatan Alhaji Saminu zai rike ta fiye da yadda aka rike ’yar sarki. Alhaji Saminu ya bar ƙauyen ba da hannu ba. Ya bar da ɗimbin kyaututtuka: kudi ga matan unguwa, jakunkunan shinkafa, kayan abinci, sabbin riguna da ɗinkin zamani ga matasa, har da jakunkuna ga yara da aka ce "na makaranta". Wajen fitarsu, aka shigo da sabuwar amarya cikin sabuwar rigar aso-ebi da kwalliyar santali, aka ɗaura mata gyale mai nauyin zinariya, aka raka ta da kalangu da wake-wake, aka saka ta cikin motar farin Lexus, sai ga kafila ta nufi birnin Abuja. Amarya ta fito daga ƙauye—amma fuskarta na cike da tambayoyi. Shin me birnin ke ɓoye mata? Me Alhaji Saminu zai kasance gareta? shin wannan aure zai fassara soyayya ne, ko wata kyauta ta biyayya ce da ba zata taɓa jin daɗin ta ba? ********************************* Juyawa tayi da ƙarfi kamar wadda aka hangi zuciyarta ta nitse cikin ruwan kogin ɓacin rai. tana mai huci da numfashi mai nauyi, ta faɗa jikin Moddibbo kamar jaririya, ta rungume shi da ƙarfi, tana kuka mai girgiza zuciya dukkan gangar jikinta na rawar jiki, murya na rawa kamar ana buɗe gidan hawaye a zuciya. Moddibbo ya kama kanta yana bubbuga bayanta da hannunsa mai sanyi da tausayawa. "Allah ya sa ki dace Halimatu," ya faɗa da wani murya da yafi shiru nauyi. "ki rike mutunci, ki tsaya da imani kiye koyar da mahaifiyar ke a fagen haƙuri zaki ci ribar zaman duniya ... rayuwa ce bata da tabbas." Shi kansa idonsa cike da ruwa, kodayake zuciyarsa ta taɓu sosai—ya jima yana kallon Halima tamkar zinariyar sa wanda yanzu ya mika hannunsa ya mika ta ga duniya. ya mika al’amuranta ga wani mutum da ya fi shi daraja da kima, amma ba shi da tabbacin soyayya. Bayan kuka da ban kwana mai cin rai, sai Halima ta shige cikin motar Alhaji Saminu da zuciyar da ba a iya fassara. Alhaji yana ƙoƙarin rarrashi da annuri, yana ƙyalƙyala dariya mai taushi yana faɗin: "Amaryata kada ki damu, Abuja ba abin tsoro ba ne ke zauna lafiya, za ki ga alheri." Halima bata ce komai ba ta fuskanci gilashin motar tana kallon ƙauyen su da ke raguwa a bayanta kamar mafarkin da ya ɓace. hannunta na cikin haɗaɗɗiyar rigarta, amma zuciyarta na cikin tsohon zanin ƙauyenta. Motoci suka fice daga Gembò, suka fasa hanyoyi masu kura, suka dosa garin Yola inda jirgi zai tashi zuwa Abuja. Halima na zaune cikin mota, amma kamar a mafarki ta kasa kallon sabbin gine-gine da suka wuce su, kamar ba su da ma'ana gareta. A lokacin da suka isa filin jirgi, an ce mata "Halimatu! Ki sauka ",ta sauka cikin rigima, tana kallon ƙasa kamar tana tsoron ƙasa ce zata buɗe ta haɗiye ta ba ta san me ake nufi da “ticket” ba ba ta san yadda ake biya ba yanzu ne Halima ke fara jin bambancin rayuwa, ta kasa cire takalmanta a wajen sakan na’ura, sai da ma'aikaciyar ta fara dariya ta ce: “Yarinya! ba salla za ki ba wannan tsafta ne da dokar jirgi.” taji kunyarta sosai Idonta ya cika da ƙyama da tozarta a zuciyarta: “kai! ashe akwai duniya kamar haka?” Bayan an kaita cikin jirgin, aka ɗaure mata seat belt, ta riƙe kujerar kamar wacce ke cikin ruwa mai zurfi. Da jirgi ya tashi, ta saki ƙara mai firgitarwa: “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Wayyo Moddibbo…! na mutu!” Alhaji Saminu ya rike hannunta da dariya “babu komai Halimatu, jirgi ne ke tashi kawai.” Kamar sabuwar tsuntsuwa aka ɗauke daga ciyawa, aka ajiye cikin gini mai fanfo. As zuciyarta, birni kamar wata. Amma tambaya ɗaya ke ci mata rai: Shin wannan sabon garin da take ciki zai taimake ta ta samu sabuwar rayuwa, ko zai ɓata mata tunanin da take tsaye da shi tun ƙuruciya? Tunda suka hau cikin jirgin sama, Halima ta kasa zaman lafiya idanunta na zagaye cikin hadadden komai wanda ba ta taɓa mafarkin wanzuwarsa ba , tana kallon tagar gefe, tana ganin sararin samaniya da ƙasa na raguwa kamar yadda aka rage wa tunaninta hankali. amma wani abu ya sake ɗaukar mata hankali... A kujerar bayan nata, wani saurayi ne zaune, ya murtuƙe fuska, idonsa kamar na damisa mai zurfin tunani , fuskar sa doguwa ce, fara tas kamar bulo, ƙuncinsa yana da ɗan launin ja, bakinsa siriri ne amma mai ɗan ƙasaita gashin kansa an rage shi tsaf yana sheƙi, sai karan agogon zinare a hannunsa na hagu ya ƙara ɗaukar hankali. Shima yana kallon Halima, ba da sha’awa ba, amma da mamaki da tausayi kadan kamar yana cewa da kansa, “Ina aka samo irin wannan ‘yar ƙauye mai tarin kamala?” suna cikin tashi ne Halima ta saki ihun da ya gigita kowa “Wayyo Allah naaa! waye ya ce jirgi zai ɗaga?! Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!” Mutane sun juya suna kallonta, mata suka dinga dariya a nutse, wasu kuma suka tausaya amma shi saurayin da ke baya—ya kalli fuskarta da jajayen idanu, yana juyar da kansa a hankali cikin murmushin gefen baki, kamar wanda ya saba da irin haka a rayuwar zuciyarsa , sun sauka a filin jirgin Abuja, wanda ya bude musu sabon shafi a rayuwa. Alhaji Saminu ya nufi Maitama da su, inda katafaren gidansa ke cike da girma da kima. gidan na da kofa babba mai lanƙwasa kamar ƙofar masallaci a Makka. farfajiya ce a waje, da lambu mai yalwa, sai tsuntsaye ke ta raira waka kamar sun san sabon baƙuwa ta iso. Yayin da Halima ta kalli ƙofar katafaren gidan, zuciyarta na wani irin doki da tsoro da fargaba, wani sashe na ruhinta na faɗin "kin fito daga ƙauye, amma an jefa ki cikin birnin masu hannu da shuni..." da zuciya ɗaya ta shiga, sanye da kayan aure na gargajiya: mayafin fulawa, zobba a yatsu, da dankwali mai yatsin zinariya. A cikin gida, motoci sun sha jerin gado, masu gadin gidan biyu a ƙofar shigowa suna miƙa gaisuwa da ban girma. Gidan kuwa – katafaren alfarma ne wanda ba a taɓa mafarkin Halima zata taka kafarta ciki ba. Babban falon yana da manyan tagogi masu labulen fata na turkiyya, cike da fitilu na chandelier masu hasken zinariya, cikin falon ne Hajiyah Nafisa ta karɓe ta da murya mai cike da mamaki: Matar Alhaji Saminu, Hajiyah Nafisa, ta fito sanye da kayan alfarma gashinta a jikin mayafi yana sheƙi kamar rigar sarauta ta kalli Halima da murmushi na ɗan lokacin, amma idanunta na cike da alamun tambaya: “Itace wannan yarinyar?” Halima ta kasa magana ganin palon gida kadai ya isheta tiles ne na zinariya da hoda mai sheƙi, fanfo a bango da tebur na gilashi. tana takawa kamar ana binsa da ƙasa. Zuciyarta na cewa: “To wallahi... haka birni yake ko dai na mutu ne an kawo ne gidan aljanna ?” kwalliyar da aka yi mata da kayan Fulani na auren ƙauye—maye da zobe da mayafi na fulawa—ya sa ta ƙara haske , amma a fuska akwai shakku, akwai salo na “ba sani ba sabo.” sai dai akwai mutunci a tafiyarta, wanda ba’a koya shi a birni. “Nafisa itta ce amaryata na biya sadakinta tun can ƙauye kamar yadda na gaya miki. Allah yasa alkhairi.” Hajiyah Nafisa ta tabe baki cikin murmushi mai nauyin fahimta daga kallon ta ɗaya ka gane ko da tana ƙoƙarin karɓarta, zuciyarta ba ta cikin hakan gaba ɗaya. Sai da aka kai ta ɗakinta da aka tanadar mata cikin gida ɗaki mai faɗi sosai, bangon sa mai launin cream da zinariya an shimfiɗa masa carpet mai laushi, akwai gado babba da labule mai juyawa kamar na sarauta taga biyu na dakin suna kallon lambun cikin gida, inda tsuntsaye ke ta shawagi, cike da kyan gani. dakin na da fanka da AC, amma Halima bata san amfani da komai ba. Sai kallon su take kamar kayan sihiri. Ta zauna a gefen gado daidai lokacin wata mai aiki – Hasiya – ta shigo da murmushi a fuskarta. Hasiya daga Sokoto ce, mai ƙanƙantar jiki da zubin kawaici atake suka fara haɗuwa Hasiya ta ce da ita: “Wallahi Aunty Halima kin yi kyau, da gaske ne ke daga ƙauye?” “Eh... daga Gembo,” ta ce da dariya mai daɗin ji. “kin taɓa jin sunan kauyen?” “A'a, amma yanzu na ji ki. sai dai ki gyara nan Abuja fa ne Idan baki yi wayo ba, sai a cuce ki.” Nan suka fara zama ƙawayen gaske. Halima ta fara ɗan sabawa cikin gidan, musamman da yaran Alhaji Saminu goma da ke gidan. akwai Muneerah da Ruqayyah – ‘yan mata manya masu haɗe da kwalliya da rashin kunya, masu jin turanci da yi wa Halima kallon kamar uwar kauye suna kiran ta “that girl from bush” a bayan ta. Sannan akwai Aminu Junior da Zaid, samari matasa da suka fi ɗaukar lokaci a wajen gidan basu damu da sabuwar mace, sun fi shagaltuwa da motocinsu da rayuwar club da Instagram. Yara uku ƙanana—Sulaiman, Abbas, da Fadilasun fi sabawa da Halima suna zuwa ɗakinta suna wasa da ita ta dinga yi musu wasan shanu da dabbobi da kida da rawa irin na ƙauye, suna dariya kamar an saka musu annashuwa a zuciya tana ɓoye wannan zumunci da su domin kada uwayensu su ji. Matar biyu kuwa, Hajiyah Mariyah da Hajiyah Sabeerah, su ne abokan huldar Nafisa amma Hajiyah Mariyah ce shaidaniya, mai haƙurin fitina da halin mugunta tana kallon Halima da kyankyami, tana cewa: “Wato wannan ƙaramar ‘yar Fulani ce ta zo mana da daddare? Allah ya sa ba za ta ja mana Alhaji ba.” Tun daga rana ta fara tsara yadda zata nunawa Halima cewa gidan ba da sauki ba ne. tana tura mata ayyuka kamar ba matar aure ba: “ki share wancan, ki gyara kicin, ki tafi can ki goge banɗaki.” Halima kuwa, da jin kunyar Fulani da biyayya, sai ta dinga yi tana mika hannu da zuciya, ba tare da kuka ko korafi ba inda Hasiya ta fi shiga tsakiya, tana mata nasiha da rarrashi: “Ki yi haƙuri Halima, nan ne birni idan kika nuna rashin juriya, sai su hana ki kwanciyar hankali amma Allah yana tare da mai gaskiya.” A haka Hajiyah Nafisa ta dinga kallon yadda Halima ke yi wa yara wasa, tana girki da kyau, tana wanke-wanke da murmushi da farko tana kyamar ta, amma wata rana ta shigo dakin Halima sai ta ganta tana dinki wa Fadila riga da hannu wani abu ya motsa a zuciyarta. Ta ce da kanta: “Wannan yarinyar... ba ta da mugunta kuma girmanta yana shigowa hankali.” Halima kuwa har yanzu bata san haka ba. zuciyarta na yawo ne da tambayoyi: “shin wannan rayuwar ita ce rabona? ina mahaifina da mahaifiyata? W wannan Alhaji Saminu fa, me yasa yake sona? wani dalili ne yasa ya kawo ne gidan sa ya ajiye tsawon lokaci bai dawo garine ba? Ohhhhhhhh ga Halima ga Abuja a sannu a hankali zamu shiga labarin Halima continued ƙanwar soja in Sha Allah ✍️ 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON🌕 BY NARNAH KANWAR SOJA MARUBUCIYAR MIJIN MAGE FARASHIN SO BIYAYYA GA UWA DUHU CIKIN HASKE RUHI BIYU HANYAR RUWA MAI CIKI CE MADOBIN IDO AHLIN LASHKAR PRINCESSS RAHILAT RAYUWAR UMMAH BAYAN WATA SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star 15 / 16 07/ 5/ 2025 Iskar hamada ta na kada yashi cikin karfi, tana fasa fuskokin su da ƙaƙƙarfar zafi gaban su babu komai sai fure-furen duhu da tsayayyun ciyayi waɗanda rana ta ƙone su har sun bushe. kusan ko motsi ba ya sake yi sai idan iskar ta kaɗa su kamar wasu fatalwun da ke kaɗa hannunsu don ƙiran mutuwa. Jiki duk jini, ruwan jiki ya bushe. Fuskarsa ta kumbura, leɓɓansa sun fashe saboda ƙishi da rana dukansu suna daure cikin zafi da juna, Yazid ya ɗaga kai da wahala, yana wani tunani kamar wani ɗan ruhi mai kaifin fahimta, ya fara rerawa da wata murya mai kauri wadda ke ɗauke da ƙyamar wahala: "Bayan wata... bayan wata akwai haske Bayan dare akwai rana a duhun daji babu alheri, a zuciya babu tsira..." Waƙar ta ja kunnensu gaba ɗaya. Ihsan ta ɗan kai hannu ta shafi kafadarsa, Maryam ta rungume ƙirjinta, tana kokarin hana kuka. "ku shirya..." Maryam tace a hankali, murya kamar tana fitowa daga wani daki mai ƙyama. "Zan baku labarin soyayya " suka gyara zama, sun sha wahala, " amma labari na da ƙarfi fiye da na ihsan domin wanan labarin soyayya da butulci cin amana da nishadi yana da matukar muhimmanci a yanayin da muka tsinci kanmu " Maryam ta sauke ajiyar zuciya mai nauyi, tana kallon abubuwan da suka gabata a cikin zuciyarta a yau, ta yanke shawarar cewa lokaci ya yi da za ta bayar da labarin soyayya. Labari wanda ba kawai soyayya ba ne, har ma yana da cike da butulci, tausayi da ƙalubale, wannan labarin yana da ban sha'awa, cike da nishadi, kuma yana dauke da darussa masu nauyi ga wanda zai saurara “amma soyayya ba ta tsaya a nan ba,” Maryam ta ce, tana dariya. “duk da haka, akwai abubuwan nishadi, da tausayi. ( Lokaci yayi da zamu shiga labari cikin labari Maryam zata bamu labari a cikin tafiyar su na Bayan wata a inda aka mafarauta suka kama su ,suna tafiya dasu cikin wahala da zafin rana da yunwa ).. RUGAR FULANI Rugar tana cikin zurfin dajin Arewa maso gabas, cike da ciyayi kore-kore da ke motsawa cikin sanyi na safe gidajen su cike da tsari na gargajiya, daga bukkoki masu rufi da itatuwa da kwari na fulawoyi masu ƙanshi. a gefe akwai madugu mai fitowa daga tsauni, yana gangarowa zuwa tabkin da shanun su ke zuwa kowane safe a cikin rugan ana jin karajin shanu, da waƙar kiwo da yara ke rerawa, kowane gida na da kangon dabbobi, da inda matan gida ke nono da jujjuya fura. Sunanta Halima, kyakkyawa ce tamkar wata a tsakiyar dare idanunta farare ne masu zurfi, suna ɗaukar hankali da kyalli mai launin kwayar gwal fuskarta farin fata ce kamar nonon shanu, tana da dogon hanci da siraran leɓɓa gashinta baƙi ne da sheƙi, an nade shi cikin ɗamara ta Fulani mai launin ja da zinariya tana sanye da zanne mai ɗinki na gargajiya, da ƙyarar kunne na azurfa, da zobba masu sarkar ƙaho tana da shekaru goma sha biyar, amma hankalinta da nutsuwarta sun fi na shekaru. Halima tana da ƙwarewa wajen kiwon shanu, ta san kowanne suna, kuma tana iya busa algaita da wake-waken daji da suka gada. Tana da natsuwa da ladabi, amma cikin zuciyarta akwai mafarkin soyayya da birni, duk da tana jin kunyar faɗa ,a kullum tana kallo daga gefen ruga tana mafarkin rayuwa mai zurfi, tana ɗora fatarta kan murya da waƙar wani saurayi da ya taɓa tsayawa bakin tabki yana kallo duk da cewa bataye ilimin zamani ba amman tabass tana da ilimin addini da ilimin sanin halayyar ɗan Adam Kamar yadda kowacce shekara take kasancewa, haka wannan shekara ma ta zo da nata alkawura ,daga nesa, ƙura ta fara tashi. Yara suka fara ƙwala ihu suna fadin: "ga motar Alhaji! ga motar Alhaji!!" Motoci biyu Honda guda fari da ɗaya baki suka bayyana cikin natsuwa, suna karasowa cikin ƙauyen Gembo Saƙa-saƙan ƙura ke biye da su, kamar girgijen albarka. dun tsaya kai tsaye a gaban bukkar Moddibbo, wanda shi ne babba kuma mai daraja a wannan yanki wata irin lumana da nutsuwa ke lullube daƙalin gidan nasa, kamar yana jiran zuwan ɗan sarki. Alhaji Saminu ya fito daga motar fari cikin dogon riga shadda mai launin zinariya, da rawanin da ke sa hasken rana ya bayyana a goshinsa. Murmushin sa na cike da annuri, yana ɗaukar zuciyar kowa da kallo kallonsa kaɗai na saka mutum jin kwanciyar hankali. Moddibbo kuwa, ya fito da kansa daga cikin ɗakinsa, cikin natsuwa irin ta dattijo mai hangen nesa. Suka runguma kamar ’yan Moddibbo kuwa, ya fito da kansa daga cikin ɗakinsa, cikin natsuwa irin ta dattijo mai hangen nesa. Suka runguma kamar ’yan uwa da suka jima ba su hadu ba. baiwa da mutunci sun kasance tsakanin su tun shekaru goma da suka wuce — alaƙar da ba kuɗi ko matsayi ba ne ya ɗaure, illa kirki, imani da gaskiya. “Barka da zuwa, Alhaji,” Moddibbo ya furta cikin murya mai nauyin daraja. “Lafiya lau, Moddibbo. Allah ya tabbatar da alheri kamar kullum,” Alhaji Saminu ya amsa da ladabi. Maza da yara sun fara taruwa a kofar gida, ana kallon motoci da murmushi, yayin da matasa ke harhada shannaye daga gindin kuka da ke kusa da gona, domin Alhaji ya saba fita da kansa yana zaɓar dabbobin da zai yanka domin hidimar Sallah ga iyalansa da maƙwabta. Bayan doguwar gaisuwa ta mutunci da girmamawa tsakanin dattijan biyu, sai ga Halima yarinya mai kyaun da ke bayyana a hankali kamar safiya mai sanyi ta fito da kwanon madara a hannunta, fuskarta daɗaɗɗiya, idonta mai cike da nutsuwa, ta isa gaban baƙi cikin kamewa da girmamawa. "Assalamu alaikum," ta faɗa da siririyar murya "Wa alaikumus salam," Alhaji Saminu da Moddibbo suka amsa a tare, suna kallonta. Alhaji Saminu ya karɓi madarar hannunta, yana dubanta cikin ido da murmushi da ke ɓoye wani sirri mai zurfi. Halima ta sunkuyar da kanta, tana juyawa cikin girmamawa kamar yadda aka koya mata. Bayan ta shige ciki, Alhaji Saminu ya ɗan juyar da kallonsa zuwa ga abokin zamansa. "Moddibbo... shekarun Halima sun cika goma sha biyar yanzu, ko ba haka ba?" Moddibbo ya gyara zamansa, ya ɗan sosa gemunsa yana murmushi mara kyar. "Eh, haka ne. shekaru goma sha biyar rabon da ka min wannan alkawarin." Alhaji ya lumshe ido. "Na tuna sosai ka ce Halima zata zamo matata, kuma kai da kanka zaka miƙa min ita ranar da ta kai munzalin aure." Moddibbo ya ɗan sauke ajiyar zuciya, yana kallon ƙasa. "Ka sani Alhaji... ban taɓa mantawa da alkawarin nan ba. kuma na tsaya akan shi har yau saboda girmanka da darajarka a idona. Amma fa mutane sun fara tambaya, sun fara zargi... wasu na cewa wai ni na hana Halima aure saboda son zuciya wasu ma na ganin kamar ina fuskantar matsin lamba daga wani ɓangare." Alhaji Saminu ya ɗan sunkuyar da kai, muryarsa na nuna laushi da tausayawa. "Moddibbo... ka sani Halima tana da muhimmanci a gareni fiye da yadda za a iya fassarawa da baki amma idan hakan zai cutar da mutuncinka ko na yarinyar... sai mu sake duba hanyar da za a bi cikin adalci da amana." Moddibbo ya ɗan kalli tsohon abokinsa, yana girgiza kai da murmushi mai ɗan nauyi. "Alhaji, ni dai ba zan karya alkawari ba kuma Halima ma ta san da cewa tana da wani babban makoma da muke jiran lokaci ina so a kyautata komai cikin tsari da girmamawa... da zarar ka ce lokaci yayi—ni a shirye nake." Alhaji Saminu ya ɗaga kai, idonsa na ɗauke da abu fiye da kalmomi. "To lokaci yayi, Moddibbo kuma Halima zata dawo gareni—amma ba kawai a matsayin amarya ba, a matsayin amanar da zan ci gaba da kulawa da ita kamar zinariya mai tsarki." Get ready fans ga Halima ga Alhaji Saminu menene abinda wannan gajeren labarin Maryam ya ƙunsa , let's go.......... https://chat.whatsapp.com/BsQ0CkOCA83FgwnQ177z9y 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON🌕 BY NARNAH KANWAR SOJA MARUBUCIYAR MIJIN MAGE FARASHIN SO BIYAYYA GA UWA DUHU CIKIN HASKE RUHI BIYU HANYAR RUWA MAI CIKI CE MADOBIN IDO AHLIN LASHKAR PRINCESSS RAHILAT RAYUWAR UMMAH BAYAN WATA SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star 15 / 16 08 / 5/ 2025 Kamar yadda aka saba duk shekara, Alhaji Saminu bai taɓa yin ƙasa a guiwa ba wajen nuna ɗimbin darajarsa a idon mutanen ƙauyen Gembò amma wannan karon daban ne. wannan karon ba kawai don shanaye ya zo ba ya zo ɗaukar amana. A gaban Moddibbo da wasu dattawan gari guda biyu, Alhaji Saminu ya fito da sadakin Halima. kudi ne masu yawan da fulani ba su fiye gani ba a lokaci guda baya ga hakan, ya kawo 'yan dabbobi da kayan gyaran amarya, tare da alkawarin dawowa bayan Sallah da sati biyu—kai tsaye daga birnin Tarayya Abuja inda matarsa ke zaune. Moddibbo ya karɓi sadakin cikin nutsuwa da girma ya san me hakan ke nufi: yanzu Halima zata koma karkashin Alhaji Saminu amma ko da yake zuciyarsa na cike da nauyin amana, bai nuna ba, saboda a rayuwa irin tasu, alƙawari tamkar doka ne da ba za a karya ba. Halima kuwa... ta zauna a gefen mahaifinta da cike da kunya, fuska a kasa kamar yadda aka koya mata, duk da cewa an ba ta labarin cewa rayuwar birni ce zata zame mata gaba, kuma Alhaji Saminu mutum ne mai arziki da daraja—amma a zuciyarta babu motsin soyayya ko ɗokin aure. Zuciyarta tamkar fili ne, babu shuka, babu furanni kawai akwai wata siririyar lafazi da take maimaitawa a ranta: "Na yarda da mahaifina na amince da kaddara. kuma zan bi Alhaji Saminu, ko da zuciyata ba ta motsa ba." Irin wannan biyayya ce da ta sa ta karɓi sadakin da lafazi guda biyu: “Na yarda.” Moddibbo kuwa kamar kowa yana ganin yana murna amma shi da zuciyarsa sun san gaskiya , ya san Halima ba ta kai matsayin aure ba tukuna ta girma da sauri, amma zuciyarta har yanzu karama ce, tamkar macen da bata fara sanin al'amuran soyayya ba. Sai dai kuma, Moddibbo mutum ne mai daraja da mutunci ya rike amanar Alhaji Saminu fiye da yadda wasu ke rike 'ya'yansu. Yana fatan Alhaji Saminu zai kare martaba da tsaron Halima kamar yadda ya rike alkawari na shekaru goma sha biyar. Wani iska ya buso daga arewa, ya kada ganyen kuka da ke bakin ruga Halima ta lumshe ido, tana jin iskar kamar wata alama ce daga sama ko soyayya zata zo daga baya? ko kuwa hakan nan ne rayuwa ta rubuce mata? Bayan sati biyu da cikar alkawari, ƙauyen Gembò ya sake fuskantar wata rana da ba za a taɓa mantawa da ita ba rana ce da komai ya sauya—rana da tarihi ya ƙara rubutun zinariya cikin ƙwarya mai ƙyalli. A safiyar ranar asabar, tun ƙarfe tara da mintuna goma, sai ga jere-jeren motoci guda shida masu sheƙi da ƙyalli irin wanda bai saba zuwa ƙauyen ba, motoci ne kirar Lexus LX 570 guda biyu, guda bakar fata, guda kuma fari ɗan haske mai cike da adon zinariya. Sauran kuwa motoci ne kirar Hilux da Toyota Highlander, dukkansu cike da kaya, kujerun zamani, manyan jakunkuna da akwatuna masu lulluɓe da furen ado da yajin rawaya. A wata ƙaramar Prado, wanda aka ɗora babban laifan jajjayen furanni da tutar Kaunar aure, Alhaji Saminu ne ya fito sanye da babban ɗan-baban Shadda mai launin zinariya da ruwan hoda , babbar hula ce ta fulani bisa kansa, mai ɗinki na musamman da adon sarka fitarsa daga mota ta sa yara suka yi tsalle, mata suka fara cewa: “Ga angonmu ya iso! Allah ya sa a dace!” Shi kuwa, yana da murmushin da ba'a san a zuciya akwai tsoro da jin nauyin amanar da ya ɗauka ba bayansa, abokansa biyu da shaidu—Alhaji Babangida da Alhaji Laushi—duk sun fito cikin kayan zamani ƙauyen ya sha ado kamar an shirya masa sallah gari ya ɗau shela da kade-kade na kalangu da waka: “Alhaji Saminu yazo! angon Halima yazo!” Tun daga makon da ya wuce, iyayen Halima sun ɗora shagalin al'ada, mata na unguwa sun taru kullum ana sallake, ana gasa binkami, koskoso, da kilishi. Halima tana zaune cikin ɗakin mahaifiyarta marigayiya, cikin duhun tunani da zumudin rayuwar da ba ta san me take cike da ita ba ,aka yi mata lalle, aka sa mata ƙwarya ta ruwan turaren wuta a gefenta, aka shafa mata manshanu a fata, aka ɗinke mata zani da riga mai alamar Fulani na gargajiya—jar zani mai adon ratsi da santali na tsaf. An saka ta cikin wani ɗaki mai ƙyalli da kilishi, ana yayyafa mata ƙamshi da bakhour, ana duba fatarta da gashinta, yarinyar ce kyakkyawa da kyau na halitta, ba ado ke ƙawata ta ba—rashin yawan maganganu da nutsuwar ta ce abin kallo. A gaban limamin ƙauye da shaidu, aka daura auren Halima da Alhaji Saminu da sadaki naira dubu ɗari biyar, da sarkar zinari da kayan gida., adaidai lokacin da aka furta "na ɗaura", Halima ta fashe da kuka mai ƙarfi. Sai dai ba kuka na soyayya ko jin daɗin aure ba ne—kuka ne na rabuwa da matar mahaifinta, wacce ta raineta tun rasuwar mahaifiyarta, wani kuzarin tunani ya cika ta, kamar tana jin kamar yanzu rayuwarta ta sauya daga yarinya zuwa amarya, daga ƙauye zuwa birni. Moddibbo ya share hawayen sa da alwala, yana murmushi mai cike da damuwa, yana fatan Halima zata dace da sabon rayuwar da zata tafi ciki, a zuciyarsa yana fatan Alhaji Saminu zai rike ta fiye da yadda aka rike ’yar sarki. Alhaji Saminu ya bar ƙauyen ba da hannu ba. Ya bar da ɗimbin kyaututtuka: kudi ga matan unguwa, jakunkunan shinkafa, kayan abinci, sabbin riguna da ɗinkin zamani ga matasa, har da jakunkuna ga yara da aka ce "na makaranta". Wajen fitarsu, aka shigo da sabuwar amarya cikin sabuwar rigar aso-ebi da kwalliyar santali, aka ɗaura mata gyale mai nauyin zinariya, aka raka ta da kalangu da wake-wake, aka saka ta cikin motar farin Lexus, sai ga kafila ta nufi birnin Abuja. Amarya ta fito daga ƙauye—amma fuskarta na cike da tambayoyi. Shin me birnin ke ɓoye mata? Me Alhaji Saminu zai kasance gareta? shin wannan aure zai fassara soyayya ne, ko wata kyauta ta biyayya ce da ba zata taɓa jin daɗin ta ba? ********************************* Juyawa tayi da ƙarfi kamar wadda aka hangi zuciyarta ta nitse cikin ruwan kogin ɓacin rai. tana mai huci da numfashi mai nauyi, ta faɗa jikin Moddibbo kamar jaririya, ta rungume shi da ƙarfi, tana kuka mai girgiza zuciya dukkan gangar jikinta na rawar jiki, murya na rawa kamar ana buɗe gidan hawaye a zuciya. Moddibbo ya kama kanta yana bubbuga bayanta da hannunsa mai sanyi da tausayawa. "Allah ya sa ki dace Halimatu," ya faɗa da wani murya da yafi shiru nauyi. "ki rike mutunci, ki tsaya da imani kiye koyar da mahaifiyar ke a fagen haƙuri zaki ci ribar zaman duniya ... rayuwa ce bata da tabbas." Shi kansa idonsa cike da ruwa, kodayake zuciyarsa ta taɓu sosai—ya jima yana kallon Halima tamkar zinariyar sa wanda yanzu ya mika hannunsa ya mika ta ga duniya. ya mika al’amuranta ga wani mutum da ya fi shi daraja da kima, amma ba shi da tabbacin soyayya. Bayan kuka da ban kwana mai cin rai, sai Halima ta shige cikin motar Alhaji Saminu da zuciyar da ba a iya fassara. Alhaji yana ƙoƙarin rarrashi da annuri, yana ƙyalƙyala dariya mai taushi yana faɗin: "Amaryata kada ki damu, Abuja ba abin tsoro ba ne ke zauna lafiya, za ki ga alheri." Halima bata ce komai ba ta fuskanci gilashin motar tana kallon ƙauyen su da ke raguwa a bayanta kamar mafarkin da ya ɓace. hannunta na cikin haɗaɗɗiyar rigarta, amma zuciyarta na cikin tsohon zanin ƙauyenta. Motoci suka fice daga Gembò, suka fasa hanyoyi masu kura, suka dosa garin Yola inda jirgi zai tashi zuwa Abuja. Halima na zaune cikin mota, amma kamar a mafarki ta kasa kallon sabbin gine-gine da suka wuce su, kamar ba su da ma'ana gareta. A lokacin da suka isa filin jirgi, an ce mata "Halimatu! Ki sauka ",ta sauka cikin rigima, tana kallon ƙasa kamar tana tsoron ƙasa ce zata buɗe ta haɗiye ta ba ta san me ake nufi da “ticket” ba ba ta san yadda ake biya ba yanzu ne Halima ke fara jin bambancin rayuwa, ta kasa cire takalmanta a wajen sakan na’ura, sai da ma'aikaciyar ta fara dariya ta ce: “Yarinya! ba salla za ki ba wannan tsafta ne da dokar jirgi.” taji kunyarta sosai Idonta ya cika da ƙyama da tozarta a zuciyarta: “kai! ashe akwai duniya kamar haka?” Bayan an kaita cikin jirgin, aka ɗaure mata seat belt, ta riƙe kujerar kamar wacce ke cikin ruwa mai zurfi. Da jirgi ya tashi, ta saki ƙara mai firgitarwa: “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Wayyo Moddibbo…! na mutu!” Alhaji Saminu ya rike hannunta da dariya “babu komai Halimatu, jirgi ne ke tashi kawai.” Kamar sabuwar tsuntsuwa aka ɗauke daga ciyawa, aka ajiye cikin gini mai fanfo. As zuciyarta, birni kamar wata. Amma tambaya ɗaya ke ci mata rai: Shin wannan sabon garin da take ciki zai taimake ta ta samu sabuwar rayuwa, ko zai ɓata mata tunanin da take tsaye da shi tun ƙuruciya? Tunda suka hau cikin jirgin sama, Halima ta kasa zaman lafiya idanunta na zagaye cikin hadadden komai wanda ba ta taɓa mafarkin wanzuwarsa ba , tana kallon tagar gefe, tana ganin sararin samaniya da ƙasa na raguwa kamar yadda aka rage wa tunaninta hankali. amma wani abu ya sake ɗaukar mata hankali... A kujerar bayan nata, wani saurayi ne zaune, ya murtuƙe fuska, idonsa kamar na damisa mai zurfin tunani , fuskar sa doguwa ce, fara tas kamar bulo, ƙuncinsa yana da ɗan launin ja, bakinsa siriri ne amma mai ɗan ƙasaita gashin kansa an rage shi tsaf yana sheƙi, sai karan agogon zinare a hannunsa na hagu ya ƙara ɗaukar hankali. Shima yana kallon Halima, ba da sha’awa ba, amma da mamaki da tausayi kadan kamar yana cewa da kansa, “Ina aka samo irin wannan ‘yar ƙauye mai tarin kamala?” suna cikin tashi ne Halima ta saki ihun da ya gigita kowa “Wayyo Allah naaa! waye ya ce jirgi zai ɗaga?! Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!” Mutane sun juya suna kallonta, mata suka dinga dariya a nutse, wasu kuma suka tausaya amma shi saurayin da ke baya—ya kalli fuskarta da jajayen idanu, yana juyar da kansa a hankali cikin murmushin gefen baki, kamar wanda ya saba da irin haka a rayuwar zuciyarsa , sun sauka a filin jirgin Abuja, wanda ya bude musu sabon shafi a rayuwa. Alhaji Saminu ya nufi Maitama da su, inda katafaren gidansa ke cike da girma da kima. gidan na da kofa babba mai lanƙwasa kamar ƙofar masallaci a Makka. farfajiya ce a waje, da lambu mai yalwa, sai tsuntsaye ke ta raira waka kamar sun san sabon baƙuwa ta iso. Yayin da Halima ta kalli ƙofar katafaren gidan, zuciyarta na wani irin doki da tsoro da fargaba, wani sashe na ruhinta na faɗin "kin fito daga ƙauye, amma an jefa ki cikin birnin masu hannu da shuni..." da zuciya ɗaya ta shiga, sanye da kayan aure na gargajiya: mayafin fulawa, zobba a yatsu, da dankwali mai yatsin zinariya. A cikin gida, motoci sun sha jerin gado, masu gadin gidan biyu a ƙofar shigowa suna miƙa gaisuwa da ban girma. Gidan kuwa – katafaren alfarma ne wanda ba a taɓa mafarkin Halima zata taka kafarta ciki ba. Babban falon yana da manyan tagogi masu labulen fata na turkiyya, cike da fitilu na chandelier masu hasken zinariya, cikin falon ne Hajiyah Nafisa ta karɓe ta da murya mai cike da mamaki: Matar Alhaji Saminu, Hajiyah Nafisa, ta fito sanye da kayan alfarma gashinta a jikin mayafi yana sheƙi kamar rigar sarauta ta kalli Halima da murmushi na ɗan lokacin, amma idanunta na cike da alamun tambaya: “Itace wannan yarinyar?” Halima ta kasa magana ganin palon gida kadai ya isheta tiles ne na zinariya da hoda mai sheƙi, fanfo a bango da tebur na gilashi. tana takawa kamar ana binsa da ƙasa. Zuciyarta na cewa: “To wallahi... haka birni yake ko dai na mutu ne an kawo ne gidan aljanna ?” kwalliyar da aka yi mata da kayan Fulani na auren ƙauye—maye da zobe da mayafi na fulawa—ya sa ta ƙara haske , amma a fuska akwai shakku, akwai salo na “ba sani ba sabo.” sai dai akwai mutunci a tafiyarta, wanda ba’a koya shi a birni. “Nafisa itta ce amaryata na biya sadakinta tun can ƙauye kamar yadda na gaya miki. Allah yasa alkhairi.” Hajiyah Nafisa ta tabe baki cikin murmushi mai nauyin fahimta daga kallon ta ɗaya ka gane ko da tana ƙoƙarin karɓarta, zuciyarta ba ta cikin hakan gaba ɗaya. Sai da aka kai ta ɗakinta da aka tanadar mata cikin gida ɗaki mai faɗi sosai, bangon sa mai launin cream da zinariya an shimfiɗa masa carpet mai laushi, akwai gado babba da labule mai juyawa kamar na sarauta taga biyu na dakin suna kallon lambun cikin gida, inda tsuntsaye ke ta shawagi, cike da kyan gani. dakin na da fanka da AC, amma Halima bata san amfani da komai ba. Sai kallon su take kamar kayan sihiri. Ta zauna a gefen gado daidai lokacin wata mai aiki – Hasiya – ta shigo da murmushi a fuskarta. Hasiya daga Sokoto ce, mai ƙanƙantar jiki da zubin kawaici atake suka fara haɗuwa Hasiya ta ce da ita: “Wallahi Aunty Halima kin yi kyau, da gaske ne ke daga ƙauye?” “Eh... daga Gembo,” ta ce da dariya mai daɗin ji. “kin taɓa jin sunan kauyen?” “A'a, amma yanzu na ji ki. sai dai ki gyara nan Abuja fa ne Idan baki yi wayo ba, sai a cuce ki.” Nan suka fara zama ƙawayen gaske. Halima ta fara ɗan sabawa cikin gidan, musamman da yaran Alhaji Saminu goma da ke gidan. akwai Muneerah da Ruqayyah – ‘yan mata manya masu haɗe da kwalliya da rashin kunya, masu jin turanci da yi wa Halima kallon kamar uwar kauye suna kiran ta “that girl from bush” a bayan ta. Sannan akwai Aminu Junior da Zaid, samari matasa da suka fi ɗaukar lokaci a wajen gidan basu damu da sabuwar mace, sun fi shagaltuwa da motocinsu da rayuwar club da Instagram. Yara uku ƙanana—Sulaiman, Abbas, da Fadilasun fi sabawa da Halima suna zuwa ɗakinta suna wasa da ita ta dinga yi musu wasan shanu da dabbobi da kida da rawa irin na ƙauye, suna dariya kamar an saka musu annashuwa a zuciya tana ɓoye wannan zumunci da su domin kada uwayensu su ji. Matar biyu kuwa, Hajiyah Mariyah da Hajiyah Sabeerah, su ne abokan huldar Nafisa amma Hajiyah Mariyah ce shaidaniya, mai haƙurin fitina da halin mugunta tana kallon Halima da kyankyami, tana cewa: “Wato wannan ƙaramar ‘yar Fulani ce ta zo mana da daddare? Allah ya sa ba za ta ja mana Alhaji ba.” Tun daga rana ta fara tsara yadda zata nunawa Halima cewa gidan ba da sauki ba ne. tana tura mata ayyuka kamar ba matar aure ba: “ki share wancan, ki gyara kicin, ki tafi can ki goge banɗaki.” Halima kuwa, da jin kunyar Fulani da biyayya, sai ta dinga yi tana mika hannu da zuciya, ba tare da kuka ko korafi ba inda Hasiya ta fi shiga tsakiya, tana mata nasiha da rarrashi: “Ki yi haƙuri Halima, nan ne birni idan kika nuna rashin juriya, sai su hana ki kwanciyar hankali amma Allah yana tare da mai gaskiya.” A haka Hajiyah Nafisa ta dinga kallon yadda Halima ke yi wa yara wasa, tana girki da kyau, tana wanke-wanke da murmushi da farko tana kyamar ta, amma wata rana ta shigo dakin Halima sai ta ganta tana dinki wa Fadila riga da hannu wani abu ya motsa a zuciyarta. Ta ce da kanta: “Wannan yarinyar... ba ta da mugunta kuma girmanta yana shigowa hankali.” Halima kuwa har yanzu bata san haka ba. zuciyarta na yawo ne da tambayoyi: “shin wannan rayuwar ita ce rabona? ina mahaifina da mahaifiyata? W wannan Alhaji Saminu fa, me yasa yake sona? wani dalili ne yasa ya kawo ne gidan sa ya ajiye tsawon lokaci bai dawo garine ba? Ohhhhhhhh ga Halima ga Abuja a sannu a hankali zamu shiga labarin Halima continued ƙanwar soja in Sha Allah ✍️ https://chat.whatsapp.com/BsQ0CkOCA83FgwnQ177z9y 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON🌕 BY NARNAH KANWAR SOJA MARUBUCIYAR MIJIN MAGE FARASHIN SO BIYAYYA GA UWA DUHU CIKIN HASKE RUHI BIYU HANYAR RUWA MAI CIKI CE MADOBIN IDO AHLIN LASHKAR PRINCESSS RAHILAT RAYUWAR UMMAH BAYAN WATA 💫ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Wannan page na sadaukar dashi ga mutum biyu Sister Juwairiyya M Lawan tare da Najeeb Allah ya bar zumunci enjoy the page guys 19 / 20 Wata bakwai kenan cif da zuwan Halima gidan Alhaji Saminu wata uku na rayuwa da ke cike da shiru, da sanyi, da kewa, da dogon kallo zuwa fitilun falon cikin dar wata bakwai bata taɓa ganin fuskar mijinta ba sai sau biyu kacal sau na farko da ya kawo ta gida, na biyu kuwa yana wucewa da mota, ya tsaya da taga yana kallon ta ba tare da ya sauka ba. Tunda lokacin, Halima ta fara tantama: “shin ni matar aure ce ko kuwa ba haka bane? ko kuma na fi zama ‘yar aikin gidan alfarma da ba ta san ko wane ne mijinta ba?” Gidan kuwa kamar gida ne na almara: bangarori fiye da shida, kowane ɗaki kamar wani gida daban. Halima ko bandakin da aka ce na nata ne ma sai da Hasiya ta koya mata hanyarsa da yadda za ta kunna ruwa daga famfon lantarki ta ƙi fita daga dakin nata sai idan da gangan, yaran gidan sun zama mafita ga zuciyarta Sulaiman da Fadila na mata wasa, suna biye mata da dariya da kida da rawar kauye ita kuma tana jin daɗin hakan, tana samun nishadi duk da zuciyarta na ci gaba da yin rauni da damuwa. a wannan daren, kamar kullum, ta zauna a dakin nata cikin sanyi mai daɗi daga AC da fitilar tagwayen da ke ba dakin ƙamshi ta jingina da kujera, tana kallon hoton kwane-kwane da aka ɗora a bango hoton tsaunuka da furen da bata taɓa gani da ido ba, hawaye ya fara gangaro mata ta shafa su da gefen zane, tana kiran zuciyarta da sunan gida: “Kauna, Kaka, Baraka... ina kuke? ko na fice a nan in dawo Gembo da ƙafa ne? ko gidan da kuke tsirfa hatsi yanzu, ko na fi wannan?” Daga nan, bacci ya ɗauketa cikin sanyin dare mai ɓoye zuciya cikin mafarki, Halima ta tsinci kanta a kusa da wani tafki mai ruwan shudi gabar tafkin akwai ciyayi masu launin zinariya, tsuntsaye na waka, iska na busa kamar karamar waka, ta tsaya cikin tufafin fararen zinariya, kanta a rufe da mayafin rawaya , can gefe kuwa, wani saurayi na kallon ta tsayuwarsa mai ƙayatarwa ce: dogo, baƙi, yana sanye da farin riga da wando. amma fuskar sa dukk ta ɓoye a inuwa kamar fuskarsa na ɓoye da nufin ya dawo wata rana. “Halima...” muryarsa mai sanyi, mai kaɗa, tana ratsawa har cikin jijiyoyinta.“kai wa kake ne?” ta tambaya da muryar yarinya. “kayi kama da wani na kusa da zuciyata...” “Ni ne mai zuciyar da ta kira ki cikin bacci... da zuciyar da zata so ki fiye da yadda kike so kanki.” ya miƙa mata hannu, amma kafin ta kamo ta farka tashi da sauri, numfashinta ya kadu, zuciyarta na bugu tana kallo sama kamar zata gan shi a cikin silin. “waye wannan? me yasa mafarkin nan ya shige ni haka? Kuma me yasa fuskar sa ta ɓoye kamar akwai abu da ba a shirya bani ba?” karo na farko tun da ta zo birni, Halima ta fara jin wani abu daban – kamar mafarkin soyayya da sabuwar rayuwa na faɗa mata, "akwai wani sirri da ke tafe... kuma akwai wanda zai sauya maki rayuwa, ko da ba yanzu ba." Kullum cikin dare, Halima na ƙoƙarin rubuta abubuwan da ke faruwa da ita a cikin wani ƙaramar littafi da ta ɓoye cikin almara ,tana rubuta mafarkinta, ƙiyayyar Hajiya Mariya, da muradinta na ganin wata rana zata fita daga gidan nan cikin daraja. “Ina mafarkin wata rana zan fita daga nan ba da hawaye ba, sai da murmushi kuma duk wanda ya raina ni, zai ga matsayi na kuma wanda ya tsare zuciyarsa a gareni, zai gane cewa ba wai 'yar kauye bace, sai dai baiwar Allah da daraja ta ɓoye.” ******************""""" Abdullahi Khalil Usman wanda da dama ke kira Mr. Abdullahi, shine shugaban babban kamfanin gado na mahaifinsa wanda aka sani da Usman Holdings International, wanda hedikwatarsa ke cikin Abuja, amma reshe-reshen sa sun watsu a duk fadin Najeriya da kasashen waje duk da wannan girman arziki, Abdullahi mutum ne mai natsuwa, mai son zaman shiru, kuma yana da ɗabi’ar kin yarda da auren dole. “Ni bana son aure yanzu. Ina jiran yarinyar da zuciyata zata karɓa ba tare da tilas ba,” inji shi kullum idan mahaifiyarsa Hajiya Binta ta taso masa da lamarin aure. Tun yana ɗan shekara ashirin da shida, Abdullahi ke yin wani irin mafarki na wata budurwa mai kamun kai, mai kyan hali, cike da nutsuwa , kullum fuskar yarinyar bata bayyana gaba ɗaya, sai murmushin ta da kuma yadda take tafiya cikin kwanciyar hankali kamar ba ta san duniya ba. Yanzu yana da shekara talatin da ɗaya, amma har yanzu bai manta wannan mafarkin ba har ya kasa yarda da kowacce mace – saboda zuciyarsa tana jiran wannan mafarkiyar da bata bayyana ba. Ranar da ya hau jirgin daga Yola zuwa Abuja, yana tsaye yana shan iska da kallon mutane, sai idonsa ya sauka akan wata yarinya da ke tafiya da Alhaji Saminu – cikin riga da zani, fuskar ta cike da tsantsar kauyanci da kamun kai. Fuskar yarinyar kamar dai fuskar yarinyar mafarkinsa ce! amma sai ya girgiza kansa: “A’a, ba zata iya zama ita ba… ai ita kauyaniya ce ko turanci ma bata iya ba.” ya fad’a a ransa, yana danne mamakin zuciyarsa amma tun daga lokacin, idonsa na bibiyar Halima, duk da cewa bai san sunanta ba, kuma bai ce da ita uffan ba. Sai dai a zuciyarsa… ya kamu da wata ƙayatarwa mai cike da ban mamaki. Yanzu da suka sauka Abuja, Abdullahi ya koma rayuwarsa, amma zuciyarsa bata daina tunanin Halima ba duk wata yarinya da ya gani, sai ya kwatanta ta da ita, amma babu mai dacewa shi kuwa Alhaji Saminu, yana cikin shirye-shiryen cin gajiyar auren Halima – yana kula da ita da nisa, amma bata san yaushe zai dawo ba Halima kuwa, tana fama da azabar rayuwa a gidan kishiyoyi, tana ta mafarkin sauyi da ƙauna, amma bata san cewar zuciyar wani saurayi mai daraja tana neman nata ba Abuja cibiyar kasuwanci da masarauta ta zamani wannan karon, babban taro ne da ya haɗa manyan kamfanoni, 'yan kasuwa, da shugabannin kasashen duniya Alhaji Saminu, wanda ya kafa taron kasuwanci, yana cikin wani kwararren d'akin taro a babban otel na Abuja, wanda ke dauke da kyan gani da yanayi mai cike da alfarma duk duniya na kallon wannan taro da alamar samun ci gaba ga kasuwancin Najeriya manya da ƙananan kamfanoni sun hada kai domin samun nasara da bunkasa tattalin arzikin kasar. A cikin wannan dakin, Abdullahi ya tsaya cikin cikakken kwalliya jikin sa yana ɗauke da rigar alfarma mai kyau, wanda ta haɗa da jallabiyah mai launin zinariya da farar rawani fuskar sa tana cike da kyan gani da kwarjini. Duk wanda ya kalli shi zai fahimci cewa yana ɗan kasuwa ne mai daraja, wanda ke dakin taro ba domin wasa ba a cikin zuciyar sa akwai fata na samun nasara mai girma, amma akwai wata yarinya da ta mamaye zuciyar sa – Halima. Abdullahi, wanda iyayensa ke son shi ya auri wata mai matsayi daga cikin iyalai masu arziki, yana neman neman soyayya ta gaskiya. bai taɓa ganin wannan soyayya ba a cikin kowanne daga cikin yarinyoyin da iyayensa suka so masa amma a cikin zuciyar sa yana ɗokin haduwa da Halima, wanda ya ga a cikin mafarkinsa a jirgin sama lokacin da suka haɗu tabbas yanzu zuciyarsa yafi karkata ga cewa ya haɗu da mafarkin sa a rashin lura irin tasa . A yayin da aka gudanar da taron, Halima tana cikin wani dakin hotel ɗin da Alhaji Saminu ya shirya mata wannan d'akin yana ɗauke da kayan alfarma da kyakkyawar kwalliya – gado mai kyau da tsayayyen fata na zinariya. Halima ta zauna cikin dakin, tana kallon kayan da aka tanadar mata, amma zuciyar ta cike take da tunani wataƙila, wani abu ya faru da ta rasa kwarin gwiwarta, ko kuwa har yanzu tana jin cewa wannan ba shi ne rayuwar da ta yi mafarki da ita ba. Alhaji Saminu ba ya kula da wannan sha'awar da ta ke nunawa a saboda haka, yana son ta zama abokiyar rayuwarsa, amma yana ɗaukar ta a matsayin daya daga cikin matan da zai kula da ita daga ɓangaren kyakkyawar tarbiyya da kuma halayen aure. A cikin taron kasuwancin, Abdullahi na cikin dakin taro, yana kallon yadda ake gudanar da al'amuran. A zuciyar sa, yana jin cewa ba zai taɓa samun zaman lafiya ba sai ya sadu da Halima. ya tuna da fuskarta a cikin jirgin sama, da yadda zuciyarsa ta shiga cikin hayaniya saboda soyayyar da ta shige masa cikin zuciya ,yana ganin ta a cikin wannan dakin, amma ba zai iya neman ta yanzu ba. wannan tsari na al’amura yana nuna masa cewa soyayya ba ta da sauki, kuma yana bukatar lokaci don samun damar yin matakin da ya dace. Tsawon kwanaki biyu ana wanan gagarumin meeting nin inda ake shirye shirye rufe taron a kwana na ukku Alhaji saminu dalilin ɗauko Halima daga gida bayan kumawae sa gida cikin gaggawar kirar taron da suke gabatar wa yanzu cikin bazata ya iso gidan ganin halin da Halimar ke ciki ne ya bashi mamaki kwarai da gaske wannan dalilin yasa ya ɗauko ta a tare dashi .... RANAR TARON ƘARSHE Ɗakin taron babban hotel ɗin na Abuja ya cika da hasken chandelier mai sheƙi kamar taurari fata-fatan zinariya da tabarmar da ta shimfiɗu kasan tiles ɗin falo suna haskakawa da salo irin na manyan duniya. An shimfiɗa dogon babban tebur na gilashi, aka jera kujeru masu launin royal blue da zinariya agefen teburin akwai lambun furanni masu ƙamshi, da sauran kayan kyauta na kamfanoni. mutane masu siriri da sirarrun suits sun cika gurin: 'yan kasuwa, manyan ‘yan banki, masu hannun jari, da CEOs daga kamfanoni daban-daban. Abdullahi, sanye da suit mai launin baki da farin riga da blue tie, ya zauna a tsakiyar babban kujerarsa girman sa da kamewar sa ya ja hankalin kowa — da kallo daya zaka san ba na yau aka haife shi ba fuskar sa ba dariya, ba kuma fushi tsaka-tsakin kamewa da matsayi Hausawa sukace yaro da kuɗi abokin tafiyar manya Har lokacin da Alhaji Saminu ya shigo cikin taron, aka mika masa gaisuwa irin ta manyan masu kuɗi ya zauna da kamun kai, yana ta gyaran hula da hancinsa lokaci-lokaci, alamar rashin jin daɗin zama saboda tunanin a maryar sa , lolz A takaice an yi taron a cike da muhimman magana: aka rattaba hannu akan sabon kwangilar gine-gine da haɗin gwiwa bayan an gama taron, mutane suka shiga gefe suna ta yin hotuna, musabaha da exchange card. A gefe kuma, Halima wacce aka bar a dakin hotel na VIP floor, tana kwance tana ƙoƙarin danne kukan kewar gida da tsoron birni. tana sanye da kayan gida masu kyau amma ƙauyanci ke bayyana sosai a fuskarta Fuskarta bata da kwalliya, sai ruwan hawayen da ta share, tana kallon window tana ganin duhun dare yana sauka kan manyan titunan Abuja. bayan taron, Alhaji Saminu cikin gaggawa ya amsa kira daga gida an kira shi da sauri, wani ɗan matsala ce ta dangi da gaggawa ya fice daga hotel ɗin... amma sai ya manta da Halima a cikin ɗakin hotel ɗin! Halima tana jiran shigowar sa, tana jin tsoron shiru da tunanin abubuwa daban daban Halima ta jawo ƙofar ɗakin a hankali, tana hango hanyoyi masu haske da furen bango. tana sanye da doguwar riga mai launin shudi mai launin ruwan sama, wanda ke fita da kyau akan fara fatarta, tana tafe da ɗan ƙaramar gyale mai launin milk da ya ɗaura mata fuskarta kamar an kare ‘yar Sarki. Tsoron da ya mamaye ta ya hana ta saka takalma — tana tafiya a siraran ƙafarta, tana kallon dukkan gefuna da tausasan idonta. tana jin kowane sauti kamar wani abu zai fito daga cikin duhun corridors ɗin hotel ɗin. ta isa ga wani ɓangare na babban hotel ɗin gaban lift — lokacin da abinda ta gani ya firgita ta. Da gudu ta nufi cikin tsoro tana neman mafaka — gaban ta a bude — tayi karo da mutum mai tsayi, sanye da baƙin suit mai sheƙi, riga fara ta ciki, wanda ba kowa bane illa Abdullahi. Shi kuma yana tsaye yana danna wayarsa, iska mai sanyin ƙanshi na air conditioner yana kadawa a gashinsa mai santsi.zuciyarsa tana bugawa da sauri kamar ana gaggauta dokin sarauta, Halima cikin firgici ta fado jikin Abdullahi — hannuwanta suka kama rigarsa, tana fitar da ƙaramar ajiyar zuciya, idanun su suka haɗu ,wani zafi mai daɗi ya ratsa tsakanin su, wani sirrin shiru mai nauyi ya cika sararin tsakanin su. wayar sa ta tsaya hannu, zuciyarsa ta kasa ci gaba da bugawa daidai Idonta ya cika da tsoro, nashi kuma da wani irin salo na jin "na gan ki amma ban gane ki ba". A hankali Abdullahi ya daidaita kansa, yana ƙoƙarin saukewa Halima daga jikinsa. Ya sauke ta a hankali kamar kar ya tsoratata, sai ya ɗauke numfashi ya runtse ido tsakanin su shiru ne mai nauyi, kamar ana iya jin karar fitar numfashin juna. Abdullahi ya tsaya wuri guda, idanuwansa suna zurfafa cikin kyawawan idon Halima waɗanda ke cike da tsoro da rashin tabbas cikin kin sauti mai kaɗan amma cike da girma da tsari, anji muryar Receptionist “Please, Hajiya Halima...! Reception is calling you, Hajiya Halima!” Muryar ya sake maimaitawa daga speaker din da ke jikin bango, kamar an daga karar. Halima ta ji sunanta a sarari, kamar daga sama, kamar ruwa an zuba mata ,wani sabon firgici ne ya sake ratsa ta kamar numfashin ta zai tsaya a firgice, ta sake matse jikinta da ƙarfi a cikin ƙirjin Abdullahi, tana neman mafaka daga kowa da komai ,Abdullahi kuwa ya saki wayarsa ta faɗi ƙasa ya kasa motsi. Numfashin sa ya tsaya cak gaba ɗaya jikinsa ya birkice kamar karamin yaro da aka tsorata masa da aljani. A hankali yana jin kamshin furen Halima — kamshin shinkafar ɗanye da ƙamshin turaren wuta idonsa ya lumshe, zuciyarsa na harbawa da irin bugun da bai taɓa ji ba a rayuwarsa. ya buɗe idonsa, ya kura mata ido, yana kallo cikin fuskarta mai tsantsar kyau da rashin fenti fatar ta laushi tamkar auduga, launin idonta kamar kalar ruwa mai tsafta Bakin Halima ya motsa kaɗan, tamkar zata ce wani abu, amma ta kasa. Abdullahi ya bi bakin nata da kallon da ya kashe masa nutsuwa — laɓɓanta sun yi ja kamar sabuwar ɗan itacen ɗinya, santsi da kauri irin na 'yar asali. Abdullahi ya shige duhu da hasken idonta. wani abu mai daɗi da tsoro na haɗuwa ya cika shi abu da bai taɓa jin sa ba tun daga haihuwarsa " tabbas ittace mafarki na ". Abdullahi ya kasa inda zai sa kansa. Zuciyarsa tmkar an kunna ganguna. wani yanki na zuciyarsa na ba shi shawarar ta hanyar hankali: "ka sauke ta, ka da ka zalunce ta!" Amma wani sashe kuma, na tunani mai zurfi da sha'awar kasancewa tare da ita a dau dai wannan lokacin yana fisgarsa tamkar walkiya: Wani numfashi mai nauyi ya saki — yana jin tamkar zuciyarsa zata fashe da nauyin soyayya da radadin rashin tabbas. idanunsa suka kai ga fuskarta. Daidai lokacin da yake shirin sauke wata ƙaramar ajiyar zuciya, sai suka ji motsi da sautin takalmi mai nauyi, Alhaji Saminu ne ya shiga jikin sa akwai alamar gajiya da fushi, yana janye zuciyarsa da sauri daga tunanin da take shirin narke shi. Alhaji Saminu ya tsaya cak, yana kallon yadda Halima ke manne da wani saurayi, shi kuma saurayin kamar an soka masa gashin zuma a ƙirji fuskarsa ya cika da shakku da mamaki. Yayi wani takun ɗan girma da iko, ya nufo su. Abdullahi ya gano hakan cikin kwana na biyu na idon sa ,ya ja hannun Halima da sauri, cikin ladabi da nutsuwa, suka tafi daga wurin. Halima kuwa, tana kallon Abdullahi tana kuka mai sanyi, hawaye na bin fuskarta tamkar silin ƙwai da ya fashe a hankali. bata so a raba su bata so a bar wannan ɗan lokaci ya wuce ba. Har lokacin da suka rabu, Halima na ta juyawa tana kallonsa cikin raɗaɗin zuciya — kamar tana jin cewa ba za su ƙara saduwa ba, tana maimaita sunan sa a zuciyar ta da jaddada cewa tabbas shine a mafarkin ta , shi kuma Abdullahi, da yatsun sa guda huɗu ya shafi labbansa a hankali yana jin ɗumin halittarta har yanzu a jikin sa, yana binta da kallo tamkar yana so ya hango sirrin da bai bayyana ba. Duniya ta yi wa zuciyoyinsu nauyi wani sanyi da rashin lafiya na musamman ya mamaye Abdullahi, zuciyarsa na fuskantar wani sabon yanayi da bai saba da shi ba. Halima ta kasa daure hawaye tana cikin ɗa Abdullahi ya tsaya cak yana kallonta, zuciyarsa na bugawa da ƙarfi, amma ya tilasta kansa ya sake ta ta tafi da Alhaji Saminu. aguje zuciya, yana ji tamkar an sare wani ɓangare na ruhinsa. yana kallon bayanta har ta ɓace a cikin motar , ya runtse idanu cike da damuwa, numfashi mai nauyi ya suɓuce daga bakinsa. Da zarar Alhaji Saminu ya dawo, ya zube a babban kujerar falo yana huci. wani irin kishi ne da fushi ya turnuƙa masa zuciya har yana jin idanuwan sa na sauya launi Hajiya Nafisa da sauran matansa suka taru suna kallon sa cikin mamaki da tausayi, amma basu isa su tambaye shi komai ba. Ya ɗauki kofin shayi dake gabansa, ya buga da ƙarfi a ƙasa, kofin ya tarwatse. yara suka firfito daga ɗakunan su suna kallon sa cikin tsoro Halima kuwa, tana zaune a bayan kofa , tana kokarin hana hawaye kwarara daga idanuwan ta tana jin tamkar wata sabuwar ƙaddara ce ke shirin saukar mata. a wannan daren, gidan ya cika da nauyin shiru da hayaniyar zuciyoyi shiru mai ɗauke da kishi, da ƙyalle-ƙyallen wani mugun fushi da za a sake fallasa a kan Halima… https://chat.whatsapp.com/BsQ0CkOCA83FgwnQ177z9y 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 AFTER THE MOON🌕 BY NARNAH KANWAR SOJA MARUBUCIYAR MIJIN MAGE FARASHIN SO BIYAYYA GA UWA DUHU CIKIN HASKE RUHI BIYU HANYAR RUWA MAI CIKI CE MADOBIN IDO AHLIN LASHKAR PRINCESSS RAHILAT RAYUWAR UMMAH BAYAN WATA 💫ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Page 21 / 22 Bayan Shekaru Biyu Tunda ranar da suka rabu a babban ɗakin taron hotel ɗin Abuja, Halima da Abdullahi basu ƙara ganin juna ba. kamar dai wata fata da iska ta ɗauka ta ɓoye a doron ƙasa, haka soyayyar da suka ambato da shiru a idanuwansu ta ɓuya cikin zuciyarsu duk da lokaci ya shude, rana ta fito ta fadi sau dubbai, a zuciyarsu har yanzu tamkar jiya aka faru. Abdullahi, da zarar ya koma gida, ya shiga tashin hankali mai tsanani mafarkin Halima, kallo daya da ya yi mata, da sautin murya da numfashinta, suka mamaye dukkan tunaninsa duk da irin dattijon haiba da ƙwazo da yake da shi, ya zama tamkar yaro a duniyar soyayya. ya yi iya ƙoƙarinsa ya guje mata, ya ɓoye a cikin aikin sa da tafiyar kasuwanci, amma zuciyarsa ta ƙi amincewa da sabuwar rayuwa har dai iyayensa suka matsa, suka zaɓa masa matar aure daga cikin manyan iyalan su, suka lallaɓa zuciyarsa da hujjar cewa "ba a dukan soyayya ake rayuwa ba." Da damuwa da karyewar zuciya, Abdullahi ya karɓi zabin iyayensa amma a zuciyarsa ya san: soyayya ta gaskiya daya tal ce kuma Halima ce yayi aure a matsayin ɗan biyayya, ba a matsayin ɗan farin ciki , bayan ya tabbatar da cewa Halima mata ce a gidan Alhaji Saminu. A bangaren Halima kuwa, rayuwarta da Alhaji Saminu ta fara dusashewa da kwanciyar aure. Alhaji Saminu bai sake kallonta da idon da ya saba da shi ba tun ranar da ya ga yadda ta rungume wani saurayi a hotel kullum yana ganin tamkar ta kai girma da zata saki jiki da wani ko da kuwa ba laifinta bane, ko da kuwa ransa ya tabbatar cewa tsoro da ruɗani ne suka jefa ta. Auren Halima ya koma tamkar ɗakin sarauta mai cike da shiru da fargaba matansa na farko na ci gaba da wulakanta ta, musamman Hajiya Mariya, wacce kullum take ƙoƙarin ganin ta gaza Halima kuwa, tana rayuwa ne tsakanin kuka da shiru, tsakanin mafarkin soyayya da gaskiyar rayuwa kullum cikin tunanin cewa ƙaddara ce ta raba ta da masoyinta, kuma soyayyar da take jin daɗinta tun ƙarama ba zata cika ba har abada. "Idan soyayya kaddara ce, to ni na riga na mallake ta, ko da da hawaye zan sha..." Halima na faɗa cikin zuciyarta a duk dare, yayin da take kwana tana duban sararin sama daga taga mai ɗimbin ƙawatawa, amma mara 'yanci. Rayuwa ta ci gaba da tafiya... sai dai zuciyoyin masoya biyu suna ci gaba da harbar juna da addu'a cikin nisa, cikin rashin sani ko Allah zai kawo wata rana su haɗu ko kuwa soyayyar su zata kasance soyayyar da bata da makoma? duk da wulakanci da mugun hali da Halima ke fuskanta a gidan Alhaji Saminu, zuciyarta ta ki rabuwa da sunan Abdullahi. Abdullahi — wanda tun ranar da suka haɗu a hotel din, zuciyarta ta tabbatar da cewa shine mafitar rayuwarta. duk daren da ta kwanta cikin kuka da zubar da hawaye, da ƙaunar da take shirin fashe mata ƙirji, sai ta runtse ido tana kiran sunansa da shiru. "Abdullahi... kai ne mafita ta... amma ka riga ka zama mafarki..." ko da cikin jikinta yana girma, bata daina jin ƙaunar Abdullahi ba. Sai ma ƙara shigewa da ƙara jin saukin duk wani raɗaɗi idan ta ambaci sunansa a ranta. Amma fa duniya bata tsaya jira ba,rayuwa ta cigaba da danne ta a karkashin ƙafa, har ta kai ga lokacin haihuwa ya kure. ranakun karshe da suka rage mata a duniya, wahala ta fi karfin bakinta cikin da ta ɗauka cikin ciwo da azaba ya girma har ta cika da tsoro da fargaba ba wanda ke kula da ita ba wanda ke tambayarta lafiya ko da take ciwo dare da rana, sai Alhaji Saminu ya ce da ita "ke kanki kika ja wa kanki, na gaji da wannan kuka da ciwo ." ba komai ya jawo hakan ba sai sanin cewa tsantsan soyayyar da takewa wani alhali tana da nata auren A karshe, ranar da komai ya ƙare ranar da zatai haihuwa Halima ta shiga wani ciwo da ba a iya kwatantawa, Alhaji na chan hotel yana meeting bai ma san cewa Qatar haihuwar ta ya kama ba. A kwance a ɗakin da aka ajiye ta cikin wulakanci, ba likita, ba uwargida, ba taimako sai kuka da ciwon da ke yawo daga ƙasan jikinta zuwa ƙirjinta yana neman karya ta. Kuka take kamar zata fashe. Tana kiran Baffa, tana kiran Abdullahi, tana neman taimako amma shiru! Abdullahi a lokacin yana cikin wani babban business meeting, yana fuskantar matsin rayuwa sakamakon tarin matsaloli da ya dinga samu tun da ya yarda da zaɓin da iyayensa suka masa. soyayya da Halima ta fara girma masa a zuciyarsa ba ta gushe ba, kullum yana mafarkin fuskar ta, murmushinta, da halayenta. amma bai san halin da take ciki ba. bai san tana shirin barin duniya ba. A cikin tsananin raɗaɗin haihuwa, Halima ta ƙara ruɗewa, ta kurma ihu, ta kifa kanta a shimfiɗa tana ihu kamar rai na fita: "Ya Allah... Abdullahi... Abdullahi... na yarda da ƙaddara..."inda yayi dai dai da shigowar Alhaji sakamakon korar Hajiya nafisa sai dai, kafin a kawo taimako, kafin a kawo likita halin ya lalace ,numfashinta ya fara yanke-yanke. zuciyarta ta yi shiru. Idonta ya tsaya a sama yana kallon wani abu da kowa baya gani, ahankali Halima ta kwantar da kanta gefe, ta saki numfashinta na ƙarshe da kalmar: shahada , ta mutu. ta mutu cikin radadin soyayya. ta mutu cikin ciwon zubar da hawaye. ta mutu ba tare da samun saukin zuciya ba. Bayan rasuwar Halima... Tunda aka sallaci Halima tare da jaririnta da bai samu damar saukar numfashi ba, gidan Alhaji Saminu ya sauya tamkar makoki. duk wata annashuwa da alfahari da yake alfahari da ita a da, ta shige masa ta barshi da nadama da dimuwa. Alhaji Saminu ya dinga zubar da hawaye cikin sirri — hawaye na butulci da rashin amana da ya yi wa baffa Moddibbo, wanda ya amince da shi ya ba shi Halima cikin kwanciyar hankali. yanzu kuma ya gane: ya ci amanar sa... kuma duniya ta rama masa cikin kunya da asara! zuciyarsa ta kasa kwanciya. Ko motsin iska da aka yi cikin gida sai ya tuno Halima ,ya zauna ya shafa kansa yana cewa: "Ni Saminu... ni na kashe Halima da hannu na. ni na lalata amana!" A ɓangaren Abdullahi kuwa, yana zaune cikin ofishinsa ne duka business da meetings ɗin sa suna tafiya, amma zuciyarsa ta gaza samun natsuwa tun ranar da suka rabu a hotel. Ana cikin haka sai ya ga sakon gaggawa daga Alhaji Saminu: "Ina mai baka hakuri, Halima ta tafe gidan gaskiya yanzu ta tafi ta tafe da kuka rashin ka tabbas soyayyar da take ma gaskiya ne ... ta mutu kuma ban cancanci gafararta ba." Zuciyarsa ta buga! Idanunsa suka cika da kwalla. ya dinga kallon sakon kamar zai kira Halima ta amsa masa amma ya sani, babu mai amsawa. "kin mutu Halima?..." Ya fadi da baki a raunane, numfashinsa yana fita da ƙyar. sai wayar ta faɗi daga hannunsa. Gaban mutane sai ya durƙusa. kamar an fasa masa zuciya, dukkan jikinsa ya rikice, gaba ɗaya duniya ta tsaya masa cikakkar shiru. "Halima... Halima... na bar ki cikin wahala, na kashe ki da rashin ƙarfin zuciya ta..." Cikin kukan da bai taɓa fuskanta ba a rayuwarsa, Abdullahi ya fito daga taron ya fice kamar mahaukaci, yana rike kirjin sa da hannuwa biyu, yana kuka tamkar jariri, yana ambaton sunanta. Duniya ta kare masa a wannan rana. ya rasa komai. ya rasa zuciyarsa. ya rasa Halimarsa sai tunanin mafarkinsu na yara ya fara dawo masa. yanda take dariya, yanda take tsoron iska mai kaɗawa... yanda suka tsaya suna kallon juna a hotel ba tare da sun fahimci komai ba — har abada. Abdullahi ya narke kamar karamin yaro yana kuka ,ya rasa inda zai kai zuciyarsa. Soyayyar Halima ta zama masa mafita da karfi. yanzu kuwa... an binne mafarkin sa da soyayyarsa a ƙasa. ƘARSHEN LABARIN HALIMA Bayan rasuwar Halima, kwana biyu kacal sai Abdullahi ya tashi daga gida ya nufi inda aka binne ta , zuciyarsa cike da nauyi kamar dutse mai nauyi, idonsa kuwa har ya kumbura da kuka da rashin bacci. Lokacin da ya isa makabarta, an waye gari — iska tana kadawa, rana na nufar faduwa. kabarin Halima yana can gefe, kamar ba halitta ce ciki ba wsai iska da tsuntsaye. Abdullahi ya tsaya daga nesa yana kallon kabarin — jikinsa ya mutu, zuciyarsa tana sukar numfashi kamar zai yanke, ya karaso a hankali, kafafunsa kamar an daure su ya durƙusa a gaban kabarin, ya dafa ƙasa da hannayensa biyu cikin rawar murya ya fara addu'a: "Ya Allah, ka gafarta wa Halima... Ka sanyata cikin Aljannah tayi ƙoƙari ta zauna da kowa da mutunci ta sha wahala ta mutu cikin rashin adalci. Allah ka mayar mata da jin daɗin da duniya ta hana ta." "Allah ka haɗa zuciyata da ita a lahira idan babu haduwa a duniya." Yana cikin addu'a sai hawayensa suka fara gangarowa ba tare da ya lura ba. Kamar yaro ƙarami ya fashe da kuka mai sauti, yana jijjiga kansa da kafadunsa. mai karatu da kansa sai ya ji zuciyarsa na karyewa — hawaye na sauka daga idonsa. Domin kuka ne na gaskiya, na azaba da soyayya da ba ta sami cikar burinta ba. Abdullahi ya zauna a ƙasa har rana ta fara faduwa. Iska mai kaɗawa tana motsa ganyen kabari. Daga nan sai ya ɗaga kansa sama, yana kallon sararin samaniya da idon da ya riga ya ƙumbura, yana faɗin cikin muryar da ta rame: "Halima... zaki kasance a zuciyata har abada." "kaddarata ta jefa ni nesa da ke, amma soyayyarki za ta kasance kamar numfashina." "Allah ya haɗa mu a wuri mafi alheri." Daga nan ya tashi da ƙyar, yana tafiya daga kabarin da matakin zuciya mai nauyi — ya bar soyayya a ƙasa, ya ɗauki kewa a zuciya. Maryam ta yi shiru na ɗan lokaci, idanuwanta na cike da hawaye waɗanda suka zuba akai-akai. Ihsan ta dafa kafadarta cikin tausayawa—tun daga farkon labarin Halima ta kasa dafa kuka. John, da alama ba zai iya zamewa ba, ya gyada kai da ƙiyayya: “Maryam, me irin labari ne wannan? mai tsuma zuciya, mai ban tausayi… me yasa ta mutu? me yasa ba su haɗu ba daga kallo na biyu suka rabu?” Yazid kuma, wanda zuciyarsa ta yi sanyi ganin halin da ƴan masarautarsu suka tsinci kansu, sai ya sauke ajiyar zuciya, ya ce: “Na yi tunanin zaki ba mu labarin da zai ƙarfafa mana zuciya amma sai gashi kin ba mu labarin da ya tabbatar mana: ba kowane buri ne a duniya zai taɓa cika yadda muke so ba.” "Ƴan uwa na matafiya "suka kalle juna Gaskiya ce: a duniyar marubuta da ’yan wasan kwaikwayo, za a samo labarin da ya haɗa auren jarumai har su cika buri amma a zahiri akwai ƙaddara a soyayya—ba duk buri ne ke cika ba. anan sai Maryam ta miƙa ɗan gajeren labari na gaba, na Ummi: “Ummi maƙobchiyar mu, tun tana yarinya take soyayya da ɗan uwanta. , sun yi rayuwar ƙauna mai ƙarfi ƙaddara bai amince ta aure saba nan ta aure wani daban amma mijinta ya sake ta, ya ci gaba da rayuwarsa ta chigaba da jimammen zawarci duk da haka, soyayyarsu ta ƙarfafa su na shekaru , suka sake ƙulla amana da alkawarin aure … Amman kash ƙaddara bata amince ba Allah bai yardar musu ba nan aka haramta mata auren sa yanzu ta kuma yin wani aure sun zaɓi ɗaya a zuciyarsu, sun ƙebewa junansu ƙauna ta musamman wannan labarin na gaske ne—ba don jin daɗi ba, amma domin mu gane: soyayya na da ƙaddara, kuma ba koyaushe ake samun ƙarshe mai daɗi ba.” sn kasance cikin shiru da tunani, kowa na jin wannan sabuwar hanyar rayuwa—ta ƙauna da raɗaɗi BACK TO STORY zamu chigaba da labarin matafiya guda biyar Maryam ta bamu labarin HALIMATU SADIYA gaskiya ne kaina wannan page ya sani hawaye tabbass soyayya gaskiya ne kuma ba kowane soyayyar bace cikakkiyar. Ihsan ta bamu labarin Princeces Rahilat zamu chigaba da tafiya daga Egypt har Dubai ko da ƙafa ne fans ku shirya wannan shine karshen Bayan wata book one sai mun haɗu a kashi na biyu ******** Alhamdullah Narnah ƙanwar soja ✍️ https://chat.whatsapp.com/FGzLF7OIMEv3GH7wxkyp0p 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 Book two BY NARNAH KANWAR SOJA 💫ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Page 25 / 26 Ganin abun da ya ƙifta kamar aljani ba ƙaramin razanu yayi ba nan suka tsorata da chanza hanya gudun faruwar wata matsalar suna ci gaba da ja da ƙyar cikin wutar sahara, ƙafafunsu sun kumbura, leɓunsu sun bushe sun fashe saboda ƙishirwa. Ihsan na karkarwa a hannunsu kamar ganyen da iska ke bubbugawa. Yazid ya ɗora kanta a kafadarsa, hawaye suna gangarowa daga idonsa, yana faɗin: " ke ƙara juriya, Ihsan... ki tsaya mana Ihsan... muna nan kusa don Allah kar ki rufe idonki..." Amma Ihsan ba ta iya magana sai faman lumshe ido take yi, kamar wacce rai ke shirin ficewa daga jikinta. fuskarta ta juya launin toka, ga zufa mai sanyi na keto mata. Maryam da John sun tsaya daga baya suna kallo, jikinsu yana tsuma da tsoro Maryam ta rushe da kuka tana roƙon Allah: "Ya Allah! Kada ka ɗauke ta! ka taimake mu! Ya Allah... mun yi kuskure amma muna neman rahamarka!" suna haka ne sai can sun hangi wani ƙaramar motar sahara mai tsawo a nesa kamar mafarki Yazid da karfi ya ɗaga Ihsan a bayansa yana gudu da ita duk da raɗaɗin ƙafarsa. Ado da John suka bi da gudu suna kiran taimako. Amma duk inda suka nufo su ne kaɗai a cikin dutsen yashi, babu wanda ke jin ihunsu. motar ta tsaya nesa, tamkar ta hango su... ta kuma juya ta tafi sukayi tsaye a gun, suka faɗi saman yashi kamar duniya ta tsaya. wani irin ciwon zuciya ne ya cika su. Ihsan ta lumshe idonta gaba ɗaya tana fidda wani irin sassanyar numfashi kamar wanda ke bankwana da duniya. Ado ya girgiza ta yana kuka "Ihsan! Don Allah ki bude idonki! Ki dubemu! bamu isa ki mutu a hannunmu ba!" John ya dafa kafaɗarsa yana girgiza kansa cikin kuka "bari ta huta... ta gaji sosai..." Maryam ta rushe da kuka ta faɗa ƙasa tana faɗin: "mun rasa ta! mun rasa Ihsan!! Allah ua karɓi ranmu cikin imani !!" Zuciyar Yazid ta cika da ƙunci yayi azamar daga hannunsa sama, yana roƙon Allah cikin karfi a lokacin ne kuma daga nesa suka hangi wani ƙaramar kungiyar masu agaji masu mashin — suna zuwa da sauri kamar iska! Shin za su iso kafin Ihsan ta mutu? ku kuwa sun makara har abada? ✨ BAYAN WATA ✨ Girgizar yashi na sahara tana ci gaba da rufe su kamar ana binne su da ruwan yashi. rana ta narka musu wuta kamar ana soyasu a cikin kwanon girki. Ihsan ta zama kaman wacce ta rasa rai gaba ɗaya hannunta ya sakko daga kafaɗar Yazid, ta rame, tamkar reshen bishiya da iska ta kifar. Ado da John suna kuka kamar yara Maryam kuwa ta faɗi ƙasa ta riƙe ƙafafun Ihsan tana faɗin: "Allah! Allah ka karɓi ranmu gaba ɗaya! kada ka bar mu muna kallon juna muna mutuwa a hankali!" wani mugun guguwa ya taso daga gabas, yana kawo yashi mai ƙona ido. Cikin idonsu, suna gani ne kamar wani haske yana fitowa daga bayan saharar. amma idon su ya kasa tantance ko agaji ne ko mutuwa ce da ta zo daukarsu. Sun ji ƙarar mota da sauti irin na mashin — da dukan karfi kamar ana fafatawa da lokaci. Yazid ya ta da kansa sama yana kiran: "Munananan!! taimako!!! ku taimaka mana!!! akwai mara lafiya!! ku taimaka mana!!" Motar ta tsaya da daddare kamar an tsaya tsaye da lokaci. mutum biyu suka fito cikin rigunan masu agaji, suna tsala gudu zuwa gare su. dayan ya durƙusa a jikin Ihsan, ya sa hannu yana duba numfashinta sai ya girgiza kai da sauri."Quick! bring the kit! she's in critical condition!!" ya faɗa da sauri da turanci mai nauyi. John da Ado suka tsuguna suna ta kiran Ihsan da hawaye a idonsu. Maryam kuwa ta riƙe hannunta tana ta kuka tana faɗin: "Ihsan... ki dawo... don Allah... kar ki bar mu!" An jefa su cikin wata ƙaramar mota — da gudu suka nufi wani wuri mai nisa. Kowanne daga cikinsu na jin zuciyarsa tana faɗuwa kamar ana yanke igiyar rayuwa daga jikinsu yayin da suka shiga mota, Yazid ya riƙe hannun Ihsan yana kuka yana faɗin: "Ki tsaya mana Ihsan! don Allah ki zauna! Ki zauna har mu kai ki wuri lafiya..." Amma Ihsan kamar wata ran da ke ƙarewa, kawai ta motsa baki kadan ta furta wani abu maras karfi: "Yazid... ka yafe min... idan na tafi... ku cika burinmu......" Motar ta yi ta fizgar da gudu, taya tana huda yashi kamar wata gungurawa cikin ruwan teku a cikin motar, Maryam ta kama hannun Ihsan gam kuka kawai take, hawaye yana zuba kamar an ballo buta. Yazid yana rububin addu'a a zuciyarsa, yana karanta duk addu'o'in da ya iya. Ado ya sunkuyar da kai yana faman kiran "Ya Allah! Ya Allah!". John kuwa ya zamanto gum, shi kadai yana rarrafe a bayan motar, idonsa ya zama jajur kamar wanda aka shayar da hawaye. Bayan tafiyar kusan rabin sa'a cikin saharar mai zabga wuta, suka isa wani sansanin agaji. wani tsohon sansani ne, wanda ƙungiyoyi masu taimako ke amfani da shi a bakin iyakar sahara da Isra'ila. Cikin gaggawa aka kwaso Ihsan da gadonta mai ɗaure da hannu, suka nufi ɗakin tiyata. an duba numfashinta, zuciyarta, suka saka mata ruwan da ake ta tsinkayar numfashi. Maryam, Yazid, John da Ado an zaunar da su a wani ƙaramin daki mai sanyi, a kan katifu na roba una kallon juna cikin shiru, dukka kowa na jin tamkar rayuwarsa na karyewa. Kusan awa guda suka zauna cikin wannan matsanancin yanayi na shiru da damuwa — har sai da wani likita mai dogon hanci da farin fata ya fito yana daure da safar hannu, yana share gumin goshinsa. ya tsaya a gabansu sannan ya dafa kafada Yazid cikin tausayi, ya ce da su da karamin murya: "She's alive... but very weak very... very weak. She needs prayers and strong heart." "ta rayu, amma jikinta yana da rauni ƙwarai. Sai da addu'a da ƙarfan zuciya." gaban su ya faɗi gaba ɗaya. Yazid ya fashe da kuka kamar karamin yaro. Maryam ta rusuna ta fasa da kuka mai ƙarfi, tana ambaton sunan Ihsan kamar wacce ta rasa komai. John ya shafa kansa da hannu biyu, yana jin kamar duniya ta tsaya. Ado kuwa ya dafa bango, yana fitar da iska mai zafi daga zuciyarsa. bayan wasu awanni, suka sami damar shiga dakin da aka kwantar da Ihsan. Idonta a lumshe, numfashinta a sannu-sannu kamar kyandir da wuta ke ƙarewa. Tana sanye da kayan lafiya masu tsafta, an ɗaura mata bandeji a wurin da macijin ya sare ƙafarta. Maryam ta durƙusa kusa da ita tana kuka. Yazid ya riko hannunta yana kuka a bayyane. Ado da John suna gefen gadon, suna addu'a cikin harshen su. Lokacin nan, Yazid ya matso kusa da kunnenta yana faɗin da kukan zuciya: "Ihsan... kin ce burinki mu tsaya tare... kin ce mu cika mafarkinmu... wallahi bazan bari ki mutu ba! wallahi sai mun kai ki Dubai... sai kin huta... sai kin cika burinki...!" Sai hawaye suka kwace daga idon Ihsan, duk da baccin da take yi — karamar murya kawai ta fito daga bakinta: "Yazid... Allah ya saka... da alkairi..." Sai ta sake lumshe idonta da ƙarfi. Jikinta yayi sanyi, har suka dinga firgita ko numfashinta ya tsaya Bayan kwana biyu da ciwo ihsan ta fara samun lafiya sosai domin kumburin ƙafarta yayi sauki hankalin ta ya fara dawowa jikin ta da taimakon ƴan uwan ta musamman Yazid wanda duk cikin su ya fisu tausayi da ban dariya shi kuwa nasani duk lokacin da aka samu matsala tabbas yana taimakawa da barkwanci sa kamar dai koyaushe Ihsan na zaune sun zagaye ta nan suka fahimci wanan filin ba gun tsaro bane domin anan tafka wasu ayyukan sirri ne tsakanin border Jordan da Ethiopia ana tafka ɓarna a kowane lokaci sojojin na iya kawo musu hari a hankali Ado yace " kafin ke ƙara samun lafiya kwana biyu zamu bar gun nan ana safaffarar kwayoyi ko matafiya ne a kowane time bamu da tsaro ammann ku kwantar da hankali ko bare na baku labarin wani masarautar mayaƙa ta zakkar da...". Bai gama magana ba Yazid ya matso " ahh haba ne fa nagama shirri zan baku labarin AlJANNIN SAJIDA idan nagama wani lokacin sai ka bayar da naka mu saurarra " cikin hasala suka fara chachakar kansu akan wazai fara bada labarin Ihsan da tai shiru tana kallon su cikin sha'awa da burgewa nan ta ɗaura da cewa " Ado tunda kaine babba kawai ka haƙura ka barshi next time sai ka bamu " Maryam ta amsa da cewa " kasan Yazid da rigima tsiyar" duk dariya sukaye nan John yace " Yazid filli domin ka ina matukar son labarun aljannu Amman ka tabbatar ba zasu zo mana a Bachi ba duk suka nitsu cikin kulawa da juna da samun nitsuwa Yazid ya ɗaura da cewa " Kar kuyi mamaki wanan Labarin nawa zan gayyamu ku tamkar labarin nawa ne ma'ana zanyi amfani da salo akaina kuma ina tabbatar muku bashi da tsawo domin dai bai kai sauran labarai da ya gabata ba '". Lokaci yayi da Yazid zai bamu labarin AlJANNIN SAJIDA labari ne cikin labari ina fatan zamu chigaba da tafiya cikin kulawar ku let's go Narnah ƙanwar soja ✍️ 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 Book two BY NARNAH KANWAR SOJA 💫ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Yawan sharhin ku yawan typing banyi alkawarin posting kullum ba , mujeee zuwa tafiya ta fara tafiya show me some love guy's 🩷 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على محمد وسلم 26 / 27 Rayuwa tana da ɗanɗano kala-kala wani lokacin kana cikin dariya amma zuciyar ka na kuka, wani lokaci kuma kana cikin shiru ne, amma ranka yana tafasa da ruɗani. Suna na Ishaq ne matashi ne mai matsakaici tsayi da kyau nagarta baƙar fata gari ne A ranar Lahadin nan ne wata ƙawarmu a makaranta, Sajida budurwa ce mai jini a jika a ƙalla tana da shekaru goma sha takwas fara ce fatt kyakkyawar yarinya kowa ya santa da suna baby Sajida ta gayyace mu zuwa bikin zagayowar ranar haihuwar ta ban yi wata-wata ba, na shirya cikin shigar ƙananan kaya wanda suka ƙara min kyau da nagarta ina cikin farin ciki da zuwan wanan ranar domin zamu haɗu da abokan makarantar mu na ɗauki mota na fara ɗauko abokaina guda biyu: Ameer da Abdul “Lafiya lau,” na faɗi a zuciyata lokacin da muka ƙaraso bakin gidan Sajida mun zo da ɗan jinkiri, domin wani abu ya ɗan tsaida mu a hanya amma da alama ba mu makara da yawa ba, domin kowa yana nan, kuma taron yana da ɗimauta. tsoffin fuska da sabbi, 'yan makaranta da 'yan unguwa, iyaye da ɗangi komai yana nan kamar ɗaurin aure idanun mutane sun zuba inda za a yanka cake, amma ban gane me ake jira ba har sai da Sajida ta nufe mu da gudu. “Lalle da babban baƙo!” ta faɗi hakan tana saki murmushi murmushin da na ji tamkar wata ƙaƙƙarfar ƙugiya ce ta ja zuciyata na tsaya cak ina kallonta, sai kuma na ji kaina na mayar da mata daidai murmushin da bata taɓa gani daga gareni ba. Sajida kyakkyawar yarinya ce don kowa ƙon wanda ya rasa Allah ya zuba mata hasken idano tamkar farin wata tsayawar fari ga cikakken tsarin halittar jiki tabbas idan tayi murmushi ko maƙiyanta sai ya tsaya kallon halittar fuskanta “Ina son mu yanka tare cake, kai ne babban baƙo kuma aboki na na musamman ,” ta faɗi hakan a cikin kasalalliyar murya da bata da karyatawa na waiwaya, idona ya haɗa daAbban ta wanda ya girgiza kai alamar amincewa haka nan Umma ta murmushi kawai take yi Abdul da Ameer kuwa sai dariya suke min. Ban san ya akayi ba, sai dai na tsinci kaina da hannu ɗaya na rike wuƙa, ɗaya kuma hannunta muna tare yankan cake shewar jama’a ta kaure, liƙi ya fara kwaranya kamar ruwan sama. Wani abu ya faɗa zuciyata: dhin wani abu ke faruwa a zahiri ne, ko kuwa mafarki ne kawai nake? domin a lokacin, hankali na ya riga ya fita daga jikina. ** Bayan an ci an sha, lokacin da dare ya fara ruruwa ne na ce wa Sajida muna shirin tafiya. amma ita kuma tace, “A'a, sai munje gida ku huta.” na ce: “gidanmu zamu huta mana.” Sai Abdul yayi dariya yace: “kai Bilal, idan kaga gida irin nasu, baza ka ce a tafiya ba.” Gidan ya fito kamar aljanna haske ke fita daga ko ina, kwalliyar da ba a saba gani ba. muka shiga muka zama kamar 'yan ƙauye, duk inda ido ya sauka sai jin kaɗa da ban mamaki. aka kawo mana abinci irin na manya, drinks iri-iri — wato lallai ba wargi ba ne wannan gidan. Bayan mun sha mun koshi, na faɗa wa Sajida cewa muna son tafiya. Tace “to,” sannan ta kira Abbanta domin mu yi sallama. Abban Sajida ya ce, “dama ina son muyi magana da kai, amma yanzu dare yayi. sai ka zo wata rana.” Yace: “kin basu kyautar da nace?” tace: “Na saka mai gadi ya saka musu a boot.” muka ce “nagode” muka fito. Muna fita, Sajida ta rako mu har mota, tace: “Kyautar na ciki, kowa ɗaya.” muna tafiya sai Abdul yace: “Wallahi dole a duba kyautar nan.” Ya buɗe boot — muka ga jaka cike da gwalagwalai da kuɗi dollars ne da wasu kuɗaɗe da ban taɓa gani ba. Zuciyata tayi wani irin nishi, wata damuwa ta fara girgiza ruhina meyasa yasa irin wannan kyauta? me nake nufi a gare su? a haka muka bar maganar a tsakanin mu da alkawarin gobe zamu kuma gidan su Sajida mu mayar musu da dukiyar su nan na ajiye Ameer da Abdul a gidan su . ** Ina kan hanyata gida lokacin da motata ta tsaya chak wurin duhu ne, babu kowa na fito na duba fetur akwai nayi ƙoƙarin tada motar taki tashi kamar wasa. Ina cikin ƙoƙari na kira wani daga abokaina kawai na juya, na hango Sajida a cikin mota. tana min murmushi , da sauri na rintsa ido na domin wanan gizo gizo da take min ya fita a kan ido na , sai dai ganin abun nakiye da gaske itace na rufe mota da sauri na fita zan gudu — na juyo, na same ta a gabana tana nan, murmushi kawai takeyi. wani murmushi ne mai saka zuciya rawa... Ina juya motar, kawai na ganta a mirror tana tsaye a bayan mota sai na ji numfashina ya tsaya... duhu ya mamaye komai. Umma na tana gefena, Ameer da Abdul suna nan zuciya ta kamar an watsa mata ruwan sanyi. “me ya faru dani?” na tambaya da rauni. Abdul yace: “hatsari kayi. wasu suka kira mu a daren jiya amma fa, abin mamaki — kai kaɗai muka tarar a wurin...” Umma na tace: “Sajida ta kira tace a maka ya jiki...” *to, me Sajida ke nufi? Wacece ita a zahiri? kuma me wannan kyauta ke nufi? " Bamuga mutanan da suka kira wayar ba sannan kuma number ɗin da aka kirani da ita private number ce ballantana mu kira muyi musu godiya, umm kuma Sajida tace ayi maka jiki kafin su zo ita da iyayenta ,wallahi , yarinyar hankalinta ya tashi jin halin da kake ciki, sai kuka take yi." Fadar sunan Sajida da Ameer yayi ya sanya na tuna da abin da ya faru da ni a wannan dare. Na faɗawa Ameer dan Allah ya kira Sajida ya faɗamata cewa na sami sauki, kar ta zo. Cikin rashin fahimta, Ameer, Umma sukace, "Haba Bilal, meyasa zakace haka, bayan kuma kana kwance a asibiti? Aikam yakamata tazo domin kasani cewa hankalinta bazai ta6a kwanciya ba muddun batasan halin da kake ciki ba." Nace, "Umma, nifa wallahi, indai sai Sajida tazo asibitin nan ne to a kira likita ya sallameni, gara nayi jinyata a gida." Umma tace, "to, wai maye matsalar ne?" nace, "Babu komai." Nan Ameer ya kira number Sajida, amma abin mamaki, wayanta a kashe, wanda tunda nake da ita ban ta6a ganin wayarta babu chaji ba. maye mai zaisa wayanta a kashe? a zuciyata nace, "Lallai akwai abinda yake shirin faruwa." Na juya na kwanta, ina tunanin shin yanzu idan Sajida tazo nan da wanne irin siffa zatazo kuma da wanne kudiri zatazo? Drip ɗin da aka sanyamin ya ƙare, hakan ya sanya Ameer ya kira doctor domin ya sakamin wani , likita tana shigowa tayi sallama, muryan Sajida naji hakan ya sanya na juyo da sauri kawai nayi arba da Sajida cikin kayan likitoci. Idanuwana suka zaro, zuciyata ta buga da ƙarfi duk da ciwon da yake jikina, na zabura na nufi kofa a guje. Ameer da Umma suka kamoni suna lafiya!!! lafiya!!! lafiya!!! nikam inata buɗe baki amma nakasa magana inata nuna Sajida da hannu. Umma tace, "Likita ce fah, nikam Sajida kawai nake gani." Tanata matsowa kusa da ni, hakan ya sanya na suma. Abinda ya tayarwa Umma hankali matuka, ta fashe da kuka tana cewa, "Ɗana Sameer , Allah baka lafiya, Allah yasa ba ta6in hankali ka samu ba." Bayan na suma ne sannan Sajida da iyayenta suka zo asibitin sun gaisa da Umma, sannan ta faɗamusu cewa anyimin alluran barci ne saboda na sami hutu sai zuwa dare zan farka. Sajida ta bukaci cewa ita iyayenta subarta a asibitin har sai na farko taga halin da nake ciki, sannan zata tafi idan ta kama ko kwana zatayi ban farko daga dogon sumar da nayi ba sai 12:45 am. Ai kam ina farkawa, nayi tozali da fuskan Sajida, tanata kallona, fuskarta cike da hawa. Inayin arba da ita na ƙwalla wani ihu mai razanarwa, hakan ya sanya Umma ta farka a tsorace, itama kanta Sajidar tayi zunbur kamar zata ruga. Umma tace, "meya sameka?" Abin mamaki a wannan karon bakina ya buɗe, ina iyayin magana amma sai nayiwa Umma karyar cewa, "Mafarki nayi, wasu mutane suna bina zasu kasheni." Umma tace, "ai mafarki ba gaskiya bane, yanzu kayi addu'a ka koma ka kwanta." Washegari, Sajida taje gida ta kawomana breakfast mai rai da lafiya, mukaci nikam, itace ma take bani a baki. Haka ta dinga dawainiya da ni har kwana 12 tukunna aka sallame ni, muka koma gida. A daren ranar da muka koma gida misalin 1:00 am, hadari ya taso sosai, anata walkiya da tsawa mai ƙarfin gaske. kawai sai aka ɗauke NEPA, sai naji kofar ɗakina tana buɗewa tamkar wani ne zai shigo cikin ɗakin. a tsorace nace, "waye? shiru shiru?" Na laluba wayana domin haskawa, nagani ina ɗauko wayar na kunna fitila, sai naga Sajida a gefen gado kusa da ni. 6angaren hagu na juya 6angaren dama, nasake ganinta, na ƙwalla uban ihu, nayi tsalle na sauka daga gadon, na nufu kofar ɗakin da nufin na fita na ruga wurin Umma. Kofar ɗakin ta kulle, sai ji nayi wata murya tare da amsa kuwwa, tana cewa, "haba masoyi, ni kake gudu, nice fah, Sajida, Sajida, Sajida." Kawai naga ta zama kusan kashi goma ko ina a bangon ɗakin, itace wata tana kiran sunana, wata tana kiran nice Sajida, wata kuma tana cewa, "Ka rabi da Sajida domin kuwa matar sarkin mu ce, hhhh hhhh hhhh." Jinayi kaina yana juyawa, naga ƙofa ta buɗe, a guje na nufin kofar da nufin nabar ɗakin, kawai sai naga wata mace da fararen kaya, babu kai a jikinta kuma ita bata sama bata ƙasa take na faɗi ƙasa a sume. Iskan da ke kadawa ne gami da sanyi suka sanya na farka daga sumar da nayi a hankali na buɗe idanuwana domin zuciyata cike take da fargabar zan sake ganin wannan hallita. Abin mamaki a wannan karon banga komai ba, da ƙyar na samu na mike a hakanma ina dafa bango domin a wannan lokacin jikina babu ƙarfi haka na koma cikin ɗakina na fasa zuwa ɗakin Umma na domin bana son hankalinta ya tashi idan tasan halin da nake ciki. na dauki wayana ina duba time sai naga ashe har 2:00, nayi addu'a na tofa ko ina sannan na kwanta zuciyata cike fargaba. Bansan lokacin da barci ya sace niba, jinayi ana tashina Ishaq ka tashi kayi sallah yau kam wanne irin barci ne kakeyi haka? a hankali na buɗe idanuwa na "Umma" nagani tace yau kam wanne irin barci kakeyi har rana ya fito bakayi sallar asubahi ba. "Umma" idan kayi sallar sai ka fito ga breakfast na haɗamaka" , ta juya ta fita haka na tashi nayi sallah sannan nayi brush sannan na fito mukayi breakfast sannan nayi mata sallama na wuce kasuwa. Bayan na shiga mota na fara tafiya jinayi wayana tana ringing, ina dubawa kiran SAJIDA nagani take jikina ya fara karkarwa tamkar wanda ya fito cikin ruwan kankara, wuri na samu nayi packing sannan na fara tunanin shin na daga wayar ko a'a. Haka dai nayi ta maza zuciyata tana dukan uku-uku na daga wayar, muryar mahaifin sajida naji yacemin" yaya jikin naka" ? na amsa da " jiki kam yayi kyau tunda yanzu gashi har na fita kasuwa. " Alhamdullah tunda yanzu kaga ka sami lafiya yau idan ka tashi daga kasuwar sai kazo gida mu tattauna maganar mu, ji nayi gabana ya faɗi zuciyata ta buga da ƙarfi kaina yamin nauyi domin naji ya ambaci zuwa gidansa, nayi shiru daga chan sai nace to Abba in sha Allah zan zo, amma yanzu da safe yakamata na zo saboda bana son yamma yamin ballantana kuma dare. Ya amsa da shikenan sai ka zo, nikuwa haka na juya motana na nufin gidan su sajida jim kadan na isa, ina shiga na tarar an hadamin abinci iri-iri tamkar za'a tarbi wani babban basarake ko shugaban ƙasa. Abba yamin izini da na zauna sannan yamin nuni da na fara cin abinci tukunna sai muyi magana, nayi breakfast kafin na fito na faɗawa "Abba ni yanzu a koshe nake, "haka dai Abba ya matsamin dole naci kadan daga cikin abincin. Bayan na kammala sannan Abba ya tara iyallan yayi gyaran murya " nasan bakasan dalilin da yasanya nake nemanka ba"? , nace eh Abba gaskiya bansani ba sannan kuma zuciyata cike take da son jin abinda zaka fada." " Ishaq na zauna nayi nazari gami da tunani ganin irin shakuwa da Aminanan taka da tausayin juna da yake tsakanin ka da Sajida. wanda yanzu har kun zama tamkar yaya da kanwa, to ne da Umma SAJIDA mun yanke wani hukunci. Wanda zan fadamaka a yanzu amma kamin alkawarin cewa zaka kar6i abinda muka zo muku da shi domin kasan bazan cutar da ku ba". Maganganun Abba sun sakani cikin rudani gami da wani dogon tunanin daban, shin maye Abba ya yanke a kanmu? Yanzu idan namar alkawari kuma ya faɗi abinda bazan iya cikawa ba fa. Haka na faɗawa Abba cewa nayimaka alkawari domin bazan iya musu da maganarka ba 'Abba" domin kana bani kulawa tamkar uba agareni duk abinda uba zayyiwa Ɗansa kanamin bazan iya butulci agareka ba." Abba yayi murmushi sannan yace Allah yamaka albarka, dama ba wani abu bane face ina son ka auri Sajida mikewa nayi zunbur tamkar wanda aka sanyawa shocking da lantarki muka hada ido da SAJIDA ta sakarmin wani tattausan murmushi sannan ta sunkui da kanta . Abba yayi murmushi " zauna mana ai dama nasan dole zakaji mamaki gami da farin ciki marar musaltuwa amma kuma ba abin mamaki bane, duba da duk abinda sajida take so to muma muna son shi. Yanzu ina son ka turo iyayenka domin muyi magana gemu da gemu bana son auren ya wuce 2 weeks," nikam tuni na fada cikin dogon tunani gami da damuwa wacce ta gagara 6oyuwa a fuskata. Ganin damuwar da take kan fuskata 'Abba" yacemin kar ka damu domin duk dawainiyar auren ni zan dauka bana son ka kashe ko naira ɗaya, Allah sarki shi a tunaninsa wannan ne damuwa ta. Nikam tunanin maganar aljanun nan ce ta faɗo a zuciyata da tunanin abinda zai faru da ni muddin akayi wannan auren, ni babban abinda yafi dawuna shin maye tsakanin "SAJIDA" da sarkin aljanu shin, aljanna ce ko bil'adama? Tabbas kyawun ta ya kai yaja hankalin duk wani ɗa namiji sannan kwalliya tsafta gami da iya ado, ni kaina ina jin kaunarta a cikin zuciyata amma tsoron abinda zaije ya dowo shine a cikin raina. " Ni zan wuce domin ina son na tafi kasuwa kar na makara " na faɗa masu mukayi sallama sannan na fito abin mamaki wannan karon batamin rakiya ba bayan na fito na wuce kasuwa. Ban iya aikata komai ba a kasuwar sai tunanin na saka wancan na warware wancan hakadai har lokacin tashi yayi sannan na rufe shago na wuce gida. Ina shiga gida Umma na tarar a falo tana karatu nikam sai na zauna na jirata har ta kammala sannan na faɗamata cewa ina son muyi magana, wacce magana ce wannan ɗana Umma tace ai da ka bari idan ka watsa ruwa sannan ka ci abinci ka huta sai muyi maganar. " Aa idan da hali muyi maganar yanzu to shikenan ina saurarenka." Na kwashe duk yadda mukayi da iyayen Sajida na faɗamata ALHAMDULILLAH "ummm" tace abinda na dade ina mafarki abinda na dade ina jira abinda na dade ina yiwa tanadi yau kam gashi Allah ya kawomu. 'Umma" tace yakai ɗana guda ɗaya tilo kasani cewa na Dade ina jiran wannan naga kayi aure domin ka zama cikakken mutum sannan naga jikana, lallai kam yau ranar farin ciki ce a garemu dan haka gobe tun safe zan tafi gidan kawunka Alh 'labaran"suje a tsayar da magana. Nikam yaƙe ne yake bayyana a fuskana domin bana son Umma ta fahimci akwai wani wanda yake damuna, yanzu ka shiga ciki ka watsa ruwa sannan kazo mu ci abinci. Bayan mun ci abinci mun kammala sannan mukayi fira da ita sosai tace " kasan fa ranar bikin nan naka duk da tsufana dole nayi rawa na chashe" Duk da ina cikin damuwa bansan lokacin da dariya ta kamani ba gami da jin kunya, nace ummana gaskiya ina alfahari da ke kuma lallai ko bayan nayi aure bazan iya barinka ba dole gida ɗaya zamu zauna. " Nan dai mukayi fira sosai har dare yayi sannan 'umma" ta wuce ɗakinta ta barni a falour nikam sai na dauka wayana ina buɗe data sakon sajida ne ya shigo wayana Kamar haka: Angaishi da autan samarin duniya ina fatan ka isa gida lafiya? gaskiya nayi sa'ar kasancewata zan zama mata a gareka burin da yadade a cikin zuciyata yau gashi Allah zai cikamin shi. Duk da baka ta6a furtamin kalmar so ba amma sai dai naga hakan a cikin idanuwanka sannan naji hakan a cikin bugawar zuciyarka, Kamar yadda nima na gagara fadar hakan a gareka yau kam zan fada. Ni 'sajida" Ina son ka ina kaunarka sonka ya riga yayi nisa a cikin zuciyata ta yadda bazan iya rageshi ba ballantana har na iya cireshi, dan Allah ina son ka zama garkuwa a gareni kazama uban 'ya'yana ka kasance tare da dani a kowanne irin yanayi, da wannan nake maka sallama masoyina bissalam ka kulamin da kanka. Babu zato ba tsammani kwatsam sai naga wani sako ya shigo wayana Kamar haka: yakai bil'adama shin ashe bakaji jankunnan mu a gareka ba ashe taurin kai ne da kai. Tabbas Auren SAJIDA a gareka tamkar tamkar ka sayi tikitin yin bankwana da farin ciki zaka kulla alaƙa da bala'i da masifu a rayuwarka, domin kuwa tun daga ranar da aka haifi Sajida" ta zama mata a gareni kuma nayi alkawarin babu wani bil'adama komai hatsabibanci shi da ya isa ya aureta take wayar tawa ta fara ci da wuta a tsorace nayi wurgi da ita ta window ɗin da yake a falon. Lekawa nayi window ɗin ina hangen wayar a haka har ta ƙone kurmus sannan naga wannan tokar ta tana rikidawa ta zama wata siririya tamkar igiya sannan tana mikewa a hankali take naga ta zama wani siririn aljani mai siffar ban tsoro. Wannan aljani yana da munin siffa kwarai da gaske idanuwansa jajaye ne tamkar garwashin wuta sanan ya wangame bakinsa yamin wata mahaukaciyar dariya yana dariya bakin nasa yana kara girma, sannan ya tsuke bakinsa ya murtuke fuska idan kaga fuskarsa saboda tsabar muni sai zuciyar mutum ta tashi har yayi amai sannan ya nunani da hannunsa wanda yake da wasu yatsu zaro zaro wanda duk iyakar kallon kurillar mutum bai isa ya irga adadin yawan yatsun wannan aljani ba. Kunbunansa kuwa suna da tsayi sannan ga tsini tamkar karamar takobi, sannan wannan aljani ya gyara tsayuwa ya rike kugu yana kallona, nikam addu'a kawai kawai nakeyi a cikin zuciyata wani lokacin ma bansan maye nake karantawa ba saboda tasanin tsoro abinda yabani mamaki shine yin arba da wannan aljani amma zuciyata ta dake har haka. Kwatsam sai gani nayi wannan aljani yayi wata girgiza sannan naga yanata chanja halitta daga Ƙarshe sai naga yazama guguwa wannan guguwa tayi sama tun ina kallonta har ta 6ace 6at jim kadan sai ganin nayi wayata ta faɗo a dai-dai wurin da wannan aljani ya tsaya, na kalli wayar nan sosai naga tabbas wayata tace wacce ta kama da wuta kuma abin mamaki babu abinda yasami wayar, tsoro ya hanani fita ballantana na iya daukar wayar. STORY BY Iliyasu Falalu Lawal WRITTEN BY NARNAH ƘANWAR SOJA https://chat.whatsapp.com/Bd1Zu1cwIO81A7rrATd4Cu 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 Book two BY NARNAH KANWAR SOJA 💫ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Yawan sharhin ku yawan typing banyi alkawarin posting kullum ba , mujeee zuwa tafiya ta fara tafiya show me some love guy's 🩷 بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على محمد وسلم Page 28 / 29 18**5**2025 " Yakai masoyina abun alfahari na kuma uban 'ya'yana lallai yanzu haka ina cikin fargaba da tashin hankali wanda bazan iya musaltawa ba domin kuwa a yanzu haka nayi wani mummunan mafarki wanda hankalina ya tashi matuka duk da nasan cewa mafarki ba gaskiya bane amma hankalina ya gagara kwanciya zuciyata ta kasa samun sukuni dai-dai da second ɗaya. Wannan dalilin ne yasa na kiraka a cikin wannan daren namaka kira babu adadi amma bakayi picking call nawa ba Hakan ne ya saka zuciyata ta sake karaya matuka bacci ya kaurace a idaniyata hankali ya gushe daga kwakwalwata nayi kokarin bare zuwa safiya ya gaggara Dan Allah idan kaga wannan sakon nawa kamin reply domin tabbatar da lafiyarka, kasani cewa bazan iya barci ba idanuwana zasu kasance suna kan screen wayana har sai naga sakonka." Babban abinda yabani mamaki dukkan abinda ya faru tsakanina da wannan aljani shine ta fadamin cewa tagani a mafarkinta sannan ta faɗamin cewa lallai idan bataga kirana ba ko sakona to gari yana wayewa zatazo har gidan mu da safe. WASHEGARI Ina gama karanta sakon kenan Horn ɗin mota naji a bakim gate a zuciyata nake fada kar dai yarinyar nan da gaske zuwa tayi. Lallai kam nasan ƙaramin abu ne a wurinta haka na fita nazo ina buɗe gate ba kowa na gani ba sai "sajida" tana ganina tayi wani lallusan murmushi nikam na mayar mata da yaƙe domin ni yanzu tsoronta nakeji matuka haka na buɗe gate sannan ta shigo ta gyara parking. Na kai hannu zan buɗe mata marfin mota amma sai tace haba ba girmanka bane ai nice zanyi hakan a gareka, nace haba kekuwa ina girma ga mijin hajiya mijin gimbiya ai idan ina tare da ke to bana da wani girma face girmanki. Dan haka idan munyi aure ni zan zama driver a gareki, kukun ki, ɗan aiken ki, a taƙaice dai ni zan zama hadiminki. Tayi murmushi tace kaikam kace zolaya ba kowa a gidan ne Sajida" ta fada naga kai ɗaya nagani kuma naji babu wani motsi a gidan eh nace domin "umma" ta fita kuma dama kin san mu biyu ne a gidan. " Alhamdullah" Sajida ta fada yanzu sai mu shiga ciki muyi magana domin magana tana bukatan jin haka yasa zuciyata ta buga da ƙarfi idanuwana suka zaro naji tamkar andauki guduma an bugamin a kirjina, domin gani nake tamkar idan dai har muka shiga gidan nan da Sajida to lallai komai zai iya faruwa da ni. Murya na tana rawa nace haba kekuwa kinga cikin gidan babu kowa bai kamata ace mu shiga mu kebe daga ni sai ke kinga mu ba mata da miji ba kuma Annabi {SAW} yace matukar mace da namiji zasu kebe ba muharraman juna to lallai shaidan zai kasan ce na ukun su kuma kinga mutane da zargi bana son wasu kananan maganun su dinga yawo a kanmu. 'Sajida" tayi murmushi sannan tamin wani irin kallo cikin alamun mamaki tace ashe baka yarda da tarbiyyar da iyayen mu suka bayar a kanmu ba ashe kana tunanin zamu iya cin amanar junan mu? cikin sanyin murya nace haba sajida ba haka nake nufi sam kafin nagama rufe tayi charaf tace to indai hakane mu shiga ciki muyi magana. Tana gama fadan hakan ta kunna kai ta nufi cikin gidan tana murmushi ko waiwaye batayi, nikam cikin Alamun sanyin jiki da fargaba nabita a baya. "Sajida" tana shiga ta nemi wuri ta zauna sannan nima na shigo nace to bari na kawomiki kayan breakfast tukunna, tace a'a nayi breakfast a gida tukunna na fito nace duk da haka to bari na ɗan kawomiki ko ruwa ne kinsan bakonka Annabinka "Sajida" tace au ashe kallon baƙuwa kakemin? Nayi murmushi sannan na wanyance nace ba haka nake nufi haba ai ni da ke mun zama abu ɗaya kawai dai naga kin sha tafiya ne shiyasaka kuma ma kinga idan baki ci komai ba ai ba zanji daɗi ace kinzo har gidan mu baki ci komai baki sha komai ba. "Sajida" tace ni yanzu ba wannan ne damuwana ba nazo domin duban lafiyarka domin jiya nayi wani mummunan mafarki a kanka wai ma tukunna ina kasaka wayanka?. Tun a lokacin da na farka daga wannan mummunan mafarki ban sake runtsawa ba hankalina bai kwanta har sai yanzu da nake tare da kai shin baka kirana ba da kuma saqonnina "sajida" tace. Nikam sai na wayance na faɗamata cewa lallai banga sakonta ba kuma banga kiranta da yake jiya nasha aiki a kasuwa na dawo gida da gajiya barci ne mai nauyi ya saceni yanzu haka kinga wayan can a chaji bari na dauka na duba sakon naki, a'a barshi kawai ba bukata" ta fada ka zauna kawai sai na fadamaka abinda yafaru da kai a cikin mafarkin ko nace ya faru da mu. Sajida ta kwashe dukkan abinda ya faru tsakanina da wannan aljani ta faɗamin tabbas babu abinda ya rage wanda yafaru tsakanin da wannan aljani wanda sajida bata fada ba, nayi mamaki matuka sannan tace shin da gaske a daren jiya hakan ya faru agareka kokuwa dai kawai mafarki ne take tambayana. Naja dogon numfashi sannan na kalli fuskanta naga lallai tana cikin damuwa kuma idan na faɗamata cewa wannan mafarkin gaskiya ne zata shiga tashin hankali yarinya ce wacce bata son damuwa ko tashin hankali kokadan kawai sai na wayance nayi murmushi nace haba Kekuwa masoyiyata tabbas wannan mafarkin naki ba gaskiya bane ai babu wata halitta da ta isa ta rabani da ke walau ko dabba ke har aljan fadan hakan ke da wuya naji wani abu tamkar guduma ya daki kirjina faɗowa nayi daga kan kujerar da nake nayi taga-taga Sajida ta tallabeni tana fadin lafiya maye ya sameka? A tsorace nace babu komai da ƙyar na koma na zauna kan kujera ina numfashi sama-sama a wannan lokacin jinake tamkar zuciyata zata fito daga kirjina tsabar zafin wannan duka da kuma fargaba da razana wanda suka addabi zuciyata, hakanan nake ƙarfin hali saboda ina tare da ita bana son ta fahimci halin da nake ciki sannan na fadamata cewa yakamata ta tafi gida tunda ta tabbatar ina lafiya kuma mafarki ne ba gaskiya ba sannan nima ina son zan fita kasuwa babu wata kasuwa da zanje kawai dai na kosa ta tafi saboda wallahi a wannan lokacin tsorace nake gani nake tamkar kasancewa da ita zai iya zama barazana ga rayuwata da kuma lafiyata. "Sajida" tace bana son rabuwa da kai ko na second ɗaya amma yazama dole babu komai idan da rai da rabo ai saura kiris ka zama nawa mallakina, ni yanzu zan wuce idan na isa gida zan kiraka. Mukayi sallama da "sajida" ta wuce. Na dauka wayana na kira Abdul lallai yazo gida akwai matsala ina cikin damuwa da tashin hankali, ganinan zuwa "Abdul" ya fada da Ƙyar na tashi na shiga ɗakina sannan na kwanta ina numfashi sama-sama ina jiran zuwan Abin mamaki sai barci ya saceni. Kiran sunana naji anayi tamkar daga sama buɗe idona ke da naga abinda yabani mamaki kuma ya tayarmin da hankali matuka Abdul nagani a tsaye fuskarsa cike da mamaki da takaici yana tambayana " shin maye ya kawo Sajida ɗakin ka? ". Ina dubawa naga lallai"Sajida" ce a gefena tana barci abinta fuskarta cikin da annushuwa nayi zumbur na mike na sauka daga gadon ina goge idanuwana a tunanina mafarki nake sannan na fahimci cewa lallai ba mafarki bane gaskiya ne. Zuciyata ta cika da sake-sake da tambayoyi wanda bana da amsar su sannan da tunanin tayaya zan fahimtar da Abdul abinda yake tunani ba haka yake ba, ina cikin wannan tunanin ne ta farka cewa take " haba masoyi gaskiya ya munajin daɗin mu zaka tashi ka barni kakuwa san yadda naji daɗinka gaskiya kaidin na mussamman ne ashe haka kake da kwarewa gaskiya idan mukayi aure zanji daɗi sosai, a tsorace na kalli cikin idanuwanta naga tamkar wacce ta sha cocaine hakan yasanya na tabbatar da cewa lallai ba "Sajida" sannan ta dago kanta ta kalli Abdul au Abdul ne mara da babban baƙo "sajida" shikam tsaki yayi sannan ya juya cikin fushi ya fita yana fadin lallai Ishaq kabani mamaki wallahi ban ta6a tsammanin haka daga gareka ba Ashe kai fasiki ne mazinaci wallahi yau da ace wani ne ya fadamin cewa ka aikata hakan wallahi sai inda ƙarfina ya ƙare domin na yarda da kai fiye da yadda na yarda da kaina. Amma abin takaici da idona naga wannan mummunan alaƙar kuma abin takaici da yarinyar da zaka aura wacce iyayenta suka yarda da kai kaji kunya Ishaq dan haka daga yau babu ni babu kai kaga tafita. Ya juya yafita daga falon nikam inata binsa ina "Abdul Abdul" dan Allah ka tsaya ka saurareni ko juyowa bayyi ba nabishi har gate kawai ya tarbi abin hawa ya tafi idanuwansa cike da ƙwalla, ya tafi ya barni cikin dimuwa tashin hankali da rashin sanin abinda yakamata nayi. Na duka tsakar gida inata kuka gami da tunanin abinda yakamata nayi, ina cikin wannan halin ne dariya naji mai kama da sauka aradu a tsorace na dago fuskata ba kowa nagani ba sai "sajida" itace take mummunan dariya mai cike da sanya fargaba da tashin hankali sannan tayi wata girgiza take naga ta zama wannan aljanin da yazomin a daren jiya. Ya fara da cewa " yakai bil'adama mai taurin kai da rashin kunya lallai bakasan sharrin mu ba kasani cewa zan sakaka cikin tashin hankali dimuwa da bala'i wanda baka tsammata ba, nasani cewa yanzu zuciyarka tana cike da tunanin yadda zaka shawo kan "Abdul" lallai bazaka iya ba domin nayi nasar rabaku har abada, kuma wannan ba komai bane daga sharrina zan rabaka da dukkan farin cikinka wanda zaka gwammace mutuwa da rayuwa Zan jefa rayuwarka cikin masifa bala'i da jalala lallai tashin kiyamar rayuwarka zai zo tare da hisabinka batare da ka mutu ba. Sannan ya sake kyalkyalewa da wannan mahaukaciyar dariya ya 6ace. Da Ƙyar da rafe da bin bango na koma cikin falo sannan na faɗi ƙasa a falon ina shiga ɗakina amma abin ya faskara take na fita hayyacina sai dai farkawa nayi naganni a gadon asibiti kokadan banyi mamakin ganina a wannan hali ba domin kuwa abinda ya faru dani kamata yayi kawai na farka a kabarina ina ganin sai nafi samun kwanciyar hankali da nutsuwa. Ummana ce kawai a tare da ni banga "Ameer" ba ko sauran dangina shi daman "Abdul" nasan ba lallai yazo ba ita kuwa ummana kuka kawai takeyi, ganin hakan ya sanya nayi tunanin shin kodai "Abdul" ya tonamin asiri ne lallai idan 'Abdul" yamin haka yaci amanata. Cikin sanyin murya gami da tsora nace "umma" kukan maye kikeyi firgigi "umma" ta dago kai jin muryata tace ALHAMDULILLAH ashe zaka tashi ai har mun cire rai da rayuwarka yau satinka 4 baka ko motsi ballantana muyi tunanin tashinka. Likita ya tabbatarmin cewa lallai saidai tsanin rabo tashinka domin rayuwarka tana cikin tashin hankali kadan ya rage zuciyanka ta buga saboda abubuwa sunyi yawa a cikinta ya bukaci sanin maye yake damunka nikuma ban sani ba. To amma ya fadamin cewa lallai idan Allah yasanya ka tashi yakamata musan damuwar ka sannan a kiyaye dukkan abinda zai 6atamaka rai, ni da uncle ɗinka mun zauna mun yanke wani hukunci wanda muke da tabbacin tabbas zai faranta ranka fiye da yadda ake tsammani zai kore duk wata damuwa da take damunka, amma yanzu idan mukaje gida zakaji koma maye. Cikin ƙarfin hali nace to amma ya naga babu kowa a tare da ni sai ke kadai kodai wani abu ya faru ne?, "Mama" tace a'a babu komai ai "Ameer" yanzu yabar nan uncle ɗinka ma ɗazu da safe yazo ita kuwa "sajida" nan take wuni yanzu ma taje karbomin wani Sako ne, amma abinda yabani mamaki ace duk wannan dadewa da kayi a kwance yaron nan "Abdul" baizo ba shin kodai kayi masa wani abu ne?. Nayi charaf nace a'a Umma wallahi babu abinda nayi masa ta yuwu ayyuka ne suka mishi yawa kokuma dai wani uzurin, murmushi tace har kayi wannan kwanankin kana asibiti rai hannun Allah baizo ba sannan kace wani uzuri ai ince ko bangon duniya yake a abotar da take tsakanin ku wacce ta rikide ta zama 'yan uwantaka yabar duk abinda yake yazo, kawai dai akwai abinda yake faruwa tsakanin ku wanda kake 6oyemin yanzu dai mu bar wannan maganar ga abinci kaci nasan kana jin yunwa. Umma tabani abinci da hannunta naci abincin sosai har na ƙoshi sannan muka cigaba da fira da ita har dare ya fara, kwatsam muryan "sajida" naji tayi sallama abinda yabani mamaki kenan tana shigowa ta tarar dani a farke " ALHAMDULILLAH naji ta fada ashe ka farka ashe rabon zan sake ganinka ashe da rabon zanyi rayuwar aure dake Ashe kafin ta faɗi abinda zata fada "Umma" tayimata nuni da tayi shiru. Nikam jin wannan kalaman nata suka sakani mamaki da tunani da kuma tunanin maye zata fada Umma ta katseta. Nace "SAJIDA" tace na'am " shin maye yasakaki zuwa asibiti yanzu ashe bakiga dare yayi ba yakamata ace kin bari sai da safe ai, tunda kinga ke mace ce bai dace ace kinayin yawo haka ba, Sajida " tayi dariya tace ai yanzu zan tafi gidan dama nazo ne kawowa 'umma" sako sai kuma nayi dace na tarar da abin farin ciki. " Ni yanzu zan wuce amma in sha Allah gobe da safe zan dawo, nace to sai da safe domin kuwa a wannan lokacin na matsu ta tafi gani nake tamkar wani abu zai sake faruwa da ni mukayi sallama ta tafi." Bayan kwana 2 likata ya sallameni sannan yace nayi kokarin cire damuwa a raina sannan duk abinda zai 6atamin a kiyeyeshi, muka koma gida kullum "Umma" burinta farin cikina duk abinda zai sakani farin ciki shi "umma" takeyi rannan sai na tambayeta akan ta faɗamin maganar da suka yanke ita da uncle tace nabari sai gobe da safe uncle dina zaizo zanji koma maye, nikam na kosa gari yawaye domin jin wannan abin farin ciki. Washe gari da sassafe sai ga uncle "labaran" yazo gidan mu a nan yayi breakfast bayan mun kammala sannan yace Ishaq a matsayin mu na iyayenka masu kaunarka masu son ganin farin cikinka tabbas wannan abin da yake damun zuciyanka wanda bamu san dalilin wannan damuwa taka ba, kai kuma ka gagara fadamana gashi abin har yana neman rabaka da rayuwarka, to ka sani cewa mu bazamu matsamaka dole sai ka fadamana ba amma dai mun zauna munyi nazari akan abinda zai kawo mafita da farin ciki na har Abada a rayuwarka. Ishaq idan baka manta ba kafin ka kwanta wannan rashin lafiyar aban "Sajida" ya baka auren 'yarsa wacce har naje mukayi magana akan auren ku nace hakane "uncle". To kasani cewa munyi nazari munyi hasashe ni da mahaifiyarka da kuma Abban ita "sajida" ɗin mun tabbatar da cewa aureka da ita shine kawai zai sanya farin ciki a rayuwarka da kwanciyar hankali wannan dalilin ya sanya lokacin kana kwance a asibiti aka daura aurenka da "sajida" a lokacin da mahaifin nata yasanya tun kana da lafiya ba'a chanja lokaci ba. A taƙaice dai yanzu sajida matarka ce dama mun bari idan Allah yabaka yabaka lafiya sai ayi biki sannan ku tare sannan mahaifinta yace zakaje a nuna maka gidajensa ka za6i wanda yayi maka domin ku tare kai da amaryarka. Innalillahi!!! innalillahi!!! innalillahi!! Na fada har sau uku domin kuwa na fita cikin hayyacina a wannan lokacin sannan na dora hannuna akai ina fadin " shikenan kun kasheni wallahi nasani yau bazan kwana ba saidai cikin kabarina nasan bazasu barni ba, suwaye fadamana "ISHAQ " lafiya kake kuwa kodai ka sami ta6in hankali ne?" STORY BY Iliyasu Falalu Lawal WRITTEN BY NARNAH ƘANWAR SOJA ✍️ https://chat.whatsapp.com/Bd1Zu1cwIO81A7rrATd4Cu 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 Book two BY NARNAH KANWAR SOJA 💫ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Page 30 "Tabbas lafiya na kalau amma abinda kuka yanke kuke tunanin shine zai sakani farin ciki to lallai kunyi kuskure, lallai hakan da kukayi tamkar kun nisantani da farin ciki ne tamkar kun salwantar da rayuwta ne lallai ina da tabbacin cewa Ƙarshen rayuwata yazo. Cikin damuwa da rashin fahimta "Umma" ta kamani ta zaunar dani nikam a wannan lokacin jikina rawa kawai tamkar wanda aka sanya cikin kankara sanna tace Ishaq " bamu fahimci duk wannan sambatun da kakeyi yakamata kayimana bayani abinda yake faruwa. Na kwashe labarin duk abinda yake faruwa na faɗamusu hatta rabuwar mu fa "Abdul" Umma" ta tsorata sosai da jin wannan labarin kuma jikinta yayi sanyi matuka hatta shi uncle "labaran" " tace lallai yakamata a nemi mafita domin ni bazan bari rayuwar ɗana guda ɗaya tilo ta salwanta ba, lallai ko raba auren idan takama dole ayi. Uncle "labaran" yace dole a nemi mafita amma lallai babu maganar raba aure akwai wani malami wanda yake garin maiduguri lallai ya kware wurin fitar da aljanu komai taurin kan wannan aljani dole ne zai fita ya barku kuyi rayuwa da matarka. Bayan kwana biyu mukaje gidajen Abban Sajida aka kewaye da mu ni da ita gidaje ne sun wuce 150 har sai da muka gaji da yawa sannan dai muka za6i wani guda ɗaya daga ciki, sannan aka kirawo wannan malamin yayi addu'o'i da rukiya a wannan gida bayan kwana biyar akayi shagalin biki muka tare ni da amaryata. Aikam a wannan dare naga bala'i da masifu wanda ko a littafi ban ta6a jin irinsu ba a wannan dare na gwammace da banzo duniya ba. Farkawa nayi naga Umma , Sajida uncle"labaran" "Ameer" umman "sajida" da Abbanta da kuma wannan malamin da yayimana saukan Alqur'ani da addu'o'in kafin mu tare a gidan malamin ya fara da cewa yakamata kayimana bayani abinda yake faruwa da kai domin musan ta wacce hanya zamu iya taimakonka ga dukkan alamu wadannan aljanu so sukeyi sai suna halakaka. Nace tabbas hakane Malam bacin tsarewa ta ubangiji da tuni sunyi gunduwa gunduwa da sassan jikana na kwashe duk labarin abinda ya faru dani na faɗamusu "umma" ta fashe da kuka sannan ta kankameni tana fadin wallahi nidai kawai a raba auren nan bazan bari a kashemin ɗana guda ɗaya tilo ba shi kadai Allah yabani. Malam ya bawa Umma hakuri sannan yayi mata alkawarin lallai a yau kuma a nan dole ne zanyi maganin wannan aljani komai taurin kansa yanzu ina bukatan a kawomin wuta take aka kawo wannan wuta malam ya ciro wani garin magani ya zuba a cikin wannan wuta sannan ya umarci Sajida da ta dawo kusa da wannan wuta domin ta shaki yakin wannan magani. Amma duk da haka a banza domin wannan wannan aljani bai bayyana ba shi kanshi malam yayi matuqar mamaki yace lallai wannan aljani hatsabibancinsa yayi yawa tunda nake ban ta6a yin wannan hayaki ba ba tare da aljani yayi magana ba amma idan yasan wata baisan wata ba, take malam ya ciro wata 'yar karamar kwalba tamkar kwalbar turare sannan yacewa Sajida ta shaka. Shakawarta ke da wuya take sai ji mukayi muryar ta ta chanja idanuwanta suka kada sukayi jajur tamkar garshin wuta, sannan ya fada cewa malam ka kirani naki zuwa amma shine sai ka kirani da tsiya to kasani cewa komaye zakayi bazan fita jikin "sajida" ba domin ita ɗin matata ce. Ina ka ta6a ganin anyi aure mutum da aljan Malam ya fada lallai kai cikakken azzalumi ne kuma yau zan kawo karshen zaluncinka ko da tsiya ko da arziki dole ne yau ka rabi da wannan baiwar Allah zan konaka da ayoyin ubangiji ko kaki ko ka so yau zaka bar jikinta dan haka ina mai shawartaka gara katafi ta lalama. Aljani ya bushe da dariya wacce ta sanya duka falon nan sai da ya girgiza tamkar za'ayi girgizan ƙasa sannan yace abinda baku sani ba dukkan ku hatta mahaifin Sajida da mahaifiyarta tun kafin ku haifeta kakanta kanta ma'ana babanka kai babanta ya dauramin aure da ita. Abinda ya matukar bamu mamaki kenan sannan Malam yace yakai wannan azzalumin aljani wannan abin da ka fada bazai ta6a kasancewa ba. Aljani yafara bada labari kamar haka:- a shekarun baya kakan wannan yarinyar Alhaji "wada" ya kasance bashi da komai shi talaka ne talakan tilik tsabar talauci ya sanya kowa yana gudunsa hakan ya sanya ya rasa matar aure babu wanda yake son hada jini da shi, wannan al'amari yana matukar damun "wada" sosai hakane ya saka ya shiga kungiyar shan jini cikin kwanaki kalilan ya sami manyan kudade ya tara gidaje na alfarma da motoci tun a wancan zamanin yayi aure amma bayan yayi aure da zarar ya sami haihuwa sai wannan kungiyar ta sha jini bukaci ya basu yaron gashi shikuma yana son yara sosai. Abin yana matukar damun sa hakan ya sanya yayi tunanin bujirewa wannan kungiya tunda yanzu ya sami kudi gara ya gudu ya chanja gari idan yaso a can zai raini duk yaran da aka haifa masa ya zauna cikin farin ciki, wannan kungiya suna sane da duk abinda yake ƙullawa hakan yasan sukayi masa kashedin cewa lallai idan ya bijirewa umarnin su zasu haukatashi sannan su kasheshi. Abin ya matukar tayar mashi da hankali kullum baya bacci yadda yaga dare haka yake ganin rana yana cikin wannan halin ne nazo na taimaki rayuwarsa da yarjejeniyar cewa lallai idan ya sake samun haihuwar 'ya mace to idan ta girma zai bani aurenta saboda ina son auren macen bil'adama. Alhaji Wada ya amince sannan na cigaba da kareshi daga wancan matsafan ina kare masa dukiyarsa sai da ya zama a lokacin duk yankin babu mai tarin dukiya wacce tayi rabin ta Alh "wada" ana hakane matar Alh "wada" ta sami juna biyu amma abin takaici sai ta haifi ɗan Namiji ba kowa bane face kai. Nayi bakin ciki matuka bisa ga rashin cikar burina amma sai mahaifinka Alh "wada" ya bani hakuri sannan yace yamin alkawarin ko cewa muddin idan ka girma kayi aure idan ka haifi 'ya mace to yabani aurenta ko yana raye ko baya raye shidai burinsa na cigaba kare dukiyarsa da kuma kai kanka, a bisa wannan alkawarin nake har yanzu da nake baku wannan labarin kasan mu aljanu bama karya alkawari kamar ku bil'adama. Munyi matukar mamaki da jin wannan labarin na wannan aljani mun shiga cikin alhini matuka kuma tabbas abinda ya fada zai iya kasancewa gaskiya saboda kudin mahaifin Sajida tabbas ko shi bai san adadin su ba, Mallam yace " to munji duk abinda ka fada amma yanzu ina son ka fita jikin wannan yarinya saboda kana cutar da ita babu aure tsakanin mutum da aljan kuma ita batasan abinda yake tsaninka da kakanta ba. Wannan aljani yace bafa zan fita komaye zakuyi kuyi Malam yace tunda haka kace zaka gani yanzu kuwa na malam yasake shakawa Sajida wannan turare tayi wata kururuwa sannan tayi zunbur ta nufi kofa a guje nan "Ameer" da abbanta suka riketa da Ƙyar sannan malam ya cigaba da addu'a da karanta ayoyin Alkur'ani sannan ya ciro wasu kalolin turaren sunkai biyar yasanya aka danne ta ya shaka mata halin da naga "Sajida" a ciki sai da nayi ƙwalla. Wani nishi takeyi tamkar gurnanin zaki sanna aljanin yace dan Allah kuyi hakuri zan fita amma komai daren dadewa sai na dawo jikinta, malam yace au haka kace ashe baka dandara ba kenan nan ya cigaba da karatu yana shaka mata wannan turari. Ba shiri wannan aljani yace wallahi zan fita daga yau babu ni babu ita haihata haita har gaban abada bazan sake dawowa ba wata irin atshawa "Sajida" take sai ta dawo hayyacinta tana kallon mu cikin mamaki, jikinta babu karfi yayi lugub lugub har sai da doctor ya sakamata drip 2 sannan karfin jikinta ya fara dawowa. Mukayiwa Malam yace godiya sannan Abban "sajida " ya ɗauko kudin masu ya baiwa malam sannan yamar alkawarin kujerar maka shi da dukkan iyalansa, ni da Sajida muka fara rayuwar farin ciki domin a wannan lokacin mukasan mu ma'aurata ne bayan shekara ɗaya Allah ya azurtamu da samun karuwa ɗa namiji. ALHAMDULILLAH nan shine karshen labarin Sajida da Ishaq BACK TO STORY BAYAN WATA Yazid bai gama rufe baki ba sukaje ƙarar bindiga ba taƙaitawa da sauri John ya Shure Ihsan Maryam da Ado suka ƙankanme hannu a yayin da Yazid ya fara Lega musu hanyar waje da gudu suka nufi ta baya suka fara gudu ba kama hannun yaro Gaban su yana bugawa da ƙarfi kamar ana buga ganga, zuciyoyin su sun kasa kamewa da tsoro da fargaba. Ado na ja gaba da sauri yana nunawa da hannu: "ga wata mashiga! wannan hanya ce ta tsallaka zuwa Jordan! mu yi gaggawa!" John da har yanzu ke ɗauke da Ihsan a kafaɗarsa, ya danne raunin sa yana bin Ado da sauri. Maryam kuwa na kokarin bin su da ƙarfin hali, hawaye yana kwaranya a fuskarta. Amma Yazid... Yazid ya tsaya baya kadan yana duban motocin da suka sake dawowa da wasu sojoji masu bindiga. "ku cigaba!" Yazid ya ɗaga musu hannu da karfi, yana fadin: "ku cigaba da gudu! kar ku tsaya! nima zan biyo baya!" ya waiga yana kallon su cikin duniyar tausayawa Suka ci gaba da gudu da ƙyar, zuciyoyinsu na kuka. Amma kafin Yazid ya juyo... Gudu-gudu — ƙarar bindiga! "TA! TA! TA!" A gaban idon su, Yazid ya faɗi a kasa yana kwance sai jini dake zuba a saman ƙirjin sa ya juyo da idon sa yana ganin hanyar da ƴan uwan sa suke , a hankali yaki motsa bakin sa idon sa tsaye chakk akan hanyar su Maryam ta ɗaga hannunta tana kiran sunansa da karfi: "Yaziiid! Yazid ka tashi! Yaziiid!!" John da Ado suka rike ta da karfi, suna toshe mata baki John ya girgiza kanta da hawaye a idonsa, yana cewa: ba za mu iya dawo da shi ba... Maryam, don Allah... don Allah ki ci gaba da gudu..." Hawaye kamar ruwan sama suka zuba daga idon Maryam, zuciyarta na shan wani raɗaɗi mai tsanani sun tsallaka shingen bodar Jordan cikin kuka da wahala. Sun tsira — amma sun rasa ɗaya daga cikin su! lokacin da suka hau ƙaramin tsauni, suka waiga baya, suna ganin hayakin harbe-harbe da ƙarar bindigu da hayaniya. Rayuwa ba ta tsaya jiran kowa ba. suka ci gaba da tafiya cikin Jordan — da hawaye, da rauni, da zuciyoyin da suka karye. kowa ya san... ba za su taɓa mantawa da Yazid ba har abada. Bayan sun shafe kwanaki biyu suna tafiya a cikin garuruwan Jordan, cikin wahala da ƙuncin zuciya, suka kusa tsallaka bodar zuwa ƙasar mai tsarki Saudi Arabia. gaban su, rana na saukar zafi kamar wuta. ƙasa ta bushe, iska na fuskantar su da ɗan ƙura kowa na tafiya kamar wanda aka shake da ƙunci da raɗaɗi John ne ya tsaya, ya ajiye Ihsan ƙasa a hankali ya shafa gumi daga fuskarsa da hannunsa mai rauni. Maryam ta durƙusa a gefe, tana hawaye da ƙyar tana kallon shafin ƙasa kamar tana gani a cikin sa Ado kuwa ya tsaya gefe ɗaya yana kallon sararin sama mai shuɗi, kamar yana neman Yazid a cikin taurari , ya sauke numfashi mai nauyi yace da raɗaɗin zuciya: "Yazid... Ka tafi ka bar mu mun zo tare, amma ba za mu ƙare tare ba ..." Maryam ta fashe da kuka da karfi, ta ɗauki yashi ta yayyafa a kanta tana fadin: " da ace zaka jure, Yazid da ace zan iya dawo da kai!..."John ya dafa kafadarta da ƙyar yana cewa: "Allah ya jikan sa, ya gafarta masa, ya sanya Aljanna makoma..." Ihsan da suka fara zargin soyayya tsakanin ta da Yazid ta buɗe baki cikin baƙin cikin rasa abokin ta " Ya sadaukar da rayuwar sa domin ya taimaka mu mu tsira ya kula damu ,munyi wasa da dariya dashi munyi kuka dashi ya zama tamkar hasken tafiyar mu yau ya kuma ga Allah mahaliccin mu mun zama mu huɗu da bamu bashi dama ya bamu gajeren labarin AlJANNIN SAJIDA ba tabbas da muna da alhakin kaurace masa ya bamu labarin soyayya ta gaskiya sai dai ya sadaukar da ransa a gari mu wanan shine soyayyar gaskiya da amana da bai tsaya a baya ba yau da an rasa rayukka biyar a madadin ɗaya ". Addu'a sukaye masa , suka ɗaura zango a can gefe, a wani yashi mai dan taushi, suka kwanta da azabar kewar abokinsu Yazid. babu motsi, babu annuri sai saukar hawaye da karancin numfashi. Ranar nan ta kasance daren da zuciyoyin su suka yi kwana cikin ƙewar mutuwa ƙewar wanda suka rasa, ƙewar mafarkin su da suka ragu da shi. A cikin shiru, su Maryam suka yanke shawara: “Dole ne mu ci gaba da tafiya ba don Yazid basai don rayuwar da muke da ita a gaba.” suka ɗauki doguwar shiru kafin Ado ya ce a hankali kamar yana karanta addu’a: "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un..." kowa ya amsa cikin zuciya mai raɗaɗi. suka ɗauki sauran gaban su cikin Jordan, sun kusa kaiwa border na Saudi Arabia... amma zuciyoyin su na tafiya cikin kewa, hawaye da nauyin da ba za su iya saukewa ba har abada. Labarin Aljanin Sajida wanda Iliyasu Falalu Lawal ya kawo labarin a inda na rubutta da tacewa Godiya ta musamman ɗan uwa da wanan gudunmawa Allah ya saka da ɗunbin alkaire Allah ya bara zumunci. Tabbas labarin bayan wata labarin ne da ke nuna mana wasu matafiya wanda azahiri gaskiya akwai masu shirin tafiye-tafiye domin neman kuɗi wahala da tsaro da hatsari hanya yake sasu mutuwa kala kala wasu kuma yunwa ce ajalin su wasu kuma jami'an gwamnati anan sai muce sojoji sun harbi Yazid har lahira Allahu Akbar Allah ya jiƙan magabata mu Allah ya musu rahama kullu nafsin za'iqatul maut... kuyi haƙuri da wanan shafin haka tsarin labarin yaki tafiya. . BY NARNAH ƘANWAR SOJA ✍️ https://chat.whatsapp.com/Bd1Zu1cwIO81A7rrATd4Cu 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 Book two BY NARNAH KANWAR SOJA 💫ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Page 31 / 32 Maryam, John, da Ihsan, sun shiga wani ƙauye mai nisa daga garuruwa da kasuwannin birni wannan ƙauye mai launin zinariya da farin ruwa yana kusa da tafkin ruwa mai tsafta, inda ruwan sama ke rarrafe daga duwatsu mai tsawo, ya bayyana kyawun duniya amma yana ɗauke da sirrin da bai bayyana ba. Wannan ƙauyen yana ba su natsuwa da sauƙin numfashi tare da sauyin yanayi da jin daɗin zaman lafiya, sai suka fara zaman cikin wannan ƙauye mai zaman kansa. Matar da suka haɗu a cikin wannan garin ta ba su abinci, suka sha ruwa mai zafi, suka yi wanka a cikin ruwan tafkin a nan, suka samu tsari, suka kafa zango da ƙawancen aiki a cikin gidan wanda aka basu damar zaman lafiya na ɗan lokaci daga nan ne suka fara lura da wani abu mai ban sha'awa: Kamar yadda wata guda ta wuce, suka fahimci cewa sun sha wahala fiye da yadda suka zata a cikin wannan tafiya mai wahala lokaci ya gudana sosai, amma su ba su lura ba, kowanne daga cikin su yana cikin tunanin cewa mai yiwuwa ba zai ƙare haka ba. lokaci yana zubowa cikin hargitsi da rashin tsari, kuma zuciyoyin su sun daɗe da wahalar rabuwa da rayuwar su da kuma tafiye-tafiye da suka yi. Tunanin abokin su da ƙaddarorin da suka bari a baya sun fara bacewa, sai dai tunanin zaman su cikin wannan ƙauye ya bayyana yadda suke gaji da tafiya amma su na jin cewa ba su fiye so ba. “Duk da haka, muna nan cikin rayuwa ba mu da wani wuri da zai fi wannan da muhimmanci a yanzu , sai dai cikin kunci da tunanin da suka dauka tsawon lokaci, lokacin ya gabatar musu da tambaya: “Ya ya muka zama kamar haka? shin za mu ci gaba da kasancewa cikin wannan ƙauye, ko kuma za mu ci gaba da tafiya?” Maryam ta sake riko hannun Ihsan da karfi, tana tunanin cewa "mun kasance cikin wannan tafiya sama da shekara daya yanzu kuma duk abin da muka fuskanta, har yanzu muna da haske na fata a cikin zuciyarmu." John kuma, a matsayin jagoran tafiyar, yana da wannan tambayar mai yawa a zuciyarsa: "amma lokacin yana kurewa, tunanin zamantakewar mu yana ƙarfafawa shin mu koma ƙasar mu, ko mu ci gaba da fuskantar duniya?" Zuciyar su tana ɗauke da nauyi, har suna jin cewa an wuce lokaci sannan suka fara tunanin wata nawa suka yi a cikin wannan hanya lokaci ya gudana cikin hargitsi ba tare da su lura ba, sunyi shekara guda a hanya, kuma yanzu kowane daga cikin su yana da babban abin da zai fuskanta daga nan gaba. zuciyoyin su sun cika da ƙarfin hali da kuma tunanin sauyin duniya, har yanzu suna neman amsoshi ga tambayoyin su game da zuciyar su da rayuwa. A cikin ƙauyen da suka zauna, kowanne daga cikin matafiya yana jin daɗin zaman lafiya da sauƙin numfashi, bayan shekaru na wahala a hanya su Maryam, John, da Ihsan, sun samu sauƙin zama a cikin wannan ƙauye mai zaman kansa suna hira sosai a tsakanin juna, suna yin tunani game da irin wahalar da suka sha da kuma yadda rayuwa ke ƙara musu ƙarfi a kowanne lokaci. A lokacin da suka zauna a cikin gidan karamar matar da ta taimaka musu, wani dare da aka haɗu a cikin ƙauyen, Ado, ɗan uwansu matan matafiya, ya ɗauki kyakkyawar dama don bayar da wani labari mai tsada wanda ya dauki hankali sosai. Ado, wanda yake da gwaninta a bayar da labarai, ya zauna a gabansu cikin jin daɗin zama, sannan ya fara ba su labarin wata masarauta mai ban sha'awa cikin wannan daren, labarin ya fara kamar haka: "Wannan masarauta ta faru ne a cikin shekaru da dama a baya," Ado ya fara, yana kallon kowanne daga cikin su, yana tabbatar da cewa suna shirye don jin wannan labari mai ban sha'awa. "Masarautar mayaƙa ce, wacce ta mamaye ƙasar, kuma ta haifar da ƙiyayya tsakanin manyan Sultana da sarakunan. wannan masarautar tana da dokoki masu tsauri da kuma manyan sojoji da suka kasance a saman mulkin." "Haka kuma, a cikin wannan masarauta, akwai wani sarki mai ƙarfin zuciya wanda aka san shi da sunan Sarki Zakar, wanda ya jagoranci masarautar cikin nasara, har ma ya yi daidai da wasu al'amuran duniya amma wannan sarki yana da sirri mai ban mamaki wanda ya jawo rashin jin daɗin wasu daga cikin jama'ar masarautar." Ado ya cigaba da labarin, yana daukar hankalin su sosai. Maryam, da ke sha'awar jin labarai daga ƙasashen waje, ta yi murmushi. "Ado, kai dai kana jin labarai sosai wannan masarautar tana da sirri ko kuwa?" Ta tambaya cikin sha'awar ganin yadda zai ci gaba da bayar da labari. Ado ya dafe kumatun sa yana dan murmushi kafin ya cigaba: "I, wannan masarauta tana da sirri mai zurfi. Sarki Zakar yana da wani dogon tunani game da yadda aka yi mulki saboda haka, ya fara yin gwagwarmaya da wani mai ilimi wanda ya saba wa tsarin mulki na masarautar sai dai, wannan mai ilimi yana da wani sirrin da ba kowa ya san shi ba wannan sirri yana cikin wata tsohuwar alƙawari da aka haɗa tsakanin Sultana da wani jarumin daga ƙasar mai nisa." "A cikin wannan gwagwarmayar," Ado ya cigaba, yana kallon kowanne daga cikin su cikin sha'awar da suke ciki, "an sami matsaloli da dama, wanda suka shafi soyayya da ƙaddara amma a karshe, wannan masarauta ta fuskanci babban yaki daga cikin dangi na sultana wanda ya sanya dukkanin masarautar cikin wani lamari mai ban tsoro." John, wanda ke cikin jin daɗin labarin, ya tambaya, "to, me ya faru? wane labari ne ya yi tasiri a cikin wannan masarauta?" Ado ya jinjina kai kafin ya cigaba da bayar da cikakken labari: " ƙarshe, sarki Zakar ya fuskanci babban barazana daga cikin dangi na Sultana amma kafin ya yi amfani da ƙarfin soja, ya zaɓi hanya mafi salama saboda haka, sultan din ya bayyana cewa, soyayya da amana sun fi ƙarfin sojoji da yaki, kuma hakan ya canza komai a cikin masarautar wannan labari yana koya mana cewa, duk da wahala da juriya, soyayya da amana su ne tushen zaman lafiya." Ado ya gama labarin, sai kowanne daga cikin su suka kasance cikin tunani, suna tunanin darasin da suke koya daga wannan labari. Maryam ta jawo hanu, tana kallon Ado. "Ado, wannan labari yana dauke da darasi mai kyau na koyi cewa, duk da dukkanin ƙalubalen da muka fuskanta, soyayya da amana suna cikin alfanun rayuwa wannan masarauta tana koyar da mu cewa, a kowane lokaci, ya kamata mu riƙe amana da juriya, domin hakan zai taimaka mana wajen fuskantar kowanne irin kalubale." John ya ƙara cewa: "Daga labarin Ado, na fahimci cewa ba ko wanne yaki zai zama mai sauƙi, amma idan muna da juriya da ƙoƙari, za mu iya cimma nasara." Ado ya kalli kowanne daga cikin su cikin murmushi, yana farin cikin ganin yadda labarinsa ya shafi zukatan su. "A'a," ya ce, "lallai wannan masarauta ta koya mana cewa zaman lafiya yana samuwa ne daga cikin mu, a cikin zuciyar mu da kuma ɗa'a da amana." A cikin wannan sabon labari da Ado zai ba su, matafiya suna ɗauke da sabon darasi a zuciyarsu, wanda ke ƙara musu ƙarfin hali da kuma fahimtar cewa duk da wahalhalu da suka sha a hanya, akwai alfanun rayuwa da za su iya koya daga juna da ƙaddara. Sun fara gane cewa kodayake sun rasa abubuwa da dama, akwai abubuwan da ba za su iya rasa ba: soyayya, amana, da karfin zuciya. John ya tsinci kansa yana mai cike da sha'awar jin labari, duk da irin wahalar da suka sha a hanya cikin farin ciki, ya ɗauki hannu cikin sa da murmushi, yana kallon Ado, yana fatan jin ƙarin bayani daga labarin da ya fara bayarwa. "Ado," John ya fara, yana mai neman ƙarin bayani, "ko wane ne jarumi a wannan labari na masarautar Zakar? Ta yaya suka shiga wannan fafatawa?" Ado ya gaji, sannan ya fara tunanin yadda zai bayyana wannan sabon ɓangaren labarin. wannan labari ba ya ƙarewa kawai da girmamawa da soyayya, har ma yana ɗauke da gwagwarmaya, ƙarfin hali, da kuma jarumta. "A wannan lokacin," Ado ya fara, "masarautar Zakar tana cikin wuri mai wuyar samu nasara. Sarki Zakar yana da ƙarfi da hikima, amma yana fuskantar wata barazana mai girma daga cikin dangi na sultana wannan barazana tana fitowa daga wata jaruma mai suna Layla, wacce take ɗan uwa na Sultan kuma tana da ƙarfi wajen gwagwarmaya." John da Ihsan, da Maryam, duk sun yi nuni da sha'awar jin ƙarin bayani. "Layla?" Maryam ta tambaya, "Ta yaya take zama cikin wannan labari? Shin ita ce mai kawo matsala ga masarautar?" Ado ya gyara zama a cikin kujerar da ke kusa da su, yana ɗauke da wani kyakkyawan numfashi kafin ya cigaba: "I, Layla tana da babban buri, wanda ke zama barazana ga sarki Zakar tana ɗaukar alhakin dukan ƙasashen makwabta, tana koyar da mayakan ta yadda za su jure ga gwagwarmaya da kuma yaki amma, Layla ba ta yi hakan ba don neman mulki kawai—ta yi hakan ne domin tabbatar da cewa akwai sauyi a cikin masarautar." John ya ɗan yi murmushi, yana ɗauke da idanuwansa cikin sha'awa, "Saboda haka, Layla na da wani babban buri a zuciyarta to, menene abinda ya faru a tsakanin ta da Sarki Zakar?" Ado ya dube su, yana ɗauke da wasu kyawawan kallo, ya cigaba "Layla ta zo daga ƙasar nesa, tana da babban ƙarfi wajen amfani da makamai da kuma dabaru na yaki tana daukar ƙungiyar mayakan ta da ƙwarewa sosai wajen shawo kan matsalolin mulki da yaki saboda haka, Sarki Zakar, wanda ba ya son ganin ƙasar ta shiga cikin rikici, ya buƙaci wani jarumi daga cikin masarautar ta shi, wanda za a fi sani da Khalid." "Khalid?" Ihsan ta tambaya, tana da sha'awar ƙarin bayani "shin Khalid yana daga cikin sabbin jarumai da aka yi amfani da su a cikin wannan gwagwarmaya?" Ado ya ƙarasa yana kallon kowanne daga cikin su, yana mai dora labarin cikin kyau da hankali: "I, Khalid wani jarumi ne daga cikin masarautar, wanda aka horar da shi tun yana ƙarami a cikin wannan fafatawar, Khalid ya zama jagora a cikin mayakan sarki Zakar, yana ƙoƙarin kawo zaman lafiya tsakanin sarki da Layla abin sha'awa, Khalid da Layla suna da alaƙa ta musamman—ko da yake Layla ta kasance tana ɗaukar matsayi mai ƙarfi wajen samun nasara, Khalid ya kasance yana nufin warware matsalolin da suke tasowa daga zuciya da hankali." "Kamar yadda muka saba, duk da cewa yana cikin wannan fafatawar, Khalid yana ƙoƙarin kiyaye manufofin sarki Zakar na samun zaman lafiya amma Layla tana da manufar ta ta sauya yadda masarautar take mulki da kuma yadda ake gudanar da harkokin yaki." Ado ya ci gaba, yana mai ƙara jaddada muhimmin abin da Khalid ke da shi a cikin zuciyarsa. "Layla da Khalid sun kasance a cikin wani yanayi mai rikitarwa duk da cewa suna cikin faɗa, suna da soyayya a tsakanin su, wanda a cikin wannan labari ke nuna yadda rashin yarda da haɗin kai zai iya kawo tashin hankali a cikin kowanne yanayi." A cikin wannan fafatawar tsakanin Sarki Zakar, Layla, da Khalid, ya bayyana yadda labarin ya tsirara daga zaman lafiya da nasara zuwa matsaloli na zuciya da juriya amma labarin zai tsaya a lokacin da Khalid da Layla za su fuskanci ƙaddara mai ban mamaki, wanda zai kai su zuwa ga wani babban yaki wanda zai iya canza dukkanin masarautar Zakar. Khalid, wanda zai jagoranci mayakan sarki Zakar, zai gwada ƙarfin zuciyarsa, yanda zai zauna da Layla cikin juriya da kuma ƙarfin hali. Suna cikin wata ƙaddara mai sarkakiya, yayin da Khalid zai ci gaba da fafatawa don ceto masarautar daga rikici. Layla tana mai tsananin kuzari, kuma za ta yi amfani da kowane damar da za ta iya samu don tabbatar da cewa an bi tafarkin da take fata. kamar yadda wannan labari ke tafiya, akwai wata alama a zuciyar Khalid da Layla, tana nuni da cewa, ko da wane ne mai tsauraran matakai da kuma ƙarfin zuciya, ƙaddara ba ta taɓa yin watsi da ɗan adam da zuciyarsa ba ,a cikin masarautar Zakar, yaki ya dauki wani sabon salo. Khalid, wanda ya jagoranci mayakan sarki Zakar, yana cikin ƙalubale mai girma. Layla, wacce ta ɗauki matsayin mai kawo sauyi a cikin masarautar, tana ci gaba da kawo wa masarautar barazana amma, daga cikin zuciyar Khalid, akwai wani abu mai cike da damuwa akwai wani haɗin kai da zuciyarsa ke kasa gane duk da cewa Layla tana cikin ɓangaren gabatar da canji, har yanzu yana jin wani abu mai karfi da sha'awar haɗin kai da ita. A cikin wannan yaki mai zafi, Khalid da Layla suna fuskantar ƙaddara guda, amma hanya ce mai sarkakiya da ta yi wuya. "Layla," Khalid ya kira, yana mai tsananin kiran ta daga gefen fili, "me kike so daga gare ni? Me yasa kike ci gaba da kawo matsala a cikin wannan masarauta?" Layla ta dube shi cikin ido mai ƙarfi, fuskarta ba ta yi laushi ba. "Khalid, ba wai na kawo matsala ba, na kawo sauyi ne Sarki Zakar yana da hukunci mai yawa, kuma yana rashin fahimtar yadda za a yi da rayuwar al'ummar wannan ƙasa ni na zo ne domin tabbatar da cewa kowanne mutum yana da damar yin rayuwa cikin walwala." Khalid, duk da cewa yana cikin haɗin kai da sarki Zakar, yana cikin wani yanayi mai rikitarwa. Yana son layin zamani, amma yana jin cewa Layla tana da gaskiya a cikin abin da take yi, har ma yana sha'awar ganin wani canji mai kyau a cikin masarautar. A yayin da yaki ya ƙara zafi, masarautar Zakar ta fuskanci wata babban matsala daga ƙungiyar mayakan Layla. sn kammala wata babbar yaki tsakanin mayakan Khalid da na Layla, inda dukkan bangarorin suka fuskanci rauni da asarar rayuka wana daga cikin mayakan Khalid, Yusuf, ya mutu a cikin yaki, wanda ya yi matukar raunana zuciyar Khalid. A cikin wannan mawuyacin lokaci, Khalid ya nemi taimakon Layla. Ya yi magana da ita cikin hanzari: "Layla, wannan ba zai kawo ƙarshenmu ba muna iya samun zaman lafiya. Dole mu yi tunanin yadda za mu iya warware wannan matsalar." Layla ta tsaya, tana kallon Khalid da kyau. "Khalid, ka gane cewa wannan ba kawai yaki ba ne—abu ne da zai shafi dukanmu. Idan muka ci gaba da wannan yaki, za mu tafka asara amma idan muka zauna, za mu iya haɗa ƙarfi don kawo canji mai kyau ga wannan ƙasa." Daga cikin zuciyar Khalid, yana jin wani abu mai ƙarfi. Wannan ba kawai yaki ba ne, wannan yana da wani abin da ke haɗa su. Wataƙila Layla tana da gaskiya, amma yana jin cewa akwai wata hanya da za su bi domin warware rikicin. Daga bisani, a cikin ɗan lokaci mai ƙanƙanci, sun yanke shawarar yin zaman lafiya. Khalid da Layla sun kalli juna, kuma cikin ɗan lokaci mai sauki, sun fahimci cewa ƙaddara tana da ƙarfi, amma haɗin kai yana da ƙarfin canza dukkan abubuwa. Amma, kafin su sami damar yin ƙarin magana, wani sabon mummunan labari ya iso daga cikin masarautar. "Mayakan Layla sun shigo da wani sabon abu mai haɗari muna fuskantar wata babbar barazana daga wata ƙungiya mai suna Al-Antar wannan ƙungiyar tana da makamai masu ƙarfi kuma tana nufin yin jagorancin duniya." Wannan sanarwa ta sa Khalid da Layla sun haɗa kai domin fuskantar sabuwar barazana. su biyun, tare da mayakan su, suka tashi domin shiga wani sabon gwagwarmaya na tsaro da tabbatar da zaman lafiya a cikin masarautar. Wannan gwagwarmaya ta zama ƙalubale mai girma, wanda zai iya kawo ƙarshen kowanne ƙungiya ko sabuwar al'umma a cikin masarautar Zakar. Kamar yadda aka saba, wannan labari yana ƙunshe da gwagwarmaya tsakanin halin jarumai da jarumar duk da haka, lokacin da suka haɗu da juna, sun tabbatar da cewa canjin da suke bukata yana da kyau. Khalid da Layla suna kallon juna tare da tsananin fahimta, suna haɗa karfi domin kawo zaman lafiya ga ƙasar su. A karshe, wannan labari yana da ban mamaki, Shin Khalid da Layla zasu iya cimma burinsu? ko kuma masarautar Zakar za ta tafka wata sabuwar rikici mai girma? Wannan ya zama wani babban tambaya da ke neman amsoshi, wanda za a gani a cikin shahararrun ƙaddarori. Khalid da Layla, bayan haɗin kai da suka yi, sun yanke shawara cewa su zauna da masu ƙungiyar Al-Antar domin ƙara fahimtar juna. cikin wannan ƙaddara mai ɗauke da gwagwarmaya, sun fahimci cewa babban abu da ke tursasa su kai ga zaman lafiya shine matsalolin rayuwa da suka shafi dukan al'umma amma ba a cika samun damar yin hakan ba, domin har yanzu akwai wasu masu ƙoƙarin kawo rikici a cikin masarautar. Khalid ya duba shahararren jagoransa, wanda yana ɗauke da nauyi mai yawa a kan kafafunsa ya san cewa idan ba su haɗa kai da Layla da sauran masu ƙungiyar ba, masarautar Zakar zata ci gaba da fuskantar matsaloli daga cikin masarautar da kuma ƙasashen da ke kewaye. "Layla," Khalid ya ce, yana kallon ta cikin idon sa. "akwai hanyar da za mu bi don tabbatar da zaman lafiya a wannan ƙasa, amma har yanzu akwai masu goyon bayan rikici da ke neman kawo ƙarshen wannan dukan ƙasa." Layla ta ɗan tsaya, tana tunanin maganar Khalid. "duk da cewa muna son canji mai kyau, akwai masu ƙarfin zuciya waɗanda ba za su amince da hakan ba amma kafin duk wani abu, ya kamata mu ƙara fahimtar juna." A wannan lokaci, Ado, wanda yanzu ya zama ɗan uwan Khalid da Layla, ya zo tare da sabon rahoto. "Sarkin Zakar yana cikin hatsari a ƙasar masarautar, akwai wani wanda ke neman jagoranci, kuma yana nufin kawo wata babbar rigima tsakanin al'ummar Zakar." Layla ta fara ƙara yawan damuwarta, "Idan ba mu ɗauki mataki yanzu ba, wannan zai iya zama ƙarshen Zakar." Khalid ya jinjina da kai, yana tabbatar da cewa lokaci ya yi da za su ɗauki matakin ƙarshe na tabbatar da zaman lafiya da canji a cikin masarautar. Duk da yadda suka yi ƙoƙari wajen haɗa kai, wani sabon rikici ya bayyana wataƙila sun kawo zaman lafiya a tsakanin Khalid da Layla, amma har yanzu akwai masu ƙarfi daga ɓangaren Al-Antar da ke neman ganin masarautar Zakar ta rushe wannan ya sa Layla da Khalid suka ƙirƙiri wani sabuwar shirin tunkarar wannan barazana. "Mu shiga cikin wannan fage na ƙarshe," Khalid ya ce, "mu nemi hanyar magance wannan matsalar daga tushe." Yayin da suke tattaunawa, sai suka samu labari cewa ɗaya daga cikin manyan farfesoshin masarautar Zakar, Farfesa Makamashi, ya yi haɗin guiwa da Al-Antar. Farfesa Makamashi yana cikin ƙungiyar masu bincike, wanda ke da alhakin kimiyya da fasaha a cikin masarautar yana da matukar ƙarfi, kuma yana da makamai masu ƙarfi wanda zai iya canza dukkanin tafiyar masarautar Zakar. "Zamu tunkari Farfesa Makamashi," Layla ta ce, "amma muna buƙatar bayanai game da niyyar sa." A cikin wannan lokacin, Khalid da Layla sun fahimci cewa Farfesa Makamashi yana da wani shiri na musamman wanda zai kawo babban canji a cikin masarautar Zakar. Amma wannan shiri yana buƙatar haɗin kai tsakanin ƙungiyar Zakar da Al-Antar. Farfesa Makamashi yana cikin wani ɗakin gwaje-gwaje na musamman wanda ke da matukar haɗari a wannan lokacin, Khalid da Layla sun shiga cikin dakin, suna buƙatar jin abubuwan da ke faruwa. Farfesa Makamashi yana cikin wani dakin gwaje-gwaje mai ban mamaki yana ƙoƙarin haɓaka wata sabon makami wanda zai iya rushe masarautar Zakar. "Khalid, Layla," Farfesa Makamashi ya fara magana, yana kallon su cikin ido mai ƙarfi, "Duk da haka, ina bukatar wannan shiri domin samun zaman lafiya mai dorewa a cikin masarautar wannan makami zai iya kawo ƙarshen waɗannan rikice-rikicen da ke tursasa mu." Khalid ya ɗan tsaya, yana jin cewa Farfesa Makamashi yana magana da gaske amma, yana jin tsoron amfani da wannan makami a cikin masarautar, saboda yana iya kawo haɗari mai girma A cikin wannan sabon yanayi mai tsanani, Khalid da Layla suna ƙoƙarin gano hanya mai kyau domin magance matsalar acikin zuciyarsu, suna ganin cewa duk wata mataki da za su ɗauka zai iya zama ƙaddara ga dukan masarautar Zakar. Wannan yana nufin cewa yanzu akwai wani babban gwagwarmaya da zai ƙara haɗa su. Shin Layla da Khalid za su iya magance wannan matsala kuma su kawo zaman lafiya? Ko kuma Zakar zai fuskanci rushewar masarautar a hannun Farfesa Makamashi da ƙungiyar Al-Antar? A cikin shahararren masarautar Zakar, da ƙarfin zuciya, Khalid da Layla sun tunkari duk wani kalubale da zai zo musu. Amma ko za su iya samar da zaman lafiya cikin wannan rikici? Khalid da Layla sun kammala taron da Farfesa Makamashi bayan sun fahimci cewa makamin da yake da niyyar ƙirƙira yana da matukar haɗari, sai suka fahimci cewa akwai wata hanya daban da za su iya bi wannan hanya tana nufin tunkarar wasu mummunan sakamako, amma tana da damar samar da zaman lafiya mai dorewa a cikin masarautar Zakar. Khalid ya ce da Khalid ya ce, yana ɗaukar hanzari a cikin magana. "Idan muka tafi da tsari mai kyau, za mu iya dakatar da shi daga kaddamar da wannan makamin." Layla ta amsa da ƙarfi, tana nuna ƙwarewar da take da ita a cikin wannan haɗin gwiwa. "Bari mu tabbatar da cewa ba zai samu damar kawo wannan makami ba zamu tunkari duk wani ɓangare na wannan shiri har sai mun cimma nasara." A cikin wani ɓangare na masarautar Zakar, wanda aka fi sani da "Gidan kula da zaman Lafiya," sarkin Zakar da majalisar dattawa sun haɗu cikin dakin taro, suna duba yanayin da masarautar ke ciki wannan dakin yana cikin wani tsaunin da aka kebe don hidimar majalisar, inda aka kafa matakan tabbatar da zaman lafiya a cikin ƙasar. Sarkin Zakar ya kalli Khalid da Layla, yana mai cewa, "Kuna son ganin Zakar ta tsira daga wannan tashin hankali, kuma kuna da shiri mai kyau amma ina ganin cewa wannan zai kasance mai wahala sosai. Farfesa Makamashi yana da ƙarfin iko." Khalid ya sauke numfashi, yana ganin cewa wannan hanya ba mai sauƙi ba ce. "Kada ku damu muna da ƙungiya mai ƙarfi a bayanmu, kuma akwai mutanen da suke son ganin zaman lafiya ya ci gaba za mu tsaya tsayin daka." Narnah Kanwar soja ✍️✍️ https://chat.whatsapp.com/Bd1Zu1cwIO81A7rrATd4Cu 🌗🌙BAYAN WATA🌙🌗 Book two BY NARNAH KANWAR SOJA 💫ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 SADAUKARWA Wanan littafin sadaukarwa ne a gunke gaba-daya ta bisa jajjircewa da bajinta a duniyar mu na marubuta Allah ya taimaka ya kara basira da hazaƙa gaba gaba sister 💕 Zahrah Royal Star Page 33 / 34 A cikin wani daki mai zurfi da ke cikin masarautar, Farfesa Makamashi yana ci gaba da gudanar da bincike game da makamin da zai kawo ƙarshen zaman lafiya. Yana cikin wani yanayi mai cike da sha'awa, yana duba rahotanni da kuma sabbin bayanan da suka fito daga gwaje-gwajen sa. "Zaman lafiya ba zai iya zama abin da ke akwai ba idan ba a kawo wannan makamin ba," Farfesa Makamashi ya ce, yana kallon wani juzu'i na tsarin makamin da yake ƙoƙarin kera. "Dole ne a samu sabbin hanyoyin da za su kawo ƙarshen wannan rashin zaman lafiya. Wannan shine hanya guda ɗaya da za ta kawo karshen rashin tsaro a masarautar." A cikin wannan lokaci, Farfesa Makamashi yana samun haɗin kai daga wani mai ƙarfi wanda ba a sani ba, wanda ke son ganin makamin ya kammala da kuma amfani da shi domin kawo karshen duk wata fahimta da ke tsakanin al'ummomin Zakar. Layla da Khalid sun yi taron sirri da sauran shugabannin ƙasar da suke aiki tare da su. Dukansu suna ganin cewa zaman lafiya a Zakar yana cikin hannunsu, amma suna buƙatar wasu matakai masu kyau don tabbatar da cewa Farfesa Makamashi ba zai samu nasara ba. "Dole mu tsaya tsayin daka. Idan muka bar shi ya yi abin da yake son yi, zai rushe dukkan abin da muka gina," Layla ta ce cikin damuwa. Khalid ya gyara zamansa, yana kallon kowane daga cikin shugabannin, "Muna da ƙungiyar da za ta tunkari wannan shiri. Zamu yi amfani da dukkan ƙwarewar mu da hanyoyin da zamu iya amfani da su." "Amma, akwai wata matsala," wani daga cikin shugabannin ya faɗi. "Farfesa Makamashi yana da ƙarfin iko a cikin masarautar, kuma yana da goyon bayan wasu daga cikin manyan mutane." A cikin wannan ɗan lokaci na shakka, Khalid da Layla sun yanke shawara cewa dole su ƙarfafa dangantakarsu da wasu daga cikin ƙasashen makwabta Suna buƙatar tallafi daga wasu ƙasashen, musamman daga ƙasashen da suka riga sun kware wajen tafiyar da al'amuran zaman lafiya. Wannan zai ba su damar samun damar taimakon da suke buƙata a wannan lokacin. "Kada ku damu," Khalid ya ce da Layla cikin ƙarfi. "Za mu tunkari wannan shiri daga cikin ƙungiyar Zakar, amma kuma muna buƙatar haɗin kai daga ƙasashen da suka san yadda za a magance irin wannan matsala." A ƙarshe, ɗukkan su sun yarda cewa wannan yana zama mai tsanani, amma har yanzu suna da damar samun nasara idan suka haɗa kai da ƙungiyar al'umma ta Zakar da sauran ƙasashen. Wannan yana zama ƙalubale ga Zakar, amma yana nufin cewa ko wanne daga cikin su yana da rawar da zai taka. "Zakar za ta kasance mai zaman lafiya ko kuwa za mu rabu da ita," Khalid ya ce, yana kallon Layla. "Za mu tsaya tsayin daka, ko da kuwa hakan yana nufin ƙoƙari mai tsanani," Layla ta amsa, tana ƙara kwarin gwiwa. "Zaman lafiya zai zama gaskiya." A ƙarshe, masarautar Zakar za ta tunkari ƙalubale na gaske wanda zai iya canza komai. A cikin wannan gwagwarmaya, Khalid da Layla sun zama jagororin, amma har yanzu suna buƙatar haɗin kai daga al'umma da sauran ƙasashen duniya. Duk da haka, haɗin kai da ƙoƙari na musamman na nufin cewa Zakar za ta iya cika burin zaman lafiya. Amma ko za su iya kaiwa ga nasara ko kuma za su fuskanci rushewar masarauta? Wannan yana cikin hannunsu yanzu. Khalid da Layla sun kafa ƙungiya mai ƙarfi tare da haɗin kai da sauran ƙasashen da suka amince da manufar zaman lafiya. Sun yi amfani da dukkan hanyoyin da za su kawo ƙasashen zuwa ga haɗin kai, kuma wannan mataki ya ba su damar samun taimako daga kasashen makwabta har yanzu suna fuskantar babban ƙalubale: Farfesa Makamashi. "Zamu tunkari wannan shiri cikin nasara, ko da kuwa hakan yana nufin haɗuwa da ƙaddara mai wuya," Khalid ya ce, yana kallon Layla da sauran shugabannin. "Duk da yake yana yiwuwa mu fuskanci ƙalubale daga cikin Zakar, akwai tabbacin cewa za mu iya dakatar da Farfesa Makamashi daga kaddamar da makamin da zai kawo karshen zaman lafiya," Layla ta amsa cikin ƙarfin hali. Masarautar Zakar ta kasance cikin wani yanayi mai ban tsoro, amma ƙungiyar ta haɗu da ƙwarewar ƙasashen duniya, sun fara tafiya zuwa ga hanyar da za su dakatar da Farfesa Makamashi daga kaddamar da aikin sa a cikin wannan lokaci, suna ganin cewa zaman lafiya zai yiwu idan sun ci gaba da haɗin kai da aiki tare da sauran ƙasashen duniya. Farfesa Makamashi ya ƙara samun ƙarfi daga wasu daga cikin manyan mutanen masarautar, wanda hakan ya sa ƙungiyar Khalid da Layla suka shiga cikin wani yanayi mai matuƙar damuwa amma suna da tabbacin cewa idan sun tunkari shi cikin ƙwarewa da tsari, za su iya dakatar da shi daga samun nasara. A ƙarshe, Khalid da Layla sun kai ga gaban Farfesa Makamashi, wanda yana cikin wani daki mai zurfi a cikin masarautar nan, suka haɗu da shi don ƙaddamar da shirin dakatar da aikinsa. "Dole ne mu dakatar da kai kafin ka kaddamar da wannan makami," Khalid ya ce, yana kallon Farfesa Makamashi cikin haɗari. Farfesa Makamashi ya kalli su da ƙyallen idanunsa, yana murmushi cikin ƙasƙanci. "Ba za ku iya dakatar da ni ba na haɗu da wasu daga cikin manyan mutane a cikin masarautar, kuma ba ku da iko a gare ni." Layla ta daga hannu cikin ƙarfin hali. "Zaman lafiya zai yiwu, kuma idan muka haɗa kai, za mu iya kawo ƙarshen wannan mummunar aiki da kake ƙoƙarin yi." A cikin wannan fafatawa mai ɗaukar hankali, Khalid da Layla sun tabbatar da nasara. Farfesa Makamashi ya gaza, kuma masarautar Zakar ta tsira daga haɗarin da yake kawo wa. Wannan ya zama wani babban ƙalubale da aka ci nasara akai, wanda ya tabbatar da cewa zaman lafiya zai yiwu idan aka haɗu da ƙoƙari da ƙarfin hali. Daga ƙarshe, Zakar ta dawo cikin zaman lafiya, kuma Khalid da Layla sun zama jarumai a masarautar a cikin wannan lokaci, sun bayyana cewa koda kuwa akwai ƙalubale, idan mutane suka haɗa kai cikin gaskiya da ƙoƙari, za su iya cimma burin su na zaman lafiya. A cikin wannan nasara, al'umma ta Zakar ta tashi, tana ƙoƙarin tabbatar da cewa ba za a sake samun irin wannan barazana ba. Khalid da Layla, tare da sauran masu goyon baya, sun tabbatar da cewa masarautar Zakar za ta ci gaba da kasancewa mai zaman lafiya da kwanciyar hankali Zakar ta kasance cikin kyakkyawar dama, yayin da Khalid da Layla, tare da sauran shugabannin, suka tabbatar da cewa al'umma ba za ta sake fuskantar wannan barazana ba. Sun tabbatar da cewa zaman lafiya zai iya cika, kuma duniya za ta iya zama mai kyau idan aka haɗu cikin haɗin kai da ƙoƙari. Duk da haka, wannan labarin ya kammala ne da tabbacin cewa a dukkan rayuwa, duk wani ɗan adam yana da damar canza ƙaddararsa, kuma idan aka tunkari ƙalubale da ƙoƙari, za a iya cimma burin zaman lafiya a kowane lokaci.... Ajiyar zuciya Maryam ta sauke "Ado, wannan labarin naka... ban ga komai ba! domin ba koyaushe ake ganin irin labarin hiƙaya mai ɗauke da sarauta da jarumtaka ba. Amma dai gaskiya yayi daɗi sosai, ya zarce tsammanina." Ihsan ta ɗora da cewa "Hakika, Ado, ka cusa mana soyayya da jaruntaka cikin wannan tafiya. Na ji kamar ina cikin masarautar nan da kaina, kuma na gamsu da labarin da kabamu muddin munason ganin chigaba a rayuwar mu to mu zauna lafiya mu hada kanmu domin zaman lafiya yafi Zama ɗan sarki , shine amfanin kungiyoyi da ake kafawa labarin ya nuna mana amfanin da fushi bashi da wani alfanu a kowane lokaci " John da murmushi a fuskarsa ya kara da cewa "Akwai ƙwarewa sosai a cikin yanda ka zana wannan duniyar mayaƙa. Haka ne gaskiya." suka duka jinjina kai cikin gamsuwa, suna dariya mai sauƙin zuciya, suna jin cewa duk wahalar da suka sha a hanya yanzu tana saukakawa saboda irin wannan nishaɗin da labarin Ado ya kawo musu. Da suka huta, wannan tsohuwar matar da ta taimake su, mai kirki, ta kawo musu wata shawara "Ku saurara, 'ya'yana babu abinda zai fi muku amfani yanzu kamar ku tsaya anan Saudi na ɗan lokaci ku nemi aiki ku tara kuɗi, ku farfaɗo da rayuwar ku kafin ku wuce Dubai, domin Dubai ba wurin da za'a shiga ba tare da kafada ba." Duk suka yi shiru suna nazari dhawarar ta daɗa musu ma'ana a zuciya, domin sun sha wahala, sun rasa abokinsu Yazid, kuma basu da cikakken shirya komawa cikin wahala. Kwana na wucewa, su Maryam, Ihsan, John da Ado suka cigaba da rayuwa cikin aiki boye a Al-Qamar City duk da wahalar aikin da tsoron da ke binsu kullum, sun dage suna addua da fatan alkairi. Wasu ranaku sukan samu rana guda hutu, inda su ke haɗuwa cikin wani ɗan ƙaramin ɗaki da suka haya tare da barin aiki na ɗan lokaci, su ci abinci su yi hira domin su rage wa junansu ɓacin rai. Bayan shawarar tsohuwar matar, su Maryam, Ihsan, Ado da John suka amince da neman mafita. Tunda basu da visa na aiki (working visa), dole suka shiga aiki boye-boye domin samun abin da zasu ci da su rayu. An kai su wani gari na tsakiyar Saudi Arabia mai suna Al-Qamar City — gari mai cike da ƙabilu daban-daban, ba a fiye tambayar mutum takarda sosai musamman idan yana aiki a boye a cikin gida ko wajen aiki mai zaman kansa. Maryam da Ihsan suka fara aiki a wani babban gida, suna gyaran gida da kula da yara (maid work). Ado aka dauka a shagon gini, yana taimakawa wajen ɗaukar kaya da gina bango (labourer). John kuma ya fara aiki a wata small cafeteria yana wanke kwanoni da share-share. Amma... Suna yawan jin tsoron a kamasu saboda yawanci masu aikin boye a Saudi Arabia na fuskantar: Ƙwaci albash Tsangwama, ko kuma kama da kora (deportation). su ɗora zuciya su na yawan addu'a, su na ce wa junansu "Allah yana tare da mai haƙuri." Rayuwarsu yanzu bata da tabbas, wasu ranaku abinci kadan suke ci, Wasu ranaku ko gurfanawa kasa suke yi don kada su fada hannun jami'an shige da fice, Wasu ranaku kuma suna kallon taurari da raye-raye suna mafarkin Dubai da rayuwa mai kyau acikin wanan halin ne suka fara tuna: "Ya Allah! Mun bar gida shekara daya da rabi, yanzu mun kara wata uku, har yanzu bamu isa burinmu ba." Cikin dare ɗaya wata rana... suka ji kiran gaggawa daga Ado yana cewa: "Wani shiri ne na tafiya... akwai wata dama... amma mai cike da haɗari." A cikin yanayi na ƙunci da fargaba, kowa ya fara juyawa cikin tunanin rayuwar su. Maryam, Ihsan, Ado, Yazid, da John sun kasance suna daga cikin wata tafiya mai nisa zuwa Dubai, suna fata da burin samun sabuwar rayuwa mai kyau. Amma ƙaddara ta kasance mai cike da matsaloli, da ƙyamar wanda ba a zata ba. A cikin haka ne, yayin da suke cikin wani daki mai ƙarancin haske, kowannensu yana tunani game da yadda suke ji da kuma yadda lokaci ke wucewa ba tare da su cimma burin da suka sanya a gaba ba. Sun bar gida, sun sha wahala, amma har yanzu suna cikin damuwa. Wannan rayuwar ba ta cika musu burinsu ba. Wannan lokaci, wata rana, kowanne daga cikinsu yana jin wani iri na kasala da bacin rai. Daga cikin wannan yanayi, lokacin da suke cikin shiru, Ado yana bayyana wani sabon shiri. Ya ƙara cewa: "Wani shiri ne na tafiya... akwai wata dama... amma mai cike da haɗari." Wannan magana ta sanya kowa cikin tunani da kuma jarumta. Ado yana bayar da shawara cewa wannan yana da alaka da wani babban sauyi wanda zai iya zama mai girma ko kuma mai haɗari. Kowa ya fara tunanin wannan dama, amma kuma yana jin ƙarar tsoro daga cikin zuciyarsu. Maryam, Ihsan, Yazid, da John sun koma cikin tunani mai zurfi, suna tambayar kansu: Shin wannan dama za ta kawo musu sauyi? Za su iya tunkarar wannan haɗari da cikakken ƙarfin zuciya? Shin wannan tafiye-tafiye da ƙalubale zai zama hanya mai kyau ko hanyar wucewa daga dukkan matsalolin da suke fuskanta? Suna cikin wannan hanzari na yanke hukunci, wanda zai tsara rayuwarsu gaba ɗaya. A cikin wannan shirin, Ado yana ganin wata hanya mai nisa, mai haɗari da kuma mai zuwa da canji mai yawa haka kuma, labarin yana ci gaba da haifar da damuwa da tunani mai zurfi ga kowane ɗaya daga cikin su zai yiwu wannan hanya ce ta haɓaka kansu ko kuma haɗarin da zai jawo musu ɓarna. Maryam, Ihsan, Ado, da John sun ci gaba da tafiya tare, suna cikin tunanin rayuwar da suka bar baya. Kamar yadda suka saba, sun riga sun saba da juna kuma suna tsarewa da juna cikin zaman lafiya, amma yau, wani sabon yanayi ya bayyana a rayuwarsu. Ado ya kawo musu wata shawara mai ban sha'awa—wani shiri mai cike da haɗari, amma wanda zai kai su ga burinsu na ƙarshe. Ado ya kawo zancen wasu boyayyun matafiya da suka samu izinin tafiya daga Saudi Arabia zuwa Dubai, inda za su bi hanyoyin kasuwanci da damar samun kuɗi. Amma, akwai babban hadari—ana samun tsangwama daga hukumomin kasar, da kuma al'amuran sirri da suka shafi hanyoyin da za a bi. Ado yana tabbatar da cewa wannan hanya zata iya zama hanya mai tsawo, amma a karshe za su cimma burinsu. Wannan shawara ta dawo da tunanin da suka riga suka manta da shi—shin sun yi dai-dai da kasancewa cikin haɗari a kowace tafiya? Amma ko da haka, sun san cewa wannan zai iya zama damar da ba za su iya bari ba. John ya ɗan murmusa, yana kallon Ado da kyau, yana jin kamar wannan shiri zai yi kyau, amma yana jin wata damuwa a zuciyarsa. "Zamu iya tafiya tare, amma a cikin wannan tafiyar, ba za mu iya tantance yadda abubuwa zasu kasance ba," John ya ce cikin shakku. Maryam ta ɗan kalli Ado da zuciya mai nauyi, tana jin wata muryar ƙyama da ta kamata ta yi. "Amma wannan hanyar tana da haɗari. Akwai abubuwa da ba za mu iya ganewa ba." Ihsan ta sanya hannu cikin tafiyar, tana jin tsoro amma kuma tana cikin shauƙi don ganin yadda za su fita daga wannan matsala ta rayuwa. Ado ya kasance cikin tabbacin cewa wannan hanyar ce kawai da za su bi. "Bari ku ƙara zuga, wannan hanya ce mai tsawo, amma kuma akwai wata hanya mai kyau ta samun nasara. Ba za ku yi nadama ba." Sai suka tafi a cikin natsuwa da haɗari, suna shirin tunkarar wannan sabon tafiyar. Wannan shawara ta zama wani babban abu, wanda ya ƙara haifar da tunani da damuwa, amma kuma yana nuna cewa akwai hanyoyi guda biyu a kowace tafiya—dama ko haɗari. Bari mu fara da garuruwan da za su ketare yayin tafiyar. Kodayake suna daga cikin kasashen Gabas ta Tsakiya, garuruwan suna da tarihi mai kyau kuma suna dauke da matukar tasiri a al'adar da kuma yanayin kasuwanci. 1. Riyadh (Saudi Arabia) Riyadh shine babban birnin Saudi Arabia, kuma anan suka fara tafiyar. A cikin wannan gari, Ado da abokansa sun ukku da wasu daga cikin matafiya da ke tafe da su. Riyadh na cike da al'adu da gine-gine na zamani, amma kuma yana da alamar zamanin da ya gabata. Anan suka sami damarmu na shiryawa don tafiya, da kuma sanin cewa a nan ne suka fara dukkanin wannan tafiyar mai cike da haɗari. 2. Al-Qassim Daga Riyadh, sun tafi zuwa garin Al-Qassim, wanda ke da ɗan nisa daga Riyadh. Al-Qassim yana daya daga cikin yankunan da aka fi sanin gona da kuma kayan abinci. Anan, sun tsaya na ɗan lokaci, suna hutu da yin sayayya kafin su tafi ƙasar daga nan. 3. Hail Hail yana daga cikin garuruwan arewacin Saudi Arabia wanda ke da ɗan nisa daga Al-Qassim. Wannan gari yana da tarihi mai kyau, musamman daga zamanin kafin Islama. Yana cikin matsakaicin yanayi, wanda ke cike da tsaunuka da dakunan zamani. Sun yi hutu a nan, suna cikin tunanin ci gaba da tafiyar. 4. Tabuk Bayan Hail, suna tashi zuwa garin Tabuk wanda ke a cikin arewacin Saudi Arabia. Tabuk na da matukar tarihi, yana da ƙasar da ke kusa da iyakar Jordan. A nan, Ado da abokansa sun yi hutu kadan, suna jin dadin yanayin garin kafin su cigaba da tafiya. Tabuk yana da dakin tarihi da ke da alaƙa da Bakar Koran da kuma sauran abubuwan tarihi. 5. Aqaba (Jordan) Daga Tabuk, suna ƙoƙarin tunkarar ƙasar Jordan. Aqaba shine birnin tashar ruwa da ke a ƙarshen Gabas ta Tsakiya. Anan, suna ɗaukar jirgi zuwa Dubai. Aqaba yana da darajar tattalin arziki saboda yana da tashar jiragen ruwa, kuma yana da muhimmanci wajen hada-hadar kasuwanci tsakanin kasashen Gabas ta Tsakiya da ƙasashen duniya. A cikin wannan wuri, suna jin ƙara samun nasara. 6. Sharm El Sheikh (Egypt) Daga Aqaba, suna tashi zuwa Sharm El Sheikh a ƙasar Masar, wanda ke a bakin tekun Bahar Maliya. Wannan birni yana da kyau da kuma kyawawan abubuwan da suka shafi yawo. Sharm El Sheikh yana daga cikin manyan wuraren hutawa na duniya. Sun yi hutu a nan don samun sauƙi daga hanyar tafiye-tafiye kafin su ci gaba. 7. Suez Canal (Egypt) A cikin tafiye-tafiye na yau da kullum, suna shige ƙasar Masar ta hanyar Suez Canal, wanda shine hanyar ruwa mafi muhimmanci a duniya. Suez Canal yana da matukar tasiri a tattalin arzikin duniya, kuma yana kasancewa mai muhimmanci a wajen hanyoyin kasuwanci. A cikin wannan lokaci, suna ganin irin wahalar da ake fuskanta wajen tunkarar wannan hanyr 8. Madinah (Saudi Arabia) Daga Tabuk, suna yin ɗan tazarce zuwa Madinah. Wannan garin yana daga cikin garuruwan tsarkaka na Musulunci, kuma yana da matukar daraja ga Musulmai. Anan, sun tsaya don ɗan lokaci don yin ibada da jin dadin yanayin garin kafin su tafi zuwa Dubai. Wannan yana cikin wata dama ta rayuwa domin ba kowanne mutum ne zai samu damar zuwa Madinah ba. Wannan ƙarin lokaci da suka yi yana ba su damar sake tunani da shirya matakan gaba. 10. Makkah (Saudi Arabia) Bayan Madinah, suna tafiya zuwa Makkah, wanda shine garin da ke dauke da Ka’abah, cibiyar ibadar Hajj. Makkah yana da muhimmanci sosai a zuciyar kowanne Musulmi. Anan, suna samun lokaci don yin addu’o'i da tunanin yadda za su ci gaba da tafiya. Sun sami damar sabunta ƙoƙarinsu, suna tunanin tafiyarsu kuma suna shirin ƙoƙarin haɗuwa da burin su na zuwa Dubai. 11. Mecca to Jeddah (Saudi Arabia) A nan, suna shiga Jeddah, wanda shine babbar tashar jiragen ruwa ta Saudi Arabia. Jeddah yana da mahimmanci sosai wajen kasuwanci da tafiya tsakanin Saudi Arabia da sauran kasashen duniya. Yayin da suke nan, sunyi duba kan tafiyar su gaba da kuma koyan sabbin hanyoyin samun nasara da kuma kasuwanci a Dubai. 12. Bahariya Oasis (Egypt) Daga Jeddah, suna tashi zuwa Bahariya Oasis a cikin ƙasar Masar. Wannan wuri yana daga cikin wurare na ƙasar Masar da ke da muhimmancin tarihi, kuma yana da damar sanya mutane cikin shauki. Sun tafi ta cikin wannan ƙasar don samun sabbin abubuwa da kuma zama cikin wani sabon yanayi na rayuwa, ko da yake suna cikin hanyoyin tsallaka zuwa Dubai. 13. Cairo (Egypt) A cikin Cairo, babban birnin Masar, sun tsaya na ɗan lokaci kafin su ci gaba. Cairo yana dauke da tsohon tarihi, wanda ya hada da gidajen tarihi na Faraon, matsayin gine-ginen zamani da kuma kasuwanci mai yawan amfani. A wannan lokacin, suna samun damar hutu da kuma ɗaukar wasu sabbin dabaru a cikin tafiyar su zuwa Dubai. 14. Suez (Egypt) A cikin Suez, suna shige cikin wani lokaci mai zurfi da kuma haɗari a cikin tafiyar. Wannan wuri yana da muhimmanci musamman saboda Suez Canal wanda ke haɗa Bahar Maliya da Bahar Meditranian. A wannan lokaci, suna amfani da damar da ke akwai don tsara hanyar su zuwa Dubai. 15. Sharjah (UAE) Daga Cairo, suna tunkarar ƙasar UAE ta hanyar Sharjah, wanda ke kusa da Dubai. Sharjah yana da muhimmanci wajen kasuwanci da al'adu, kuma yana da wurare na musamman da ke ba da damar jin daɗin rayuwa. Sun tsaya a wannan garin na ɗan lokaci don yin shiri kafin su shiga Dubai da ƙarshen tafiyar su. Garin Madinah: A Madinah, dukkansu sun haɗu, suna cikin yanayi mai sanyi da annashuwa, amma kuma suna jin tsoron mai zai faru a gaba. Wannan garin, mai daraja sosai ga Musulmai, yana cike da dumin tarihi. Daga Madinah, sun fara jin cewa tafiyar su tana da wani dalili mai girma fiye da neman kudi ko dumin rayuwa kawai. Duk da haka, sun bar garin da babban buri – samun nasara, samun sabuwar rayuwa a Dubai. Makkah: A Makkah, kafin su tafi daga ƙasar Saudi, sun samu damar yin tawassul da addu'a a Masjid al-Haram. Sun fara ɗan jin motsin zuciya – ko da yake suna cikin tafiyar da aka tsara, suna haɗuwa da wani matsayi na ruhaniya. Anan ne suka tuna cewa kowanne daga cikinsu yana da burin da yake son cimmawa. Yazid wanda ya mutu a cikin wata ƙasada daga baya yana da tasiri, amma har yanzu yana cikin tunanin su. Kodayake su Jeddah: Bari su shiga cikin Jeddah, wanda ke kusa da tekun Red Sea. Sun samu hutu na ɗan lokaci kuma suna tunani kan burin da suka haɗa da kuma irin ƙalubalen da za su fuskanta daga ƙasar Masar zuwa Dubai. A nan ne suke shaƙatawa tare da tunani kan waɗannan lokutan da suka yi a cikin tsawon shekara biyu da kuma yadda rayuwa ke canzawa da sauri. Sun kuma sake jin kasadar da ke tunkaro su, kuma kowane daga cikinsu yana haɗa burinsa. Cairo: Daga Jeddah, suna tunkarar Cairo, babban birnin Masar. Cairo yana ɗauke da kyau da kyan tarihi, amma da yake suna cikin matsanancin yanayi, suka ɗauki lokaci don duba kansu. Daga wannan matakin, suna karɓar nasarar samun shahararrun damar kasuwanci da kuma sabuwar rayuwa a cikin Dubai. Cairo yana taimakawa su wajen fahimtar cewa tafiyar tana da mahimmanci sosai, kuma suka tsunduma cikin tunanin yadda za su tafiyar da harkokinsu da kyakkyawar fata. Tafiyar ta kasance mai wahala, amma kowane daga cikin su yana da burinsa da yake son cimmawa a Dubai. Ko da yake suna cikin ƙalubale, suna jin daɗin tafiya tare da hadin kai, suna fatan burinsu za su cimma. Fans tafiya da yayi nisa yanzu me kuke tunani zai faru next? https://chat.whatsapp.com/Bd1Zu1cwIO81A7rrATd4Cu Share Fisabillilahi 💕 duk wacce tayi share page nan Allah ya biya mata buƙatar ta na alheri ko namiji ne ko macce fans na wannan littafin ina matukar godiya da yanda kuke nuna min kulawa na musamman ⭐ Hawaye Ihsan ta share da handkif tana sharewa wasu na tahuwa Iman ce ta rungume ta haka sauran duk suka matso " Mommy kiye haƙuri ke chigaba da bamu labarin Bayan wata, shin bayan mutuwar Uncle Yazid me zai faru bayan Daddy Ado yagama bada labarin su Layla me yasa ke kaka tsaya kina wannan kukan shin akwai wani abu da zai faru ne ko Mommy?! cewar Little Yazid " Iman ce ta dafa kafaɗar sa Bro Yazid ne kaina wannan lamari ya tsananta tunani na shin ne Mommy ke nufi a wannan labarin shin Mommy ce Ihsan da Daddy Ado kai kuma kaine Yazid na cikin labarin Matafiya Biyar , to wacce ce Maryam ina John duk bamusansu ba ? Mommy please talk chigaba da bamu labarin yanda yakasance? muna bukatar sanin asalin iyayen mu , muna bukatar jin tarihin mutanen Bayan wata mun fahimci cewa duk labarin nan ke da Daddy kuna cikin wannan labarin ina labarin John shin bai bayar da labarin sa bani kamar Uncle Yazid? ina labarin Maryam shin kun samu burin ku shin akwai wani mummunar abu ne da yasa ki ka tsaya kika fara kuka ya akaye kuka dawo Nigeria da zama? Ihsan ta kalli yaran nata da ido mai cike da hawaye, tana ƙoƙarin murmushi amma zuciyarta na kuna. “Eh... ku ne dalilin da yasa muka yi wannan tafiyar, ku ne mafarkin da muka tafi nema a Dubai. Amma kafin ku gane komai, zan gaya muku gaskiya game da Maryam da John...” Ta kalli Ado, wanda ya sauke numfashi tare da jinjina kai. Ado: “Maryam... ita ce matar da ta fi ƙarfin zuciyarmu gaba ɗaya. Daga cikinmu biyar, ita ce mafi tsayawa akan gaskiya, ittace likitan mu mai kula da lafiyar mu kuma ita ce ta fi shan wahala a karshe amma sai ta ɓace… ban san ko ta mutu ba ko kuwa rayuwa ta ɓoye ta labarinta yana da nauyi.” Ihsan: “John... shine Christian ɗin da ya fi kusa damu Ya kasance dan ci gaba da wayewa sosai. Amma yana da boyayyen sirri da bai gaya mana ba har zuwa lokacin da muka kusa isa Dubai. Ya rabu da mu a Sharjah...” Little Yazid ya furzar da iska tare da zare ido “Don Allah Mommy, Daddy… ku ci gaba mun cancanci jin komai.” Ihsan ta gyara zaman ta: “Zan gaya muku komai zan gaya muku yadda aka juyo garin da muke yanzu, yadda rayuwa ta sauya mana, yadda Dubai ta rikita zuciyarmu, kuma yadda muka dawo Nigeria da daraja da yawan asara amma da farko… ku zauna ku saurara domin Bayan Wata bai kare ba…” BAYAN WATA SABON SALO TYPING BY NARNAH KANWAR SOJA ✍️✍️ 08101235739 SHARE FISABILLILAHI https://chat.whatsapp.com/Bd1Zu1cwIO81A7rrATd4Cu 💫⭐BAYAN WATA 💫⭐ sabon salo By Narnah Kanwar soja Page 36 A part nasu na ofis, an kawata wajen da jan balloon da kyanduna masu ɗanɗano wakokin birthday suna tashi a hankali a cikin sautin iska, kowa da murmushi a fuska yana jiran fitowar ta. Iman ta fito cikin rigar fara da ke haskaka fatarta, ga agogon hannunta mai ɗaukar ido kyautar mahaifinta sai jan lips ɗinta da ke fid da ita tamkar furen jan tulip. cikin nishaɗi, Mufeedah ta ƙarasa ta rungume ta: "Lalle birthday girl yau kin bayyana kamar Sarauniya daga wata duniya.” Iman ta yi dariya ta ce, “Kuma dai ni ce. Amman ke Nana, wallahi yau na haɗu da wani mahaukaci da bai da hakuri. Ya goge motata kuma yana wani cika da isa. ban ma san ko waye ba.” Nana ta tabe baki da cewa, “to ai wasu maza haka suke, kai dai ki kwantar da hankalinki wwani lokacin wasu suna saka fushi ne don a kula da su.” A nan Mufeedah ta miƙo mata ƙaramin kwali da rubutaccen taken "To my Queen Sister". ta bude, sai ta ga wani ƙaramin turare Zara Femme Pink, da ɗan rubutu cikin ƙananan haruffa: "Domin Sarauniya kamar ke — mai ƙanshin kirki da farin ciki." Sai Habeeb da Khalid abokan aikinta suka miƙo mata ƙananan kyaututtuka ma: Habeeb ya kawo mata karamin murfin fensir da ke ɗauke da sunanta: "Iman B." Khalid kuma ya kawo mata kwali da cupcake ɗin da aka rubuta da icing: Happy 18th, Miss Sunshine! Iman ta rufe baki cikin dariya da godiya tana cewa: "Na gode sosai, wallahi kun burge ni!" Nana ta matso da ɗan kwali mai launin zinariya, ta ce: "Wannan naki ne daga garesu duka ki buɗe dare ne." Da wannan murnar, Iman ta rike kwali tana murmushi, zuciyarta cike da ƙauna da gamsuwa — bata san cewa wata sabuwar rigima na gab da shigowa rayuwarta daga hannun wani “mahaukaci mai kyau” mai suna Najeeb ba... Suna cikin dariya da tattaunawa, sai suka ji ƙarar ƙofa tana ƙara. Gabansu ya ɗan fadi kaɗan, kowa yana zaton wata muhimmiyar taro zata fara cikin nutsuwa da kamala, ogansu — Alhaji Faruq — ya shigo da murmushi yana tafe da wata babbar leda mai kwali. "Assalamu alaikum jama’a," ya faɗa da fara'a. "Ina fatan ba na hana muku shan cake na birthday ba?" Iman ta yi dariya cikin mamaki, ta ce, "Oga! Kai har ka sani?"ya matsa kusa da ita ya ce, "Ai Iman, irin aiki da halinki yana sa mutum ya tuna ranarki daga ofis gaba ɗaya, munyi shawara mu nuna miki godiya da ƙauna." Ya ajiye kwali a gaban su, yana buɗe shi. Cake ne mai tsayi guda biyu, an rubuta a kai da topping mai kyau: "Happy Birthday Iman B. — Our Pride, Our Smile." Iman ta rufe baki tana dariya da ɗan murmushin kunya ta ce, "Na gode sosai oga, wannan abin ya bani mamaki!"Ogan ya ɗaga hannu ya ce: "To mu yanka mana, kafin kiyi kuka!" dukkan su suka yi dariya, sannan ogan ya ɗauki wuka ya miƙa mata da cewa, "Ke ki yanka, mu ci, mu murna ba kowace rana ake haihuwar Sarauniya ba." Iman ta ɗauki wuka, cikin sanyi da natsuwa, ta yanka gefen cake ɗin su Habeeb da Nana suka fara tafi da hura iska kamar an yi bikin aure. Ihsan ta ɗauko wayarta tana ɗaukar bidiyo, yayin da Nana ke rera: "Iman dinmu ce fa! Mai kwalliya, mai kamewa!" Su duka suka ci cake da farin ciki, zuciyarsu cike da kauna da haɗin kai, ba tare da sanin cewa daga nan gaba ne labarin zuciya da juyin rayuwa zai fara bayyana... Gaba ɗaya suka zauna cikin kwanciyar hankali, daga ita sai Little Yazid da yake ta dariya kamar wanda aka shafa masa zuma. "Allah ya taimake ke da irin nane," yace yana dariya, "sai na bikin da mari ma kin ɓata min. har yanzu baki iya mota ba? zan gayawa Daddy ya ƙwace miki motar!" Matsowa tayi kusa da shi da sauri, ta dafe hannunsa. "Haba Bro Yazid, please kar ka gayawa Daddy. I'm sorry, please don't do it." daidai lokacin suka lura da su Mommy da Daddy sun sauko. Nan suka kama nutsuwa kamar ba su da laifi "Daughter," cewar Ihsan tana kallonta da kulawa, "Ina ganin kamar barar abu kike yi wajen Yazid." "Noo Mommy, kawai hira muke," ta amsa da murmushin yaudara. "Shikenan," Ihsan ta ce cikin sanyin murya, tana kallon su gaba ɗaya. "Zan ƙara samuku labarin Bayan Wata a daren yau... Shin kun shirya jin karshen wannan tafiyar?" Gaba ɗaya suka nitsu, suna sauraron Ihsan. Ado kuma, yana zaune yana lumshe idanu kamar yana ganin wani hoto daga baya cikin zuciyarsa... A lokacin da suka iso bakin garin da suka nufa – garin da ya rage kafin su isa inda suka yi fatan samun sabuwar rayuwa suka zauna a ƙarƙashin wata tsohuwar bishiyar gawo. Rana na shirin fāɗuwa, iska na busawa da sanyi mai ɗauke da ƙura da ƙamshin wahala. Kowa na cikin tunani mai zurfi: su Maryam da Ihsan na ɗauke da damuwar mata da mafarkin gida; ta na lumshe idanu kamar mai adana sirrin zuciya; Ado kuwa sai kallon sararin sama yake yi kamar yana neman amsa daga sama.Sai John ya kalli kowa, yana murmushi da ƙaramin dariya mai sa nutsuwa. "Ku saurara," ya ce, yana zura ido ga kowannensu, "zan baku labarin nishadi – na gaskiya domin mu ɓata lokaci mu manta da ƙuncin hanya." kowa ya juyo gare shi. Ihsan ta ɗago kanta tana fadin, "Toh John, bari mu ji. Amma kar ya kasance na ban tsoro fa." John ya dariya. "Wallahi ba tsoro ba ne, sai dariya, amma ku zauna lafiya ku saurara." sai ya fara da murya mai ɗauke da salon barkwanci: ................................... https://chat.whatsapp.com/Bd1Zu1cwIO81A7rrATd4Cu 💫⭐BAYAN WATA 💫⭐ sabon salo By Narnah Kanwar soja 08101235739 PAGE 37 Kauyen Tsuntsuwa ƙauye ne da ke labe a cikin zurfin wani kwari, inda duwatsu suka zagaye shi kamar gadin sirrin duniya. Rana tana faɗuwa kamar kullum, amma a Tsuntsuwa, faɗuwar rana na nufin ƙarewar alfarma domin daga nan ƙauyen yana komawa hannun duhu da shiru. Babu lantarki, babu hanya mai kyau, babu makaranta sai ƙarar kwanoni da gudun yara, sai shawagi da kururuwar matan da ke wanke wanke a bakin rafi , idan ka taka ƙasa a Tsuntsuwa, zaka ji ƙurar da take ɗauke da tarihin shekaru ana cewa kauyen yana da shekaru fiye da ɗari uku, kuma babu wani mai rikodin tarihi da ya rubuta komai a kansa. Gidajen mudu ne, daga laka da kwalli, sai rufin buhu da zogale gidan mai unguwa shine mafi girma, amma da ka shiga zaka san sarki da talaka daidai suke mutane suna rayuwa cikin sauƙi da daraja, amma jahilci ya shafe zukatan su har ya zama girma. A tsakiyar kauyen akwai tsohuwar bishiyar tsafe-tsafe, wacce kowa ke shakkarta ana cewa an binne aljanun da suka kafa Tsuntsuwa a karkashin ta a kusa da bishiyar kuma akwai rijiya mai zurfi da aka hana yara kusantar ta ance rigima a ciki ke jawo mutuwa wasu kuma na cewa “duk mutumin da zai yi hankali a Tsuntsuwa, sai ya manta da hankali nasa.” A cikin wannan ƙauye ne aka haifi Kashifa wata kyakkyawar halitta mai kimanin shekaru goma sha ukku fari a launi, doguwa a halitta, mai idanu dara-dara kamar dare ba kowacce yarinya bace ba; facce ce ta ƙauyen. Ita ta tashi cikin cikin duhun jahilci da namun daji, amma zuciyarta cike take da haske da tambaya. Kashifa yarinya ce mai kwaikwayo, mai yawan tambaya, mai son saka ido cikin komai ta fi ƙarfin 'yan mata, ta fi kuzari da saurayi. Idan Kashifa ta ce zata shiga rafi, kowa zai hau tsaye; idan ta ce zata hau itace, to ka yi shirin cin kwallon kunya. Tsakar rana rana na dumama tamkar ana soyayya da rana kai tsaye. Kashifa da ƙawarta Fatu suna zaune a ƙarƙashin bishiyar ɗan kanzon su na gunduma idon su biyu sai kalle-kalle suke yi, suna nazarin hanyar da zata fi sauƙi su kutsa gonar Mangoron Malam Dandago. "Kashifa wallahi yau zan ci sabuwar mangoro!" cewar Fatu tana ɗaura zaninta kamar jaruma a film. "Fatu ki rage murya mana! ki manta da yadda ya kama Mu’azu ya sa shi tonon kasa da cokali har sai yazo har ƙasa!" Kashifa ta faɗa tana dariya. "Eh mana, amma Mu’azu gajere ne, mu fa muna da gudu!" da sallama suka zura kai cikin gonar, suka fara zabga wa mangoro mari. Mangoro na faɗowa kamar ana jefar da azurfa daga sama. Fatu ta zuba cikin buhun riga, Kashifa kuma tana tsince mai laushi. Cikin kwana da wani, muryar Malam Dandago ta daki kunnensu kamar karar kararrawa "A’a yau na kama ku! wai ni da gonata ba komai ba ce?!" Kashifa ta zura mangoron hannu cikin hijabi, Fatu kuma ta jefar da nata tana fadin: "Gudu Kashifa gudu! Dandago ya fito da sanda!" gudu suka rika yi kamar an sako su daga rijiyar sha'ani. Fatu ta ruga ta faɗi ta tashi, Kashifa tana cewa: "Idan ya kama mu wallahi sai ya sa mu shan ruwan tafki da cokali!" Dandago ya biyo su amma sai ya tsaya yana huci da tsaki: "sai dai in kama ku da duban hankali... amma wallahi sai na ce da iyayenku!" Suna isa bayan gida, suka shaƙa juna da dariya suka faɗa a kasa suna juyi Fatu ta ce: "wallahi wannan shine mafi zafi da daɗin mangoro da na taɓa ci!" Yayin da gudu ke neman sufi sauri da iska, Kashifa ta ruga da kafa irin ta gudun “Marathon”, bata ko kallon gaba tsautsayi “Yiiiiiiii!” wata kara ta tashi! Gani aka yi wani tsoho ya yage ya zube a ƙasa, wata leda mai fassarar “Egg carrier from heaven” ta baje, ƙwai ya watsar tamkar an watsa jinin rake! “na shiga ukku na lallace !” Kashifa ta tsaya cak tana fadin: "Wayyo na shiga uku! Wallahi ban ganka ba Malam!" Tsohon ya tashi da cikar ƙwazo da huci yana nunata da yatsa: "Ni Malam Sambo ne! Na shekara biyu ina kiwon kaza don in samu na kasuwa, ke kuma cikin 'yan saniyar ware kike zo ki lalatamin arziki da gudu!" Fatee ta taho tana dariya tana rik'e ciki tana faɗin: "Kai Kashifa! kin lalata kwai! Wallahi ke ce makashiyar kwai kaza' yanzu!" Kashifa tana tafa hannaye tace: "Wai Malam don Allah ya rage fushi! Wallahi gudun Malam Dandago muke, shi kuma sai na makale a jikinka." Malam Sambo ya dumfari Kashifa yana faɗin: "To wallahi sai kin biyan kudin kwan nan! ko kuma ki zo ki kwana da kaji na in zaki gane yanda ake kiwon su!" Fatu ta daka tsalle tana faɗin: "Ai wallahi Kashifa sai kin yi 'nagudar kaji! kin lalata arzikin mutumin kirki!" Kowa da kallo a kauyen, yara sun zo suna tsugunne suna tattara 'yan kwan da suka rage da rai. wata kaka tace: "sai addu'a ya shirya 'yan mata yanzu, gudu kawai ba kallon gaba!" Ya zata kaya tsakanin Malam Sambo da Kashifa?... https://chat.whatsapp.com/Bd1Zu1cwIO81A7rrATd4Cu BAYAN WATA SABON SALO BY NARNAH KANWAR SOJA ✍️✍️ 08101235739 SHARE FISABILLILAHI MASU TAMBAYA DA WANDA SUKE KARATU KAR KU MANTA CEWA JOHN NA BAMU LABARIN KASHIFA NE INDA SABON SALO YA SHIGO LABARIN DA CEWA IHSAN DA ADO MA'AURATA NE SUNA BAWA YARAN SU LABARIN BAYAN WATA LITTLE YAZID DA IMAN . *********************************** PAGE 38 Wani ƙwarya-ƙwarya rikici a tsakiyar ƙauyen tsuntsuwa Kashifa na tsaye a gaban Malam Sambo, jikin sa duk ya baɓɓare da kwai, fuska ta kumbura da fushi kamar zai lashe duniya. Fatu dai tun can tuni ta juya gefe kamar mara lafiya da gudu. "Wallahi Kashifa, yau zaki gane cewa ni ba ɗan wofi bane! wannan kwai zan siyar ne a kasuwa gobe!" ya daka murya da karfi Kashifa ta runtse ido, ta ce da wata muryar tausayi, "to Malam ai ba da gangan bane... Ka sani dai ni yarinyar da bata da laifi ce..." "Karya! Karya nake ji! Idan kin dafa ni da gangan ko a'a, sai na ɗau fansa!" Kashifa na kallon shi da alamar rauni da kuka, ta sunkuya kamar mai neman gafara mutane sun tsaya gefe suna jiran yadda rikicin zai kare. Amma kafin ya ƙara magana, Kashifa ta zaro ƙasa daga gefen hanya – daidai wani dattin laka da ruwan kwai a ciki – ta fizga hannu kamar zata mika masa hakuri… sai kawai ta watsa masa duka a fuska! "Kai! Idona! Idona Kashifa!" Malam Sambo ya kama ihu yana taka rawa, hannunsa na gogewa cikin ido da kwai da laka. Mutane suka saki dariya. "To wallahi malam, daga yau ka sani, ba a hura mini ido da kwai kuma a bani cin mutunci ni ce Kashifa ƴar Kulu, ba’a tsorata ni da kwai ba!" Sai wata mata ta fasa dariya tana cewa: "Allah ya isa! Wannan dottijo yaci karo da Kashifa ƴar magajin dare! ai sai dai ya wanke ido da ruwan daddawa!" Kashifa ta fizgi ƙafafunta da karfi, ta fasa gudu tana cewa "In ka gama kuka malam ka bar hanyar mangwaronmu!" Yara suka biyo ta da dariya da ihu, wasu suna taɓa Malam Sambo da: "Malam, munce kar ka yi wa Kashifa magana, ai kace kai dodo ne!" suna shigowa gida kamar gwaggwabar iska — Mangoro a hannu, dariya a baki, turɓaya a ƙafafu. Kakarsu, Inna Mairo , na zaune bisa tabarma tana tsuma kayan ƙauye: kifi mai ƙamshi, dambu da kwai da aka bar a kasa saboda tashi tana sanye da mayafi mai datti wanda ba’a iya banbance launi ba — kamar tsohuwar barkono da gishiri sun yi aure. "Kashifa! Fatu ! ku daga ina haka da wannan yunƙuri kamar an aiko ku daga Sahabbai?" Kashifa ta ajiye mangoron ta kamar zakaran da ya lashe dambun masara. "Inna, ba laifi bane idan yaro ya ci abinci daga gonar da Allah ya halitta! ai ba mu sace ba, mu dai ɗiba muka yi!" Fatu ta karɓa da cewa: "Inna kuma Malam Sambo ya ce zai ga mana kashi saboda an buge shi da kwai! Wallahi da yaga halin Kashifa, ya gane ba buɗa-baki ba ce." Inna ta girgiza kai tana dariya: "Kashifa, ke ba mace bace ke muguwar tsuntsuwa ce da aka haifa da kafa biyu da laɓɓe guda biyu! wata rana zaki tada ƙauyen nan gaba ɗaya!" Fatu na gefe tana jujjuya mangoro tana cewa: "To inna tunda muna da wannan ɗakin garwaya na kaɗan da ke da firam mai rami, sai mu zauna mu huta mu ci mangoro." Kashifa ta haye tabarma suka zube a cikin ɗakin ƙanana: gadon kara biyu, tulu mara aiki, da bokiti mai fashe a gefe. Sun jera mangoron a cikin kaskon tuwo, sai su ce:"Wannan shi ne gatan mu a yau jikan mangoro da dare cikin dakin tsohuwa!" Kaka ta ajiye gishirin da take tumshewa, ta ce: "Sai ku san da safe zaku tashi da gudawa — in Malam Sambo ya shigo da sanda ku san ba satar mangoro ake yi ba." Kashifa ta ɗan buɗe kofa tana kallon waje, sai ta ce "Inna idan ya zo, mu turo kwai da dambu sai ya koma da burin shi." wani irin ihu da hayaniya ya tashi a waje kamar ana kwasar mutane zuwa Llahira. Kashifa da Fatu suna tsakiyar ci mangoro, sun kasa ci sun kasa hadiyewa kamar tsuntsaye da suka hango baƙin gizo. Kaka Inna Mairo ta ja zani ta fito, tana zare idanu da sandarta a hannu. "Wa ke ihu a kofar tsohuwa haka?! Ko dai gobarar rijiya ce?!" sai kawai ta hango Malam Sambo, mai mangoro da wasu maza biyar, kowanne da sanda ko kasko a hannu, wasu suna da kwai a riga sun kwara musu. Idanunka su sha. Malam Sambo na ihu yana cewa: "Ina Kashifa! wacce ta buge ni da kwai ta kuma kwace mangoro kamar Allah ya sauke su a saman gonar mutane?!" Mai mangoro ya ce: "Wallahi in ban ga ta ba yau, sai dai an zo da karar kwashe gawa a kwashe ni da zuciya!" Kaka ta dafa bango tana shan numfashi kamar mai zazzaɓi. "Wayyo ni Mairo wannan Kashifa zata bani tabo a ƙarshe ashe mangoro da kwai suka jawo min rundunar maza a kofar gida?" Kashifa ta leƙo daga ƙofar ɗaki, tana tafe da ɗan kwano cike da goro da mangoro da dan buhuna a wuya, ta ce: "Malam Sambo... wallahi bugeka da kwai ba da gangan na yi ba amma ka duba lafiya da shan kwai da magani , ai komai da lada." Malam Sambo ya ja numfashi ya daka tsalle, "Wato kin taya ni ci gaba da hauka? Ku fito! Ku fito ku fuskanci ƙaddara!" Fatu ta ce: "To malam mu fito, amma kayi hakuri fa ai mangoron naka ya janyo rikici fiye da gwangwani!" Kaka Mairo ta tsaya tsakanin su da runduna kamar tsohuwar gwarzon soja. "Ku yi hakuri, ku gafarce su gaba dai za mu rama na rantse da sandar nan ba zasu ƙara ba."Malam Sambo ya ce: "Ai sai sun gyara gonata kuma sai sun bani kwai hamsin na fansa! kuma...!" Kashifa ta yatsine baki ta ce "to me kuma? sai a ce mu biya da yawu kenan?" "wallahi malam..." ta ce tana sunkuyar da kai, "...ina so na ce maka..." kawai ta ɗibo ƙasa a hannu — CHUWA! — ta watsa masa. "Ahhhhh! ido na! wayyo mangoro na!" Malam Sambo na birgima yana rike ido Kashifa da Fatu suka yi sukuwa kamar an aiko su daga sama. Fan's ya wannan page nin ina fatan labarin Kashifa na kayatar da zuciyar ku mujeee zuwa muga karshe labarin Kashifa.. Narnah ƙanwar soja ✍️✍️ https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC BAYAN WATA SABON SALO BY NARNAH KANWAR SOJA ✍️✍️ 08101235739 SHARE FISABILLILAHI MASU TAMBAYA DA WANDA SUKE KARATU KAR KU MANTA CEWA JOHN NA BAMU LABARIN KASHIFA NE INDA SABON SALO YA SHIGO LABARIN DA CEWA IHSAN DA ADO MA'AURATA NE SUNA BAWA YARAN SU LABARIN BAYAN WATA LITTLE YAZID DA IMAN . *********************************** 1 / 6 / 2025 PAGE 39 Yayin da rundunar maza ke zazzaga ihu da gudu Kashifa da Fatu suka nausa wajen rijiya, rigima na biye da su kamar gobara a daji wani daga cikin mazajen ya hango inda suka nufa ya yi kara: "kai! kada ku shiga hanyar rijiya mai hatsari! ai an hana kowa wucewa can tun shekaru masu yawa!" Sai dai Kashifa da gudunta na agwagwa a iska, ba ta ji komai ba Fatu na kiranta tana haki: "Kashifa! Kashifa! daga nan ba wucewa! Sarkinmu ya ce ya hana zaki mutu ne!" Kashifa na cigaba da tsalle kamar ƙaramar damisa sai gashi ba zato, ta shige har tsakiyar hanyar rijiyar. Fatu ta tsaya cak! tana haki, tana duban baya da gaba, tana jin saukar ƙafafun mazan da suka tsaya su kansu suna fargaba. mun shiga ukku !” wani daga ciki ya furta. “Yarinya ta shige hanyar da sarki ya ce shaidanu ke rayuwa a can.” Malam Sambo ya ja baya da sassarfa: “Ni dai na riga na ce mu dawo ido ɗaya ya isheni…” Fatu ta fashe da kuka: “Kashifa! ki fito wallahi ba wanda zai kamamu. ki fito kafin wani abu ya same ki!” sai dai an wayi gari — Kashifa ta ɓace cikin hayakin rijiya. Wata ƙasa ce mai fashewa da iska irin ta tsufa, ana jin ƙarar iska tana kiran sunanta kamar an saka mata sunan a cikin guguwa: “Kaaaashiiifaaa… Kaashiiifaaa…” Fatu ta tsugunna, tana kuka kamar karamar yarinya "wayyo Allah, don mangoro ne da kwai Kashifa ta shiga wuta ta mutu ta bi iska " Malam Sambo ya ja sanda ya ce: "Wallahi wannan yarinya ta kai mu ga hauka. ba zan sake binta ba." Kaka Mairo da ta iso da gudu ta tarar da Fatu a kasa, sai ta ɗauke ta da duka sanda, tana cewa: “Ke , kin kai diyata ga rijiya mai tsafi? wallahi zan buga ki har mangoron ya fito da kansa!” Washe gari... rana bai ko fara hango ƙasa ba, sai ga garin ya cika da hayaniya. A kofar hanyar rijiyar nan mai hatsari, mutane sun taru kamar ana raba sadaka: dattijai, matasa, yara da kowa na firgice, wasu na hawaye. Sarki Idris da rawanin sa mai fadi, ya iso cikin takun mulki. gaban sa akwai fadawan sa, kuma Malam Sambo yana bin bayansu da sanda a hannu, yana yatsina fuska kamar wanda ba ya jin daɗin shiru. Wani dattijo ya yi magana cikin murya mai ƙarfi: “Shekaru 300 da kafuwar kauyen nan kuma kowa yasan hatsarin daki tattare da hanyar nan kenan da aka hana wuce wannan hanya. duk wanda ya shiga bai fito ba ashe yau yarinya ‘yar gidan Mairo ta shiga!” Sarki ya kalli hanya da idon tsoro da mamaki: “Wannan ba wasa ba ne akwai abin da ke faruwa a nan cikin.” Kaka Mairon tana kuka tana tsugunne: “Sarki ka ceci jikan ta… Kashifa bata da hankali, wallahi kawai satar mangoro ce ta jawo mata shiga banza.” Fadawa na kalla juna suna girgiza kai. wani ya ce “Wallahi ko kuwa jinnai na nan me ya sa ba wanda ke rayuwa idan ya shiga?” Sai ga Fatu da kai a ƙasa, tana tsugunne tana hawaye kamar ruwan sama: "Ni ce na jawo ta nice nace mu je ai da ban ce mu ɗebo mangoro ba..." Sarki ya ce: “Shiru! A turo malam bori a san menene ke faruwa ta mutu ko zata ko akwai rayuwa kuma a ajiye alƙalami da lauje a rubuta wannan rana, domin tarihin gari ba zai manta da ita ba.” Takalmin Kashifa aka tsinta a bakin hanya da jinin yatsar ƙafa a gefe.Wani tsoho ya furta da harshen kauye: “Idan Kashifa ta fito da rai, to akwai sirri. kuma akwai wuta a cikin ruwa.” Washe gari... Garuruwa uku sun haɗu a kofar hanyar rijiyar da aka daina bi tun zamanin Sarki Gidado. Mutanen kauye da Sarki Idris, dattawa da malaman tsafi sun taru kowa da dariya mai ƙarewa da damuwa mara iyaka. Kaka Mairo na kuka da kururuwa, tana ta kiran sunan Kashifa da murya mai firgita Fatu ta durƙusa gaban Sarki, hawaye na gangarowa daga idonta: Sarki Idris ya juya ya kalli masu bori “shin me yasa babu wanda ya taɓa shiga ya dawo? me ke ciki? mun san aljani ne ko tsafi?” Shehu ya girgiza kai cikin tsananin fargaba: “ bayan shekaru 300, ma’anar wannan hanya ta ɓace a cikin tarihinmu. Littafin duhu ne ya ɗauke ta amma duk wanda ya shige ta ko mutum ne ko dabba ba a taɓa ganin sa ba ko jin sa.” Jama'a suka hau ihu “Kashifa! Kashifa! A Sarki Idris yace cikin kururuwa “ba wanda zai kusanci wannan hanya! a kafa doka — a fitar da sanarwa! wanda ya sake yunƙurin shige hanyar nan zai fuskanci hukuncin kauye. amma yanzu...a kewaye hanyar nan da shaida ko bayan mutuwar ta sarki magana kiyaye zaiga alamar bazai iya ƙetarewa baa maso bori suka zauna cikin shiru, kowa ya durƙusa, zuciya cike da ɓacin rai da tsoro. a can cikin daji... shiru ne tsit. kamar ba a taɓa rayuwa ba a duniya.... Narnah ƙanwar soja ✍️✍️ https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC BAYAN WATA SABON SALO BY NARNAH KANWAR SOJA ✍️✍️ 08101235739 SHARE FISABILLILAHI MASU TAMBAYA DA WANDA SUKE KARATU KAR KU MANTA CEWA JOHN NA BAMU LABARIN KASHIFA NE INDA SABON SALO YA SHIGO LABARIN DA CEWA IHSAN DA ADO MA'AURATA NE SUNA BAWA YARAN SU LABARIN BAYAN WATA LITTLE YAZID DA IMAN . *********************************** 03 / 6 / 2025 PAGE 40 Bayan kwana bakwai da ɓacewar Kashifa… ƙauyen tsuntsuwa tabbataccen duhu ya koma kamar baya da haske ba a jin dariya a ƙofar rafi, ba a ƙara ganin yara suna wasa da kekuna a kasan itacen tsamiya kowanne gida ya ɗauki shiru, kamar ana azumi na musamman. Kaka Mairo tsohuwar dattijuwa mai murya irin ta ƙwarƙwasa, ta koma ta hana kanta bacci. Zuciyarta na ci gaba da tafasa da zafin ɓacin rai da rashin yarda idan aka ce mutum ya ɓace cikin iska, ita dai bata yarda da hakan ba. "Kashifa zata dawo itta ce Kashifa… mai tsalle tsalle da dariya kamar kurege. wane iska zai ɗauke ta?” A daren nan ne, aka ji Kaka Mairo tana kuka har cikin dare, tana rugumowa zaninta kamar tana taƙama da abin da ya fi ƙarfin zuciya: “Na raini Kashifa tun tana jaririya tasha nonon Zainabu a hannu na ina za ta je? Ai idan rijiya ta haɗiye ta, to ni zan buɗe ta da karfin soyayya ta!” Dattawan kauye sun rinka shigowa suna lallashi, amma Kaka Mairo ta ƙi daina kuka. H har wani lokaci ma ana jin ta tana kuka cikin bacci tana cewa: “Wayyo Kashifata... mangoro ne ya cinye min ranki.” Tana jin kamar iska ce ke ɗaga ta, tana tura ta gaba, tana shawagi da ita cikin wani sarari mai duhu da shiru da farko ta cigaba da gudu kamar ba zata tsaya ba sai dai kwatsam… ba motsi shiru. Kashifa ta tsaya cak! tana juyawa da hanzari, tana fuskantar baya da idon tsoro. “ Fatu?” “Kaka Mairo?” ta ɗaga murya da ƙarfi, tana fatan jin amsarsu. "Fatu Kaka Mairo! ku juyo mana! na tsaya!” amma babu motsi babu amsa. Sautin muryarsu da suka rika kiranta a baya kamar an ɗora su a cikin mafarki suna ƙarewa a hankali kamar sautin ƙaho a cikin iska mai nauyi. Ta cigaba da juyawa, sai idonta ya sauka akan wani katanga — dogo, baki, ba kofa, ba hanya. Tsaye kamar an dasa shi domin raba duniya biyu ta ruga da gudu tana faduwa tana miƙewa, tana ƙoƙarin hawa, amma babu mafita yana da sanyi kamar dutse, kuma yana da ƙamshi irin na kura da tarihin da aka manta. Ta fashe da kuka “Wayyo Allah… me na shiga haka?” Tana duba ƙafarta… sai ta hango yatsarta tana zubar da jini takalmin dama ya ɓace tun tana gudu, sai ƙafar ta shiga cikin wani karan dutse mai kaifi. Idonta ya cika da hawaye, zuciyarta na bugu kamar gangar yaki. “Fatu Kaka Mairo ! ku ceto ni mana! Ku dawooo!”Sai dai komai ya koma shiru. Duhu ya ƙara cika sararin da take ciki. Sai iska mai kaɗan, mai ɗauke da ƙamshin ganyen da aka binne shekara da shekara… tana shawagi tana yi mata ƙara kamar ana furta sunanta daga wani gefe: “Kaaashiiiifaaa… Kaashiiiifaaa…” Kashifa ta sunkuyar da kai, ta runtse idonta da karfi, tana faɗin: “In mutu zan mutu, amma wallahi ba zan ƙyale ruwan mangoro ba…” sai idonta ya fara “raina fata” kamar yadda kika ce sai ta gane cewa mangoro ba zai cece ta ba! Ga wata ƙawata don wannan sashin da kika buƙata yanzu ne Kashifa ta tsaya cak! tsintar kanta tayi a cikin duhu da shiru mai nauyi ba motsin Fatu , ba muryar kaka Mairo sai kawai karar zuciyarta tana bugawa kamar ta buga ganga. Ta juya tana kiran su da rawar murya: “Fatu ! Kaka Mairo ! ku fito wallahi ba zan sake sata mangoro ba!” Amma babu wanda ya amsa — sai murya ta fara ƙarewa cikin tsoro mai cike da nadama. Tana kallon hanya... sai ga doguwar katanga mai duhu da duwatsun ƙaya — babu inda za ta tsallake idanun ta suka cika da hawaye. Sai gashi iska ta fara kaɗawa — iska mai ɗauke da ƙura da ƙarar guguwa kamar tana kuka. Sai kuma muryar iska na kiran sunanta a hankali: “Kaashiiifaaa... Kaashiiiifaaa...” Tsoro ya mamaye ta kamar ruwa hannunta na rawa, ta kalla ƙafarta takalmin hagu ya ɓace, kuma akwai jinin yatsarta yana gangarowa cikin ƙasa mai taushi nan take rai ya fara raina fata. jama'a a kawo mata agaji.......... Guguwar ta tunkaro da hayaniya, tana huci kamar ta fito daga bakin wuta tsaye Kashifa ke yi kamar wacce aka dasa, hannunta na rawar sanyi da tsoro sai numfashinta ya tsaya cak lokacin da iska ta zazzage ta — kamar abu ne ya fizge ta daga ƙafafunta. ta yi ƙara! Ta yi yunkurin riƙe wani dutse — amma kafin ta kai, iska ta ɗauketa gaba da huci, ta fado da ƙarfi — sai kuma shiru... ta sume. Lokacin da ta buɗe ido, sai ta tsinci kanta a cikin wani daji babba, baƙi, mai girma kamar ba zai ƙare ba komai shiru babu rana, babu wata, babu haske hatta tafin hannunta bata iya gani kamar ta faɗo cikin wani wuri da ba a taɓa rayuwa a ciki ba zuciyarta na bugawa kamar ana busa gangar faɗa. Ta miƙe a hankali, tana jiyo karar ruwan da yake zuba daga wani nesa amma babu inda ta san ko tana gab da ruwa ne, ko ma wata halitta ce ke shan jini “Wayyo Allah... idan na fita daga nan wallahi zan bar mangoro har abada...” Kashifa na ƙoƙarin miƙewa, amma ƙafarta na rawa, zuciyarta na jijjiga kamar za ta tsinke ta runtse ido amma ba ta jin komai sai wani irin murya ba na mutum ba, ba na dabba ba kamar ana jan karan itace a cikin ƙasa, yana karadawa a cikin kunnenta: “Kaaa...shiiii...faa...” ta bude ido da sauri! sai taga wani haske... yana tashi kamar harshen wuta amma ba wuta ba ce, hasken yana motsi ne, yana yi kamar yana kiranta. tayi baya amma sai itacen da ke bayanta ya fara girma ba kamar yadda itatuwa ke girma ba a'a, yana tashi kamar an hura iska a cikin sa! Ta juyo gefe sai ta ga wani inuwa mai siffar mutum, amma ba ya da fuska kamar guguwa, yana tafiya ba da ƙafa, yana shawagi a cikin inuwa. Kashifa ta narke a ƙasa, idonta ya rufe da hawaye — ta yi ƙoƙarin kiran "kaka Mairo", sai muryarta ta bace sai gashi... wani sanyi ya hura a cikin kunnenta, da murya mai zurfi: “Na dade da jiranki, Kashifa…” “Duk wanda ya zo nan, baya fita da rai muna kashinsa… muna sha jinin sa!” Wannan kalmar ce ta fito daga muryar da ta kama tsakanin murya da ƙara murya ce da ba ta da asali, ba mace ba namiji, kamar wata ƙwakwalwa ce ke magana daga waje. “ki duba bayanki "zuciyar Kashifa ta fara dukan duniya hannunta na rawa, jikinta na yamutsewa, amma ta juya... a hankali kamar ta san ba alheri ke jiranta. Idanunta suka sauka a kan haske mai cike da sirri da tsoro, ya bazu kamar walkiya, ya bayyana fuskoki daban-daban: wasu kamar su mutane ne, wasu kuwa kamar su bayin wuta fuskokin da babu murmushi ko rai, idanunsu fari-fari, baki cike da jini suna kallonta... suna yinta da ido guda kamar za su shanye ta. Zuciyarta ta daki numfashi hannayenta suka yi sanyi harƙoƙin jikinta suka tsinke. “me ke faruwa a nan?” ta furta da sassanyar murya, cikin kuka da tsoro. Sai wata murya mai taushi amma mai girgiza zuciya ta dawo, wadda ke da ƙamshin mutuwa da duhu “yanzu zan faɗa miki dalilin da ya sa kika zo nan…” aljanin ya tsaya Idanunsa sun yi jajayen wuta kamar gawayi da aka hura, sannan yana kallonta ba tare da motsi ba. "zauna..." Ya faɗa da wata murya mai ƙarfi amma mai sa zuciya ta tsaya "na baki labari—na shekarun baya… shekaru ɗari uku da suka wuce." wani ƙwarya ya bayyana a gabanta – ba ta san daga ina ba sai ruwa mai kama da madubi ya fara bayyana a ciki. "Kalli…" Kashifa ta ƙasa da idanu. Sai ta fara ganin wani kauye… tsohon kauye, ginin ƙasa, mutane na dariya, yara na wasa "wannan... Tsuntsuwa ce." nuryarsa ta faɗa cikin siririyar murya, kamar iska mai shigowa ta tagar dare. "Shekaru ɗari uku da suka wuce, kauyen nan cike yake da albarka amfanin gona, mutane masu kyau amma..."ya ɗan tsaya. "...sai soyayya ta haifar da ƙiyayya mugunta ta bijiro daga zuciyar mace ɗaya budurwa... mai kishi da bakar zuciya." sai hoton ya sauya an ga wata mace kyakkyawa, tana tare da wani saurayi da wata yarinya sai murya ta faɗa da ƙara: "Kishinta da bakar zuciyarta ya jawo jini ya zubo a ƙasar nan ta kira wani abu da ba mutum ba… kuma ta bude ƙofa da ba a kamata ba." wani haske ya sake ɓallewa daga ƙwaryar sai hazo ya rufe komai, sannan aljanin ya ce: "tun daga ranar, kauyen nan ya zama maɓoyar baƙin sirri duk wanda ya shiga ba tare da kiran izini ba—bai fita da rai." Ya kalli Kashifa da ido guda, "kuma ke… kin zo da zuciya iri ɗaya da tata." Aljanin ya ƙara matsowa kusa da Kashifa, murya na rawa kamar iska mai sanyi daga ƙasa: "Waccan matar… ita ce farko tana da kyawun da ke ɓoye mummunan zuciya wani irin bala’i ta jawo mana?" Sai ƙwaryar da Kashifa ke kallo ta sake nuna hoto: Ana ganin wata budurwa cikin kaya na asiri, tana dariya yayin da yara ke zagaye da ita suna wasa. Yaran sun fito a siffar majizai – mutane amma masu ƙarfi da annuri – ƙwayar idonsu na haske kamar taurari. "Su ne danginmu – zuriyarmu, tsarkaka. amma ita…" Muryarsa ta dushe cikin bacin rai. "...ta kashe su da gangan." "Ta janyo su kusa da ita, cikin wasa da ƙarya. Ta tara su a bakin rijiyar ɗibo ruwa, inda ta ɓoye wani hadin sihiri da ba a faɗa ba." Sai aka nuna yadda ta dora majizan a ƙasa, ta zubo musu wani ruwa da ke ƙone jiki. Sai kiran larabci da ba a fahimta ba ya fara fitowa daga bakinta. "Ta kunne musu wuta… a cikin rijiyar nan." "Jikinsu ya kone, ruhinsu ya ɗaki cikin ƙasa. Amma ba su mutu gaba ɗaya ba – sai dai aka mayar da su zuwa Aljanun da ba su da salama mu…" ya nuna kansa. "Mu ne." Duhu ya cika gun sauti ya fara birkicewa a cikin kunnen Kashifa zuciyarta na bugu sai kuma ya ce cikin ƙasa da murya mai nauyi: "Zan nuna miki komai amma daga yanzu... ke ba 'yar jiki bace ke 'yar tarihin ne." "Itace… ita da mijinta suka kafa kauyen Tsuntsuwa," Aljanin ya ce, yana duban Kashifa da idanuwansa masu ƙona zuciya "sun zo da baƙin shiri, tare da murmushin shaidanu Sun ci amanar girmamawa da karɓa tare da kalmomin ƙarya da soya zuciya, suka ɗaura tushe na kauyen da laifi, suka jefa mana ɗariƙa mai jini." Sannan sautin ƙwaryar da Kashifa ke kalla ya fara sauyawa an fara ganin tsohon zamani: mata da yara sun taru a bakin rijiyar kauyen, wasu na wasa, wasu na diban ruwa, wasu na shagali da dariya. "Sai ga ita... da mijinta... da shaidanci a zuciya." Sai aka nuna ta cikin baƙin mayafi, hannunta riƙe da kwanon zinariya mai ƙyalli, tana kiran mutanen kauyen da kira mai ruɗi a haka suka taru. Sai mijinta ya jingina da itacen rijiya yana dariya, kamar bashi da hannu a cikin shirin. "Suka tarwatsa mu." "Ta ƙona matanmu da 'ya'yanmu da suka taru a bakin rijiya. Ta zubo musu ruwan sihiri, ta kunna wuta daga ƙarƙashin ƙasa – wutar da bata mutuwa." Sai murmushin baƙin ciki ya bayyana a fuskar Aljanin. "Daga wannan rana, iyayenmu suka ɗauki alkawari: duk wanda ya kusanci rijiyar nan… zai sha jini zai zama ragon fansa mun ɗora tarihin azaba a kan rijiyar nan – mun jirkita shi cikin duhu da yaji." Sai ya matso kusa da Kashifa: NARNAH KANWAR SOJA ✍️ CDuk suna cikin farin ciki marar misaltuwa, kowa na murnar dawowar John, wanda yanzu ya koma Munir, cikin addinin Musulunci. fuskar Maryam cike take da annashuwa, tana ta mikewa da saukowa, tana godiya ga Allah da ya bude masa idon zuciya. "Sannu Munir, mun yi matukar farin ciki da ka samu wannan haske," ta furta da murya mai taushi cike da jin dadi. Abokai suka taru, suna rungumar Munir, wasu na hawaye suna zuba saboda wannan canjin da ya yi na rayuwa. Ado ya ce cikin murna, "Labarin Kashifa ya koya mana darasi mai mahimmanci, yafiya da fahimtar juna su ne mabuɗin zaman lafiya." Sai aka ji wani daga cikin su na cewa, "Munir, yanzu kana da sabuwar rayuwa, za mu tsaya tare da kai a kowanne lokaci." A cikin wannan yanayi na farin ciki da godiya, an shirya daukar su a cikin trailer zuwa wani sabon wuri — wurin da za su fara sabon babi na rayuwarsu, da cikakken sabo da tsarkin zuciya. Maryam da Munir, suna zaune tare a cikin trailer, suna kallon juna da murmushi, suna jin dadin wannan sabon farawa da Allah Ya basu. - Bayan mintuna arba’in da tirelar ta fara tafiya, sai muka ji ana harbi da farko mun ɗauka ƴan sanda ne ko jami’an bincike amma harbin ya wuce ƙima. Tirelar ta tsaya cak wani daga cikin masu raka mu daga baya ya ce da karfi, "ƴan bindiga ne! masu garkuwa da mutane!" Cikin kwantenan, su Maryam da John sun fara kuka a shiru. Ihsan ta kulle baki da hannunta, tana juyi kamar mai jiri. Fuskar ta cike da damuwa da tsoro. “Wannan ba aikin gwamnati bane,” Ado ya ci gaba da bayani, “waɗanda suka tare tirelar ƙungiyar masu safarar mutane ce, waɗanda ke sayar da ƴan gudun hijira kamar kaya. Suka ce daga cikinmu za su ɗauki guda biyu su kai Oman don su saida sauran idan har suna da kuɗi ko an biyansu, za su tsallake.” Duk mun tsaya a cikin rashin tabbaci da firgici. Sai ga Maryam da John cikin kuka, suna rabuwa da sauran ƙawayensu da ƙanƙancewar zuciya. Wasu daga cikinmu suna ta addu'a cikin zuciya, suna roƙon Allah ya cetar da su. Maryam ta rungumi Isham da ƙarfi, hawaye na zuba daga idon ta. "Munir, za mu tsira, za mu haɗu da iyayenmu, mu rayu cikin salama," ta furta da ƙarfi da ƙoƙarin kwantar da hankali. Munir kuwa, duk da tsoron da ke ransa, ya murmusa ƙanƙanta. "Insha Allah, Maryam, ba za su raba mu ba. Zan kiyaye ki har abada." Sai dai kuma, dukkanmu mun san cewa wannan rana za ta kasance jarabawa mai girma ga zuciyarmu da ƙarfinsu. Ihsan da Ado suna kiransu da ƙarfi, suna ta kiran sunayensu cikin damuwa da kuka. Amma a cikin ƙwantenan, Maryam da John sun riga sun tsaya, sun rufe idonsu da hannu suna ihu, kamar mutane biyu da zuciyarsu ke ƙaryewa a hankali. Sai aka fisge su daga ƙungiyar, aka ɗaga su cikin ƙarfin hali, ba tare da wata tausayawa ba. "Ku bar su, babu wanda zai ceci su," wani daga masu garkuwa da mutane ya ce da tsanani. Maryam ta yi ƙoƙarin riƙe John, amma an raba su kamar yara masu laifi. "Munir! Munir! Kada ka bar ni! Kada ka bar ni!" ta yi ihu har cikin ƙwairo, ƙarfin zuciyarta ya fara raguwa kamar ruwa mai zuba daga tafki. John kuwa, ya rike hannun Maryam ƙoƙarin nuna ƙarfin hali, amma hawaye sun fara kwarara daga idonsa, ya yi ƙoƙarin cewa, "Maryam, za mu tsira, kada ki yi kuka…" Amma sautin muryarsa ya tsaya, ya zama kamar ƙamshin iska mai saurin shuɗewa. Mun tsaya a wajen hanya, cikin azaba da baƙin ciki, muna ganin yadda suka tafi daga garemu, amma zuciyarmu na karyewa. Wani lokaci zuciyar mutum ta fi jikin sa nauyi, mu kuwa mun ji kamar an fasa zuciyarmu da ƙarfin zafi. Mun tsallake checkpoint ɗin cikin wahala da tsoro, numfashin mu na matsewa, zuciyoyin mu na cike da fargaba da rashin tabbas. Amma cikin duk wannan bakin ciki, sai muka haɗa ƙarfi da addu’a, muna roƙon Allah ya kawo ƙarshen wannan duhu, ya ba mu damar haɗuwa da ƙawayenmu cikin salama. Hawaye sun zuba daga idon kowa, ba wai kawai saboda baƙin ciki ba, har ma saboda ƙarfin soyayya da bege da muka ɗauka a zuciyarmu. b SUKE KARATU KAR KU MANTA CEWA JOHN NA BAMU LABARIN KASHIFA NE INDA SABON SALO YA SHIGO LABARIN DA CEWA IHSAN DA ADO MA'AURATA NE SUNA BAWA YARAN SU LABARIN BAYAN WATA LITTLE YAZID DA IMAN . *********************************** 03 / 6 / 2025 PAGE 41 “Bayan iyayenmu sun dauki alkawarin fansa, kowanne mai rai ya zama makami rijiyar nan ta koma harami – hanyar da ba a wucewa, kuma duk wanda ya kusanci, sai ya zama abin hadaya “sai lokaci ya ja, shekara ta rika bin shekara… har wani abu ya faru." Aljanin ya runtse idanu, yana cigaba da magana da murya mai nisa kamar yana tuna wani lokaci mai tsayi: “Mu biyu ne muka tsira daga wutar fansar da ta cinye rayuka daa yar uwata… mai tsarki ce. zuciyarta ta daina amsar ƙiyayya tana mafarkin wata rana mu zauna da mutane ba tare da jini ko tsoro ba.” “Kwatsam… sai muka samu labari game da addinin Musulunci.” “mun ji ana kiran sallah. mun ji ana karanta Qur’ani mun ga wata rana ta bayyana cikin duhun zuciyarmu zuciyarmu ta girgiza. mun nemi ilimi mun gane gaskiya.” Sai ya shafi ƙasa da yatsansa, yana fadin: “Zuciyarmu ta yafe mun daina sa rai a cikin fansa mun bar rijiyar nan ba wai domin mun mance ba, sai domin mun gane: ba kowa ne ya cancanci azaba ba.” “Iyayenmu sun mutu cikin ƙiyayya amma mu… muna rayuwa cikin gafara.” ya kalli Kashifa da ido mai tsanani amma cike da natsuwa: “To me ke kawo ki rijiyar da ta haɗa tarihi da jini da adalci? Kin zo ne da ruɗi… ko da gaskiya?” Aljanin ya kalli Kashifa da ido masu bayyana ciwon tarihi, yana fadin: "Lokacin da aka haife ki... ne muka fara ganin haske muka fara jin cewa wata rana za mu zauna cikin zaman lafiya da 'yan Adam. amma ke ba zaki gane ba." ya ja numfashi, kamar yana kokarin cin nasara akan zafin zuciyarsa "shin kin san me ya faru bayan mutane sun daina zuwa hanyar rijiyar nan?" "Baba na... sarkin aljanu, wanda ya sha jinin dubban mutane saboda ƙiyayya, ya fusata ya fusata ƙwarai yana ganin ana mantawa da azabar da muka sha, yana ganin ana kushe fansar da iyayenmu suka yi." "A dare daya... ya fantasma kauyen." muryarsa ta sauya, ta koma kamar tana zuwa daga ƙasa mai zurfi "duk wanda ya gan shi... sai ya sha jinin sa, ya mutu babu wanda ya tsira shi ne ya kashe baban ki shi ne ya cinna wa mamanki wuta." ya runtse ido, yana fadin da duka takaici da nadama: "A ƙarshe... ya dawo cikin rijiyar da kansa ya nutsa ya mutu." "Yanzu rijiyar nan tana rike da sirrin mutuwar sa da sirrin zurfin ki saboda ke… ke ce ’yar wanda aka kashe, ’yar wacce aka ƙone kuma ke ce kaɗai da za ta iya komawa bakin wannan tarihi—don shiryawa ko rushewa." Aljanin ya saki wata doguwar ajiyar zuciya, sannan ya dago idanunsa masu launin toka yana kallon Kashifa. "Yar uwata... ita ce ta fara kuka." muryarsa ta yi rauni, kamar yana tuna da wani lokaci mai cike da azaba. "Kukan tausayi gare k kukan nadamar abin da iyayen mu suka aikata. Ihu ta saki – ihu na hakikanin takaici da juyayi. Ihu mai karfi da ya girgiza sama da kasa, ya barin kauyen nan da bak’in duhu." "Tun daga wannan rana... ƙauyen nan bai sake fitar da amfanin gona ba ƙasa ta bushe. Itatuwa sun karye ruwan rijiyar ya koma ja kamar jini." ya sauke kansa ƙasa, yana cigaba: "mun bar ƙauyen mun nufi birni a can muka sami labarin addinin Musulunci muka karɓa da zuciya daya muka tsarkake zuciyarmu da imani." "Amma duk da hakan... ba mu taɓa daina kallon ki daga nesa ba mun kasance muna lura da ke, Kashifa." ya dan yi shiru, sannan ya karashe da murya mai zurfi: "Saboda ke... ke ce muka yarda kin fi kowa cancanta. Cancanta ta ɗaukar fansar da ke cikin jin daɗin yafiya. Fansar da ke a cikin ƙaunar da ke shirin dusashe tarihi." Aljanin ya ɗago ido ya zuba su cikin na Kashifa wutar hasken da ya haskaka dajin ta dan ja baya, kamar tana sauraron shiru. Sai kawai muryarsa ta sake rawa, da ɗan kuka a ciki: "Rashin tsoro ki shi ne ya jawo zuwanki nan. kuma saboda hakan, mun fahimci cewa lallai mun kai ga karshen fansa." Ya durƙusa kamar yana neman afuwa daga wata sarki, ya ce: "Mun tuba, Kashifa muna neman gafara ba mu sake jin daɗin kisa ba mun fahimta, mun gane... mummunar azabar da iyayenki suka sha ba ta da laifi sai rashin fahimta tsakaninmu." "Yanzu muna tambayar ki da zuciyarmu gaba ɗaya... ya kalli ƙasa, sannan ya ɗaga idanu da hawaye: "Zaki ɗauki fansa a kanmu kamar yadda iyayen mu suka ɗauka akan ku? ko kuwa... zaki yafe mana, ki tsarkake wannan ƙauyen da zukatanmu daga laifin da ya gabata?" Shiru ya mamaye wurin. Iska ta daina motsawa dajin ya mutu duhu ya tsaya cak, yana jiran amsarta. Zuciyar Kashifa ta fara narkewa kamar ƙanƙara cikin rana hawaye suka gangaro a idonta — ba don rauni ba, sai don tarihi. Ta kalla su aljanun biyu da ido mai daci da tausayi. "An muku rauni tabbas kisa kisa ne wannan zalunci ne amma ku kuma… kun ɗauki fansa akan bayin Allah waɗanda ba su san komai ba. Laifin wasu baya shafan kowa!” Ta runtse ido, ta dafe kirjinta da hannunta mara takalma, jin radadin da ya wuce rai. “Na ji, kuma har yanzu nake jin radadin mutuwar iyayena... amma hakan ba zai sa ni ci gaba da jini ba fansar da ba ta hana jini zuba ba, ba fansa bace... zalunci ne da aka ɗinke da sabon zalunci.” sai ta miƙe a hankali, kamar wata sarauniya da hawaye suka tsarkake zuciyarta. “zan yafe zan tsarkake zuciyata — ba don cewa ban damu ba, amma don in fara sabon fata. Amma ku kuma...” ta nuna su da hannu: “Ku zama haske a cikin wannan duhun. Rijiyar da aka haifar da kukan jininku, ku mayar da ita rijiyar salama. Ku kare rayuka, ku wanke wannan wuri da alfarma.” Duhu ya fara raguwa... wani walƙiya ya bayyana a sama... kamar rahama ce ta sauka daga sama. Kashifa ta ɗaga kai, tana mai tausasa murya. “Yanzu kuma… ku bi bayana ku tafi da ni ku koya addinin musulunci wannan hasken da kuka gani yana tasowa daga zuciya ce mai neman gaskiya tsawon lokaci ina ganin wannan mafarki, a kullum ina ganin ku, amma rawar da kaina ke yi ba ya bari in gane da gaske menene.” ta juyo da ƙarfi, idonta cike da ƙarfi da ƙasaita. “Yau na gane, kuma zan ɗauke ku a matsayin ’yan’uwa mu tafi ilimi zamu nema, haske zamu bi. Allah yana karɓar tuba.” Aljanin ya zube ƙasa kamar dutse da aka karya daga tsauni ya fashe da kuka kamar ƙaramin yaro. “Subhanallah... Subhanallah! Yabo ya tabbata ga Allah, Mahaliccin Aljannu da Mutane!” Ya fashe da kuka, yana sunkuyar da kai ƙasa, yana faɗin: “mun ga haske… mun ji gaskiya. An tsarkake zuciyarmu da kalmominki. Allahu Akbar! Allahu Akbar!” haske mai launin zinariya ya rufe gun. Daidai lokacin rana ta fito, kamar ana bude sabon shafi. BAYAN SHEKARA ƊAYA A lokacin da jama’a suke kallon wannan mamaki, sai ga Kashifa ta bayyana cikin kwanciyar hankali, murmushi a fuskarta, tare da bayanan ilimin Musulunci da ta kawo wa ƙauyen Tsuntsuwa bayan hannunta na dama da hagu, aljanu biyu ne tsaye suna kallon kowa cikin shiru, kamar masu tsaron ta a gefensu kuma, babo mai sanyi da kallon firgita, wanda ke sa kowa jin tsoro, ya tsaya. Kashifa ta ɗaga murya cikin nutsuwa, tana bayyana cewa yanzu lokaci ne na warkarwa da fahimta, ba na tashin hankali ba ta yi kira ga al’ummar ƙauyen su rabu da tsohuwar al’adun fansa, su rungumi zaman lafiya da ilimin addini jama’ar ƙauyen na saurareta da cikakken hankali, duk da har yanzu akwai wasu da ke rikicewa a zuciyarsu. Kashifa ta yi nuni da cewa wannan hasken da aka gani da ruwan sama mai rahama alamar albarka ce daga Allah, kuma daga yanzu za a fara sabon zamani a ƙauyen Tsuntsuwa. Daga nesa, sai ga Kaka Mairo ta bayyana cikin hanzari, idanuwanta cike da hawaye, tana rungumar Kashifa da ƙarfi sosai kowa a wurin ya tsaya cak, yana kallon wannan lamari da mamaki, suna tambayar juna cikin shiru, “Me ya faru? Kashifa bata mutu ba? Me yasa wannan haske ya bayyana?” Kashifa, cikin tausayi da ƙarfi, ta amsa da muryar da ta ɗan yi rauni: “Ban mutu ba… wannan haske da kuka gani, alamar ne ta albarka da rahama daga Allah. Wannan rana ce ta sabon farawa, babu ƙarfi a cikin fansa ko azaba, yanzu lokaci ne na zaman lafiya da gafara.” Fatu kuwa, tana tsaye kusa da su, fuska cike da farin ciki da kwanciyar hankali, amma bata yi magana ba ta duba kowa da ido mai cike da amincewa da fata, tana jin cewa wannan shi ne ƙarshen duhu da suka rayu a ƙauyen Tsuntsuwa. Sarki Idris ya ɗaga hannu a hankali, ya yi shiru na ɗan lokaci yana kallon Kashifa cikin nitsuwa. Sai ya ce da murya mai laushi da hikima: “Yarinyata, mun san cewa ba sauƙi ne ke gare ki ba. amma mun zo nan domin mu saurari labarinki, duk abin da kike da shi a zuciyarki. Kada ki ji tsoro, wannan ƙauye gaba ɗaya na tare da ke, kuma muna son mu fahimci komai daga bakin ki.” Kashifa ta ɗan yi shiru, ta duba kowa da kowa a idon su kafin ta fara bada labarinta cikin nutsuwa da ƙarfi. Kowa ya yi shiru, suna sauraron kowace kalma da take faɗa, suna jin cewa a ƙarshe an kawo ƙarshen wannan tsananin duhu. Kashifa ta fara bayar da labarin cikin hikima da natsuwa, tana bayani dalla-dalla yadda ta tsira daga duhun ƙauyen, yadda ta gano addinin Musulunci, da kuma yadda wannan ilimi ya kawo mata kwanciyar hankali da canjin rayuwa. Yayin da take magana, idanuwan mutanen ƙauyen sun yi ƙara haske, wasu na damuwa, wasu kuma suna jin wani sabon fata na farawa a zukatansu. Maganganunta sun shafi zukatan su, suna jin gaskiya da nufin zaman lafiya. Bayan ta gama, Sarki Idris ya mike tsaye, ya yi addu’a tare da roƙon Allah ya sa wannan sabon haske ya tabbata a cikin ƙauyen ya yi kira ga kowa da kowa da ya rungumi addinin Musulunci cikin kwanciyar hankali, fahimta, da yarda, domin kawo ƙarshen dukkan ƙiyayya da tashin hankali da suka yi ta addabi ƙauyen. Mutanen ƙauyen suka amsa da farin ciki da karɓar wannan sabon tafarki, suna yi wa Kashifa godiya da fatan alheri. An fara gudanar da ibada, koyar da al’adar Musulunci, kuma ƙauyen tsuntsuwa ya fara sauyawa zuwa wuri mai albarka da zaman lafiya. Nan suka kutsa cikin hanyar, ga rijiyar da bishiya, inda Kashifa ta kafa ƙaramin makarantar karatu don manya da yara. A cikin wannan makaranta, mutane na koyon karatun Al-Qur’ani, ilimin addini, da sauran darussa masu amfani da za su taimaka wajen bunkasa rayuwarsu. Kashifa na koyar da su da zuciya ɗaya, tana ƙarfafa su da nuna musu muhimmancin zaman lafiya da haɗin kai. A hankali, ƙauyen tsuntsuwa ya fara haskakawa da farin ciki, yara suna dariya, manya suna tattaunawa cikin kwanciyar hankali, kuma kowa na jin cewa wannan sabon rayuwa ce mai albarka. https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC BAYAN WATA SABON SALO BY NARNAH KANWAR SOJA ✍️✍️ 08101235739 SHARE FISABILLILAHI MASU TAMBAYA DA WANDA SUKE KARATU KAR KU MANTA CEWA JOHN NA BAMU LABARIN KASHIFA NE INDA SABON SALO YA SHIGO LABARIN DA CEWA IHSAN DA ADO MA'AURATA NE SUNA BAWA YARAN SU LABARIN BAYAN WATA LITTLE YAZID DA IMAN . *********************************** PAGE 42 / 43 . Kashifa ta dube Malam Sambo da mai gonar Mangoro da dariya mai sanyi, tana cewa, “Don Allah, kar ku bini da sanda, ku bar ni a hankali. Wannan haske da kuka gani ba nawa bane kawai, na mu ne duka — na wannan ƙauyen tsuntsuwa, na zukatanmu, na zaman lafiya da muka fara ginawa.” Ta yi murmushi sannan ta ci gaba da cewa, “Ku sani, wannan sabon shafi ne, ba zamu bari tsohuwar duhu ta dawo ba.” Malam Sambo da mai gonar Mangoro suka kalle ta da mamaki, suka fahimci cewa yanzu lokaci ne na hadin kai da yafe wa juna. Daga nan suna zaune a cikin gida, sai ga Kashifa ta shigo gun Fatu da magana a kunnenta, tana cike da kwadayin Mangoro. Ta ce, "Fatu kin san dai gonar Mangoro na da mahimmanci a gare mu tunda halittar Allah ne, ba sata ba ce, kuma ba za mu bari a ci gaba da barna ba mu tafi gonar Mangoro mu gyara ta, mu kula da ita yadda ya kamata." Fatu ta kalle ta da murmushi, ta amsa da cewa, “Lallai, kin fadi gaskiya zamu tafi tare mu tabbatar da cewa gonar ba ta sake zama wurin rigima ba.” Suka shirya suka fita tare zuwa gonar Mangoro, cike da burin kawo zaman lafiya da gyara al’amura. John ya kalli Ihsan da Maryam da murmushi mai ɗauke da natsuwa, sai ya ce: “To, mun dawo cikin kabarin bayan wata… yanzu zan baku labarin Kashifa sosai, domin na bayyana muku wani sirri da na ɓoye daga ƙasar Makka.” Ihsan ta yi ihu a hankali, idanuwanta sun kumbura da hawaye, ta ce: “Ka sani, kafin ka fara, kai ka ga ido na ya kumbura da kuka labarin Kashifa ya taɓa zuciyata sosai.” Maryam ta matsa kusa da su, ta ƙara cewa: “Irin wannan labarin yana da matuƙar amfani, musamman ga waɗanda ke neman ilimi da fahimtar gaskiya.” Sai John ya ɗauki numfashi, ya fara bada labarin cikin nutsuwa, duk suna sauraro cikin shauƙi da tsananin sha’awa. A lokacin da muka isa Makka, na karɓi addinin Musulunci yanzu kuma, ba a kira ni da suna John ba, sai Muhammad Munir sabon suna na cikin wannan sabon rayuwa da na fara. DARASIN LABARIN KASHIFA Labarin Kashifa ya kasance ɗaya daga cikin labarai masu ƙarfi da suka taɓa zuciya, inda ya nuna mana muhimmancin yafiya, canji, da imani a rayuwa Acikin wannan labari, mun ga yadda kisan kai, rikici, da aljanu suka addabi wani ƙauye har tsawon shekaru, amma kuma yadda zuciyar ɗan adam zata iya canzawa idan aka yi amfani da ilimi da addini. 1. Yafiya: Hanya Mafi Karfi Ko da yake ƙauyen Tsuntsuwa ya sha wahala da azabar rashin adalci da kisan kai, Kashifa ta nuna mana cewa mafita ba ta cikin ɗaukar fansa ba, sai dai ta hanyar yafiya. Wannan yafiya ta kasance ba ta manta da abin da ya faru ba, amma ta zama hanya ce ta tsira da zaman lafiya Yafiya tana kawo sauƙi ga zuciya, tana kawar da girman kai da ƙiyayya, tana kuma bada damar sake gina rayuwa cikin nutsuwa da jituwa. 2. Canji Mai Dorewa Ta Hanyar Imani Bayan tsawon shekaru na rikici da firgici, mutanen ƙauyen sun yanke shawarar karɓar addinin Musulunci, wanda ya kawo musu sabuwar hanya ta rayuwa da fahimtar juna. wannan canji ya nuna mana cewa babu abin da ba zai yiwu ba idan mutum ya bude zuciyarsa don karɓar sabon ilimi da kyawawan dabi’u. Imani ya zama tushen da ya mayar da ƙauyen tsuntsuwa wuri mai haske da walwala. 3. Ilimi A Matsayin Makami Kashifa ta kafa makaranta a ƙauyen domin koyar da yara da manya ilimi na addini da na duniya, domin tabbatar da cigaban ƙauyen. wannan yana nuna cewa ilimi ba wai kawai karatun littattafai bane, har ma da koyar da tausayi, hakuri, da fahimtar juna, wanda yake da muhimmanci wajen tabbatar da zaman lafiya da cigaba a kowanne wuri. 4. Hankali Da Hikima Wajen Yanke Shawara A lokacin rikici, mafi yawancin mutane sukan dauki matakai cikin fushin zuciya da fargaba. Amma labarin Kashifa ya nuna mana cewa a kowanne yanayi, yin amfani da hankali da hikima wajen yanke shawara shi ne babban makami na warware matsaloli. Shawarar da aka dauka ta dogara ne akan ilimi, yarda da addini, da kuma fahimtar gaskiya, ba bisa son zuciya ko ƙiyayya ba. 5. Haske A Cikin Duhu Labarin Kashifa yana koyar da mu cewa duk da yanayi na duhu da wahala, haske zai bayyana idan an dage da hakuri da yawaita addu'a da imani. Tsuntsuwar da aka rufe da duhu ta rikici ta koma wuri mai albarka da zaman lafiya bayan zuwan Kashifa da koyarwar musulunci. Wannan yana nuna mana cewa ba wai duhu ne zai dade ba, sai dai haske ne zai wuce. Kammalawa Labarin Kashifa ba kawai labari bane na ƙauye da aljanu ko rikici, amma babban darasi ne ga rayuwarmu ta yau da kullum yafiya, ilimi, da imani suna da muhimmanci wajen kawo zaman lafiya a zukatanmu da kuma al'ummarmu baki ɗaya wannan labari ya karfafa gwiwa cewa kowane mutum yana da damar canzawa, kuma akwai haske a kowane duhu idan muka rungumi gaskiya da alheri. John ya dawo Muhammad Munir daga yanzu sunan matafiya biyar IHSAN wacce ta bamu labarin ( PRINCESS RAHILAT) MARYAM wacce ta bamu labarin ( HALIMATU SADIYA ) YAZID wanda ya bamu labarin ( ALJANIN SAJIDA) ADO wanda ya bamu labarin ( MASARAUTAR ZAKAR ) JOHN WATO MUNIR ya bamu labarin ( KASHIFAH ). A yanzu mun gama dukkan labarai nasu zamu afka cikin Bayan wata sabon salo Duk suna cikin farin ciki marar misaltuwa, kowa na murnar dawowar John, wanda yanzu ya koma Munir, cikin addinin Musulunci. fuskar Maryam cike take da annashuwa, tana ta mikewa da saukowa, tana godiya ga Allah da ya bude masa idon zuciya. "Sannu Munir, mun yi matukar farin ciki da ka samu wannan haske," ta furta da murya mai taushi cike da jin dadi. Abokai suka taru, suna rungumar Munir, wasu na hawaye suna zuba saboda wannan canjin da ya yi na rayuwa. Ado ya ce cikin murna, "Labarin Kashifa ya koya mana darasi mai mahimmanci, yafiya da fahimtar juna su ne mabuɗin zaman lafiya." Sai aka ji wani daga cikin su na cewa, "Munir, yanzu kana da sabuwar rayuwa, za mu tsaya tare da kai a kowanne lokaci." A cikin wannan yanayi na farin ciki da godiya, an shirya daukar su a cikin trailer zuwa wani sabon wuri — wurin da za su fara sabon babi na rayuwarsu, da cikakken sabo da tsarkin zuciya. Maryam da Munir, suna zaune tare a cikin trailer, suna kallon juna da murmushi, suna jin dadin wannan sabon farawa da Allah Ya basu. - Bayan mintuna arba’in da tirelar ta fara tafiya, sai muka ji ana harbi da farko mun ɗauka ƴan sanda ne ko jami’an bincike amma harbin ya wuce ƙima. Tirelar ta tsaya cak wani daga cikin masu raka mu daga baya ya ce da karfi, "ƴan bindiga ne! masu garkuwa da mutane!" Cikin kwantenan, su Maryam da John sun fara kuka a shiru. Ihsan ta kulle baki da hannunta, tana juyi kamar mai jiri. Fuskar ta cike da damuwa da tsoro. “Wannan ba aikin gwamnati bane,” Ado ya ci gaba da bayani, “waɗanda suka tare tirelar ƙungiyar masu safarar mutane ce, waɗanda ke sayar da ƴan gudun hijira kamar kaya. Suka ce daga cikinmu za su ɗauki guda biyu su kai Oman don su saida sauran idan har suna da kuɗi ko an biyansu, za su tsallake.” Duk mun tsaya a cikin rashin tabbaci da firgici. Sai ga Maryam da John cikin kuka, suna rabuwa da sauran ƙawayensu da ƙanƙancewar zuciya. Wasu daga cikinmu suna ta addu'a cikin zuciya, suna roƙon Allah ya cetar da su. Maryam ta rungumi Isham da ƙarfi, hawaye na zuba daga idon ta. "Munir, za mu tsira, za mu haɗu da iyayenmu, mu rayu cikin salama," ta furta da ƙarfi da ƙoƙarin kwantar da hankali. Munir kuwa, duk da tsoron da ke ransa, ya murmusa ƙanƙanta. "Insha Allah, Maryam, ba za su raba mu ba. Zan kiyaye ki har abada." Sai dai kuma, dukkanmu mun san cewa wannan rana za ta kasance jarabawa mai girma ga zuciyarmu da ƙarfinsu. Ihsan da Ado suna kiransu da ƙarfi, suna ta kiran sunayensu cikin damuwa da kuka. Amma a cikin ƙwantenan, Maryam da John sun riga sun tsaya, sun rufe idonsu da hannu suna ihu, kamar mutane biyu da zuciyarsu ke ƙaryewa a hankali. Sai aka fisge su daga ƙungiyar, aka ɗaga su cikin ƙarfin hali, ba tare da wata tausayawa ba. "Ku bar su, babu wanda zai ceci su," wani daga masu garkuwa da mutane ya ce da tsanani. Maryam ta yi ƙoƙarin riƙe John, amma an raba su kamar yara masu laifi. "Munir! Munir! Kada ka bar ni! Kada ka bar ni!" ta yi ihu har cikin ƙwairo, ƙarfin zuciyarta ya fara raguwa kamar ruwa mai zuba daga tafki. John kuwa, ya rike hannun Maryam ƙoƙarin nuna ƙarfin hali, amma hawaye sun fara kwarara daga idonsa, ya yi ƙoƙarin cewa, "Maryam, za mu tsira, kada ki yi kuka…" Amma sautin muryarsa ya tsaya, ya zama kamar ƙamshin iska mai saurin shuɗewa. Mun tsaya a wajen hanya, cikin azaba da baƙin ciki, muna ganin yadda suka tafi daga garemu, amma zuciyarmu na karyewa. Wani lokaci zuciyar mutum ta fi jikin sa nauyi, mu kuwa mun ji kamar an fasa zuciyarmu da ƙarfin zafi. Mun tsallake checkpoint ɗin cikin wahala da tsoro, numfashin mu na matsewa, zuciyoyin mu na cike da fargaba da rashin tabbas. Amma cikin duk wannan bakin ciki, sai muka haɗa ƙarfi da addu’a, muna roƙon Allah ya kawo ƙarshen wannan duhu, ya ba mu damar haɗuwa da ƙawayenmu cikin salama. Hawaye sun zuba daga idon kowa, ba wai kawai saboda baƙin ciki ba, har ma saboda ƙarfin soyayya da bege da muka ɗauka a zuciyarmu. https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC BAYAN WATA SABON SALO BY NARNAH KANWAR SOJA ✍️✍️ 08101235739 SHARE FISABILLILAHI MASU TAMBAYA DA WANDA SUKE KARATU KAR KU MANTA CEWA JOHN NA BAMU LABARIN KASHIFA NE INDA SABON SALO YA SHIGO LABARIN DA CEWA IHSAN DA ADO MA'AURATA NE SUNA BAWA YARAN SU LABARIN BAYAN WATA LITTLE YAZID DA IMAN . *********************************** PAGE 44 Daga wancan lokac bamu sake jin labarin Maryam da Munir ba rayuwa ta cigaba da gudana amma ba tare da nutsuwa ba cikin zuciyarmu akwai gibi – wani ɓangare da aka yanke mana da kyar mun rasa su cikin harbi, cikin ƙwantenan duhu, kuma har yau, bamu sani ba – shin sun tsira? ko kuwa duniya ta ci nasara a kansu? Dani da Ihsan muka cigaba da tafiya… muka iso Dubai cikin gajiya da karyewar zuciya ba mu da komai sai juna da ɗan ƙaramin kaya da muka zo da shi amma zuciyarmu ta cika da mafarkin Maryam da Munir – su ne tamkar jinin tafiyarmu, farin cikin tafiyarmu. Rayuwar Dubai ba ta karɓe mu da fara’a ba, sai dai da ƙalubale amma a kullum kafin mu kwanta sai mu kalli sama, muna addu’a: “Ya Allah, idan suna raye, ka ba su ƙarfi. Idan sun mutu, ka ba su rahama kuma idan akwai wata hanya, ka haɗa mu da su.” Watanni suka shige... duniya ta cigaba... muna nan cikin gwagwarmayar rayuwa, amma a cikin kowace rana, muna jiran wata rana da za ta bayyana kamar hasken safe a bayan dare mai duhu... Rayuwa a Dubai ba ta zo da sauƙi ba, amma da ƙoƙari da juriya, ni da Ihsan muka fara sabawa muka kama sana’o’i a boye, karatun sana’a, aikin gini da gyaran gidaje a hankali, Ihsan ta fara ɗinki, ni kuma na shiga harkar ɗaukar kaya a kasuwar Dragon Mart. A cikin wannan wahalar… soyayya ta fara hure cikin zukatanmu duk da cewa mun sha alwashin barin zuciya ta huta, amma lokaci ya tabbatar mana: mun zama juna mun fahimci cewa ba wai kawai haɗuwa ce ta bazata ba – alƙawari ne daga Allah. Mun yi aure cikin tawali’u, ba tare da dangi ba, ba tare da kawaye ba – sai dai zubar hawaye da addu’a wannan aure ne da ya yi asali daga wahala, ya tsiro cikin kuka, ya girma da tausayi, kuma ya zama ginshiki na sabuwar rayuwa. Ado ya samu wata dama ta musamman wani dattijo dan Najeriya mai suna Alhaji Abdulrahman ya ɗauke shi matsayin ɗa ya yaba masa da gaskiya, rikon amana da tausayi ya koya masa dabarun kasuwanci, har ya saka shi a cikin harkar shagunan kayan masarufi. Ado ya fara haskawa… ya girma a kasuwa, amma zuciyarsa ba ta manta da abokansa ba – musamman Maryam da Munir da Yazid. Kowanne daga cikinmu yana da rana da dare, amma a zuciyarmu akwai tambaya ɗaya da ke daure tunani: “Ina Maryam da Munir?” A yau idan muka zauna, idan muka yi dariya, ko muka ci abinci, sai mu tuna: wasu biyu sun tafi tare da mu daga gida, amma yanzu... har yanzu ba mu san inda suka ƙare ba. A Dubai muka haife ku. Sunan ka — Yazid mun sanya shi ne saboda wani aboki na gaske, wanda ya sadaukar da ransa wajen kare rayuwarmu. 'Yar uwarka kuma — sunanta Maryam. ba domin baƙon suna bane, a'a mun sanya mata sunan ne domin tunawa da Maryam, wacce muka rasa a cikin hanya. Maryam da zuciyarmu har yanzu tana yi mata addu’a ta kasance mace mai ilimi, mai jajircewa da zuciya mai kyau ga tausayi da ban dariya amma duk da wannan wadata da kwanciyar hankali... bamu taɓa mantawa da wahalar rayuwa ba. wannan shi ne... BAYAN WATA. Ta ɗaga kai, ta kallesu ta fara: “mun tashi daga gida da buri mun bar ƙasarmu ba domin mun wuce, a’a domin rayuwa ta ƙi barinmu lafiya muka nufi hanyar da ba kowa ke komawa ba hanya mai cike da hazo, da duhu. a wannan hanya muka rasa abokai, muka rasa jini, muka rasa zuciya… sai dai bamu rasa fata ba.”idanunta suka cika da hawaye, amma sai ta murmusa. “mun tafi da Yazid — wanda sunan ka ke ɗauke da shi ya rasa ransa wajen kare mu mun rasa Maryam — wacce sunan 'yar uwarka ke ɗauke da shi — har yanzu bamu san inda take ba, ko ina take ba amma duk da haka, Allah ya azurta mu da wata Maryam — wacce ta koma Iman, mace mai kyau da nagarta da rahama.” “Kuna rayuwa mai kyau yau. Kun tashi da lafiyayyen gado, abinci mai ƙamshi a ɗakin da ke da duminsa, makaranta mai tsari, da soyayyar da ba ta da tsoro amma ku sani akwai wani lokaci, lokacin da ruwa ne kawai ke ɗaukar mu.ruwa mai duhu, mai cike da fargaba ko zai zubar da mu, ko zai ɗauke mu zuwa gaba mun zauna da duhu mun tashi da safiya, da yunwa a ciki, ƙishi a leɓe, hawaye a ido mun rayu akan shata mun shiga tsakiyar dabbobi don su ɓoye mu kashin awaki a jikin mu , rashin ruwa bala'e ne har fitsaren mu munsha a sanadin rashin ruwa ƙishi ya kusa zama ajalin mu muna tashin hankali tsakanin rana da da zafin sa cikin wannan yanayi muka nemi halal — halal namu da wuya, ba da wulakanci ba. Yau da za a zana mana hoton masu tafiya — ba tare da sun san inda za su sauka ba tabbas zamu dakatar da su, mu ce musu: ‘Ku jira.’ domin azabar da muka sha ta fi wadda harshe zai iya fassara. Wannan shine… Bayan Wata.” Cikin rawar murya da dukan zuciya, Ihsan ta kalli ‘ya’yanta, tana faɗa da tausayi: A wannan lokacin yaran suka rungume su Ihsan da Ado, zuciyoyinsu cike da tausayawa. Daya daga cikin yaran ya ce: “Daddy … Mommy … zamu rayu da daraja. zamu tuna da inda muka fito. zamu zama masu taimako da tausayi. zamu ci gaba da alkhairan da kuka fara.” Ado ya daga kansa cikin nuna jin daɗi, ya ce: “ku zama sakonmu ga duniya.” Suka ɗan rungume juna cikin nutsuwa shiru ya lulluɓe dakin, amma zuciya tana magana. kuma daga wannan rana, sabon babi ya fara. Wannan shine Bayan Wata – lokacin da duhu ya janye, rana ta fito. https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC 🎇BAYAN WATA 🎇 ( Beyoung the moon ). SABON SALO Labari da tsarawa Narnah ƙanwar soja ( Sayeedan Adda ) ********* HIKIMATA ABIN ALFAHARI NA Marubuciyya tana da damar halittar mutum ta kashe shi ta raya shi, tunda 'ƙirƙirar labari ne. ta haɗa masoya, ta wargaza soyayya tsakanin masoya. Itta baiwa daga Allah ce, ubangiji ke bada itta ga wanda ya so duk wanda aka ba wa itta, sai ya sarrafa ta yadda ya ƙi so: wani ta jawo masa arziki, wani kuma ta janyo masa ɗaukaka da masoya masu girma da daraja... *****"" Sadaukar wa littafin Bayan wata sabon salo Ga Abokina Mallam Najeeb wanan Sabon salo naka ne shi ke ɗauke da martabar sunanka thank you with your support 🙏 Page 45 "Sometimes... agogo baya karya yana nuna wanda kaddara zata haɗa ka da shi." Yammacin Jumma’a ce mai sanyin iska da launin zinari a sararin samaniya rana na dushewa a hankali, tana barin haskenta cikin launin kwalli mai laushi anan ne, cikin cunkoson jama’a da motsin kasuwanci, wata ƙamshi mai sanyi da tsabta ke tashi daga babbar kofar Sahad Stores Abuja. Najeeb ya iso cikin shiga mai kyau, ya zubo white senator ɗin da aka yanke bisa tsari, an danna masa ɗinki na zamani da ɗan kyan embroidery a wuyansa hularsa ta jitu da safa, sai takalmansa masu walƙiya da suka haura baƙi suka karawa tafiyarsa annuri wuyansa na sanye da agogon zinariya, wayarsa a hannu, yana latsawa kamar mai karanta wasu bayanai masu muhimmanci. Idanunsa suna haske kamar waɗanda ke ganin gaba da nesa, sai miskin kyalli na confidence da ke daddare a fuskarsa. Jama’a na kallonsa – wasu suna fadin: "Waye wannan kamar Balarabe ?" "Ba shakka ɗan manya ne ko diplomat!" Wani kidan qasida ne na Maher Zain yana tashi daga cikin motar da ya fito daga ciki, yana ɗaukar zuciyar wanda ke kusa duk cikin Sahad, babu wanda bai lura da zuwansa ba – kamar yana ɗauke da wani ɓoyayyen saƙo daga wata rayuwa da suka taɓa mantawa da ita. fitillu suna sheƙi kamar taurari da suka sauko don bautar masu siyayya kowa na gab da kammala siyarsa, amma a ɗaya gefen katafaren building ɗin nan, lefṭar ya buɗe cikin kakkarfar murya da "tingg...". Najeeb, cikin kamala da nutsuwa, ya taka ya shiga hannunsa rike da katanin electronics, wayarsa a hannu ɗaya, yana kallon notification na "New shipment received - Check email." Kanshi ɗauke da ƙamshi mai sanyi, daga nesa zaka ce kamar an fitar da shi daga cikin kwali. A ɗaya ɓangaren store ɗin kuwa, Iman na fitowa daga sashen home décor, Iman ta shigo cikin rigar Valentino purple da gyale mai launin zinariya, doguwar gashi na gyararre da leɓanta masu sheƙi. Hannunta na ɗauke da small purse daga Louis Vuitton kayan da take duba amma sai ga shi yana ɗaukar hankalinta... "Shine? ko dai yana kama?" Najeeb na tsaye da natsuwa irin ta wanda ya saba da rayuwar manyan kasuwanci. Hannunsa ya na sauƙa kan agogon hannu — Rolex Sky-Dweller, silver da blue — yana duban lokaci ba tare da ya kalli Iman kai tsaye ba. 🌀 Tana ƙarasowa leftar, sai ido ya sauka kai tsaye kan fuskar Najeeb. Shi kuwa ya danna maballin close, ƙofar na fara rufewa — amma da gaggawa ya fasa, yana nazari kan kyakkyawar mace da ta tsaya a gabansa. "After you," ya ce, da muryarsa mai laushi wacce ta daɗe da jin turanci da harshen duniya. Iman kuwa ta shigo cikin lefter kamar sarauniyar wadda duniya ke bi da hange. Idonta a na'urar maballin, amma kunnenta na sauraron numfashinsa ta juyar da kai, ta ce da murya mai kaifi: "Ba lallai ka tsaya ka rufa min ƙofa ba. I've seen better manners elsewhere." Iman ta lumshe ido, ta ce da siririyar murya: "Thanks sorry, I was distracted." Kofar ta rufe iska mai sanyi ta buga jikin leftar. Shiru ne ya mamaye tsakanin su wanibl ƙamshin turaren su na ratsa zukatansu, amma zuciya biyu na bugawa da sauri wata rana, wata hanya, amma kamar an jima ana jiran wannan haɗuwar. seconds biyu suka zama kamar mintuna. Najeeb ya kalli bayan Iman, ya ce: "You remind me of someone I once lost… deeply." Iman ta juyo da mamaki. "really? that’s strange… you look like someone from a story I wrote and forgot." Nan ne suka kalli juna – kamar dare da rana da suka hadu a fata tashin hankali, juyin zuciya, da alamomin cewa: "wannan ba haɗuwa bace – wani ɓangare ne na KADDARA." Najeeb ya ɗago kai a hankali, sai kallon ɗaya kawai ya yi mata — wanda ya cika da izza da confidence — sannan ya ce da siririyar dariya mai nauyi: "You’re welcome... but next time, try leading instead of assuming you own the place." Tsiwa ta hadu da izza. Iman ta kura masa ido tana jin kamar ya karya mata ginin girman kanta na yar masu kuɗi amma ba zata baje ba ta gyara tsayuwa, ta ce: "Hmm. I guess 'big boys' now come with too much attitude and too little courtesy." Najeeb ya matse dariyarsa ya zare wayarsa daga aljihu, yana dannawa kamar ba a gabansa ba, sannan ya ce da sauƙin murya: "Exactly that’s why some of us don’t wait for likes to feel important you just know who you are." Kafin Iman ta bata rai sosai, lefṭar ya tsaya. sai kowannensu ya fice a gefe daban — kamar ba su yi magana ba, amma zuciyarsu na kwaɗayi, tamkar sautin tambaya: "Waye wannan?" "A ina na san shi?"amma rana ce da za ta bar sanyi. Ranar da kaddara ta ɗan jefa ƙuri'a — kuma ta gyara tsari a cikin zukata biyu da ba su san sirrin juna ba tukuna... "Sometimes... agogo baya karya. Yana nuna wanda kaddara zata haɗa ka da shi." Sahad Store upstairs yau kamar wani mini Dubai yake kayan alatu, turaruka, agogo, jakan fata, da kayan designers sun sha kwalliya a racks kamar su na jira mutum guda — Iman. Turarukan “Maison Francis Kurkdjian” — wanda ba kowa ke iya kamshin su ba. Ya kalli kayan, sannan idonsa ya sauka a kan turaren da Iman ke dubawa Sai ya ce da murya mai sanyi: "You won’t find your scent in shelves… such a presence deserves exclusivity." Iman ta ɗaga kai a hankali, kamar ba ta sa ran magana ba, amma murmushinta ya ɗan bayyana ta ce: "Really? and what exactly does exclusivity smell like?"wata rana, wata rana kuma yau ce. Idonsu ya haɗu, zuciyarsu ta ɗan bugawa. Najeeb ya ɗauko wani turare daga glass case, ya ce: "Try this. It's called ‘Oud Satin Mood’ — classic, deep, unforgettable… kinda like the person I'm seeing right now." Kamshin turare ya buɗe musu ƙofar zumunci, kalmomi sun fara fita a sanyi, ƙila a rikice, amma zuciya na ɗaukar ajiya. Kusan suyi magana sai wani staff ya ce: "Sannu ku duka... turaren nan da agogon nan suna cikin exclusive couple’s gift package." kallon da suka yi juna sai suka saki dariya... A hankali zuciyarsu na furta kalmar da ba su ce da baki ba: “Shin kece?” “Ko kai ne? Iman ta ce da tsawa mai kwalliya: "I don't need a timekeeper. I make my own timing." Najeeb ya ce, yana dariya: "That’s exactly what I thought the first time I saw you I guess timing agrees with us again." Sai kallon idanu ya jima, har sai jikin turare ya faɗi daga hannunta ya zaro hannu ya tare kafin ya faɗi ƙasa. Ta kwace masa da ƙarfi kamar zata zuba masa a fuska. Fuska a haɗe ta juyo a zafafe da nufin bangaje shi, cikin rashin sa'a santsin plat shoe na ƙafarta ya haɗu da na tiles ya zamar da ita suuu!!. Zazzaro ido suka yi daga uta har shi, cikin zafin nama ya finciko hannunta ta faɗo kan ƙirjinsa. Dim!!, dim!! didim!!! dim!!! Zuciyoyinsu ke bugawa a tare cikin wani mugun gudu, gabaki ɗaya sun manta inda kansu yake sun ƙure juna da kallo ido cikin ido yayin da kowa ke karanta wani babban lamari a tare da ɗan uwansa. Da sauri Iman ta ɗan gyara numfashi tana ƙoƙarin zamewa. "Lokaci yana faɗin abu daban da zuciya, ko?" Najeeb ya faɗa cikin muryar raɗa. Ta kalle shi tana turo baki gaba, kafin ta ce "Ka cire hannunka ko sai na saki kukan da zai tarwatsa wannan shagon." Ya janye jikinsa cikin hanzari yana sakin wani yalwataccen murmushi gami da sauke nannauyar ajiyar zuciya “Sai dai kukan zuciyar ki, shi ba zan iya tsayar da shi ba.” Iman ta ji kamar zuciyarta ta faɗi — ba saboda soyayya ba, a'a saboda kunya da ƙiyayya da shagwaba da suka haɗu waje guda. “Wuce ni! Ina ruwanka da ni!” ya ɗan matsa gefe yana faɗin “Toh, Allah ya bada haƙuri tunda nayi abun a yaba ya zama laifi, ban shirya ganin wannan kyakkyawar halittar a ƙasa bane shi yasa na tare!” Wufff! Ta yi yunƙurin tafiya da sauri, tana kaɗe gyalenta, ya tashi kamar banner, amma ƙafarta ta sarke da gefen rug. rimm!! Ta faɗi a ƙasa. Kayan leda na “Lancome” da “Versace perfume” suka zube… shagon yaja ido. Masoya biyu sun zo ta hanyar agogo suna rike hannu — sai suka tsaya suna kallon ta. Ɗaya daga cikinsu ya furta da mamaki: "Wallahi kamar scene ne daga 'Karma in High Heels'." wata budurwa na gefe ta ɗan lumshe ido ta ce: “OMG! Ta faɗi a gaban that fine guy! 😩😭” Najeeb dai… Ya tsaya hannayensa zube a aljihunsa, yana ƙoƙarin hana dariyarsa fitowa. A hankali ya taka kusa da ita ya ɗan durƙusa saitin fuskarta kafin ya ce “Next time ki karɓi turaren ki zauna lafiya zaki fi dacewa da Rolex fiye da ƙasa.” Iman ta haɗiye numfashi ta kalle shi — kallo na kunya da zafi, kallo mai cike da tambaya: “Waye kai?” Sai kawai ya janye Versace turaren daga ƙasa, ya miƙa mata: “Wanda zai saka ki manta da faɗuwar yau... ko ki tuna da ita har abada.” Iman ta miƙe daga ƙasa da sigar ɗan rawar jiki, sai ta gyara mayafinta kamar wacce za ta ɗauki fansa a gasar duniya. Ta matso kusa da Najeeb, idonta cike da ƙyashi da borin kunya da girman kai irin na 'yan manyan gida. “Daga faɗuwa har zaka bi ni? Me nake da kai?” Sai ya yi murmushin da ke iya janyo fans a TikTok: “Kinyi kyau da fushi, amma fushi ba zai iya janyo min gaba da ke ba...” Ta ɗan buɗe baki da mamaki, sai ta haɗe rai ta ce: “Kai ne kawai kake ganin haka ka daina min ruwan yawu da magana kamar ‘classic line’.” Sai ta juyo da sauri — gyalen ta na tashi kamar tsintsiyar shara tana tafiya da ƙyau, duk da cewa zuciyarta na bugawa saboda faɗuwar da ta sha. Ta harare wasu budurwai da suka ƙyalƙyale da dariya, sai suka kama baki da “OMG! 😭 She’s fierce!” Najeeb kuwa...? Yayi ƙasa da ƙafa yaje payment section da style irin na manyan masu kudi, yana kadawa da card ɗin sa na black platinum. “Dukkan kayan da waccan budurwar ta saya – hada da turaren Versace da agogo – ka haɗa su cikin bill ɗina.” Ma’aikaciyar store ɗin ta buɗe baki: “Toh ranka ya daɗe.” Ya ɗan murmusa, ya juya kamar wanda ya gama mission, sannan ya wuce ba tare da waiwayar baya ba. Iman ta iso wajen cashier, tana ta hararan duniya, zuciyarta cike da faɗuwar lamarin da ta sha. Sai tace da ƙarfi: “Ina bill na please?zan biya.”cashier ɗin ta ce da fara’a: “Already paid, .adam gentleman din da kika faɗi a gabansa ya biya komai.” “Whaaat?!” ta buɗe ido, ta ɗauke numfashi. Sai kawai ta lumshe ido tana fadin: “Wayyo Allah, faɗi guda na mayar da shi ‘Prince Charming’?” Wani murya daga nesa ta ce: “kuma kin ce masa ya daina bibiyarki...” ta juya da sauri. Najeeb ya ɓace. Iman ta lumshe ido, zuciyarta na bugawa tamkar kararrawar wuta kawai ta ce da cashier din: “Yayi hakan da gangan wallahi wannan raini ne!” Cashier ɗin ta ɗan matsa gaba da voice of gossip: “To Madam, ai duk abinda ke faruwa muna ganin sa a camera hakan ma ya faru a gabanmu sai fa nace ke kika faɗi, ya kamaki kamar Cinderella, agogo ya zube...” “Keeee!” Iman ta hargitsa mata harara da dariyar kunya. “Yanzu har CCTV na Sahad yana kallon fall daga sama?” Ma’aikaciyar store din ta ɗan bushe da dariya tana cewa: “Madam ki kwantar da hankali, ai romance in public abu ne na yau da kullum. Muna yi muku repost a Instagram?” Iman ta ɗan ruɗe! “Allah ya isa! Wallahi sai na rama wannan. Wani random guy ya tarwatsa min girman kai a gaba da duniya! Wuffff... ni kam nayi alwashin DAUKAR FANSA!” Ta janye bags dinta, ta janyo turaren da aka saka cikin leda, ta ɗan ɗanɗana shi cikin jin daɗin daddadan ƙamshi, sai tace da murmushi mai cike da shakku: “Kai Najeeb... idan baka raina ni ba, toh baka san irin wacce ka tabo ba.” Ta juya da ƙasaita, takalminta na “click click” a kan tiles, kamar tafiyar model a runway. Sai kawai tace a ranta: “Kayi yaro , sai mun haɗu, sai na rama wannan sweet insult ɗin da ka yi min da card dinka.” NAJEEB AND IMAN COMEDY LOVE SHOW BY NARNAH ƘANWAR SOJA ✍️ ✍️ https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC 🎇BAYAN WATA 🎇 ( Beyoung the moon ). SABON SALO Labari da tsarawa Narnah ƙanwar soja ( Sayeedan Adda ) ********* HIKIMATA ABIN ALFAHARI NA Marubuciyya tana da damar halittar mutum ta kashe shi ta raya shi, tunda 'ƙirƙirar labari ne. ta haɗa masoya, ta wargaza soyayya tsakanin masoya. Itta baiwa daga Allah ce, ubangiji ke bada itta ga wanda ya so duk wanda aka ba wa itta, sai ya sarrafa ta yadda ya ƙi so: wani ta jawo masa arziki, wani kuma ta janyo masa ɗaukaka da masoya masu girma da daraja... *****"" Sadaukar wa littafin Bayan wata sabon salo Ga Abokina Mallam Najeeb wanan Sabon salo naka ne shi ke ɗauke da martabar sunanka thank you with your support 🙏 Page 46 / 47 "Sometimes agogo baya karya yana nuna wanda kaddara zata haɗa ka da shi." Yayin da Iman ta buɗe motarta, tana kokarin tura ƙafarta cikin ginin motar nan mai kyau, wayarta ta fara kiran notification ɗin Instagram da sauti mai karfi kamar da gangan. Ting! Ting! Ting! wani sanyi ya ratsa ta, sai ta tsaya cak tana kallon allon wayarta ta buɗe app ɗin Instagram da dan karfi, zuciyarta na bugawa da karfi kamar ana dukan tambari. "Subhanallah...!" ta faɗi a hankali hotonta ne hoton nan lokacin da ta zube a ƙasa a Sahad Store, hannu a cikin na Najeeb, su na kallon juna kamar scene ɗin Bollywood ba kawai repost ɗaya ba, repost da comments suna malala: "New couple alert " "kai wannan film ne ko gaske?" "Najeeb ya fara relationship da pretty rich girl?" "waye sunan ta please? 😍" Zuciyarta na bugawa, fuskarta ta dau zafi. Ita dai ba soyayya ta fara ba, balle a duniya a ce suna tare. Zuciyarta na harbawa kamar an kunna gangar fadahawaye sun tsaya a ƙoƙon idonta, amma zuciyarta ta fi kukan nunawa raɗaɗin da ke ciki. Jin kamar ana bankado wata boyayyar duniya ce a gabanta — duniya da ita kanta bata taɓa shiga ba Ita dai ba ta taɓa fara soyayya ba, balle har a ce duniya na zaton suna tare da wani. Da sauri ta duba wayarta, ruwan notification ya buɗe kamar ambaliya – group ɗin ‘Ƴa mace Sirri,’ ‘Arewa People's,’ da sauran su na birge da saƙonni daga can cikin duhun saƙonni sai gani tayi da hotonta da wani saurayi Najeeb sun haɗu tamkar sabuwar ma'aurata, ana ta repost, ana tsokaci, ana dariya, wasu ma har sun fara hasashen sunan ɗansu na fari. Tayi ƙarar ihu – ihu da ya fito daga tsinkayen ciwon da ba a iya gani. Wayarta ta zame mata kamar wuka tayi switch off da sauri kamar zata yanke kanta da duniya ta fasa shiga cikin mota, ta fito da ƙarfi – takalmi daya ya kusa zamewa ta kuma motar cikin damuwa ta kama hanya zuwa gida, zuciya na tafasa, tunani na rikicewa. “me yasa ni? waye ya ɗora hoton? Najeeb ne? to me yasa?” Tambayoyi sun cika kanta fiye da yadda iska ke cike da hazo bayan ruwan sama. Little Yazid na shigowa gida yana tufke fuska, wayarsa a hannu kamar yana nemowa zuciyarsa mafita tunaninsa ya ɗaure — Iman ce a zuciyarsa, hoton da ya gani a Instagram da yadda aka fara yayyafa shi a social media kamar wuta a cikin ciyawa. Ya shiga call log, ya danna sunanta — Iman amma sai wayar ta ci banza, “Number not reachable.”ya tura saƙo, bai samu double tick ba.ya sake kira — babu amsa. “No, this is not ordinary,” yace da kansa, zuciyarsa na ta karan tsoro da rashin tabbas. A wannan lokacin kuwa Iman ta iso gida ba ta tsaya ko da a parking ba yadda ya kamata — motar sai da ta buga gate na ƙofar gida kaɗan, saboda hanzarin da ta ke ciki da kuma tashin hankali da ya mamaye ta ta rufe mota da ƙarfi kamar tana shure da kowa da komai. Ta shiga cikin gidan a guje, kamar mai neman mafaka daga harin duniya. ‘Yar gata ce amma yau zuciyarta ta sake mata gaba. Fuskarta ta kumbura, idanunta sun rine da hawaye da takaici. "Waye ya haɗa ni da shi? Najeeb? Ko wani daga cikin friends dina ya akaye ya tafe viral ?!" Duk da ba ta da amsar tambayoyin, tana da tabbacin daya: rayuwarta zata canza daga wannan rana. Kuma sauran su za su fuskanci Iman daban — Iman mai fansa. Zan iya ci gaba da wannan salo mai salo da ƙayatarwa idan kina so. Kina so mu shiga sashe na Yazid da Najeeb su fara jin wani abu? Ko sai Iman ta shirya ruwan fansarta tukun? Ga yadda zamu ci gaba da labarin Iman cikin ƙayatarwa, adabi da zaurance kamar yadda kika buƙata: Daga nesa ta hango katafaren parlour, haske mai launin rawaya yana kankare ƙasan tiles ɗin zinariya. Mommy ta Ihsan na tsaye a gefen kujera tana kallon hanyar shigowa, fuskar ta a cike da alamar tambaya. Little Yazid kuma na gefenta, hannunsa sanye da agogo mai kyalli, yana fidda numfashi da sauri kamar wanda ya gama gudu. Koda ta ƙaraso, bata tsaya ba — Iman ta faɗa jikin Mommy kamar ƙaramin yaro da aka tursasa masa ƙarya. Sai kuka kuka irin wanda zuciya ke magana fiye da baki. "Mommy... su sun... sun saka ni a Instagram... hotonmu da shi... kowa yana gani... Yazid...!" Mommy ta dafe kanta. Yazid ya matso da sauri yana cewa "Wani hoton? Waye shi? waye ya yi haka Iman? waye shi?!" Iman ta share hawayenta, ta gyara zama a kafet, sannan ta zuba musu ido — "shi ɗin da muka yi karo da shi a Sahad... najeeb! Shine asalin haduwar mu... amma yanzu an juya komai tamkar... tamkar mu soyayya muke yi! hotonmu... yana yawo! Yazid..." Gaba ɗaya ɗakin ya ɗauki shiru, sai karar AC da karar bugun zuciyar kowa. Mommy ta zauna kusa da ita tana dafa kafaɗarta da taushi. "My baby calm down ba komai komai zai gyaru amma dole ki bani gaskiya duka, ba zaki ɓoye min ba." Yazid ya tsaya tamkar dutse, ido cikin ido da Iman. A zuciyarsa "Waye Najeeb? Me ya haddasa wannan fitina? kuma yaushe hakan ya fara...?" A wannan daren, ƙaƙƙarfan alwashin ɗaukar fansa da kare mutuncin Iman ya shiga zuciyar Yazid. Zai nemo Najeeb. Zai nemo gaskiya. Ko da kuwa da hakan zai zubar da jini. Yazid ya ɗauki kwanaki a cikin duba da fashin zuciya, yana neman wataƙila ko shigowar sunan Najeeb zai bayyana a sahun wayar Iman ko a timeline na wani. Yana neman a sa a wayarsa, ya ce: "Ko da kuwa yana ɓoye bayan fuskar karya zan gane shi." amma ko a cikin duhu, Najeeb ya ɓoye kamar iska. Babu suna, babu account mai cikakken suna, babu labari duk hanyar da Yazid ya nufa, sai ta kulle. Iman kuwa… Tayi biyu kwana kamar tauraruwa da aka laƙe a cikin gajimare wayarta? a kashe. fuskarta? A rufe da hawayen da suka bushe a cikin zuciya. Kofa bata bude ba. Bata karɓi baƙo bata ɗaga waya. Friends nata sun gama damuwa, kiran sun koma saƙon voice note. “Iman, please ki fada mana me ke faruwa. Ki daina tsorata kanki da duniya.” Amma babu amsa. Sai wata rana, daga gidan aikin Mommy, wata ƙawarta ta zo da wata magana da ta tsuma zuciyar Iman kamar barkonon tsohuwa: "Wallahi wannan saurayin da kike yawan haduwa da shi a Sahad — Na-jeeb ko me kuke ce masa — ya dace da ke sosai mutum da mutunci kamar Balarabe har muna cewa, Allah ya halicce ku ne domin ku zama mallakin juna sai dai ke… baki fuskantar hakan ba." Iman ta ji kamar an daki ƙirjinta. Tayi shiru ta lumshe idanu. “Najeeb... ance mun dace?” Zuciyarta ta kada kamar gangar ƙasa a bikin gargajiya. Amma fa har yanzu bata gane ko menene gaskiyar shi ba. ko da gaske Najeeb ne ya wallafa hotonsu? Ko akwai wata manufa a cikin haɗuwarsu? "Shin idan ya so ni... ya ya zan yarda da shi bayan haka?" sai ta fuskanci cewa wannan haɗuwa ba ce ta bazata ba kuma ƙaddara ce da za a gudu daga gare ta ba. Bayan mako guda na ɓoye da yin shiru, yau Iman ta fito daga ɗaki kamar tauraruwar da ta jima a cikin gajimare. Tana sanye da wando Pakistan mai launin sky blue, dogon riga white mai ɗinkin zamanin Larabawa, sai takalma masu launin beige da suka dace da ƙaramin jaka da take riƙe. Gashin kanta a saki ne, ya baje har baya cikin laushi da sheki. Fuskar ta sanye da light makeup wanda ya ƙara fito da kyanta irin na ƴan mata masu nutsuwa. Da ta fito zaure, ƙamshi mai dadin turare irin na Surrati Amber ya ratsa iska ko Yazid da ya saba da ita, sai da ya kalle ta da ban mamaki. Mommy kuma tayi murmushi, ta ce: “A’a! an bamu fitowar laraba ko kuwa wata rana ce mai albarka?” Iman ta dariya kawai ta ce “toh ai ranaku suna canzawa da mutum...” A DINING... Kusan minti goma kenan ana jiran ta, yanzu kuma ta iso da annuri, ta zauna a kujerarta daidai da Mommy. Daddy yana zaune yana karanta jaridar Leadership, sai ya ɗago ido yana kallon ta “Kai Iman... kin fito da kamala kamar Sarauniya masha Allah.” Abincin safe kuma gidan ya ɗauƙa da kamshi. Croissant mai ciki da keɓaɓɓen kwai mai cheese Toast mai man zuma da lemun tsami Farfesun kwai da dankalin Turawa aka dafa da basil da thyme Zobo mai sanyi da lemo na fruits, Ruwan ginger tea a cikin cups masu launin zinariya Yazid ya ce cikin dariya "Wannan girki irin na gidan sarki ne, amma me yasa sai Iman ta dawo rayuwa muke ci haka? Mommy ta ce: "Toh ai sai farin ciki ne ya motsa girki! Mun rasa dariyar Iman tsawon mako guda, yau kuma Allah ya dawo mana da ita." Iman tayi murmushi tana kallon su cikin tausayi zuciyarta har yanzu ba ta warke ba, amma kuma tana ƙoƙarin sabawa da karɓar fuskantar duniya. Sai ta ɗauki toast ɗinta, ta ɗan tauna, tana jiyo sautin dariyar Yazid da Dad suna ta magana game da wata siyasa a shafin jarida. Yayinda suke cikin annashuwa da shan lemo da ɗan raha, sai Daddy ya ɗago kansa daga jaridar da yake dubawa, ya kalli kowa da fuskar farin ciki. “toh ku saurara da kyau... Na daɗe ina ɓoye muku wannan kyakkyawan labari har sai yau!” Mommy ta ɗan kafe shi da dariya. “Alhaji da wani sirri kuma? mu ma fa muna da zuciya!” Yazid ya ce “Daddy dai idan ya ce "albishir", toh tofa! Lallai akwai something big!” Iman kuwa, da kyar take iya ƙarewa kwai a bakinta saboda jin daɗin zaman lafiya da kulawa. Sai Daddy ya dafa tebur ya ce da murya mai cike da annashuwa: "Albishirinku ya 'yan gida! An gama komai. Visa ɗin ku duk an fitar, an kammala booking, zamu tafi aikin UMRAH gobe da yamma insha Allah kuma wannan Ramadan ɗin, a Madinah zamu karɓe shi!" "Allahu Akbar!!" Cewar Mommy da Iman da Yazid a tare. Iman ta runtse idanu da hawaye na farin ciki yana cika su dama zuciyarta tana neman sabuwar hanya da zata samu nutsuwa... sai gashi ƙofofin albarka sun buɗe da kansu. Yazid ya ɗan yi tsalle a kujerarsa yana faɗin: “Wannan Ramadan ɗin sai da Madinah! Iman, ya kika ji? ba Dubai ba, ba Paris ba, sai dai Al-Masjid An-Nabawi!Mommy ta ce: "Alhamdulillah, Allah ya saka da alheri Alhaji. Wallahi wannan rana na da albarka." Teburin ya cika da farin ciki, zuciyoyi suka cika da godiya, da fatan sabon tafarkin rayuwa.Iman ta kalli Daddy tana murmushi cikin nutsuwa: "Nagode Daddy... wannan dama ce ta sabuwar rayuwa. Allah ya bar ka mana." Ya Allah ga kukan bayin ka Ya Allah ka sa mu amsa kira zuwa ƙasa mai tsarki Ya Allah ka dube mu da idon rahamar ka Ya Allah ka amsa mana zuwa birnin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ♥️ ya Allah ka amsa mana addu'a mu har cikin zuciya mu muna bukatar zuwa wanan garin mai tarin albarka 💖 da ne da masu cewa Ameen NARNAH ƘANWAR SOJA ✍️ ✍️ https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC 🎇BAYAN WATA 🎇 ( Beyoung the moon ). SABON SALO Labari da tsarawa Narnah ƙanwar soja ( Sayeedan Adda ) ********* HIKIMATA ABIN ALFAHARI NA Marubuciyya tana da damar halittar mutum ta kashe shi ta raya shi, tunda 'ƙirƙirar labari ne. ta haɗa masoya, ta wargaza soyayya tsakanin masoya. Itta baiwa daga Allah ce, ubangiji ke bada itta ga wanda ya so duk wanda aka ba wa itta, sai ya sarrafa ta yadda ya ƙi so: wani ta jawo masa arziki, wani kuma ta janyo masa ɗaukaka da masoya masu girma da daraja... *****"" Sadaukar wa littafin Bayan wata sabon salo Ga Abokina Mallam Najeeb wanan Sabon salo naka ne shi ke ɗauke da martabar sunanka thank you with your support 🙏 ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 Page 48 / 49 "Sometimes agogo baya karya yana nuna wanda kaddara zata haɗa ka da shi." Suna tashi daga teburin nasu na ƙoshin lafiya da albishir, Iman ta ɗan harare Little Yazid cikin dariya tace: "Kai yanzu fa dole mu fara shiri sosai ni bana so a ce Iman ce ta fi jinkiri, ai ya kamata mu fara ɗiban abubuwa tun yanzu kafin tafiya." Yazid ya gyara agogon hannunsa yana murmushi: "toh Madam Alhaja! ki shirya mu wuce kenan? nima bana son sakaci, musamman idan Umrah ce, ba Dubai ba.” "Gaskiya ne let's go!" Gwagwarmayar Shirye-shirye – Dune Central Plaza, Abuja Suna fitowa daga gidan nasu mai tsari a Maitama, suka hau wata sabuwar mota Lexus LX 600 – ta Daddy ce – Yazid ke tukawa, Iman na zaune a gefensa cikin shigar Pakistan mai tsabta, kanta sanye da silken veil mai launin ruwan toka da shudi. Wurinsu na farko: Dune Central Plaza, Abuja. Wannan katafaren wuri ne na manyan masu kuɗi da 'yan kasuwa masu class anan ake samun kaya na kasaita – kaya na Chanel, Dior, Versace, Gucci, da turaruka masu daraja daga Maison Francis Kurkdjian har da na musamman kamar Oud Satin Mood. Da suka karasa, sai komai ya canza lokacin da Iman ta fito daga motar, wutar rana na haskaka fuskarta mai santsi da shigar alfarma mutane da yawa sai kallonta suke kamar tauraruwa ce ta sauka a duniya. Yazid ya zuba agogo yana cewa "Ki kalli wayarki idan kin buƙaci taimako. Ni zan je bangaren electronics.” Iman ta nufi bangaren turaruka da kayan hijabi na musamman, duk da babu hijabi mai sauƙi a wurin nan – komai luxury ne ta zaɓi wata mayafi ta Zuhair Murad mai dullin zinariya a gefe, sannan ta je wajen turaruka. > “Please, can I try this Oud Silk Mood?” Cewar Iman cikin wata nutsuwa da class da ma’aikaciyar turare ta rasa inda zata saka idanu. A gefe guda, Yazid ya shiga bangaren agogo da safa na kudi, ya sayi Tag Heuer Carrera ya ce "Wannan sai a Madinah na saka shi.” sun haɗu a kafet ɗin Dune Plaza suka zauna. Iman ta ce: > "Wai little Yazid... me kake tunani game da tafiya nan da kwana uku?" Yazid ya ɗan lumshe ido, ya ce "Na fi tunanin yadda tafiyar nan zata canza rayuwarmu ni da ke... da komai.” Iman ta ɗan sunkuyar da kai, zuciyarta cike da tunani – da begen sabuwar hanya da tsarkakken sauyi. A ranar Lahadi mai ɗauke da hasken rana mai daɗi, an wayi gari gidan su Iman da Yazid yana cike da fara'a da motsin shirye-shiryen tafiya Umrah. A lokacin suna zaune a cikin mini sitting area na bene na biyu, inda akayi decorating da fararen sofas masu lulluɓe da furen zinariya, gilashin tagogi masu haske, da Bakhoor mai ƙamshi yana tashi a ko'ina. Iman ta zube a rumfar kujera tana sanye da shigar Pakistan milk white da net veil mai hasken lu'u-lu'u. Wayarta na gefenta, tana bude album ɗin kaya da ta jera domin tafiyar. Yazid na kwance akan dayar kujerar, yana danna laptop nasa, yana share waya da apps da hotuna, yana kuma bibiyar flight booking confirmation. "Iman..." Ya kalle ta da idanunsa masu annuri. "Kin fuskanci cewa this trip is different? tun da muka soma yawan tafiya, ba ta kai wannan ba sai kamar zuciya na na ce min... wani abu na alkhairi yana zuwa." Iman ta lumshe ido tana murmushi, hannunta yana karkado mayafin kanta "Ni ma haka nake ji Yazid tafiyar nan kamar daɗin soyayyar Allah ce kuma sai na ji kamar zan samu sabuwar nutsuwa… kamar zan fara sabuwar rayuwa ta ruhu da zuciya." Daddy ne ya tsara tafiyar Group Umrah, domin dama shi babban dan kasuwa ne da ke yawan jagorantar tafiya irin haka ga iyalai da aminansa wannan karon, Mommy da Daddy za su fita tare da 'ya'yansu bayan dogon lokaci – domin kowa a busy yake da makaranta, aiki da project. > "Bayan shekara biyu kenan da tafiyarmu ta ƙarshe wannan karon, Umrah duka zamu je tare " Baku ga ɗan daraja ba?” Daddy ya faɗa a cikin living room yana kallon su Iman da Yazid. Mommy tana nesa, tana duba passport ɗin su cikin kwali mai kyau ta ɗago kai da murmushi: "Sai mu ɗauki azumi a can. Ramadan a ƙasa mai tsarki ba shi da kama." A lokacin da suka je Hilltop Mall da ke Maitama domin sayan kayan tafiya na ƙarshe, suka ɗauki wasu hoto a wurin masu kayataccen wuri. Kwana guda bayan haka, sai Instagram ta yi mugun girgiza! Hoton Yazid da Iman sanye da abaya da shadda a wajen sayayya, naƙasasshen rubutu yana cewa: “Power siblings headed for Umrah – Abuja's elite…” #YazidAndIman #Umrah2025 #SiblingsGoals Tafiyar Na Gabatowa... An kammala shiryen passport, visa, kayan azumi, da na kiran sallah – komai cikin tsari. An tanadi turaruka, miswak, alwala bottle, da hijab masu tsada. Tafiyar za ta kasance kamar mafarki – cikakken tafiya daga Abuja → Madinah → Makka → Jeddah. *************** Zuwa Ƙasa Mai Tsarki Washegari da safe, Abuja International Airport ya cika da hayaniya, walwala da motsin tafiya. Iyayen Iman da Yazid – Daddy da Mommy – suna sanye da kaya masu kyau da nutsuwa, fuskokinsu cike da annuri da godiya ga Allah. Tare da su akwai ƴan uwa da abokan arziki da suka yi nasara samun wannan tafiya. Iman ta fito cikin doguwar abaya blue mai sheƙi da veil white, fuskar ta cike da natsuwa da fara’a. Yazid na gefenta yana rike da small carry-on luggage, yana duba boarding pass ɗin su. Tayi murmushi cikin zuciya. "Ya Allah, na bar komai a bayana… har da Najee– ehm…" ta taɓe baki tana sauke ajiyar zuciya. Gaskiya, zuwa ƙasa mai tsarki ba kamar duk tafiya ba ce. Rayuwa da abubuwan duniya na koma baya, ruhu na kama tafarkin Allah. “Iman! Ga takalman ki sun kusa zamewa…” Mommy ta ce da dariya, tana gyara mata hijab Yazid ya leƙa daga bayan trolley: “kin fi kowa kyau yau… kamar ba ke ba!” Iman ta saki dariya tana jefa masa harara. “bari dai ka gani lokacin da na iso Harami, da ka ga tsoron da zan ji da farin ciki, da wata irin nutsuwa…” A cikin jirgi, komai cikin lumana da salati ana zaune cikin jerin kujeru business class, inda aka raba kayan karatu, dates da ruwan zamzam. Flight attendant ɗin sun amsa da "Assalamu Alaikum" cikin ladabi, kowa da fuskar tsarki. Iman ta kalli tagar jirgi, tana ganin kasa na raguwa ƙasa "Wai ni har na bar Abuja kenan? Wannan rayuwar can, rubuce-rubuce, Instagram, kukan zuciya… komai na duniya ya bace a idona yanzu." ta lumshe ido, hawaye suka sauko cikin farin ciki "Allah! Na barka da komai ka kawo ni gun Ka lafiya, ka karɓi zuciyata kamar yadda take." Yazid yana gefenta, ya sauke ajiyar zuciya “Na saba da tafiya, amma wannan tafiyar... sai dai in ce haji ce ta ni’ima. Allah yasa mu dawo da rahma da canji.” Bayan tafiya mai albarka da natsuwa, jirgin ya sauka a King Abdulaziz International Airport – Jeddah. An karɓe su cikin kulawa da jagora na musamman, an ɗauke su cikin mota mai sanyi da tsabta – sun hau hanyar zuwa Makkah Al-Mukarramah, gari mai albarka. Kamar mafarki ne a zuciyar Iman lokacin da suka fara hango babban Clock Tower da minaret na Masjid Al-Haram suna leƙo daga nesa. Ta sauke hawaye, zuciyarta na bugawa da ƙaunar wurin da Allah Ya ke kira har aka karɓe su. > “Wannan ba gidan kowa ba ne, ba wurin yawon buɗe ido ba ne – wannan ƙasa ce mai tsarki. Ni dai Iman… na sauka.” ( tare da ƙanwar soja mai ɗauko rahoto daga cikin jakar Iman lolz) HOTEL: Swissôtel Makkah An kai su Swissôtel Makkah, ɗaya daga cikin fitattun hotel-hotel guda bakwai da ke cikin ginin Abraj Al Bait Complex – d’aya da Clock Tower. Hotel ɗin yana da fuska kai tsaye zuwa Harami, kuma suna kallon Ka’abah daga manyan windows ɗinsu. Swissôtel Makkah ya amshi su da kulawa an basu suites masu kyau da tagogi masu kallon Ka’abah kai tsaye. Komai ya cika da tsari da tsabta: – Gidan wanka mai fumfuna na zamani – Beddings farare masu ɗumi da tsafta – Kayan sha da kayan ciye-ciye na musamman – Wi-Fi da Qur’ani a cikin kowane ɗaki Iman ta hau gadon ta, ta kalli Ka’abah daga taga “Allahu Akbar wannan wurin ya fi kyau da tsarki fiye da duk inda na je. Nima fa yau na iso ƙofar rahama.” Ta dafa kirjinta, zuciyarta na bugu da sabuwar soyayya – ba soyayyar duniya ba, sai wacce ke cike da tsoron Allah da shauƙin kusanci da Ubangiji. Mommy ta shiga ɗakin tana kallon ta. “Iman, Allah Ya albarkaci zuwan mu wannan tafiya za ta canza mana komai imanin sabon yanayi tamkar ban taɓa zuwa nan ba inajin wani bayyanar abu tamkar Ubangiji ya amshe addu'a na na tsawon shekaru …” Iman ta kalli mahaifiyarta, ta ce cikin tausasayyen murya: “Mommy… na yarda yanzu: akwai natsuwa da zaman lafiya a ƙasar da zuciya ke kiran Ubangiji fiye da duniya.” Cikin natsuwa da tsoron Allah, Iman, Yazid da iyayensu suka shirya cikin kayan Umrah — Iman cikin farar abaya mai ɗaukar ido, da nikabinta da ya leƙa da kyakkyawar nutsuwa. Yazid cikin farin ihram yana waƙar Qur’ani cikin ƙasa da murya. Su Daddy da Mommy kuwa, kowanne ya sha ado da dattijantaka da ladabi na masu tafiya ga Allah. Gaban ƙofar King Fahd Gate, zuciyar Iman na harbawa kamar ana bubbuga ganga. Sai da ta kama hannun Mommy tana dafe ƙirji. "Mommy... wannan shine Harami? Shine nan Ka’abah ke ciki?” Mommy ta dafa kanta, ta ce: "Eh... nan ne mafita ta duniya. Mafarkin kowane mumin." Suna taka kafarsu cikin masallacin, sai kwarjininta ya daki su. Fuskokinsu suka kai ƙasa, zuciya ta cika da rawar murya, hawaye na zuba... har suka isa da'irar Ka’abah. Iman ta tsaya cak tana kallon wannan Ginin Mai Tsarki da aka gina da duwatsu masu ɗauke da tarihih. “La ilaha illallah…” “Subhanallah…” “Na iso… ya Rabb.” Suka kama tawaf – juyawa bakwai suna ambato: “Labbayka Allahumma Labbayk…” Kowace juya, Iman tana kuka cikin zuciya. Idanunta a rufe, zuciyarta na faɗin: “Ya Allah, ka tsarkake zuciyata kamar yadda Ka tsarkake wannan Gini.” Yazid yana gefenta yana karanta Suratul Ikhlas da Suratul Falaq, yana kariya gareta cikin sirri. Suna kammala tawaf, sai suka nufi Safa da Marwah. Iman tana dafa hannu, tana kallo yadda mutane ke gudu da nutsuwa — tana tuna da labarin Sayyida Hajarah. “Ina son in zama kamar ita, mai tawakkali dakwazo Bayan kwana biyu na ibada da natsuwa a Makka, Iman, Yazid, Ihsan, da iyayensu suka kama hanya zuwa Madīnatul Munawwarah — birnin Annabi ﷺ, birnin haske da rahma. Suka hau jirgin ciki sharaf, kamar aljanna a duniya. Duk sun sa kayan hajjajai masu kyau. Iman cikin doguwar abaya mai launin ruwan zuma, Ihsan cikin sky blue hijab mai laushi da tsafta, Yazid da farin jallabiya da hula, Mommy da Daddy cikin kamun kai da kwalliya irin ta masu biyayya ga Allah. Cikin jirgi, Iman ta kalli Ihsan tana murmushi: "Kin san me? Ni a Madinah zan sake jin numfashina." Ihsan ta share hawayenta, ta ce "Shekaru ashirin da biyar kenan... kullum addu’a nake Allah ya bayyana 'yan uwana. Kwanan nan ina jin zuciyata na karɓar amsa. Suna sauka, gabar Masallacin Annabi ﷺ tana lumshe ido kamar tana karɓar bakinta. Sai suka sauka a Dar Al Taqwa Hotel – hotel mai kallon harabar masallaci. Tana fitowa daga mota, kallon minaret na masallacin ya sauya dukkan jikinta. Ta zube ƙasa tana kuka. “Ya Rasulallah ﷺ... ga bawa mai laifi, amma mai ƙauna… na zo!” Iman da Mommy suka dafa ta, suma hawayensu na gangarowa. Suna shigowa, zuciyoyi suka narke. Hasken fentin masallaci, kafet ɗin kore mai santsi, da ƙamshin miski sun rufe kowacce damuwa. Suka nufi Raudah, wurin da ake ce wa Aljanna ce a duniya — daga mimbarin Annabi ﷺ zuwa gidansa. 🌿 Addu’ar Iman… Iman ta durƙusa tana faɗin: > “Ya Allah, ina gaban ƙabarin Annabinka ﷺ. Ka tsarkake rayuwata, ka bani zaman lafiya da wadata cikin halal. Ka rufe tarihin na baya ga bamu zaman lafiya a kasar mu na Nigeria ka sauwaƙa mana fittintunin zamani .” Yazid na gefenta, yana fadin “Ya Rabbi, ka haɗa zuciyoyin mu cikin ƙauna sabodaKa. Ka bamu aure mai albarka da zuriyya masu tsoronKa.” A gefenta kuma, Ihsan ta zuba ido cikin girgiza kai, tana tuna lokacin da suka sha wahala, baƙin ciki, yunwa da ƙorafi. Sai ta kalli Iman tana fadin: “Allah ya rubuta farinciki a ƙaddara ta. Idan wannan ce hanya ta, to na yarda Ya Rabb.” Bayan sallar Isha'i, suka koma hotel. Gaba da gaba da masallaci, dakin su na kallon Rawdah, Iman ta tashi da Azkar. Daga window tana kallon al'umma masu shiga masallaci da daren dare. ( 🕊️ Wanda ya bar komai saboda Allah, Allah zai bashi komai fiye da tsammani. ). Bayan kwana biyu da isowarsu Madinah, watan Ramadhan ya kama. Gabar masallacin Annabi ﷺ sai armashi da ƙamshin shaƙaƙƙen ruhin tsarki da tausasawa. Duk inda ka kalle, sai ka ga darajar wannan wuri da wannan lokaci. 🕋 Iman, Ihsan, da Yazid sun tashi da azumi… Cikin dakin hotel, saƙon megaphone daga Masallaci ya shiga: "Ya ayyuhan-nas… qad jaa’akum Ramadhan… shahrur-rahmah, wash-shahrul-maghfirah!" Duk suka bude idanu, zuciyarsu cike da natsuwa. Iman ta kalli agogo — ƙarfe 4:30am, lokacin sahur. Sai ta tashi a hankali, ta nufi kitchen na suite ɗin su. Ihsan na biye da ita, Yazid yana tafe da 'yar murmushi. Sahur a cikin zaman lafiya… Sun shirya abinci: Khobz (bread na Larabawa), foul (wake mai miya da man zaitun), qahwa (coffee na Arab), dates masu ɗanɗano, da lemon tea mai zafi Iman ta kalli Yazid “Wallahi natsuwa irin ta Madinah daban ce. Kamar zuciyata na sabuwa.” Yazid ya murmusa: “Sabuwar zuciya, sabuwar fata… da sabuwar soyayya.” Bayan azahar, suka je ziyara: Uhud — inda Annabi ﷺ ya yi yaƙi. Gidan Sayyidah Fatimah – sun tsaya suka yi addu’a. Masjid Quba – wanda Annabi ﷺ ya ce: “Duk wanda ya yi alwala a gida, ya je ya yi sallah a Quba, yana da lada kamar Umrah.” Ihsan ta kalli Iman “Zuciyata na ta kuka, amma cikin farin ciki. Na ji kamar ina ganin su Sayyada Khadija da Fatimah.” Lokacin iftar, duk suka fito suka samu taburma a harabar masallaci. Gaba da su, wani dattijo daga Pakistan ya jero: ruwan sanyi dabino ruwan yogurt da gurasa mai zaƙi. Sun bude baki cikin tsarki da albarka. Bayan sallah, sai Yazid ya kalli Iman ya ce: “Wallahi duk duniya babu inda na fi jin cewa Allah yana kusa da ni irin Madinah.” Iman ta ce cikin sanyi: “Ina fatan daga nan Allah ya cigaba da rufe mana tarihin baya da bude sabuwar dama.” A daren Tarawih, duka suka tsaya kamar an dasa su. Hawaye na gangarowa, zuciya na mika, da harshen su yana faɗin: “Rabbighfir li, wali-walidayya, warhamhum kama rabbayani saghira.” BAYAN AZUMI Iman da Yazid suna tsaye a bakin window na dakin su da ke Fairmont Makkah Clock Royal Tower Hotel, kallon masallaci suke cikin nutsuwa da shauƙin kwana guda kafin Laylatul Qadr. Bayan sallar Asr, Yazid ya juyo ya ce: "Yanzu kam lokaci yayi… mu shirya mu je siyayyar sallah. Mun gama azumi " Iman ta murmusa, tana gyara gashin ta cikin veil mai launin zinariya da fure-fure. Kwalliyar ta da ta kwanta cikin fararen kaya masu sulbi, sai ka ce sarauniyar Larabawa. Sun hau lif din hotel din su suka sauka kai tsaye zuwa ƙasa, inda yake haɗe da Abraj Al Bait Mall — shahararren wuri mai ɗauke da shaguna na duniya irin su: Harrod Cartier Gucci Zara Arabian Oud da kuma shagunan kayan Musulunci irin su Al-Haramain da Ajmal Perfumes. Yazid ya siya: Agogo Rolex, White Thobe mai ɗinkin saudi style, da turaren Oud Muattaq. Iman kuwa ta shiga: Boutique na Abaya, ta zaɓi riga black silk abaya da aka yi da zinariya, Turare mai suna Shaghaf Oud Aswad, Da kuma takalmi mai launin lu'u-lu'u daga D&G. > "Yazid, wannan turaren kamar zuciyata ya shige," tace tana lumshe ido. "Ke ce ke cikinsa," Yazid ya amsa da murmushin kaunar ƙanwar sa Bayan siyayya, sun zauna a wani café da ke saman bene — Al Makan Café, inda aka musu: Vanilla Qahwa Ajwa smoothie Date tartlets Suna zaune suna kallon masallaci, sai Iman ta ce: "Na ji kamar ba zan koma duniya ba. Wannan Makka sai ta tsarkake ni gaba ɗaya." Yazid ya ce: "Ni ma dai kamar zuciyata ta sake. Kuma nasan wannan siyayyar, ba sallar ce kawai muke shiryawa ba… sai mun yi siyayyar sabuwar rayuwa." ✨ Kafin su koma hotel... Suka wuce gold jewelry store — Yazid ya siya mata ɗan ƙaramin sarka mai sunan "IMAN" da lu'u-lu'u. "Za ki riƙe wannan kamar yadda na ke riƙe ki cikin raina." Iman ta ɗaga kai, hawaye ya kawo ƙyalli a idonta, tace: "Ka cancanci fiye da zuciya, My brother Yazid." Haurawa upstairs sukaye inda zata raka sa ya zaɓi kayan tsaraba ga abokan sa little Yazid dake ta faman gwada wani jalabiyya a madubi ya hango Iman ta tsaya chakk ko ƙofta ido bata iyawa jinin hukunta ya tsaya chakk duk ruhinta ya tafe akan ................ To be continued by narnah Khadijah 🥰🥰🎊 Happy weekend https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC 🎇BAYAN WATA 🎇 ( Beyoung the moon ). SABON SALO Labari da tsarawa Narnah ƙanwar soja ( Sayeedan Adda ) ********* HIKIMATA ABIN ALFAHARI NA Marubuciyya tana da damar halittar mutum ta kashe shi ta raya shi, tunda 'ƙirƙirar labari ne. ta haɗa masoya, ta wargaza soyayya tsakanin masoya. Itta baiwa daga Allah ce, ubangiji ke bada itta ga wanda ya so duk wanda aka ba wa itta, sai ya sarrafa ta yadda ya ƙi so: wani ta jawo masa arziki, wani kuma ta janyo masa ɗaukaka da masoya masu girma da daraja... *****"" Sadaukar wa littafin Bayan wata sabon salo Ga Abokina Mallam Najeeb wanan Sabon salo naka ne shi ke ɗauke da martabar sunanka thank you with your support 🙏 ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 Page 50 / 51 HAPPINESS IN BAYAN WATA 🎇 Ana cikin haka… Yazid na daga gefen madubi yana gwada jalabiyya, yana ɗan murɗa hannun rigar, idanunsa suka kai ga fuskar kanwarsa Iman. Sai ya hangi canjawa a fuskarta: zuciyarta ba kamar da ba. fuskarta ta dau wani launin zafi da ɗan firgici. kamar wacce ta ga abin da ya tayar mata da ƙwaƙwalwa. “La haula wala quwwata illa billah…” ya furta a ransa cikin mamaki. Ya riga ya san halin kanwarsa ba shirme take ba amma yau, kallon da take yi wa wancan saurayin mai gilashi ya girgiza shi. Ya maida kallonsa gare shi. Sai ya ce a ransa: “Innalillahi… wannan ba ƙaramar halitta ba ce. Ga kwarjini, ga nutsuwa, ga kyau irin na mutanen da aka fi ƙima. Idan ba ɗan wani sarki ba ne — to sai dai ya fito daga gidan gwamnati kai tsaye.” Yazid ya ɗan ƙanƙame jikin sa cikin riga, yana fitar da numfashi a hankali. Sai ya ƙara cewa a zuciyarsa: > “Kanwata Iman ta kusa rikicewa saboda kallo ɗaya. Wannan saurayin akwai shi da wani sirrin shanye zuciya. To amma ni da nake nan da ita shekaru, ban taɓa ganin tana rawar jiki haka ba...” Ya kalli Iman, ta kasa tsayawa wuri guda. Hannunta na ɗan karkarwa. Idonta yana ƙoƙarin komawa gefen saurayin, amma sai ta murɗe fuskarta kamar wacce ta ci karo da tunanin da bata shirya ba. Sai Yazid ya ɗan sosa gemunsa yana dariya a zuciya: “Watakila yaron Sarkin Makka ne ai ga yadda ya ɗaura alkyabba kamar wani amintaccen ɗan gidan girmamawa ga arziki, ga girmamawa a fuskarsa ga nutsuwa da kwarjini… Allah ya kyauta.” ya matso kusa da ita, yana faɗin da dariya: “Iman… me kika hango ne haka? ko aljani ne a madubi?” Iman ta yi ƙoƙarin dariya, amma muryarta ta sare, tana jan numfashi tana juyar da kai: “Kamar wani ne na sani kawai… babu komai.” Yazid ya yi shiru, amma zuciyarsa ta fara leƙen bayan madubi. Waye wannan saurayin? Iman ta danna rigarta, ta matso da hijabinta sosai kamar tana buya da hijabin tace da murya mai rauni amma cike da ɗoki: "Yazid… mu bar shagon nan… yanzu-nan…" Yazid ya kalleta da mamaki. Amma ya lura da yadda idanunta ke yawo kamar masu neman mafaka ba ta iya tsayawa wuri ɗaya. Yayin da suke ficewa daga cikin babban shagon tsarabar dake cikin katafaren "Abraj Al-Bait Mall", suka kusan kai ƙofa kenan… Sai suka ji muryar namiji mai sanyi da natsuwa, amma tana da sauti da zai tsaya maka a ƙwaƙwalwa "Iman?" Tayi turus kamar ba ita ba, taji jikin ta yayi sanyi har ƙafafunta suka kasa ɗaukar nauyinta. Yazid ya tsaya cak. Cikin faɗuwar gaba, ya juyo ya kalli inda muryar ta fito. Wannan ba kowa ba — sai NAJEEB! Sai lokaci ya tsaya kamar an yi shiru a duniya. yana tsaye a gefen wata madubaiyar bulo, jalabiyyarsa ta milk white tana shan hasken fitila, gashinsa yana murɗewa a gefen hancinsa, fuskar sa tana cike da halin jarumta da kwarjini. Iman ta kasa furta komai. Kallon ta a kansa, numfashinta na wani irin sauka da hawa. Zuciyarta ta ce "toh ashe ba mafarki bane? Ashe shi din ne — da gaske NAJEEB ya bayyana?" Yana kallonta da kyau, cikin nutsuwa, ya ƙara matsowa, muryarsa cike da ladabi "kin yi shiru Iman… baki gane ni bane?" Iman ta kura masa ido, sai ta daga hannu kamar wacce zata ce "kai ne?", amma sai ta kasa sai ta juyo gefe tana ƙoƙarin ɓoye hawaye da suka fara cika mata ido. Yazid ya tsaya yana kallon ikon Allah. “Da gaske wannan ne Najeeb? Ashe shine wanda ya yaye hankalin ‘yar uwata cikin mintuna kaɗan…” Iman ta lula… A zuciyarta, komai ya ƙage wani sanyi ya mamaye zuciyarta, amma kuma wani irin ɗaci ya shige mata makogwaro sai yanzu ta kara tabbatar:"Na rasa… kuma na samu. Amma a wane hali?" A lokacin da kalmar "Iman?" ta fita daga bakin Najeeb — ba Yazid kaɗai ne cikin mamaki da razana ba... . Daddy Ado da Mommy Ihsan suka shigo shagon, suna tafe da sauri kamar masu bin kira daga zuciya. Mommy Ihsan har da ƙarin ledoji a hannu, Daddy Ado kuma na saka agogon sa, tamkar wanda yake fuskantar abu mai nauyi da yake so ya tabbata. Da suka shiga — sai suka tsaya cak. Hankalinsu ya kwanta kan fuskar saurayin da ya kira "Iman" da muryar da ke jirkita jin zuciya. Kallon su ya canza... daga mamaki zuwa shakku, daga shakku zuwa amincewa da abu mai nauyi da suka daɗe suna jinkirta yarda da shi. Mommy Ihsan ta lumshe ido. Ta buɗe. Ta tsinci kanta cikin tunani mai nauyi. Sai ta faɗa da ƙasa-ƙasa, kamar magana da kanta: "Wannan shi neNajeeb." Iman kuwa... Ta riƙe hannun rigarta da ƙarfi, zuciyarta na bugawa kamar ana busa gangar yaki a cikinta. Sai ta juyo a hankali… Ta haɗa ido da Najeeb kamar kiran zuciyarta ta ce: "me kake nema yanzu? wane abu kake so ka kawowa rayuwata a cikin wannan tsarkin da na samu?" Najeeb ya matso ƙasa fuskar sa cike da ɗoki amma yana ƙoƙarin zama mai nutsuwa. Mommy Ihsan ta share hawayen da ba ta sani ba ya gangaro mata. Alhaji Ado ya matso gaba yana ƙare wa Najeeb kallo "kana da tambaya a cikinmu yaron nan…" Daddy Ado ya matso daga bayanta. Sai da ya taka sau biyu kamar mai kallon tsohon hoto da aka ba shi mamaki. Ya tsaya ya lumshe ido. sai kuma ya furta da murya mai taushi amma mai nauyi:"In dai wannan ne… to fa gaskiyar duniya tana da salo." Suna kallon sa kamar ƙauyawa da suka fara ganin silima — ko kamar iyaye da suka ga abin da ‘ya’yansu suka ɓoye tun shekarun baya. Yazid ya kalli Mommy Ihsan da Daddy Ado — yana kallon yadda suke kallon Najeeb da irin wannan shakkar da ake gani a fuskar wanda ya gane abu amma har yanzu bai yarda ba. "Me yasa suke kallon sa kamar haka?" ya tambayi kansa, zuciyarsa na bugawa da tambayoyi. Har yanzu bai iya haɗa hoton da ke yawo a kafar sada zumunta da wannan mutum mai tsayin daka, sanye da farar jallabiya, wanda yanzu ya tsaya gaban su da tawali’u da kwanciyar hankali. Iman kuwa... Tana jin nauyin duniya a ƙirjinta. Tana jin zuciyarta na bugawa da sauri kamar ana busa gangar yaki a cikinta. Sai ta juya... Ta haɗa ido da Najeeb. Idanu hudu. Kamar hoton da aka ɗauka shekaru baya yana dawowa cikin rayuwa. Kamar lokaci yana neman dawo da duk abinda ta ɓoye tun cikin duhu na zuciyarta. "Me kake nema yanzu?" "Wane abu kake so ka kawowa rayuwata a cikin wannan tsarkin da na samu?" Zuciyarta ce ke tambaya amma bakinta shiru. Najeeb ya matso ƙasa Fuskar sa cike da ƙaunar da take ƙoƙarin fitowa daga cikin damuwa da nadama. Ya tsaya. Ya kalle ta. Ya furta cikin muryar da bata canza ba — murya mai sanyi, mai ɗauke da raɗaɗin wanda ya farka daga mafarkin baƙin ciki: Mommy Ihsan ta share hawayen da bata sani ba ya gangaro mata. Daddy Ado ya lumshe ido, sannan ya ce da murya mai ƙarfi amma mai natsuwa: "Kana da tambaya a cikinmu, yaron nan..." "Kana da tarihin da bai ƙare ba." Sai Iman ta numfasa... Ta kalli Mommy Ihsan ta kalli Daddy Ado ta kalli Yazid wanda ke tsaye cikin rudani. Sai ta ce Kafin Iman ta iya motsawa daga inda take tsaye… Wata Balarabiya ta shigo cikin shagon. mace ce sanye da abaya mai kyalli kamar an dinka ta da zinariya, haɗe da mayafin da ya lullube kanta daidai da al’adun gida, amma kuma jikinta yana bayyanar da ɗaukaka, kima da zallar kuɗi. Fuskarta cike da annuri, sheƙi na lafiya da kwanciyar hankali yana bayyana a kowanne motsinta. Takalminta sun shige ƙasa suna yin ɗan ƙara mai laushi kamar ana bi da murmushi a kasa. Tana tare da wani babban mutum – mai shekaru kamar tsakanin hamsin sanye da shadda mai tsada, fuska mai cike da kwarjini da nutsuwa irin ta manyan masu mulki ko ‘yan kasuwa. Ana ganin kamala da daraja a ko’ina a jikinsa. Sun tsaya cak. Dukansu suna kallon Najeeb da murmushi mai ɗauke da gamsuwa da alama kamar sun same shi cikin abin da suka daɗe suna jira. Sai babban mutumin ya furta da murya mai ƙarfin kwarjini da taushin tausayi: da harshen larabci"Najeeb, yaro na… haka ka zo? ba ka fa sanar da mu ba." Balarabiyar ta matso ta riƙe hannunsa da dariya "Anta! Ma sha Allah… da gaske kana nan mun gaji da jiranka!" Mommy Ihsan ta kalli Daddy Ado da sauri. Yazid ya waigo da sauri ya kalli su. Iman kuwa… gaba ɗaya jinin jikinta kamar ya tsaya. Hannunta ya soma rawar da ba za ta iya hana ba. “Yaro na…” “Mun gaji da jiranka…” Waɗanda suke ne? su waye a rayuwar Najeeb? shin shin zai yiwu yana da wata rayuwa da babu wanda ya sani? kuma me wannan ke nufi gare ni? Zuciyarta na faɗaɗa da tambayoyi. Duk da haka, sai idonta ya sake sauka kan fuskar Najeeb — wanda ke kallonta da tausayi da damuwa, kamar yana fargabar lamarin zai ɓace masa kafin ya bayyana komai. "Maryam…?" Daddy Ado ma a tare da ita kamar an saka su cikin script ɗin ɗaya ya furta: "John…?" Maryam da John, waɗanda suka waigo a lokaci guda kamar jikin su ya gane da kiran. Iman ta juya a hankali tana kallon su. Yazid ya ɗaga gira yana so ya tabbatar da abinda ya gani. A cikin shiru mai nauyi, an ji Maryam cikin wata kakkausar murya, kamar wadda aka kama da laifi "Ihsan? Ado??" John ( Munir ) kuwa kamar zai ja baya yana kallo da tausayi da ruɗani. Bai san ko ya matso ko ya tsaya ba. Kowa ya zuba ido. Wani shiru… kamar na wuta kafin ta kama. sai Mommy Ihsan da Daddy Ado a lokaci guda kamar an saka su a fim ɗin dariya su ce da murya ɗaya "ke da kai? kuna tare?! " Sannan suka juya su kallon juna su sake faɗin: "Ihsan?" "Ado?" Hankali ya tashi! Yazid ya fashe da dariya yana kama ciki. Najeeb ya kalli Maryam da John da mamaki yana cewa "Kuna nan ma?" Iman kuwa tana kallon kowa tana jin kamar ta faɗi a ƙasa — amma sai ta kama baki tana dariya ƙasa-ƙasa. Duniya ta rikice a cikin babban mall na Makka. : Maryam Al-Fulan – Fitacciyar ‘yar kasuwa a gabas ta tsakiya. Munir John Al-Mujtaba – Masanin tattalin arziki da haɗin gwiwar kamfanonin duniya. Suna kallon Najeeb da murmushi mai cike da ƙauna, wanda shi kuma yake kallon su da ɗan ɗoki da kunya. Fuskar Najeeb na nuna cewa wannan al'amari mai nauyi ne — ya san lokacin bayyanar gaskiya ya zo. Maryam ta ƙaraso da sanyi da kwanciyar hankali. Ta ce cikin muryar da Iman ta sani daga nesa Mommy Ihsan ta zaro ido tana kallon Maryam sosai. Daddy Ado kuwa ya furta da karfi: "Maryam! Munir!!" Iman ta kalli su, sai kuma ta kalli Najeeb — tana kallon zuciyarta na fasa kamar ƙaho. Sai Mommy Ihsan ta furta, cikin mamaki da dariya, tana kallon Ado: "Ka ce min wannan shi ne Najeeb ɗin da Iman ke kuka dashi shekaru biyu da suka wuce!" Ado ya ce "Ke kika ce a rufe! amma yanzu… shi kenan wannan ai Allah ya riga ya rubuta!" Yazid ya zura hannu a aljihu yana kallon shirin silima live! Ihsan ta saki ledar tsaraba daga hannunta kamar wacce ta manta da komai a duniya, ta yi tsalle ta rungume Maryam da hawaye mai zafi amma na farin ciki. "Maryam! ashe kuna raye?! ashe baku mutu ba?! ash ashe duk wannan rayuwa sai yau zan sake jin wannan ƙamshi?!" Maryam ta rungumeta da ƙarfi, cikin tausayi da murmushi mai taɓa zuciya. "Ihsan... muna tare da ku ne duk wannan lokacin. Sai dai zaman lokaci ya hana bayyana." Daddy Ado kuwa ya isa gaban Munir, suka kalli juna na tsawon lokaci. Daga nan ya buɗe hannuwansa ya rungume shi kamar babban ɗan’uwa da suka dade ba su haɗu ba. "Munir! Ashe kai ne?! ashe kai ne?! Wannan ba mafarki bane?" Munir ya ce cikin natsuwa: "Rayuwa ce Ado, sai da ta ɗauki ruwa, sai yanzu ta dawo da iska mai sanyi." Little Yazid kuwa ya kwaso gudu ya faɗa jikin Munir suka rungume juna sosai. Najeeb ya dafa kan sa yana murmushi: "Kai Yazid! Ashe yanzu kai ne ƙaramim Yazid namu da na rasa shekaru da dama?" Iman kuwa... ta tsaya daga nesa, tana kallonsu kamar wanda ke kallon fim. Ta ɗauki wayarta, ta fara ɗaukar hoto da hawaye a idanuwanta — hawaye masu daɗin gaske. tana ɗaukar hoton komai da komai — kama daga Ihsan da Maryam, zuwa Ado da Munir, har zuwa Yazid da Najeeb. Sai ta ce da zuciyarta: "Wannan hoton, ba kawai na dauka bane. Na ɗauki tarihi ne... labari ne da zan tuna har ƙarshen rayuwata." AFTER SOME HOUR'S Motoci uku ne suka ratsa cikin wani sanannen layi na 'Yan larabawa a Makka. Layin da kowanne gida ke da masallaci a ciki, kuma gidaje masu ƙamshi da tsari na Musulunci da larabci irin na asali. A cikin mota ta farko akwai: Maryam, tana riƙe da hannun Ihsan, sai Iman dake gefe tana kallon titin da shakku da tsoro da farin ciki ke rikicewa a fuskarta. Mota ta biyu: Najeeb a kujerar direba, sai little Yazid Motar ƙarshe: Ado da Munir suna hira da dariya irin wacce ba su yi tsawon shekaru goma ba. A karshe suka tsaya a gaban wani katafaren gida mai babbar ƙofa da alamomin larabawa a jiki — filastik na zinariya da yashi. Kofar gidan har da gardin larabawa biyu masu rawani da alamomin tsaro. Gidan yana da babbar alamar "Bayt Al-Rahma" — Gidan Rahama. Sun shigo babban parlour mai faɗi kamar fili — fentin fari, ja da zinariya, fitilun chandelier guda biyu sun rataye daga saman rufin da ke da ado na gold calligraphy (zane na kalmomin larabci). Cikin gidan akwai: Sofa masu launin beige da ruwan zinariya. Big-screen plasma TV a bango, yana nuna hoton Ka’aba kai tsaye daga Masjid al-Haram. A tsakiyar bango babban Frame da aka rubuta “After the Moon – Bayan Wata”, tare da hoto na matafiya biyar a cikin sahara – Ihsan, Maryam, Munir, Yazid Ado. Haddimai larabawa biyu suka karɓi jakunkunansu, suka miƙa musu ruwa da gahwa a gilashin zinariya. Sautin oud (wakar larabawa) mai sanyi na fita a hankali daga bangon waje. Maryam ta kama hannun Ihsan suka zauna akan kujera, Iman ta zuba ido tana kallon bangon da hoton su. "Wallahi... wannan gida ne na gaskiya," Ihsan ta faɗa cikin sauke numfashi. Najeeb ya kalli frame ɗin hoton da ke bango ya ce "Wannan shine burin Mahaifiyata – a taƙaice rayuwar ta na baya ya dawo a zahiri cikin hoton da zai zauna har abada." Munir ya dafa kafadar Ado ya ce "Ado, yanzu gaskiya ta bayyana. Rayuwa ta gyaru mun dawo gida." Yazid kuwa yana zagaye da dariya, yana shan juice, yana cewa: "Daddy Najeeb, ni yanzu na zama ɗan gida biyu fa!" Idan har kunjee daɗin page nin naga alert a opay na 🤣🤣🤣🤣 Narnah ƙanwar soja ✍️✍️ https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC 🎇BAYAN WATA 🎇 ( Beyoung the moon ). SABON SALO Labari da tsarawa Narnah ƙanwar soja ( Sayeedan Adda ) ********* HIKIMATA ABIN ALFAHARI NA Marubuciyya tana da damar halittar mutum ta kashe shi ta raya shi, tunda 'ƙirƙirar labari ne. ta haɗa masoya, ta wargaza soyayya tsakanin masoya. *****"" Sadaukar wa littafin Bayan wata sabon salo Ga Abokina Mallam Najeeb wanan Sabon salo naka ne shi ke ɗauke da martabar sunanka thank you with your support 🙏 ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 Page 52 / 53 Yau da rana bayan sun sauke kaya, sun yi wanka sun ɗan huta, gidan ya dauki shiru mai daɗi irin wanda yake zuwa ne kawai bayan gajiya da soyayya, a ɗayan zauren falon, little Yazid da Najeeb suna zaune akan ɗaya daga cikin ƙananan kujeru kusa da window mai labulen zare. Yazid: “kamar ka taɓa zama dan sanda fa, yadda kake tafiya da tsari.” Najeeb (yana dariya): “kai kuma kamar ka taɓa zama dan leƙen asiri – sai ka ce kana da sirrin duniya.” Suna nan suna dariya, kamar yara biyu da Allah ya haɗa saboda zuciyarsu ta dace – duk da cewar yau ne haɗuwarsu ta farko. IHSAN & MARYAM A ɗaki mai launin sanyi da kyawawan labule masu zinariya da shukoki na artificial, Ihsan da Maryam suna zaune akan gado suna shan gahwa da busassun ƙwai da miya. Ihsan (ta kama hannun Maryam): “Maryam... ashe rayuwa zata dawo da mu haka?” Maryam: “Ni ma ban taɓa tsammanin ba. Amma in Allah yana rubuta abu – zai faru ko ina, ko ta yaya.” Suka yi shiru na lokaci, suna kallon juna da hawaye masu ɗauke da dariya a cikin idonsu. A wani ɗaki na yara da aka kawata da ‘yan teddy bear da ƙamshi na vanilla, Iman ta zauna tare da wata yarinya mai shekaru 12 mai farin fata da dogon gashi. Yarinyar: “Sunana Layan Momi Maryam ce ta ce ki zauna da ni har sai kin huta sosai.” Iman (ta rike hannunta): “Na gode Layan. Kin daɗe a nan gidan?” Layan (ta murmusa): “Tun ina shekara shida. Gidanmu ne yanzu.” Suka zauna suna hira, har Layan ta kawo mata hijabi mai launin ruwa da hoda. Iman ta sanya shi a kai, suka kallon juna cikin madubi suka ce a tare “Beautiful!” DA DARE DINING ROOM Ana kwana biyu da isowarsu, da dare suka haɗu a babban daining table mai zagaye. Fitilun zinariya suna kan low dimming, kamar cikin film Abincin da ke jikin table: Kabsa mai daddawa da nuts Maraq da lamb Hummus, tabouleh, da fatayer Kunun zaƙi da dates Laban (madarar larabawa mai sanyi) Maryam ta zauna gefen Ihsan, Najeeb kusa da Yazid, Munir da Ado a gefen hagu. Iman da Layan suna gefe suna dariya a hankali kamar ‘yan mata masu sabuwar ƙawance. Ado: “To yau mun huta gobe mu fita ziyara!” Ihsan (ta ɗaga glass ɗinta): “Ga rayuwar da muka dade muna mafarki da ita.” Suka ɗaga hannu suna yi wa Allah godiya. Duniya ta dawo da murmushi bayan Wata ya ɓullo. Suna zaune a falon da yake kallon ka’aba daga tagar gilashi mai shara-shara kowa na sanye cikin kayan sanyi masu kyau, dakin na ƙamshi da turaren Oud da jasmine. Dining table na jiya an gyara shi yanzu zuwa karamin round-table mai coffee da snacks. Iman ta ɗauko karamar wayarta ta ajiye a gefenta. Ta gyara zama, ta gyara murya, ta ɗan tabe hancinta da style irin na ‘yan jarida Iman (ta kalli Munir): “Daddy Munir, kafin mu fita ziyara — ni dama akwai tambaya mai nauyi a zuciyata tun jiya. *Yaya kuka tsira daga ‘trailer’? Bayan aka kwashe ku — me ya faru da ku da Aunty Maryam? Bayan wata… yaya ‘bayan watan’ naku ya kasance?” Ɗakin yayi shiru. Kamar ana sauraron azan daga sama Munir ya kalli Maryam, ta gyada kai da idon da ke cike da kewa. Ya lumshe ido sai ya fara da muryar tausayi wanda zuciyarsa ke da ƙarfi, amma yana ɗauke da raunukan tunani: “Bayan mun rasa motar nan… bayan an kwashe mu daga trailer ɗin nan da ba zan taɓa mantawa da wari da zufan cikinta ba — sai muka tashi ne a wani sansani a chan gabashin Makka, inda aka ware mu daga juna. Ban san inda Maryam take ba ban san ko tana raye ba kuma lokaci bai tsaya mana ba — sai ya cigaba da juyawa.” Ya cigaba da cewa: “Wata mata Balarabiya ce — ba ta da haihuwa, ta karɓe ni a matsayin ɗanta a lokacin da nake a asibitin da suka ajiye mu bayan mugun ciwon da na sha. A can na girma... amma zuciyata kullum na mafarkin wani abu daban. Na san ban da cikakkiyar dangantaka da kowa a can — amma rayuwa ta tilasta in gamsu.” Maryam ta ɗora: “Ni kuma na samu wani bawan Allah da ya kai ni hospital a Isra'ila. Daga baya ya shirya min takardun tafiya Makka inda na zauna a gidan wata tsohuwa har muka sake haduwa da Munir inda yake aiki a ɓoye kamar ne wasa da gaske muka bayyana wa junnan mu sha'awar aure bayan wani lokaci kadan na samu cikin NAJEEB kuɗi ya fara budewa mukaye biza har muka samu Manyan manyan dama na samun kuɗi Muka koma Saudi da aka ba shi aiki.” Duk suka juya suna kallonta. Maryam ta kama hannun Munir. Maryam (cikin shashsheƙar murya): “Mun shafe shekaru muna addu’a mu sake haɗuwa. Sai Dubai — sannan Makkah — yanzu Allah ya cika mana.” Iman tana ta rubutu da ido da zuciya. NAJEEB kuwa — sai kallon Iman yake yi. Yadda take saurare da nutsuwa, yadda kukan ta ke boyewa cikin dan murmushi — ya tabbatar da wani abu: Soyayyarta na fizgar zuciyarsa fiye da duk wata sanarwa da ya taɓa karantawa. Sai yace a cikin zuciyarsa “Bari na bayyana komai… amma a lokacin da zai dace — tunda yanzu na san ina da muhimmiyar mace a gabana.” Ado ya gyaɗa kai. Yazid ya shaƙe gaban Najeeb yana kallon sa kamar jarumi a cikin fim. Layan da Iman suka kama juna da ido suka ɗan yi dariya. Falon ya cika da nutsuwa — kamar an yanke ruwan rahama aka zuba. Wannan lokacin — ba wai shiru suka yi ba — sai hawaye da murmushi. Bayan jawabin Munir da Maryam, sai kowa yayi shiru yana ƙoƙarin lissafa irin wahalar da suka sha kafin su haɗu. Nan fa Ihsan da Ado suka ɗago kai. Ihsan (ta dafe kirjinta): “Wannan labarin sai dai a jikin zuciya — wallahi rayuwa ta juyi ne da kaddara. Amma yanzu, tunda Allah ya haɗa mu, zamu ci gaba da zama tamkar iyali.” Ado ya ɗan share kwalla, sannan ya kalli su Maryam da Munir yana murmushi. Ado: “Mun shirya gayyatar ku zuwa gida da gobe — domin yanzu muna da kamfani mai suna “TALLAFI MATAFIYA” a Najeriya mun kirkire shi domin taimaka wa matasa da suka shiga wahalar neman visa ko tafiya ba bisa ka’ida ba. Mun riga mun buɗe rassan Lagos, Abuja da Kaduna.” Maryam da Munir suna kallon juna, sai suka murmusa. Maryam ta kama hannun Iman tana kallonta da dariya. Maryam: “Ke dai ƴar jarida ce, amma sai kin ji namu ma. Komai da muke da shi yanzu yana nan a Makkah — ba Dubai ba. Mun mallaki gida, kamfani mai suna Zauren Tafiya, inda muke bayar da training ga matafiya kafin hajji da umrah da kuma ‘yan kasuwa. A nan Makkah muke — gida ne nan, kasuwanci na nan.” Ihsan ta lumshe ido tana dariya, tana kallon Ado Ihsan: “Toh mu fa arzikinmu na Dubai ne — nan da har sai an kira mu a Tashar Arabiya suna ce mana “Ƴan Kasuwar Duniya”.” suka yi dariya gaba ɗaya. “Bari in faɗi gaskiya nan da nan: kun zama labari, darasi, da abin alfahari a rayuwata. Na gane cewa arziki ba Dubai ba, ko gida mai hawa goma ba — arziki shine lokacin da Allah ya yarda ka tsira kuma ya haɗa ka da mutanen da ka rasa.” Sai Iman ta ce da murmushi tana kunna recorder Iman: An gama ziyarar Ka’aba da sallar harami, sun gama siyayya — kaya na larabawa, turaruka, agogo, ababen tunawa. Fuskokin su cike da annuri da kwanciyar hankali. Motoci sun shiryu a gaban katafaren gidan da suka sauka. Ƴan haddimai na jera akwatuna cikin natsuwa. Ihsan da Maryam na cikin motar gaba suna sanye da kayan hula da tabarau masu kyau. Iman da yarinyar gida na gefe suna dariya. Najeeb da Yazid suna musayar waya kamar tsofaffin abokai. Ado da Munir suna kallon komai da jin daɗin cikar buri. Yazid (yana kwala kira): “Dubai... we are coming!” Iman ta fito daga wanka cikin hanzari, ruwan zafi na ci gaba da fita da ƙamshi a dakin. Guntun tawul ɗin da ta ɗaura a jikinta ya janyo hankalin numfashinta da gaggawa. Gashinta ya barbaje bisa kafadunta, yana ɗiga ruwan sabulu mai ƙamshi kamar 'attar Halabi'. Tana juyawa zata ɗauki doguwar rigarta kenan — Sai taji an bubbuga ƙofar sau biyu, da ƙarfi, kamar ana neman rai. Ta tsaya cak Gabanta ya fadi. “Iman…” murya ce daga waje — muryar da take gudu tun jiya. Najeeb. Yadda muryar tasa ta fito, a matakin da ke tsakanin tausayi da ƙauna, sai zuciyar Iman ta shiga wani sabon yanayi. Ba ta buɗe ba, sai dai ta jingina da bango, zuciyarta na bugawa. “Ba wai zan tilasta ki ba, amma… Iman, ki saurare ni. Idan ma zan bar duniya ne da kaina, zan fi so na bar ta bayan kin ji gaskiyar zuciyata.” Shiru. Sai murya mai rauni daga cikin ɗaki: “Kayi tafiyarka Najeeb babu wani abu da ya rage tsakaninmu.” Shiru sai dai a zuciyar ta, Iman ba ta iya kwantar da ruwan da ke motsa a kirjinta ba. bai ce uffan ba — ya bar kofar a hankali. Ita kuma ta zauna kusa da gadonta, tana matse tawul ɗin jikinta, tana kallon hular gashinta da ke gefen madubi, tana tunanin yadda zuciya ke da rauni fiye da fata. Iman ta juya da sauri, tana ƙoƙarin buya, amma ruwan da ke ratsawar jikinta da tawul ɗaya ya hana ta daidaituwa. Sai wani yatsin ƙafarta ya kwace... Wuffff! Kafin ta faɗi — hannunsa ya kama ta. Ya tallabe ta da ƙarfi, jikinta ya sauka daidai a ƙirjinsa, inda fuskarsu ta gogar juna. Shiru... Numfashinsu na haɗuwa, kamar ana karanta sirrin zuciya a cikin iska mai dumi. Gashinta mai ɗumi da kamshin sabulu ya rataya a gefen fuskarsa, yana bin ƙamshi kamar furanni masu tsiro bayan ruwan sama. Idanunta biyu sun lumshe, na shi kuma suna kallonta — a tare da mamaki da al'ajabi. “Iman…” ya ce da ƙasa-ƙasar murya, kalmomin da suka fita daga cikin zuciyarsa kamar kirari. “Na…na faɗi,” ta ce a hankali, tana juyar da kanta a hankali cikin kunya. Ya jinjina kai “Na kamaki ne... ba don na shirya ba, sai don zuciyata ta kasa bari ki faɗi.” Zuciyarta na dukan wani irin bugun da ya saba da kwanciyar hankali. Ya lumshe ido, ya dan ja numfashi — kamar yana gasa da zuciyarsa ta gaskiya da wuta. “Ki yarda da ni Iman... Ina sonki ba son da ya zo da ido ba — son da ya fara da tsoro, ya girma da ƙauna, kuma yanzu ya zama imanina.” Ta ɗago kanta da ɗan sauri, tana kallonsa. sai ya janye hannunsa cikin nutsuwa da ladabi “Ina jiran lokacin da zaki so na... da zuciyarki. Amma har yanzu — bari na tsaya a gefe.” Ya juyawa ƙofar baya yana tafiya, amma a karon nan, ita ce ta kalla bayansa. Kafin ya fice, ta ce cikin siririyar murya: “ba zan manta wannan rana ba.” Ya tsaya kadan, ya dan lumshe ido. Sannan ya fice Ƙofa ta rufe, zuciya ta buɗe. Iman ta zauna a gefen gadonta, tana matse tawul ɗin jikinta, amma ba sanyi take ji ba — zuciyarta ce ke tafasa. A tsakankanin kaifin tunani da sanyin zuciya, kalaman Najeeb suna maimaituwa a kwakwalwarta kamar faifan waka mai raɗaɗi: "Idan zan bar duniya... zan fi so na bar ta bayan kin ji gaskiyar zuciyata." Ta runtse ido. Ta tuna lokacin farko da suka haɗu, lokacin da zuciyarta ta fara dukan wani irin bugun da bata taɓa saninsa ba. Duk da girman laifin da ya taɓa aikatawa a baya, zuciyarta ta ƙi daina tuna shi da haske fiye da duhu. Sai kawai... Ƙofar ta bude. Iman na zaune a bakin gado, lulluɓe da dogon veil mai launin zinariya, amma ba zuciyarta bace da launin farin ciki ta rasa yadda zata warware duniyar da take ciki — soyayya, kunya, da wani abu da ya fi ƙarfi da kalmomi. Kallon da ya biyo bayanta a jiya har yanzu yana ratsawa a kwakwalwarta. Murmushinsa, shigarsa, murya mai natsuwa... da hannunsa da ya riƙe ta a lokacin da zata faɗi. Tunani ke nan har sai ga ƙaran takun sa na shigowa falo. Najeeb. Ya shigo cikin shigar jallabiya ta larabawa, farin karfi, gwanin burgewa, da hula mai ƙyalli a kansa. Fuskarsa ta shafa attar mai ƙamshi, gashinsa yana kwance a gefe, idanunsa kuwa su ne suka dawo da ita daga cikin tunani kamar an buɗe kofar sirri a zuciyarta. Ta ɗan girgiza kai, tana maida hankali. Ya ce da murya mai nutsuwa: “Iman, lokaci ya yi muna shirye tafiya.” Ta ɗan gyaɗa kai, tana ƙoƙarin ƙyale kallonsa, amma bai yiwu ba kallon da yake mata yanzu… shi ya fi duk wanda ya mata a baya girma da nauyi. Ta miƙe tana kallon ƙasa, zuciyarta na rawa kamar rigar ruwa. Suka kama hanya zuwa filin jirgi a cikin mota ana dariya da raha. Ihsan da Maryam a gaba, Ado da Munir a wata motar, sai su Najeeb da Yazid a motar su. Iman na zaune kusa da Najeeb, amma sai da nisa — kamar tana jin ana karanta sirrinta. A cikin jirgi, komai ya lafa. An zauna cikin nutsuwa. Ana cikin iska mai sanyi, ana kallon ƙasa daga sama. Ta juya ta leƙa Najeeb da sauri, sai suka haɗa ido. Bai ɗauke nashi ba. Ita kam sai ta kauda nata, amma zuciyarta na ambato: “Wannan kallon, me yake nufi? Me yasa yaki sauka?” Ta daure zuciyarta, ta kifa kai, amma numfashin zuciyarta na tafasa kamar ba jirgi suke ciki ba — kamar zuciya ce a gaban gobara. An sauka. Sun sauka lafiya a Dubai. Wata babbar motar kirar Rolls-Royce Phantom ce ta karɓo su daga filin jirgi — sai wata bus mai zaman kansa don ɗaukar kayayyaki da sauran su. Iman ta kalli birnin daga cikin gilashin motar. Hasken fitilu yana walƙiya kamar taurari sun gangaro duniya. Dukkan alamun birni mai wayewa da yalwar arziki ne — amma zuciyarta… zuciyarta ba fitilu take gani ba, kallon Najeeb ne kawai ke mata haske da duhu a lokaci guda. Bayan mintuna talatin, suka isa. Gidan ya tashi har sama: Ginin bene ne na falon hawa biyu, fentin launin shunayya da zinariya, tare da fitilun chandelier masu launin blue crystal daga Austria. Kofar gidan ba ƙaramar ƙofa bace — ta sarauta ce! A saman kofar, an sassaka sunan: "Bayt Al-Hikmah — The House of Wisdom & Grace." Falon shiga kuwa… babu inda za ka kalla ba tare da ka tsaya ba. Kushin Turkish, gilashi na Paris, shinfidar Morocco, bust of love carved in white marble — komai na nuna cewa Ado da Ihsan sun mallaki duniya da duniyar zuciya. Wata sabuwar mace ta karɓi Iman, ta ce: “Welcome, beautiful lady. Your room is this way…” An kai Iman wani ɗaki da ya dace da sarauniyar larabawa. Gado mai launin milk gold, labule mai sheƙi, da jakuzi a wani sashe mai moonlight tiles. Ta tsaya tana kallon kanta a madubi, sai kuma taga Najeeb a baya. “Iman,” ya ce da wata murya mai sanyi, “zaki iya hutawa yanzu. Amma bana tunanin zan iya hutawa idan har...” Sai ya tsaya. Ita ma bata ce komai ba. Zuciyarta sai harbawa take kamar ana bugunta da rawani. Ya ɗan matso kusa “Na san akwai abinda ke yawo a zuciyarki, Iman. Amma ki sani — tun farko ba zato ba tsammani na faɗa tarkon da ba zan so kubuta ba...” Ta juya a hankali, idanunta sun cika da soyayya da tsoro. Ya matso. Kamar ba kowa a duniya sai su biyu. Sai yayi murmushi yana faɗin: “Jiya... lokacin da na tare ki daga faɗuwa, na fāɗa — a zuciyarki. Kuma har yanzu ban samu hanyar fita ba.” Iman ta kauda kai, amma fuskarta na fashe da laushi da launin fatan so. Kafin ya ce wani abu, sai wata yarinyar gida ta shigo da ruwa mai sanyi da kunu, tace: “Ma’am, dinner is ready. Everyone is at the table.” Najeeb ya janye a hankali, yana kallonta har ya fita. Ita kuwa ta zube a jikin madubi, zuciyarta na bugun kalmarsa. “Na faɗa… kuma ban fita ba.” Dinning Hall — Cikin Dare, Cikin Rabo Wurin cin abinci kuwa wani sashe ne daban. Babban teburin marble mai siffar daraja, fitilu a sama kamar taurarin Burj Khalifa, abinci kuwa larabci da na Nigeria sun gauraya — hummus, lamb mandi, dankali spicy, tuwon shinkafa da miya. Maryam da Munir, Ado da Ihsan, su Yazid da Najeeb da Iman — sun zauna cikin farin ciki da raha. Amma idanun Iman da Najeeb… su kadai suka fi magana a ɗakin. Kallon da bai da kalma, murya da bai da lafazi. Sai zuciya da zuciya ke karɓar saƙo. Washegari da safe. An shirya. An sa kaya masu kama da casual official. Iman na cikin wando mai siririyar fata da riga mai launin cream, gashinta a daure cikin salo na 'Elegant Bun', Najeeb kuma cikin farin shirt da bakar wando, sai turaren sa mai sanyi da gwaninta ya gama janye hankalinta. Sun fito tare da Maryam, Munir, Ihsan da Ado. Motoci biyu suka nufi katafaren “Al-Manāra Travel Support Holdings”, wato Company ɗin da ke taimaka wa matafiya da kuma masu neman mafita daga wahalhalu irin su hijira, asara, da barazana. AL-MANĀRA HOLDINGS — CIGABA DA JINƘAI Ginin yana tsakiyar Dubai, kusa da Business Bay. An yi masa gini mai siffar fatauci da aiki — amma cikin aminci da kamala. Ko da suka sauka, wasu ma’aikata suka fito da gaisuwa da fara’a. “Marhaban! Mr. Ado, Mrs. Ihsan! Welcome home!” An yi musu jagora zuwa babban hall — inda hotunan matafiya biyar (Maryam, Munir, Ihsan, Ado da Yazid) suke rataye cikin manyan frame, suna wakiltar labarin gaske da azanci. Najeeb da Iman na tafiya gefe guda. A lokacin da ake gaisawa da shugabannin ma’aikata, Iman da Najeeb suka ɗan ja gefe suka tsaya a wani corridor wanda aka kawata da window masu kallon Emirates Tower. Kamar daga sama aka saukar da nutsuwa — babu hayaniya, babu kururuwar birni. Sai numfashin juna kawai. Najeeb ya ce da ita a hankali: "Iman, na fahimci duniya ba ta da wani armashi idan babu wanda kake so a cikinta." Ta kalle shi kamar tana ƙoƙarin musun kanta. “Ka tabbata kuwa?” ta ce, idonta a rufe, muryarta na raɗa. Ya matso kadan, ya kama hannunta cikin nata: “A cikin wahala na rayuwa, Allah ya ajiye min ke a matsayin rahama kuma soyayyarki… tafi Dubai da duk daular duniya daraja a zuciyata.” Ta fashe da murmushi, sai hawaye suka gangaro kadan. “Na so ka tun farkon haduwarmu, Najeeb. Amma tsoro ne ya hanani furtawa.” Sai suka rungume juna a hankali — hug mai cike da soyayyar gaskiya ba wani lallata ba. Kamar komai ya tsaya sai su biyu. Sai shiru sai bugun zuciya. A wannan lokacin ne Ado ya leƙo daga gefe, sai ya kalli Maryam yana faɗin: “Na ga hasken soyayya. Yau kam, mun cika alkawari — daga wahala zuwa farin ciki.” An yi hoto tare a gaban ginin, tare da ɗaukar documentary short daga Iman, domin jaridar da take aiki da ita a Najeriya. Ta bayyana cewa yanzu Al-Manāra Holdings za ta buɗe reshe a Abuja domin taimakawa matafiya marasa galihu. Iman ta juya ta ce: “A duk inda mutum yake a duniya, akwai fata. Amma idan aka ba mutum ƙauna da dama — sai ya zama tauraro da kansa.” Najeeb ya ce “Iman… ke tauraruwa ce da ba zata taɓa dushewa ba.” DUBAI TO ABUJA Bayan dawowa daga Dubai, su Najeeb da Iman da sauran iyalai sun huta a wani katafaren gida a Asokoro, Abuja — gidan Ihsan da Ado suka mallaka tun kafin tafiyarsu. Lokacin da aka shakata, sai suka shirya tafiya Kano domin cika wata alkawari da suka ɗauka tun lokacin da suka sha wahala. Yazid ya mutu a hanya — mutuwar da ke ɗaya daga cikin manyan tabo da suka ɓata zuciyar su. Amma yanzu lokaci ne na fansa, na lada da alheri. KANO – GIDAN YAZID FOUNDATION Sun iso cikin manyan motocin girmamawa. Wani sabon katafaren gini da ke gabar kwanar Hadejia Road, an ɗora Foundation ɗin da sunan: Yazid Foundation — Gida na Ƙauna da Taimako. Cikin gidan marayu da dakunan kwana da nishaɗi. Makarantar addini da boko mai girma da aka rubuta a saman kofar sa: "Wannan gida ne na kyautatawa domin ladar rayuwar Yarima Yazid — wanda bai rayu ba amma ya bar daraja." Maryam ta tsaya a bakin kofar masallacin da hawaye suka cika idonta. Munir ya riketa a hankali. Ihsan da Ado na tsaye gefensu, suna fuskantar sabuwar hanyar alheri. A CIKIN MASALLACI An gudanar da walimar saukar Alkur’ani daga yara marayu guda goma sha biyu da suka rigaya suka haddace., domin girmama sunan marigayin. Najeeb da Iman sun zauna gefe a gaban masallaci. Lokacin addu’ar kabari, Iman ta saka ƙwalla cikin zuciya ta ce: "Ya Allah, ka bawa Yarima Yazid mafaka mai albarka. Ka sanya wannan gida hujja mai haske gare shi." Najeeb ya kama hannunta a hankali, ya ce: "Yazid ba ya nan da jiki, amma ran mu cike yake da shi. Kuma wannan gida, wannan aiki, ya fi duk daular duniya." a nan aka roƙi addu'a, aka karanta suratul Mulk, sannan aka watse da nutsuwa da tausayi. Gida ya cika da yara marayu. Najeeb da Iman sun kafa wani shiri mai suna "Matafiya Cikin Ƙauna" wanda ke ba da tallafi da damar rayuwa ga marasa galihu da ‘yan gudun h da ‘yan gudun hijira. ALƘALAMIN NARNAH ƘANWAR SOJA ✍️✍️✍️ https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC 🎇BAYAN WATA 🎇 ( Beyouda ‘yan gudun hijira. ALƘALAMIN NARNAH ƘANWAR SOJA ✍️✍️✍️ng the moon ). SABON SALO Labari da tsarawa Narnah ƙanwar soja ( Sayeedan Adda ) ********* HIKIMATA ABIN ALFAHARI NA Marubuciyya tana da damar halittar mutum ta kashe shi ta raya shi, tunda 'ƙirƙirar labari ne. ta haɗa masoya, ta wargaza soyayya tsakanin masoya. *****"" Sadaukar wa littafin Bayan wata sabon salo Ga Abokina Mallam Najeeb wanan Sabon salo naka ne shi ke ɗauke da martabar sunanka thank you with your support 🙏 ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 Page 54 / 55 SECOND TO THE LAST PAGE BARKA DA JUMA'ATU BABBAN RANA Washegari bayan dawowa daga ziyarar kabari da buɗe gida, Maryam ta buƙaci su tafi wani wuri — wani wuri mai nauyi a zuciyarta, inda duk wasu damuwa da jin ƙasa suka fara a rayuwarta. Su Munir da Iman da Najeeb da sauran ‘yan gida suka rakata cikin nutsuwa. Motoci suka nufi tsohuwar unguwar su Maryam, anguwa da yanzu lokaci ya sha kanta amma ƙuruciyar rayuwa ta Maryam ta tsaya a cikinta har yanzu. Gidan da suka tsaya ba babba ba ne. Gida ne da duwatsu da tubali suka hau a kai, buhun shara ya makale a jikin bango, ruwan famfo na zubowa a gefe. Wani ƙaramin bishiya ya toshe rabin kofar gidan. Amma duk da haka, akwai ɗan ginin tarihi da ke bayyana cewa: "Wannan gida na Maryam ce — iyayenta suka gina shi da hannu, da jinƙai da addu’a." Maryam ta tsaya gaban ƙofar gida, tana kallon fatar bango da ke fallarwa kamar yana faɗin: "Kin dawo, ‘yar gida. Mun kiraki shekaru talatin da suka wuce." An shiga ciki. Duk da cewa gidan yana buƙatar gyara, amma yana cike da numfashin ƙuruciya bango da aka daɗe ba a shafa ba, ɗakin da ta taɓa kwana a ciki tana kuka da yunwa, da kwandon da mahaifiyarta ke ajiyewa shinkafa. Maryam ta tsuguna a ɗaya daga cikin dakuna tana shafa ƙasa. Munir ya tsaya yana kallonta. Iman ta kama hannunta tana kuka. Maryam ta ce a hankali: "Wannan ƙasa ce ta rayuwata. Duk duniya na zagaya, amma ina da iyaye da suka fara gina mini mafarki a nan — duk da ba su da komai sai kauna." Motar Maryam ta tsaya a ƙofar tsohon gidan mahaifinta. Wata ƙaramar kofa ce amma har yanzu tana da ƙwanƙwasa da ke sa mutum ya dakata kafin shiga. Duk gidan yana da warin tarihi, ko ƙamshin ƙasa mai ɗumi da fatar mutane masu tawali’u. Tana fita daga mota, sai zuciyarta ta ɗauki wani irin nauyi mai nauyi da sauƙi a lokaci guda. “Baba…” Kafin ta kai kofa, wani dattijo ya fito daga tsakar gida. Fatar jikinsa mai tsufa, kayan jikinsa daɗɗaɗɗu amma tsaftattu. Idanunsa suka sauka a kanta cikin mamaki da ƙanƙan da kai. “Maryam?” ya furta da wata murya mai karkarwa, kamar wanda ya kira mafarki ya amsa masa. Maryam ba ta iya jurewa ba. Ta yo guje kamar ƴar shekara goma, ta faɗa jikinsa tana fadin: “Na dawo Baba… Na dawo daga duniyar da ta raba ni da ku.” ya rungume ta, yana hawaye kamar karamin yaro. “Ashe ke kike nan? Ashe haka kika wahala? Ashe auren tsoho ya mayar da ke arziki da sayar da raina? Maryam… na rasa ke tsawon shekaru talatin. Kamar yau aka yanke ni daga zuciya ke gafarta min tursasawa da na miji a baya .” Daga cikin gida, sai ga wasu matasa guda uku sun fito da mace guda. Maza ukun ƙanninta ne — yara da suka tashi ba tare da cikakkiyar uwa da ta ci zarafinsu da azaba. Duk sun girma, amma zuciyarsu har yanzu da raunin rashin Maryam. Maryam ta zuba musu ido. Ta fahimce su — kamar yadda take fahimtar wuta idan ta ga hayaki. Ta rungume su ɗaya bayan ɗaya tana kuka, tana cewa: “Ku gafarceni. Na yi tafiya da ba zan iya bayani ba amma daga yau, zan zame muku uwa da ‘yar’uwa.” Matar kuwa, ‘yar kishiyar da ta wahala da Maryam, ta tsaya gefe tana kallon su. Maryam ta matso kusa, ta kama hannunta da ƙyautatawa tana fadin: “Kin sha wahala a nan, ba laifinki ba ne. Amma yanzu ba za mu sake rayuwa da ƙiyayya ba wannan gida zai koma gida na kowa da kowa.” Maryam ta ce da mahaifinta:“Baba, daga yau wannan gida zai zama Cibiyar Azanci da Kyautata Rayuwa. Za mu gina masa dakin koyon sana’a, dakin karatu, Kuma za mu sanya sunan ka a ƙofar gidan." Mahaifinta ya fashe da kuka yana fadin: “Maryam, ke ce ƙarshen mafarki. Wannan mutunci ya fi na duniya.” Munir da Iman da Najeeb da su Ado da Ihsan suna kallon abin cikin jin daɗi da girman zuciya. Duk suka yarda cewa gidan da aka barwa Maryam da hawaye, yanzu ta dawo da shi da alfahari. Dukkan maƙwabtan tsohon unguwar Maryam sun fito don maraba da ita. Kamar ba ita ba ce da aka manta shekaru talatin da suka wuce. Da wuya a tantance tsakanin hawaye da murmushi a fuskar mutane, domin dawowar Maryam tamkar dawowar haske ce bayan duhun shekaru. “Maryam, wannan gida har yanzu gida ne. Kuma yanzu mu ne za mu taimaka miki, ba ke kadai ba,” in ji wata tsohuwa da ke tsaye da kwanon tuwo a hannunta. Wani dattijo ya kawo jakar shinkafa. Wata mace ta kawo masara. Sauran suka kawo barguna, kwanuka, da kayayyakin amfani. Wasu kuma suka bada ginin da za a dawo da su ciki su huta kafin tafiya. “Wannan gari ba zai sake barinki ki fita da hawaye ba, Maryam,” cewar wani saurayi da ya taba kasancewa ɗan ƙaramin yaro lokacin Maryam tana da shekaru goma. Maryam ta juyar da idonta zuwa danginta: “zamu kwashe ku gabaɗaya zuwa Abuja. komai ya canza wannan gidan zai zauna a matsayin alamar juriya, amma zamu tafi domin a ji daɗi da walwala.” Bayan makonni biyu a Abuja, inda suka samu nutsuwa da kwanciyar hankali, sai abubuwa suka ɗauki sabon salo. Iman, ƴar jarida ce mai kwazo wadda ta tattara tarihin tafiyar su biyar cikin littafi a kafar BBC Hausa, an shirya ƙaddamar da litattafin mai suna: "BAYAN WATA" Labarin Gaskiya da Ƙalubalen Rayuwa Littafin ya ƙunshi: Tafiyar su daga Najeriya har zuwa Dubai Wahalar da suka sha Soyayya da ya fito daga cikin ƙura Mutuwar Yazid da yanda sunansa ya rayu Sabon duniya da suka buɗe a gida da ƙasashen waje, an gayyaci manyan mutane daga hukumomin lafiya, walwala, ma’aikata, da jaridu. Maryam, Ihsan, Ado, Munir, Najeeb da Iman sun zauna a gaban dandalin BBC suna kallon yadda littafin da Iman ta rubuta ke zama abin magana a duniya. “Labarin mu ba wai don a tayar da hankalin mutane ba ne, amma domin a fahimci cewa tafiya mai wahala ba dole ta ƙare da baƙin ciki ba. Akwai haske... a bayan wata,” cewar Iman cikin ladabi da ƙwarewar jarida. An kawata harabar BBC Hausa da tulin furanni, red carpet, da hoton murfin littafi "BAYAN WATA" a babbar bango. Dandazon mutane sun cika wajen. Ana watsa shirye-shiryen kai tsaye. Manyan mutane daga duniya suka halarta: Ƴan jarida, malamai, kungiyoyi masu tallafa wa matafiya, da wakilan kasashen waje. MC: “Bismillah… a yau muna maraba da labari wanda ya gigita zukata – da rai ya rayu cikin littafi. Mun haɗu domin ƙaddamar da BAYAN WATA, littafin Iman Ado matafiya” Da shigowar Maryam cikin shadda ta alfarma, sai aka ɗaga murya da tafi. Ihsan da Ado cikin zinariya da kayan alfarma. Munir da Najeeb cikin rigunan zamani masu kamshi. Iman kuwa cikin launin kore na natsuwa, tare da takalmanta masu walƙiya, ta shigo da dariya tana nuna tawali’u. JAWABI DAGA IMAN: “Na rubuta wannan littafi ne ba wai don in shahara ba, sai don duniya ta ji cewa rayuwa tana da tafarki — kuma a ƙasan ƙura akwai zinariya. Wannan littafi na fatan zai kasance haske ga masu rasa fata.” Maryam ta shafa hawaye tace: “Bana tunanin wata rana zan tsaya a gaban duniya in faɗi abinda na tsira dashi. Amma Allah ya kawo wannan rana.” NAJEEB & SOYAYYA Najeeb ya kalli Iman yana murmushi. Iman ta juya kanta, amma fuskarta na nuna jin daɗi. Bayan kammala jawabi, sai Najeeb ya miƙa mata furanni a gaban kowa: “Kin cika da ƙarfin hali. Littafinki ba kawai ya ba mutane ilimi ba, ya koya mana cewa soyayya tana da tushe.” Jama’a suka ɗaga hannu da tafi. An ɗauki hoto na musamman da hoton littafin, duka su biyar sun tsaya a gaban frame mai rubutu: 🖋️ “To all who walked in the dark, may you find your moon – Bayan Wata.” A cikin satin da ya biyo bayan launching, sun ƙaddamar da YAZID FOUNDATION a Kano: Gidan marayu Masallaci Makaranta Ruwan sha Tallafi ga mata da marasa galihu An buɗe kamfanoni a Abuja, Kano da Dubai. Littafin Bayan Wata ya zama sabon abun karatu a makarantu da kwasa-kwasai na lafiyar kwakwalwa da juriya. SECOND TO THE LAST PAGE BAYAN WATA NA BANKWANA FAN'S NARNAH ƘANWAR SOJA 🖋️💞 https://chat.whatsapp.com/Iw0DqQGrB3UJg7MK20pgRC 🎇BAYAN WATA 🎇 ( Beyoung the moon ). SABON SALO Labari da tsarawa Narnah ƙanwar soja ( Sayeedan Adda ) ********* HIKIMATA ABIN ALFAHARI NA Marubuciyya tana da damar halittar mutum ta kashe shi ta raya shi, tunda 'ƙirƙirar labari ne. ta haɗa masoya, ta wargaza soyayya tsakanin masoya. *****"" Sadaukar wa littafin Bayan wata sabon salo Ga Abokina Mallam Najeeb wanan Sabon salo naka ne shi ke ɗauke da martabar sunanka thank you with your support 🙏 ROYAL STAR WRITTER'S ASSOCIATION 💫 Page 56 / 57 THE LAST PAGE 23 / jun / 2025 Littafin Bayan Wata ya zama wani katafaren abin koyi a duniya baki ɗaya. Bayan an fassara shi zuwa harsunan Larabci da Turanci, ya zamo abin karatu na dalibai a makarantu, musamman a shirin JAMB Novel da darussan Hausa na zamani. Haka kuma, an ɗauki labarin zuwa tashoshin rediyo da talabijin inda aka shirya series na musamman da ke bayyana ƙalubale, soyayya da juriya, yana ja hankalin matasa da manya. Masu taimako da suka bayar da gudummawa a rayuwar Iman, Maryam, Najeeb da sauran su, an saka sunayensu cikin littafin da aka wallafa, da kuma nuna godiya ta musamman a cikin shirye-shiryen rediyo da fim-fim. Wannan ya ƙara musu ƙarfafa gwiwa da farin ciki, suna ganin yadda labarinsu ya taimaka wajen kawo canji da haske ga al’umma. An shirya gasa na maida labarin zuwa wasan kwaikwayo (drama/series) a cikin gida da kasashen waje, inda matasa da masu sha’awar adabi ke yin wasan kwaikwayo kan kowane muhimmin sashe na littafin. Wannan ya haɓaka sha’awar karatu da koyon darussa masu amfani cikin salo mai jan hankali. 1. Princess Rahilat Labari: Rahilat, yarinya mai zurfin hankali da jarumta , ta fuskanci ƙalubale da yawa a rayuwarta, musamman a cikin masarauta . Duk da haka, ta yi amfani da hikima da jajircewa wajen canza tsarin da ke kawo rashin da’a. Darasi: Adalci da kishin al’umma su ne ginshiƙan cigaba; kowa na da rawar da zai taka wajen tabbatar da gaskiya da tausayi. 2. Halimatu Sadiya Labari: Halimatu Sadiya, mace mai ƙarfi da himma, ta tashi daga ƙanana cikin talauci da ƙauyanci soyayya ce tsaftaciciya Amman kash mutuwa da rashin rabo shine sillar komai Darasi: Juriya, haƙuri da dogaro ga Allah sune makullin cimma nasara, musamman ga mata masu neman zaman kansu. 3. Aljannin Sajida Labari: Sajida ta samu wata aljaanin tun na kakan ta , wanda ya hana mata samun sukunin a zuciyar saurayin ta ko nace mijin ta . Darasi: Tsarkin zuciya da nufin alheri suna kawo kariya daga munanan abubuwa; addu’a da imani na da muhimmanci sosai shi kuɗi ba sai kayi tsafi kasa dangin ka cikin fitina ba . 4. Masarautar Zakar Labari: Masarautar Zakar ta kasance tana fama da rikici da rashin zaman lafiya, har sai wata mace mai hikima ta samu damar kawo sulhu da hada kan jama’a. Ta yi amfani da ilimi da sulhu don kawo zaman lafiya. Darasi: Sulhu da fahimtar juna sune mafita mafi inganci wajen magance rikice-rikice a kowanne mataki na rayuwa. 5. Kashifa Labari: Kashifa ta yi tafiya mai wahala dgaa satar Mangoro zuwa tsibirin aljannu Darasi: Fahimtar kai da taimako ga sauran mutane su ne tushen rayuwa mai ma’ana da jin dadi yafiya shine matakin rayuwa mai tsafta . Bayan Shekara Biyu AFTER TWO YEAR'S Bayan shekara biyu na aiki tukuru da bautar Umrah, rayuwar matafiya ta fara samun nutsuwa. A cikin wannan lokaci, an fara shirye-shiryen aure tsakanin Iman da Najeeb a Makka, cikin farin ciki da annashuwa. Duk da cewa sun sha ƙalubale, soyayyarsu ta ƙaru har ta kai ga wannan mataki na rayuwa. A cikin wannan lokaci, Yazid kuma bai tsaya ba. ya afka cikin soyayya da wata balarabiya mai ɗaukar hankali, mai ɗabi'a da mutunci a Makka wannan sabon soyayya ya ba shi sabon salo da sabon burin rayuwa, inda yake ganin wannan soyayya zata ciyar da shi gaba. Ana cikin shirin aure na Iman da Najeeb, yayin da Yazid ke cikin sabuwar soyayyar da ta ba shi kwarin gwiwa. Rayuwa ta ƙara ɗanɗano, kowane daga cikinsu yana cikin sabuwar babi na soyayya da ƙauna. Bayan bikin auren Iman da Najeeb, labarinsu ya bazu kamar wutar daji a kafafen sada zumunta — TikTok, Instagram, Facebook, Twitter, da duk wani shafin yanar gizo. Hotunansu suna ta yawo, mutane suna murna, wasu kuma suna kwaikwayon salon suturarsu da yadda suke nuna soyayya mai tsafta da ƙayatarwa. Suna sanya kaya iri ɗaya, masu launi da ƙayatarwa, sun yi fitowa cikin wani shahararren lambu mai tsarki a tsakiyar Dubai, inda hasken rana ke ta yi wasan launuka a cikin shuke-shuke masu ƙyalli. Najeeb, Iman, Yazid, da Muhibbat suna zaune a kan kujeru na fure, suna shan shayi da kayan zaki, suna hira cikin annashuwa. Najeeb ya mike ya ja hankalin kowa, ya ce, "Wannan shi ne farkon sabon rayuwa, ba kawai aure ba, har ma da soyayya da abokantaka. Mu kasance masu godiya ga juna da ga Allah." Iman ta yi murmushi mai cike da ƙauna, ta miƙa hannunta, suka rike hannu. "Na gode maka Najeeb, ka zama hasken zuciyata, abokin rayuwata." A gefe Yazid ya dube Muhibbat yana dariya, "Kin san dai, soyayya tana zuwa da ban dariya, kamar yadda kika kawo min farin ciki a Makkah." Muhibbat ta mayar da martani cikin wasa, "Toh, zan ci gaba da kawo maka farin ciki har abada." Sai su duka suka yi dariya, har wurin ya cika da annashuwa. Daga nan suka tashi suka fara rawa cikin salo na zamani, sai kuma suka yi wasan kwaikwayo na kalaman soyayya da barkwanci, inda kowa ya fara kwaikwayon yadda suke furta kalmomin ƙauna a lokutan ban dariya. Kowa na nuna salon sa na musamman, har suka jawo hankalin masu shan shayi a lambun da ke kusa. Bidiyon rawar su da nishadi ya bazu a dandalin yanar gizo, ya zama trending, inda mutane ke maimaita bidiyon, suna yi wa junansu tag, kuma suna ƙara godiya da fatan alheri. Hashtag ɗin #SoyayyaDaFarinCiki ya kasance a saman jerin abubuwan da ake ta hira akai a duniya, mutane suna aika hotuna, bidiyo da labarun soyayya da nishadi. Su ne jaruman soyayya, abokantaka, da farin ciki a duniya, kuma wannan rana ta kasance abin tunawa, wanda za a rika tunawa da shi a cikin zukatan masu karatu, a matsayin ƙarshen labarin da aka soma da ƙalubale amma aka ƙare da nasara da farin ciki. Duk wanda ya karanta wannan labari, ya fahimci cewa soyayya ta gaskiya tana buƙatar hakuri, tsayayye, da girmama juna, kuma farin ciki yana zuwa ne idan aka hada zuciya da zuciya cikin gaskiya da amana. Sakon Godiya daga Marubuciya: Sayeeda Assalamu alaikum wa rahmatullah, ALHAMDULLAH ALHAMDULLAH ALHAMDULLAH Ina mai mika gaisuwa da godiya ta musamman ga ku duka – masoya, masu karatu, da waɗanda suka ɗauki Bayan Wata ba kawai a matsayin littafi ba, har ma a matsayin aboki, mai karantarwa da mai tausasa zuciya. Nayi amfani da sako ukku Tunani bada labarin cikin labari rayuwa kamar ta gaskiya Labarin Bayan Wata ya fara ne daga tunani, ya zama kalmomi, daga kalmomi ya zama rayuwa. Kuna daga cikin waɗanda suka ba shi rai. Na gode da yadda kuka bi tare da shakku, hawaye, murmushi da daɗin zuciya. Na gode da comments ɗinku, da shawarwarinku, da jin dadinku a kowane page. Kun sa ni jin cewa kowanne rubutu yana da daraja, kowanne labari yana da tasiri. Ina mika godiya ga: Masoyan da suka tsaya tare da ni daga shafin farko har ƙarshe; Masu sharhi da karfafa gwiwa; Da wadanda suka raba littafin ga wasu har ya kai duniya. "Bayan Wata" ba zai tsaya nan ba. Wannan shi ne matakin farko. Ina fatan cewa zaku kasance tare da ni a sabbin littattafai da labarai da nake shiryawa – waɗanda za su ci gaba da nuna gaskiyar rayuwa, kalubale, da fatan nasara. Rayuwa cike take da darussa — daga soyayya, gwagwarmaya, da mafarki. Dukkan ku kun zama wani bangare na mafarkin nan. A karshe, ina cewa: Ku ci gaba da karatu kuci gaba da ƙarfafawa. Ku ci gaba da kasancewa sassa na zuciyata. Da soyayya mai tsarki, MY NEXT MOVE ZAƁIN ZUCIYA KADANGARE BAKIN TULU RUHIN MARAICE ZAƁIN ZUCIYA ZAI FARA ZUWA MUKU 1 GA WATAN BAKWAI Sayeedan Adda ❤️✍🏽 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels